Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

YARINYAR BABA
[01:02 PM, 01-Oct-16]
by ZAINAB ELKASEEM
*YARINYAR*
*BABA*
_*Written & Edited*_
_*By Zee Mmn Khady*_
*```Just a short story```*
*Page* 1-10
"Gaskiya ni Momy bazani school d'innan ba,
kawai sai mutum yaje wannan banzan malamin
yari'ka yimashi kallon banza, kamar wata tsiya
yafika, Ilham tafad'a tana shagwa6a.
Matar data kira da Momy tace "ke ilham banison
shashancin banza da wofi, ki maza ki tashi kitafi
tun kafin ranki yayi mugun 6aci cikin gidannan.
Wasu 'kyawawan yara su biyu mace da namiji
'yan kimanin shekaru bakwai, suka fito sanye
cikin uniform d'insu, gwanin ban sha'awa sukace
"momy mun shirya, sannan suka maida dubansu
ga ilham wacce keta zo6ara baki ita a dole
bazata school ba, sukace "aunty ilham dan Allah
ki shirya mutafi kinsan idan muka makara uncle
zemana duka.....
Cikin masifa ta kallesu ta daka masu uwar tsawa
"bazaniba nace ku wuce Ku bani wuri idan ba so
kuke in 6ata maku rai ba, dan uwarku ni
sa'arkuce dazakuce sai kunjera dani kuntafi
school.....
Saukar wani lafiyyayen mari taji wanda momynta
ta shimfid'a mata a kunci, wasu star's tagani
suna zagaya mata kai saboda bala'in zafin marin
saida ta fasa 'kara.
Hakan yayi dai-dai da fitowar dadynsu daga
d'akinsa,
Ganinsa yasa ilham fad'uwa 'kasa kan kafet d'in
dake shimfid'e tsakiyar falon tana kuka "wayyo
Allah nashiga ukku dady ka taimakeni....
Da sauri yazo yakamata ya d'agota sannan ya
rungumeta jikinsa yana tambayarta "lafiya ilham
waye yata6a min ke,?
Cikin muryar kuka da shagwa6a take magana
"momy ce wai dole sai naje school nikuma nace
bazaniba.
Haba ilhama danme bazaki school ba ga
'kannenki sun shirya suna jiranki,
'Kara shagwa6ewa tayi tare da 'Kara narkewa
jikin dad d'inta tace "ni bazaniba.
Cike daso da 'kauna dady ke rarrashinta yace
"shikenan tunda baki zuwa je d'akinki ki kwanta
ki huta, kukuma Hassan da hussaina kuje driver
ya kaiku.
Yaran sukace "dady meyasa yau bazaka kaimu da
kanka ba? Yace "saboda yayarku bazataba, dama
saboda ita nake kaiku....
Yaran suka tafi suna turo baki, duk da suna yara
basu son abinda dady yake masu, 'kiri-'kiri yake
nuna yafison yayarsu akansu.
Cikin takaici Momy ta kalli dady tace "wallahi
karage tsananin son da kake nunama ilham,
saboda duniyar nan batada tabbas, kaso naka
duniya ta 'kishi, ka'ki naka duniya tasoshi,...
Cike da jin haushin momy dady yafita yabar
gidan, dan bayason jin maganar yarage nuna
soyayya ga ilham, kullum fatanshi Allah 'kara
ninka mashi son dayake mata a cikin zuciyarshi.
Cike da takaici momy ta nufi d'akinta, a zuciyarta
tana cewa *Hmm yau naci sa'a ba'a rufeni da
fad'a ba*
Dan some time duk randa tayima ilham fad'a
itama ranar sai ranta ya 6aci...
love u all
Zee Elkaseem

YARINYAR BABA
[01:18 PM, 01-Oct-16]
by ZAINAB ELKASEEM
YARINYAR
BABA
Written & Edited
By Zee Mmn Khady
*```Just a short story```*
*Page* 11-20
Ilham kuwa tana shiga d'akinta kan gado ta fad'a
ta jawo wayarta 'kirar iPhone6 tashiga danne-
danne, kusan kullum haka take batada wani ayki
daga karatun novel's sai games a waya, kuma a
haka dadynta ya d'aure mata gindi yahana Momy
ta tsawata mata, acewarshi Momy tabarta ta
huta tunda itama Momyn ba wanda yahanata ta
huta, tunda gidansu cike yake damasu yimasu
hidima kome yaimasu ake hatta da sharar d'akin
dasuke kwana akwai meyi.
