Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

MAGAJIN WILBAFOS
Fita na biyu 2
Marubucin littafin
Dr Abdullahi Muhammad Ibrahim
Ebook creat by Shuraih Usman
Ebook publish by www.hausaebooks.cf
Ebook din nan yazo maku ne daga shafin www.hausaebooks.cf
Kuna ziyartar shafinmu don samun sababbin littatafai
Ga duk wanda ke bukatar ebooks nashi ya samu shiga cikin wepsite namu sai ya turo mana da littafin ta Email namu hausaebooks@gmail.com
MAGAJIN WILBAFOS
Marubuci: Dr Abdullahi Muhammad Ibrahim
Babi na 51: Umarnin Ururu
Post by: Shuraih Usman
@shuraih 99%
www.facebook.com/hausaebooks
.
Daga:- Taskar Magajin Wilbafos
___
SHEKARU DA SUKA GABATA (ALAƘA TSAKANIN HIDAYA
DA ALJANI JIDAIME)
___
Hidaya ta ɓata rai tana duban aljani Jidaime wanda ke
tsaye yana lilo akan iska, "Kasan mai yasa Ururu suka fi
kowacce ƙabila ƙarfi a wannan zamani, ba komai bane
saboda su basu dogara da aljanu ba. Saboda haka babu
wata farar-laya da zata iya aiki a kansu. Sun dogare ne
kachokam da ƙarfin Izzar dake cikin baƙaƙen
idanuwansu. Haka nake so Armad shima ya dogara da
ƙarfin jininsa na Wilbafos. Bana son ya dogare dakai a
matsayinka na aljaninsa, domin hakan bazai kaishi ko'ina
ba."
Aljanin najin haka ya murtuke fuska, "Kina nufin kin raina
ƙarfina ne. Kuma kema ai kina amfani da aljaninki,
danme yasa kike so ki hana shi amfani da nasa."
Hidaya ta ɗanyi murmushi sannan ta amsa da cewa
,"Bawai ina cewa ban yadda da ƙarfin ka bane, Jidaime.
Kawai dai nasan akwai ƙarfin Izza irin wadda ni kaina ban
san iyakacin ta ba acikin ruhin ƙani na, saboda haka ina
so yayi amfani da ita maimakon ya dogara da ƙarfin
aljaninsa. Saboda haka kayi haƙuri zan ɗaure ka ta yadda
babu yadda Armad zai iya amfani da haƙiƙanin ƙarfinka.
Kuma ina mai yi maka gargaɗi na ƙarsge da kada wani
tsautsayi yasa ka ƙara haɗa kanka da aljani na domin yin
hakan zai jawo maka hukunci. Aljani na bai taɓa biyayya
ga Ururu ba kuma Ururu basu isa su baahi umarni ba. Kai
kasan mai nake nufi."
Tana rufe baki Aljani Jidaime ya fara jada baya yana
neman guduwa, amma ina tuni Hidaya ta saukarda
al'amudan Farar-laya akansa.
Tun daga wannan rana yake a ɗaure, kuma basu samu
wata damar ganawa da Armad ba sai a wannan lokaci.
Hasalima Armad baisan cewa aljaninsa a matsayi ɗaya
suke dana Ikenga ba. Kuma bawai kaɗai Walƙiya aljanin
nasa yake sarrafawa ba. Kai a taƙaice ma wannan walƙiya
ba daga aljanin nasa take fitowa ba. Tana fitowa ne daga
ainahin cikin ƙarfin ruhin Armad wanda aka haifeshi
dashi. Irin ƙarfin da yayarsa Hidaya take so yayi amfani
dashi.
_____
Acikin filin Jinzidal kuwa, har wannan sadauki mai
muƙamin kyaftin ya ɗauki Armad a sume da niyyar tafiya
dashi sai Uznu Ururu ya dakatar dashi.
Uznu na tafiya taku ɗai-ɗai ya iso ga jikin Armad ya kuma
saka hannunsa akan zuciyar Armad. Haka na faruwa wani
haske ya fara fita daga jikin hannunsa yana shiga jikin
Armad.
____
Acikin duniyar aljanun nan kuwa Armad yana tsaye yana
tunani wacce shawara ya kamata ya yanke kawai sai yaga
duniyar ta fara cika da wani baƙin haske. Lamarinda yasa
shi ajiyar zuciya. Amma tun kafin ya gama gane maike
faruwa yaga fuskar aljaninsa Jidaime ta canja.
