Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[7/3, 7:58 PM] Rabi: [9:23PM, 7/2/2022] RSN: https://chat.whatsapp.com/E4JKvmLLlKFDlPYRLgp
[9:24PM, 7/2/2022] RSN: BEBE'ARTH


CIN AMANA


Wattpad@Rashuna


Godiya mai tarin yawa ga sarki Allah, wanda babu wani sarki sai shi, shi zai bani ikon fara rubuta wannan littafi, Allah ina rok'onka ka bani ikon rubuta shi dai-dai, ka kuma saka na kammalashi cikin k'oshin lafiya da amici, Allahuma Amin.

Na sadaukar da wannan littafi ga mahaifina, don haka ina rok'on duk wanda ya karanta wannan littafi da yayi masa addu'ar Allah ya k'ara masa lafiya da nisan kwana mai amfani, yayi masa tukuici da gidan aljanna sakamakon babban JIGO da ya zamowa ahalinsa Allahuma amin.
i love u so much Babanmu abin alfaharinmu Yaya jigon tafiyarmu, Allah bar mana kai cikin aminci.

Ina sunkuyar da kaina gami da durk'usawa bisa kawo gaisuwa ga Iyayena na gari, ina adduar Allah ya k'aro d'aukaka da albarka,lafiya wadata, nutsuwa kwanciyar hankali, Amin.

Ina yaba muku 'yan uwana, ina rok'on Allah ya k'aro mana d'aukaka da cigaba gami da albarka a rayuwarmu ta duniya da lahira amin.
Ina ji da ku, ina al'fahari da ku Allah ya k'ara hada kanmu ya bar zumunci, amin.
Falalu Shu'ayb Nababa
Na'ima Shu'ayb Nababa
Halifa Shu'ayb Nababa
Fadila Shu'ayb Nababa
Rabee'ah Shu'ayb Nababa
Mardiyya Shu'ayb Nababa
Abdul Rahaman S Nababa
Murja Shu'ayb Nababa
Allah kaiwa mahaifanmu tukuici da gidan Al'janna, sakamakon gina KATANGAR k'aunar dake tsakaninmu Allah kuma kar ka bawa wani damar rusa mana ita, Amin ya Allah.

Babban tukuici ga yarana.
Aseep,Aydha,Abrar,Aseefa.
Allah ya kawo albarka cikin rayuwarku, ya k'aro mana zuri'a mai tarin albarka da wadata Amin.


1
――――――
Da gudunta ta shigo falon, ta na k'walla kiran ‘’Dad‘’ tana nbaza ido taga ta ina zai fito, kacibis sukai a k'ofar da za ta sada ka da falonsa na biyu, jikinsa tai saurin fad'awa tana ruk'unk'umeshi yayin da shi kuma ya k'ara matseta a cikin jikinshi yana me lumshe idanuwansa·
‘’Nayi kewarka Dad‘’
Ta fad'a da siririyar muryarta mai taushi, yayin da shi kuma ya kuma shigar da ita jikinsa sosai kamar zai tsagata biyu kana yace.
‘’Nima nayi kewarki shalelena, amma meyasa ba ki gayan yau za ki dawo ba?‘’
‘’Suprise zan baka that is why.‘’
Takai k'arshen maganar tana sakar masa kiss a wuya, wanda yai sanadiyar dakatawar maganar da yai nufin yi, jikinsa ya d'au d'umi sosai, yayin da ita kuma ta fara k'ok'arin barin jikinsa amman ta kasa saboda ba k'aramar matsa yayi mata ba·
‘’Dad‘’
Ta fad'a da k'arfi ganin tunaninsa ya tafi wani guri da ban, murmushi ya sakar mata yana me sauke lab'b'ansa kan lab'b'anta ya bata,hot kiss, murmushin itama ta sakar masa ya ja hannunta suka fita daga falon zuwa falo na biyu, dining area suka nufa yaja mata kujera ta zauna, da kansa ya zuba mata abincin ya kuma zauna ya ciyar da ita, wannan ya zame masa jiki ko kuma nace k'aida, muddun yana gari, itama tana gari da kansa zai zauna ya ciyar da ita, inkwa ba ya gida baza taci ba har sai ya dawo.
Bayan gama cin abincin nata ya dubeta da kulawa yace·
‘’Yanzu kije ki wanka ki huta sai kizo ki sameni a d'aki mui magana·‘’
Mik'ewa tayi tana murmushi ta d'an durk'usa ta gefensa tai masa kiss a kumatu kana tace.‘’Thank you so much Dad.‘’
Ta juya ta bar falon, yayin da shi kuma yabi bayanta da mayun idanuwansa kamar ya cinyeta d'anya yana ayyana abubuwa masu yawa a ransa·