Haka ilham tayita game a waya data gaji ta ajiye
ta d'auko wani English novel tacigaba da
karantawa, kusan awa biyu tana karatu, saida taji
idanunta na zafi sannan ta tashi ta kashe fankar
daketa faman juyawa tana ba d'akin iska, Ac ta
kunna lokaci guda d'akin yad'au sanyi takoma
tabi lafiyar gado, bacci me dad'i yayi awon gaba
da ita.
Kusan awa ukku tana bacci, ba sallah ba salati,
wannnan shine baccin asara, sai bayan sallar
la'asar sannan ta tashi mi'ka tayi tare dayin wata
uwar hamma, sannan ta fita falo, zama tayi kan
dining sannan ta 'kwalama Ameeno kira,
"Ameenoo.... Da gudu tazo har tana tuntu6e
kad'an yarage yafad'i tace gani, cike da isa da
gadara ilham take magana, "maza ki kawomin
abincina, da sauri Ameeno ta amsa da "to
,sannan tanufi kitchen jiki na 'kyarma, Ameeno
itace yarinyar dakema ilham hidima, wacce da
kad'an ilham d'in ta girmemata, dan yanzu lham
bata wuce shekara sha tara ba yayinda Ameeno
takeda shekaru sha shida zuwa sha bakwai,.
Haka Ameeno takawo abincin tajera gaban ilham
sannan tanufi pridge ta d'auko mata lemu da
ruwa, saida ta tabbatar tagama had'ama ilham
duk wani abu dazata bu'kata sannan takoma
d'akinsu na 'yan aiki, saratu meyima su Hassan
da hussaina hidima ta kalleta tace "hmm 'yar
mulkin taki tatashi kenan, naga sai hidima kike
tun d'azu, Ameeno tace kedai bari wallahi bacin
Albashin da ake bani yanada tsoka da tuni nayi
ritaya da aikin waccan 'yar izgilin.
Inna jummai dake zaune tana jin duk firarsu
wacce itakuma itace me aikin Momy, a gidan
dady ne kawai beda me aiki dan momy tahana
tace itace zatari'ka yimashi kome, hatta da girki
indai name gidanne ita ke Shig kitchen tayi
dakanta.
Inna jummai tace "Hmm aini narasa halin wannan
yarinya, wallahi Albasa batayi halin ruwaba,
iyayenta mutanen kirki basuda wula'kanci, amma
ita sai ahankali.
Haka 'yan aikin suka ri'ka tattauna matsalolinsu,
da kokawa akan yanda ilham ke wulakantasu,
hatta inna jummai wacce a girme ta girmi uwarta
amma bata ganinta da gashin arzi'ki...
Love u all
Zee Elkaseem

YARINYAR BABA
[01:26 PM, 01-Oct-16]
by ZAINAB ELKASEEM
YARINYAR
BABA
written & Edited
By Zee Mmn Khady
*```Just a short story```*
*Page* 21-30
Ilham na kammala abinda take d'akinta tanufa
toilet tafd'a kai tsaye ta she'ka uban wanka, tana
fitowa taje gaban dressing mirror tafara
d'and'asa kwalliya saida tagama sannnan tanufi
wadrope d'inta wacce ke sha'ke da kaya ta tsaya
tana tunanin wane zata Sanya, zuwa can ta
hango wasu riga da wando English wear's shi ta
d'auko haka ta sanya wando wanda yayi masifar
d'ameta domin irin pencil d'innanne , sannan ta
d'auko wata riga wacce zamu iya kiranta akwai
ya babu, dan rigar purple colour ce tanada
kwalliyar fari agabanta sai akayi ado da purple
d'in duwastu aka rubuta *TOUCH ME* haka tasa
rigar wacce ko hannuwan kirki batadasu
gashinnan na kanta yasha gara ta d'aureshi ya
zubu har kan kafad'unta.
Ba 'karamin kyau ilham tayiba kamar wata
baturiya, dan kusanma tafi turawan kyau dan
ilham kya'kkyawace ajin farko, farace me madai-
daicin tsayi, tanada shafe me kyau, ga dogon
hanci manyan idanuwa sai d'an 'karamin baki.
Bayan tagama shiri saida ta kalli kanta a madubi
ko ita tasan tayi masifar kyau, sannan tajawo
takalminta kalar purple me matsakaicin tudu ta
Sanya, wani d'an yalolon gyale ta yafa a kanta
wanda zamu iya kira akwai ya babu, dan kusan
beda wani qmfani.
Haka tafito daga d'akinta tana taku ahnkali kamar
wacce ke tausayin 'kasa.
Falo ta iske momynta, kallonta kawai tayi sannan
tanufi 'Kofa tace Momy zanje Unguwa, Momy
bata tanka mataba saida takai bakin 'kofa zata
fita taji muryar momy tana magana cikin d'aga
murya...
"Ilham kada ki kuskura kibar gidannan, cak ta
tsaya dan duk abinta tana shakkar momynta,
shiyasa tafison idan zatayi abu yakasance
dadynta nanan, dan idan yana kusa momy bata
Isa ta taka mata burkiba.
Muryar momyce ta dawo da ita Daga duniyar
tunanin data Lula,
"Wallahi bazaki fita a hakaba kamar d'iyar kafirai,
wai ilham kinada hankali kuwa?.....
Tsaye tayi bakin 'kofar batada niyyar motsawa,
ringing d'in wayarta yasa ta motsa ta fiddo wayar
Daga side bag d'inta, tana dubawa sunan
'kawarta tagani Leena, saboda haka da sauri ta
danna OK dan tasan tare suka tsara tafiyar,
sannan ta kara a kunnenta........
Love u all
Zee Elkaseem

YARINYAR BABA
[01:49 PM, 01-Oct-16]
by ZAINAB ELKASEEM
*YARINYAR*
*BABA*
Written & Edited
By Zee Mmn Khady
Just a short story
*Page* 31-40
hellow Leena kin isone, a d'ayan 6anagaren
Leena tace "kefa nake jira ina a mota bakin get
d'in gidanku kinsan su big boy basu san westing
time, ilham tace "na dad'e da sanin haka gani
nan fitowa yanzu, tafad'a tana niyyar ficewa
daga falon.
Jitayi an shaqota an d'auketa da wani lafiyayyen
mari wanda saida taga wani duhu ya gifta mata,
Momy ce ke cika tana batsewa tace "wallahi
ilham bazaki fita a hakaba, kodai ki canja shiga
kokuma ba inda zaki, ko ubanki daya d'aure maki
gindi kina abinda kikaga dama nasan baze barki
kifita a hakaba, kamar ba jinin musulmi ba.
Ilham kuwa dafe kunci tayi tana zubar da wasu
zafafan hawaye, da gudu tanufi d'akinta kan
gado tafad'a tana sharar hawaye, hankalinta be
'kara tashiba saida taduba madubi taga sawun
yatsun Momy guda biyar kwance a kumatunta.
Gashi tariga ta 'kwallafa rai ga zuwa birthday d'in
class mate d'insu akeyi kuma itace best friend
d'insa tare ma zasu yanka cake, to idan batayi
wannan shigar ba wace shiga momy keso tayi,
sotake tasaka atamfa ko less idan taje a
d'auketa bush girl, wasu zafafan hawaye suka
'kara zubowa a fuskarta tasa hannu ta goge.
Wayarta tashiga 'kara alamar 'kira na shigowa,
kobata dubaba tasan Leena ce dan tasan tana
Bakin get tana jiran fitowarta su wuce.
Bata ko kalli inda wayar takeba har tayi ringing
ta tsinke, kira ya 'kara shigowa karo na biyu,
sannan tasa hannu ta d'auka ta danna 'ok'
sannan takara a kunne cikin muryar kuka take
Sanar da Leena abinda Momy tayimata, wani irin
haushin momy yakama Leena, shiyasama koda
tazo bata shiga gidanba dan tasan data ganta da
ahigar dake jikinta yanzu tafara yimata wata
nasiha marar kai, wacce idan zata shekara tanayi
bazatayi amfani da itaba.