Idan tana tare da Dad d'inta dukkan wata damuwa mantata take, yanzunma hakanne ya faru da ita, tana barin sashensa damuwar da ke ranta game da mahaukaciyar nan ya dawo mata sabuwa, ta rasa me yasa matar ta shiga ranta ta zauna, tausayi ne ko kuwa son taimakonta ne? babu me bata wannan amsoshin kuma zucitarta ma ta gaza bata, wayo to zai bata? shi d'inma dai babu·
Tana shiga d'akinta, wanda tsayawa gaya muku tsaruwar da yayi b'ata lokacine kawai ku k'iyasta, kayan jikinta ta shiga cirewa ta fad'a toilet ta dad'e sosai cikin ruwan d'umi kana tayo wankan ta fito had'e da d'auro alwala, don ta jiyo ana kiran sallah ta masallacin dake cikin gidan, don yanzu lokaci ya juya shida dai-dai ake kiran sallar magariba·
Riga mara nauyi ta samu ta zira, ta saka zumbulelen hijabinta ta kalli gabas, yadda ta nutsu ku baza kuce NAFISA ce SHA LELEN Dad ba·

Ba ita ta fito daga d'akinta ba sai da ta gabatar da sallar isha tukunna, d'akin Dad ta nufa suyi maganar da zasui don wani nishad'an d'an bacci take ji, idanuwanta har wani lumshewa suke, tare da Mom ta tarar da shi suna hira dukkaninsu murmushi suka sakar mata tare da bud'e hannuwansu alamun ta taho garesu, tsayawa tayi tana binsu da ido, tana tantance tsakanin Mom da Dad wa ya fi k'aunarta amsar da har yau ta gaza samunta a k'wak'walwarta idan tana wannan tunanin kanta,har ciwo yake, kusan had'a baki sukai wajen fad'in·
‘’Tawo mana·‘’
Tsakiyarsu taje ta zauna, ta kamo hannuwansu ta rik'e ta kwantar da kanta a kafad'ar Mom, yayin da Dad ya matso yana kai hannunsa wuyanta·
‘’Baki da lafiya ne shalele?‘’
‘’UMUM bacci kawai nake ji·‘’
‘’Yau ba fita kenan?‘’’
Kai kawai ta d'aga masa, Mom tace·
‘’Ai in kika fita sai kin fi jin dad'i, amman bacci da farar safiyar nan ai sai ki gaji da kwanciya kafin gari ya waye tashi maza muje na shirya ki·‘’
‘’To ai magana zamui da Dad·‘’
‘’Kwayi maganar idan Allah yai mana yawan rai zuwa gobe‘’
Takai k'arshen maganar tana mik'ar da,ita tsaye, yayin da ita kuma takai dubanta zuwa fuskar Dad ganin baice komai ba yasa ta bin Mom d'in·
Hmmmmm masu karatu, idan zan shekara inai muku rantsuwar Nafisan d'azu ce da ta kalli gabas itace yanzu Mom ta shirya ba za ku yarda ba, cewa zakui wannan Rani Mukhraji ce ta cikin film d'in india don basu da maraba hatta k'wayar idonsu, da kyakkyawan murmushin da ke k'ara fito da zallar kyansu, wata arniyar rigace a jikinta black nd white, samanta ne black in me gashi-gashi sai walwali yake,da d'aukar ido k'asan kuma white shikumar kamar net yake, iya kacin rigar guiwarta, sai santala santalan k'afafuwanta dake ta shek'i, ba kwalliya a fuskarta sai jan jambaki kawai da ya k'ara k'awata lab'b'anta masu gwanin burgewa, girarta a gyare take sai ku rantse jagira tayi, sai dogayen eye leshers inta da suke a tsaitsaye gazar -gazar,gashin kanta kuwa yasha gyara sai shek'i yake tai mata parking insa a tsakiyar kanta da black nd white in riborm jelar sai reto take kasancewarsa ba mai cika tsayinma dai ba wani can ba, wata had'ad'd'iyar bandana ta saka black mai d'an fad'i don ta kusa rufe rabin kanta, stone d'in jikinta white ne yane ta walwali, a santalelen wuyanta siririyar sark'a ce ta diamond haka abin hannu da agogo da zobuna. A ko da yaushe ba ka rabata da su, kuma iri da ban da ban, plat in takalmi ta saka white, kasancewarta me tsayi ba ta fiya saka heals din takalma ba, sai dai idan tai ra'ayi·
Har cikin mota ta rakata, taso taje gurin Dad Mom ta hana ta, rafar 'yan dubu ta bata, don tasan ba kud'i a hannunta sai A·T·M shiyasa ta bata don ta wutar da ita, cike da jin dad'in wannan soyayya da Mom take mata ta bar harabar gidan, yayin da Mom ta juyo idonta ya sauka akan Dad da ya saki labilen tagar da ya gama lek'e tsaki ta ja had'e da fad'n·
‘’ Jarababbe·‘’