Leena tace "kiyi ha'kuri kitashi ki saka wasu
kayan saiki sako wannan a jaka idan mukaje can
saiki canja,
Haka kuwa akayi wata jallabiya me adon
duwatsu ilham ta saka sannan tayi rolling da
gyalen jallabiyar wancan kayan kuma ta zubasu a
site bag d'inta, sannan ta d'an gyara face d'inta
tafito, bata ko kalli inda Momy takeba tasa kai
tafice, cike da takaici Momy tace "Allah dai ya
shirya.
Dan duk abinda ilham keyi dadyntane yake bata
go a head, yanzuma wannan abin datayima ilham
d'in dayana gidan da sai rayuka sun 6aci, dan
Momy tarasa wane irin so yakema ilham, momy
ta girgiza kai tace addu'a kawai zan dage dan
Al'amarin ilham da dadynta sai du'a'i......
Love u all
Zee Elkaseem

Yarinyar Baba
[04:38 PM, 01-Oct-16]
by ZAINAB ELKASEEM
*YARINYAR*
*BABA*
_*Written & Edited*_
_*By Zee Mmn Khady*_
*```Just a short story```*
*Page*41-50
suna Isa gidan da za'ayi birthday d'in sukayi
parking motor d'insu sannan suka fito, shigar da
Leena tayi bazaka ta6a cewa tanajin yaren
Hausa ba.
tun 'kofar gida sukejiyo sautin kid'a na tashi jikin
ilham har tsuma yake dajin tashin kid'an,
A cikin gidan kuwa duk wanda yakamata ya
halacci birthday din ya halarta mutum biyu kawai
ake jira ilham da leena, in ran Hakeem yayi dubu
ya 6aci sai cika yake yana batsewa gashi sai
kiran wayarta yakeyi taki d'agawa, Hakeem ya
kalli big boy yace "gskiya ilham bata kyautamin
ba, ace duk taron nan ita kawai ake jira......
Big boy yace "nima inata try no Leena ya'ki
Shiga......
Kafin yarufe baki yaga shigowarsu da sauri
yataso ranshi 6ace yace haba ilham tun d'azu
ake jiranki amma sai yanzu kikazo, kuma ji.....ji
dan Allah wata shiga da kikayi miye wannan?
Yafad'a yana nuna kayan jikinta.
Tace sorry my wlh Momy ce tayi west time
d'inmu ka duba kaga face dina, yakai dubanshi
ga fuskarta yaga sawun yatsu biyar kwance
akumatunta take yaji tausayinta yakamashi yace
sorry my dear, Yakama hannunta suka nufi wani
d'aki a can ta canja kayan jikinta zuwa Wanda ta
taho dasu a jaka, Hakeem yashiga rarrashinta
har yasamu ta saki ranta, yayi murmushi yace
yauwa my dear ga wannan ki saka a bakinki
sweet ya mi'ka mata ba musu ta kar6a ta 6are
ta jefa a bakinta, shima wani ya 6are yasa a
baki.
Ilham kuwa tunda tasha wannan sweet d'in da
hakeem yabata sai taji duk wani 'kunci da
damuwa da 6acin ran da Momy tasata duk sun
gushe.
Sun shiga gun birthday d'in mutane na zazzaune,
suma sun samu guri zun zauna sannan aka fara
gabatar da shagalin, ga kida sai tashi yake, ilham
da Hakeem suka yanka cake mutanen gurin suka
d'auki tafi, Hakeem ya yanko yasmata a baki,
itama haka tayimashi,
Bayan wannan aka shiga shagali anata ciye-ciye
da lashe-lashe, bayan angama kowa yakama
harkar gabanshi wasu sun shiga fagen rawa wasu
kuma sun kama friend d'insu sunata fira,
A da duk inda ilham taje magrib nayi idan
hankalinta yayi dubu tashi yake, kuma kome take
saita koma gida, amma yau sai taji duk wannan
tsoron yafita daga zuciyarta, soyayya sosai
sukasha a ranar itada Hakeem, Leena kuma
itada big boy,
kada kuyi mamaki idan nacemaku duka gurin
birthday d'in ba wanda ya haurama shekara
ishirin, dan duk class mate d'insu ilham d'inne.