‘’Yanzu ita kad'ai ta tafi?‘’
‘’To ni kake so naje na kaita?‘’
Itama ta jefo masa tambayar a zafafe, ganin hakan yasa shi kwantar da kai had'e da fad'in·
‘’Ba haka nake nufi ba, da kin bartan tun da tace bacci take ji, zuwa gobe drivern nata zai fara aiki, shine ma maganar da nake son muyi da ita don ni sam bana son fitarta ita kad'ai·‘’
‘’Nifa ina jin tsoron d'aukar mata irin drivern da ta lissafa tana so, don kasan nak'i jinin saka ido cikin rayuwata·‘’
‘’Haba-haba Jamila ni jakin ina ne zan d'auko abinda zai zame mini matsala, kema kin san sam bazai yuhu ba, amman kuma kinsan ya zamo mini farilla na cikawa Shalelena burinta, na samo mata drivermara muni, kuma me tsafta, amman bagidaje ne sam bashi da wayewa, kuma yana da tsagu a fuskarsa har da bille, bashi da asali don nayi bincike sosai a kansa kafin na daukeshi aiki, mahaukaciya ce mahaifiyarshi, kuma ta mutu, a wani gida yake gadi, to shine me gidan ya rasu iyalansa suka koma kano da zama, dalilin da yasa yake neman wani aikin kenan har aka kawosa gurina sai naga shi ya can canta da drivern Shalelena, kuma kan na d'aukesa sai da na kafa masa sharud'a·
‘’Auho, to har naji sanyi a raina, don da har na tsorata da zsbin FANAN kar muje mu d'ebo ruwan da zai dafa kawunanmu gaba d'aya‘’
Takai k'arshen maganar tana dariya yayin da Dad ya tayata kafin su shiga wata hirar ta da ban, wacce sam ba fahimta nake ba·


# N·W·A
[7/3, 8:01 PM] Rabi: BEBEARTH

https://chat.whatsapp.com/JPKVCkDzizKFRFZcpvfF1v
[11:51PM, 11/24/2021]
Ga link na gruop nan, dan Allah dan Allah, don soyayyarku da manzon Allah duk wacce ta san ba karanta littafin ne zai kaita ba kar ta b'atawa kanta lokaci, nima ta b'ata mini gurin fiddata.


CIN AMANA



Wattpad@Rashuna


2
A hankali take driving kasancewar akwai baccin sosai a cikin idanuwanta, a haka dai har ta isa harabar k'ayataccen Hotel, wanda sai d'an wane da wane ne ke shigarsa saboda mugun tsadarsa, parking in motarta tayi ta fito tai locking inta, ba ta d'auko komai ba sai rafar 'yan dubun da Mom ta bata, gefen hannunta na hagu ta bi wanda ya sadata da clube in da ya tara maza da mata, musulmai da k'abila yare da ban da ban, ko wanne yana harkar da ta kawo shi, tana shiga gurin aka saka ihu da sowa ana mata kirarin da aka saba, musamman da sun kwana biyu ba su ganta ba.
‘’'YAR DA DUNIYA KE YAYI, KI TAKA A SANNU SHALELEN DAD, SARAUNIYA AMARYA A GIDAN SAMEER‘’
Babu gefen wanda ta kalla, kujera kawai ta jaho ta na yatsina fuska, in da sabo dama sun saba da miskilancin nata, yayin da wasu kuma suke mugun jin haushinta, wasu kuma take birgesu ainun.
Sameer ne ya shiga yi musu ruwan kud'i ko ta ina, saboda jin dad'in kalmarsu ta k'arshe, kana ya isa ga gimbiyar tasa da take ta cin magani, kujerar da ke facen inta ya jaho ya zauna, yana binta da wani shu'umin kallo me fito da zulamarsa a bayyane, siririn tsaki ta ja had'e da kautar da fiskarta gefe a dai-dai lokacin wetres in gurin ya ajiye mata tire a gabanta me d'auke da kwalbar giya da glass cup a kai, yayin da Sameer ya saki shu'umin murmushin da shi kad'ai ya san ma'anarsa, kana yayi saurin d'aukar botle in giyar yana k'ok'arin bud'ewa ya zuba mata zazzak'ar muryarta ta ratsa kunnuwansa.
‘’Kar ka wahalar da kanka yau ban jin shanta‘’
Tsayawa yayi yana kallonta rik'e da botle in a hannu, kallon cikin ido tai masa, had'e da d'an zaro idanuwanta ta juyasu gami da cewa.
‘’Yes‘’
Ta mik'e ta nufi filin casu, don jin an saka wak'ar da take mugun k'auna, ta shiga tik'ar rawa ba ji ba gani don FANAN gwana ce wajen iya rawa.
Sameer kuwa wani mugun dafi ta zuba masa, wanda yayi sanadiyar sumansa na wucin gadi a zaune, har sai da sowa da tafin da ake mata ya dawo da shi tunaninsa da hanzari ya mik'e yana cin alwashin sai tazo tasha giyar nan da kanta, don yau so yake ta mallaka masa kanta, babu musu babu jayayya, yau yake so yai bankwana da k'ishiriwar da ta dad'e tana damun mak'oshinsa.


――
‘’ Likita ya jikin nata?‘’
Sai da likitan ya fara zare gilashin idonsa kana ya kalli I.G Mustapha da ya jefo masa wannan tambayar kana yace.
‘’To Alhamdlillh za'a ce, amman muddun ba ta cire tunani da damuwa ba to ciwonta kullum jiya iyau zai kasance, kuma hakan zai haifar da babbar matsala, don yanzu haka ma jininta yai mugun hawa ba komi nake jiye mata ba sai ciwon shanyewar b'arin jiki, Allah dai ya kiyaye faruwar hakan.‘’
A sanyaye I.G Mustapha yace.
‘’Amin, insha Allahu zanyi k'ok'arin gurin ganin na kwantar mata da hankali, dama a kwana biyun nanne abin ya juyo mata, na gode likita.‘’
Daga haka ya bashi hannu sukai musabaha ya fita daga ofis in, d'akin da aka kwantar da ita ya nufa, dukkan familyn gidan suna cikin d'akin ganin shigowarsu yasa suka fara fita d'aya bayan d'aya, daga gefenta ya samu ya zauna had'e da kamo hannunta.
‘’Muddun kema kika bari na rasaki to tabbas banga amfanin cigaba da tawa rayuwarba don ko wa'adina bai cika ba to zan k'are rayuwata ne cikin rashin lafiya, ki taimakeni ki rage tunani da damuwa dan Allah Ummu Aymana.‘’
‘’Ka sani kaima ina k'ok'arin fitar da komai daga raina, abinne ya juyo mini yake k'ok'arin fin k'arfina, amman insha Allah zan danneshi da k'arfin addu'a kaima ka tayani.‘’
‘’Rana ba ta hudowa ta fad'i ba tare da na miki addu'a ba Ummu Aymana. Insha Allah komai ya kusa zuwa k'arshe, muna bin komai daki-daki ne don mutumin yana da mugun had'ari, kuma komai yana yinsa cike da wayo, idan ya fuskanci muna bibiyarsa yana iyai mana b'atan dabo, b'atan da baza mu sake ganinsa ba, kiga wuyar da muka sha kafin samuwar tan'ameme inda yake zaune ba, amman insha Allahu sai na kaiwa Hajja shi gabanta ya durk'usa ya nemi yafiyarta.‘’
‘’Ba yafiyarsa muke buk'ata ba, ya gaya mana inda Fina da Faruoq suke kawai muke da buk'ata.‘’
‘’Wannan ba matsala ba ce insha Allah kamar yau za kiga Finanki da Farouq a gabanki.‘’
Kyakkyawan murmushi ne ya bayyana a fuskarta tace.‘’Allah yasa amin.‘’ Har lokacin murmushi bai bar kan fuskarta ba, da ‘’Amin‘’ D'inma shima ya tayata yana jin dad'in yadda yasata cikin farin ciki amman k'asan zuciyarsa fal tarin damuwa da fargaba ne, yana fargabar zatonsa ya tabbata na Faruoq ba ya tare da shi Finan ma bai da tabbas d'in itace..