Haka sukayita bad'ala tsakanin mata da mazan
gurin, sune basu tashi birthday d'inba sai karfe
sha biyu da Minti ashirin da biyar na dare.
Hankalin ilham yayi matu'kar tashi lokacin data
lura da daren datayi bata koma gidaba, cikin
rud'ewa tafara magana "dan Allah Hakeem ka
maidani gida wallahi nasan yau sai Momy ta
6atamun rai, Hakeem yayi murmushi yace kada
ki damu babyna nina gayamaki yau Momy bazata
maki fad'aba, dama nasan bakida matsala da
dady, itadai hankalinta tashe yake tace nidai
mutafi, yace "to muje, ilham ta kalli Leena wacce
ke kwance kan cinyar big boy, yanata latsata
bako kunya, tace "Leena nizan wuce kedai nasan
ba yanzuba, Leena ta d'ago da rikitattun idanunta
wad'anda suka canja launi saboda tsabar jaraba
tace "ni gaskiya ba yanzuba sai naga abinda
yaturema buzu nad'i.
Cikin minti sha biyar Hakeem ya sauke ilham
'kofar gida, kwankwasawa tayi megadi ya bud'e
mata ta wuce, zaune ta taradda Momy da dady a
falo da Alama dawowarta suke jira,
Ganinsu zaune yasa gabanta yayi mummunar
fad'uwa sai yanzu ta tuna da kayan jikinta
Wanda Momy tahanata fita dasune......
Love u all
Zee Elkaseem

YARINYAR BABA
[04:42 PM, 01-Oct-16]
by ZAINAB ELKASEEM
*YARINYAR*
*BABA*
_*Written & Edited*_
_*By Zee Mmn Khady*_
*```Just a short story```*
*Page* 51-60
ilham tayi matu'kar mamaki yanda momynta ta
tarbeta da fara'a ta taso tana cewa "ilham sai
yanzu kika dawo kinsa munata jiranki dadynkima
yakasa runtsawa saboda rashin ganinki, jiki na
'kyarma ilham tace "wallahi Momy abubuwane
sukayi yawa a gun birthday kuma kinsan nice
best friend d'in Hakeem dole kome dani za'ayishi
yanzuma tahowa nayi badan angamaba kawai
saboda ina tunanin kada kiyimin fad'a.
Sai lokacin dady yasa baki yace "ba damuwa
ilham _*YARINYAR BABA*_ sunanda yake kiranta
dashikenan "jeki ki kwanta ki huta, cike da
mamaki ilham tanufi d'akinta a zuciyarta tana
cewa _{yau meya faru da Momy hartakemun
magana me taushi haka, Wanda nasan duk
lokacin danayi ba dai-daiba ba wanda ya Isa
yahana tayimin fad'a idanma duka yakama ta
dokeni}_
Momy kuwa binta tayi da kallo tanason yimata
fad'a amma data kalleta sai taji wani Abu ya
dakar mata zuciya bakinta yayi nauyi takasa
furta mata wata kalma me zafi.
Tana shiga d'akinta ta cire kayan jikinta ta d'aura
wani d'an 'karamin towel tafad'a toilet ta ahe'ka
wanka sannan tafito tashafe jikinta da wani
lafiyayyen lotion me dad'in 'kamshi, sannan
tasaka kayan bacci tabi lafiyar gado ba sallah ba
salati, barantana tayi addu'a yayin kwanciya
bacci.
Kullum idan ilham zata kwanta sai momynta
tashigo d'akinta ta tambayeta tayi sallah idan
batayiba nan zata tasata gaba tayi sannan tasata
tayi addu'oi ta kwanta, amma yau Momy tana
tunkaro d'akin ilham sai taji kamar ana ri'ke mata
'kafa ana maida ita baya, sai taji bata son zuwa
d'akin ilham d'in komawa tayi d'akinta ta kwanta
wani irin bacci me nauyin gaske yayi awon gaba
da ita.
Ilham kuwa koda ta kwanta sai taji kanta
yayimata wani irin nauyi, sai juyi take kan gado
zuwa can sai taga d'akin na juyamata, lokaci
guda wani irin haya'ki ya turnu'ke d'akin wanda
idan da mutum ze shiga ciki baze iya ganin
abinda ke gabanshiba, ganin haka yasa ilham
rud'ewa wani matsanancin tsoro yashiga cikin
zuciyarta duk illahirin jikinta 'kyarma yake,
Kusan mintuna sha biyar d'akin na juyamata
sannan kome ya lafa yakoma yanda yake jitayi
anyi sama da ita, tafiya akacigaba dayi da ita
cikin sararin samaniya batare dataga Wanda ke
tafiya da itaba.......
Love u all
Zee Elkaseem

[04:48 PM, 01-Oct-16]
by ZAINAB ELKASEEM
*YARINYAR*
*BABA*
_*Written & Edited*_
_*By Zee Mmn Khady*_
*```Just a short story```*
*Page* 61-70
Wani 'katon fili aka jiyeta tskiyar wasu mutane
wanda ganinsuma abin tsoro ne, su duka sanye
suke da jajjayen kaya sunyi d'amara da wani
ba'kin kyalle sannan sun d'aura wani a
kawunansu, fuskokinsu anyi wani zane a
goshinsu da farin Abu, sannan bakunansu
ba'kikkirin kamar sun shafa ba'kin tukunya.
Wata mace ce zaune kan wata katafariyar kujera
wacce akayima kwalliya da zanen kwarangwal
d'in kan mutum, matar tana ri'ke da wata farar
yazga a hannunta, koda ganin matar basai ka
tambayaba kasan itace shugabar wannan
mutane.
Ilham na durkushe tsakiyarsu takasa d'ago da
fuskarta barantana ta kalli mutanen dake gurin,
saida wannan matar ta taso tazo gaban ilham ta
nunata da wata sanda take wani haske yafito
daga jikin sandar yashiga jikin ilham, lokacin
ilham taji duk wani tsoro ya kawar daga cikin
zuciyarta ta d'ago da manyan idanuwanta tari'ka
bin mutanen dake gurin da kallo, abinda yabata
mamaki shine mutum na farko data fara tozali
dashi shine Hakeem best friend d'inta sannan big
boy sai kuma Leena sai sauran class mate d'insu
sunkai su goma sai sauran mutanen dabata
saniba.
Wannan matar wacce itace shugaba ta kalli
ilaham tace barka da shigowa wannan 'kungiya
tajin dad'in rayuwa, my name is Abigael, nice
shugabar wannan 'kunhiya tajin dad'in rayuwa
yawanci duk wanda kikagani a nan suna cikin
wannan 'kungiyar ne kuma sun shigetane dan
sunason jin dad'in rayuwarsu batare da sun samu
takurawa daga gurin iyayensu ko waniba.
Nasan jiya zakiyi mamakin yanda Momy takasa
aiwatar da kome a kanki lokacin dakikayo dare
gurin birthday d'in Hakeem to wannan 'kad'an
kenan daga cikin aikin wannan 'kungiya tajin
dad'in rayuwa idan zaki lura cikin wannan
'kungiya duk yarane yan kimanin shekaru sha
takwas sha bakwai zuwa ishirin, zakiga a zahiri
suna aikata abinda sukaga dama ba tare da
iyayensu sun takurasuba duk da wasu daga
cikinsu basuda iyayen kuma hakan besa sun
shiga cikin gararin rayuwaba, to daga yau kema
kinzama member ta wannan 'kungiya.
Sannan Abigael takoma kan kujerarta ta zauna
bayan tagama ma ilham wannan bayani, ilham
kuwa zuciyarta tagama dakewa da 'kungiyar
lokacin tagama amicewa da zama yar 'kungiyar.
Abigael ta d'aga sandar tsafinta sama take wani
haske ya mamaye gurin duka yan 'kungiyar suka
had'a baki sukace
*AJI DA'DIN RAYUWA*
Abigael ta kalli ilham tace gobe munason jinin
momynki koya yake kiyi kokari yazuba 'kasa.
Ba'a jira jin abinda zata fad'aba Abigael ta
sallami taro Kowa Yakama gabansa.