KATANGA labarine mai tab'a zuciya, da sanyayar da jikin mai karatu, zai yi wuya ka gama karanta shi ba tare da ka zubar da k'walla ba, da dad'in dad'awa kuma littafin yana da shiga rai.
Babban abinda ya kuma birgeni ga littafin KATANGA marubuciyar ta baje nutsuwarta, hikima, fasaha,hazak'a,basira,tunani duk a cikin wannan littafi mai suna KATANGA zai zamo bakandamiya da zarar ya ratsa duniyar marubuta, akwai abin amfani a ciki, yi k'ok'ari ka mallaki naka kar ka tsaya jiran na aro, domin kwa akwai hanyar da zamu bi mu gyara zaman auranmu a gidajenmu cikin tarbiya da koyarwar islama, ba nan kad'ai ya tsaya ba akwai hanyar da mace za ta tsaftace jikinta cikin koyarwar islama ba tare da ta sanya abinda zai cuceta ba, akwai d'umbin abin amfani a ciki mudai had'e a cikin KATANGA an jima ba'ayi kamarsa ba maza neme shi akan farashi mai sauk'i naira 200 kacal.
09037093702


#N.W.A
[7/3, 9:18 PM] Rabi: [10:01PM, 7/3/2022] RSN: https://chat.whatsapp.com/E4JKvmLLlKFDlPYRLgpNaf
[10:12PM, 7/3/2022] RSN: Ga link na gruop nan, dan Allah dan Allah, don soyayyarku da manzon Allah duk wacce ta san ba karanta littafin ne zai kaita ba kar ta b'atawa kanta lokaci, nima ta b'ata mini gurin fiddata.


CIN AMANA



Wattpad@Rashuna


3

Filin casun ya shiga ya ruk'o k'ugunta daga baya yana jujjuyata, tasan mutum aya ne zai mata irin hakan, kuma ta gargad'eshi yafi sau ba adadi, neman zare hannunsa daga jikinta take amman ta kasa saboda ba k'aramin rik'o ya mata ba, juyo da ita yayi, ya sak'alo k'ugunta da hannu d'aya, ya rik'e hannunta da d'aya yana jujjuyasu yana sakar mata murmushin mugunta, na babu yadda zaki da ni yarinya, janyota jikinsa yayi ya rungumeta yayin da gurin ya d'au tafi da sowa, in ba Sameer in ba wa zai gigin ko da tab'a farcen Shalelen Dad.
Takaici da bak'in ciki ne yasa idanuwanta cika da ruwan hawaye har suka fara zuba, k'ok'arin had'e bakinsu yake Allah ya bata sa'ar gantsara masa cizo a wuya,ba shiri yai saurin sakinta yayin da ta nufi gurin da bottle in wine in yake ta b'incike murfin ta d'aga sama ta farai mata shan hauka, yana tsaye yana kallonta yana murmushi, bayan ya dawo daga azabar zafin cizon da ya tafi.
Sai da ta sha kusan rabi kana ta cire kwalbar daga bakinta, ji tayi kanta ya fara wani irin yamutsawa kafin ta fara ganin bibbiyu ta tafi luuu za ta zube a k'asa da hanzari Sameer ya taho zai tarota yana me jin dad'i a ransa yau burinsa na shekaru me yawa zai cika, amman kaishhh kafin ya k'arasa gareta yaji ya gabza uban tuntub'e da wani abu, bai aune ba yajishi a zube a k'asa, hancinsa da bakinsa ya daku da k'asa, wata ratsatstsiyar azaba ce ta ratsa ta k'wak'walwarsa, abinka da namiji haka ya jure wannan azabar ya d'ago yaga a wani hali Fanan take amman wayam babu ita a gurin babu alamunta, da hanzari ya mik'e mutanen gurin suna masa sannu amman tambayarsu yake ‘’Ina Fanan‘’
Babu wanda yaga abinda ya faru da ita saboda duk hankalinsu yayi kan Sameer d'in da zai fad'i, wasu kuma suna can harkar gabansu, hakan yasa ko wanne yace bai ganta ba, da hanzari ya fice zuwa harabar motoci wayam nanma babu motarta, abinne yayi mugun d'aure masa kai.
‘’To ta ya , ta ya ya hakan ta faru?‘’
Wannan itace tambayar da ke kai kawo a kwanyarsa, gurin wetres d'in da ya kawo mata giyar ya nufa ya tuhumesa akan wacce ya bashi ya kai mata ya kawo matan? ya tabbatar masa lallai ita d'in ya kawo mata, kansa ne ya kuma d'aukar cagi muddun dai wannan giyar tasha, baza ta tab'a iya barin gurin ba bare har ta ja mota, wayarsa ya cira ya lalibo number Mom, kira kusan sau uku amma ba tai picking ba, tsaki kawai yake ja ransa duk a jagule, yana jin kishin ace wanine ya d'auki Fanan d'insa, inkwa hakan ya tabbata bazai tab'a k'yale ko waye ba.
Duk da k'asan ransa yana son ya d'an rage zafi da ko wata 'yar babyn ce amman haka ya yanke shawarar zuwa gida ya duba Fanan, duk da bai wani yadda za ta iya mayar da kanta gida ba, yana shirin tayar da motar kiran wayar Mom ya shigo, da hanzari yayi picking, ya rigata magana.
‘’Fanan fa, ta dawo gida?‘’
‘’Ta dawo, me ya faru?‘’ Ta bashi amsa had'e da jefo masa rambaya itama, wata wawiyar ajiyar zuciya ya sauke yana busar da iska mai zafi kafin yace.
‘’Shikenan kawai Mom sai da safe‘’
Saurin dakatar da shi tayi da cewa.
‘’Kar ka sake ka kashen waya,baka da hak'uru Sameer, ita gaggawa da kake gani gaba d'ayanta daga shaid'an take, abinda mallakinka za ta zama meye na damun kanka kuma?‘’
‘’Allah ba abinda kike tunani bane Mom, zan dai shigo da safe zamui maganar.‘’
'Kit ya kashe wayar ba tare da ya jira me za tace ba, ya bi bayan wata Beb da ta wuce tana karkad'a jiki duk ta d'aga masa hankali, dama abinka da wanda yake kusa...


Washe gari har kusan shabiyu na rana tana bacci ba tasan inda kanta yake ba, Mom nd Dad kuma ba su bi ta kanta ba don sun san in ta shahu irin haka tana ma kaiwa fin haka tana bacci.
A hankula take bud'e idanuwanta da take jin sun mata nauyi sosai kanta yayi mata wani irin dumm, ak'alla ta kai kusan minti ashirin a kwance ba tare da ta motsa ba, tana search in abinda ya faru da ita, ita dai tasan ta tafi luuu za ta fad'i kuma ba ta jita ta fad'in ba, to waye ya tareta, waye kuma ya kawo ta gida? Bata da me bata wannan amsoshin.
‘’Na shiga uku, kaddai Sameer ya samu biyan buk'atarsa a gurina?‘’ Wani b'ari na zuciyarta ya jefo mata wannan tambayar, yayin da d'aya b'arin zuciyar kuma ya kwantar mata hankali da amsar.
‘’Kai ba haka bane ai da zan ji wani sauyi kuma a jikina‘’
A hankula ta yunk'ura ta mik'e, wani k'amshi ne me dad'i ya dabaibaye hancinta, shinshina jikinta ta shiga yi da hannuwanta gaba d'aya k'amshin suke.
‘’ Ni 'yatsu ina na samo wannan k'amshin?‘’
Itace tambayar da ta jefowa kanta, bata da me bata amsar hakan yasa ta yanke shawarar tambayar me gadi wane ya dawo da ita gida, daga haka ta tashi gaba d'aya ta shige toilet, a gurguje tayo wanka da brush had'e da d'auro alwala, saboda tunawar da tayi ba tai sallar asuba ba, gashi tana da case d'in da zasu shiga tun k'arfe goma, gashi yanzu tayi lousing insa, dalilin da yasa kenan jiya tak'i shan wine, amman sai da wancen mayen ya b'ata mata rai har taje ta
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5

Please Login or Register in order to submit comment