Love u all
Zee Elkaseem

YARINYAR BABA
[04:52 PM, 01-Oct-16]
by ZAINAB ELKASEEM
*YARINYAR*
*BABA*
_*Written & Edited*_
_*By Zee Mmn Khady*_
*```Just a short story```*
*Page* 71-80
Washe gari ilham ta tashi jikinta ba kwari ko
kad'an, ba abinda take tunawa sai abinda yafaru
da ita daren jiya, a zuciyaryta tace _(Ashe dama
shiyasa su Hakeem da Leena da big boy basuda
wata matsala a rayuwa kullum zaka gansu cikin
farin ciki, basuda wata damuwa a rayuwa abinda
sukeso shi sukeyi,)_
Ta numfasa tace _"to ay nima banida matsala
kan kome tunda duk abunda nakeso dady
yanayimin kuma bayason 6acin raina, matsalata
dai Momy, kuma itama yanzu tazama labari
tunda Abigael ta tabbatar min bazata 'kara yimin
fad'aba zanyi duk abinda nakeso_.
Cike da 'karfin gwiwa ta tashi tafad'a toilet tayi
wanka sannan takira Ameeno ta kawomata break
fast, bayan ta gama shirin tsaf cikin kayan
makarantarta, sannan tayi kalaci tagama ta
tsallake ta wuce, bayan fitarta Ameeno tazo ta
d'auke kayan ta maida kitchen...
d'akin su hassan da husaina ta wuce ta iske me
aikinsu tagama shiryasu takamo hannunsu suka
fito, falo suka iske Momy da daddy sun kammala
nasu kalacin, dady cikin shigar manyan kaya
yana shirin fita gurin aiki, ganin fitowar su ilham
yasashi washe baki yana dariya yace "Ilham
*_YARINYAR BABA_* yau zakije school d'in, cikin
sanyin jiki tace "eh dady zanje, cikin fara'a yace
to kuzo muje in saukeku, ilham tace "to amma
dan Allah dady inaso kabani 10k zanba wata
friend d'ina gudummuwa zatayi birthday, dady
yace "ba damuwa kije d'akina ki bud'e loka ki
d'auko 20thausand ay dubu goma me
zasuyimaku a gun birthday, wani irin farin ciki
yakamata tace 'thanks my dear dad, tanufi d'akin
cikin rawar jiki a zuciyarta tanata godema
dadynta da yanda yake biya mata duk wata
bukata data kawomashi.
Harta kai bakin 'kofar d'akin, Momy ta daka mata
tsawa
Ke Ilham dakata.....
Jiki na 'kyarma ilham ta tsaya cak inda take bata
ko 'kara taku d'ayaba.
Momy tace kada ki kuskura ki d'auki
kud'innan......
Love u all
Zee Elkaseem

YARINYAR BABA
[04:59 PM, 01-Oct-16]
by ZAINAB ELKASEEM
*YARINYAR* *BABA* _*Written & Edited*_ _*By
Zee Mmn Khady*_ *```Just a short story```*
*Page* 81-90 Ke Ilham kada ki kuskura ki d'auki
kudinnan..... Ke yanzu dan kina hauka zaki d'auki
dubu ishirin ki kaima wata dan zatayi birthday
dan bakisan ciwon kankiba, ke shikenan kullum
aikinki kenan daga biki sai birthday fatty, haba
ilham kiyima kanki fad'a mana, Sannan Momy ta
juya gurin daddy tace "haba dadyn ilham
bekamata ace ka d'auki kud'i kamar hakaba kaba
ilhan takaima wata 'kawarta dan zatayi birthday
fatty, ga mutane nan masu Neman taimako da
yawa kaje ka basu mana Allah zebaka lada.
Daddy ya fusata da maganar Momy yace
"banison abinda kikemun kibarni inyima 'yata duk
abinda takeso idan banyimataba waye
zanyimawa, ilham itace farin cikina kuma itace
nafara sawa a idanuna amatsayin 'yarda na
haifa, saboda haka kada ki kuma yimin haka.
Momy ta 6ata rai tace "to wallahi Alhj yau duk
abinda ze faru saidai yafaru Amma wallahi ilham
bata isa ta d'auko 20k takaima wata banzar
'kawaba wacce batada tarbiya, ni wallahi wannan
makarantarma ko kad'an yanzu bani 'kaunarta.
Dady ya kalli ilham yace "jeki d'auko ninace ki
d'auka kuma kud'inane bana momynkiba, ilham ta
matsa da niyyar shiga d'akin Momy ta daka mata
tsawa "kada ki d'auko.... Dady yace jeki
d'auko..... Ilham tawuce tasa kai d'akin Momy na
kada tayi amma bata sauretaba ta kutsa kai cikin
d'akin aiko a fusace Momy tabita d'akin ta
ficikota ta falla mata wani lafiyayyen mari, tace
wuce dan ubanki. Ilham ta dafe kunci tafasa
'Kara saboda tsananin zafin marin da momy
tayimata, jin haka yasa dady shigowa d'akin yana
tambayarta abinda yafaru. Su Hassan da
Hussaina kuwa sungaji da jira saboda haka
sukaje driver ya kaisu school, dan dama kullum
shine ke kaisu idan kaji dady yace ze kaisu to
tare da ilham za'ayi tafiyar to itakuma ba kullum
take zuwa school d'inba. Ranar dai hatsaniya
akayi sosai tsakanin Momy da daddy, Momy
kuma ta dage akan baza'a d'auki kud'inba
'karshema kulle d'akin tayi ta tafi d'akinta da key
d'in. Cikin 6acin rai daddy Yakama hannun ilham
suka nufi mota, suna tafiya yana rarraahinta
itakuma sai kuka take, har cikin ransa yakejin
kukan nata, Bank suka biya yasaka ATM yaciro
kud'i yabata 30thausand sannan ya wuce. Haka
ilham tashiga school d'in ranta 6ace. A class ne
bayan anyimasu break fast duk Kowa yafita
amma ilham batada niyyar fita saboda har yanzu
zuciyarta zafi take, tunda tashigo Hakeem ya
kula da halin datake ciki saboda haka shima kasa
fita yayi ya tsaya yana tambayar ilham dalilin
6acin ranta. Nan ta kwashe kome tagayamshi,
cike da damuwa yace "ilham bakiyi abinda
Abigael tace kiyiba da kinyi da Momy bata Isa ta
6atamaki raiba, ilham ta share hawayenta tace
kada ka damu Hakeem yau Dana koma zan
aiwatar da kome, Hakeem yayi murmushi yace
yauwa babyna saikin daure bekamata ace babbar
yarinya kamarki kullum kina cikin 6acin raiba......
Aranar dai haka Hakeem ya rinka 'karfafama
ilham gwiwa tare dayimata kalamai masu dad'i
harta saki ranta. Love u all Zee Elkaseem

YARINYAR BABA
[05:04 PM, 01-Oct-16]
by ZAINAB ELKASEEM
*YARINYAR* *BABA* _*Written & Edited*_ _*By
Zee Mmn Khady*_ *```Just a short story```*
*Page* 91-100 Da misalin 'karfe d'aya aka tashi
su Hassan da hussaina driver yazo d'aukarsu
ilham naganin haka ta tattara yanata-yanata
tayima 'kawayenta sallama, duk da ba wannan
lolacin bane na tashinsu tunda yanzu ilham tana
ss 3 ne sai 'karfe biyu ake tashinsu, yan biyu
kuma suna primary 2 ne ana tashinsu 'karfe
d'aya, abinda yasa zata bisu shine tanaso tayi
amfani da wannan damar taba 'kungiuarsu jinin
momynta, dan bakin iya 6acin rai yau momy ta
6atamata, amma daga yau angama. Saboda haka
'yan biyu na isa gurin motar itama tana isowa,
sun Shiga itama shiga kawai tayi ta zauna batare
datacema kowa 'kala ba, husaina ce ta kalleta
tace aunty ba'afa tashekuba kuma naga kin
shigo mota,..... Ilham ta daka mata tsawa na
shigo d'in dan ubanki kinfini sanin ba'a
tashemuba d'in, ainasani yanzu nakeson tafiya.
Hassan yace "mudai ki sauka kibari daddy yazo
ya d'aukeki tunda dama kullum shine ke kawoki
kuma yana d'aukok....... Kafin ya ida fad'a tasa
hannu ta dokemar baki, cikin masifa tace tunda
bansan da hakaba Kaine zaka
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2

Please Login or Register in order to submit comment