"Armad ko ka kwance ni yanzu ko kuma baza ka iya ƙara
amfani da fasahar walƙiya ba." Aljanin ya faɗa cikin sauri
da alamun tsoro.
Idanun Armad suka cika da mamaki a lokacin da yaga
canjin yanayin da aljanin ya samu kansa aciki. Nan take
ya buɗe baki ya tambayi aljanin, "Mai yake faruwa?"
"Uznu Ururu ne yake neman ƙara ƙarfin ankwar dake
ɗaure dani. Ban san tayaya ba, amma da ƙarfin baƙaƙen
idanun sa yana iya gani har cikin ruhinka. Wato dai a
taƙaice yana ganinmu a halin yanzu. Kana da ƙasa da
daƙiƙa biyar ka yanke shawara akan abinda zakai."
Aljanin na rufe baki ya fara karkarwa lamarinda ya ƙara
ruɗa Armad, domin har a wannan lokaci ya kasa yanke
shawara.
Abu ɗaya dai da Armad ya sani shi ne ba dukkan
maganganun da aljanin ya faɗa zai yadda dasu ba, yasan
cewa lallai ba'a raba aljanu da ƴan ƙarairayi nan da can.
Amma a halin da yake ciki bashi da wani zaɓi face ya
bawa wannan aljani dama yaga kozai iya kuɓutar dashi
daga halin da yake ciki.
Saboda haka Armad yayi tsalle izuwa wannan aljani, ya
kuma ja ankwar da ƙarfin tsiya. Abun mamaki bai taɓa
tsammani ba, amma kawai sai yaga ankwar tana
murmushewa tana sakar wannan aljani. Wanda a iya
lissafinsa cire ankwar zai ɗau lokaci kuma yana buƙatar
makami kafin ya faru. Amma koda Armad ya tuna cewa
ai ankwar ta tsafi ce, sai kuma ya gane yadda abin yake.
Aljani Jidaime yai ƙaraji tare da miƙe hannayensa sama
bayanda yaji shi a sake. Ranar daya daɗe yana jira tazo.
Amma kafin ya fara komai yana buƙata ya kashe Uznu
Ururu dake waje, wanda idan baiyi saurin yin hakan ba
wannan baƙin hayaƙi zai iya ƙara ɗaure shi ya maida shi
gidan jiya.
Nan take ya finciko ruhin Armad daga wannan duniya ya
dawo dashi izuwa jikinsa a wannan fili. Shi kuma ya
bayyana a gaban Uznu Ururu yana mai riƙe da farin
al'amudin aljanu a hannunsa na dama.
Koda bayyanarsa sai dukkanin kyaftin guda biyar ɗinnan
dake biye da Uznu sukai tsalle suka dira a gabansa domin
su kare shi. Amma suna dira aljani Jidaime ya kawo wata
muguwar wafta da al'amudinsa inda ya share su baki
ɗayansu a lokaci guda. Sannan kuma yayi kan Uznu
gadan-gadan. Lallai ƙarfin aljanu da bil-adama da
banbanci.
Nan da nan fuskar Uznu ta canja, yanayin firgici ya
bayyana akanta. Amma a wannan lokaci ne ya ciji
ɗanyatsansa na dama, inda jini ya fara ɗisa. Uznu baiyi
wata-wata ba wajen saka wannan jini acikin idanunsa
baƙaƙe guda biyu. Ai kuwa haka na faruwa wani baƙin
haske ya fara ɓulɓula daga ciki, sannan Uznu ya fara
magana, "Ina mai umartarka da ƙarfin Ururu dake jini
na, da ƙarfin Ururu dake bisa ƙasa ta farko daka tsaya a
inda kake."
Abin mamaki yana rufe baki wani irin ƙarfin izza marar
misaltuwa mai cike da buwayar Ururu ya fara ambaliya
acikin filin. Kan kace meye wannan aljani Jidaime ya tsaya
a inda yake cak ya kasa motsi. Sannan kuma Izzar Uznu ta
fara hawa tana ambaliyar har saida takai Shekaru dubu
huɗu da ɗari tara da casa'in da tara. Uznu ya cafi
takobinsa yayi kan aljani Jidaime.
Tun kafin ya ƙarasa akaji muryar aljanin na cewa, "Idan
ka kashe ni kasan ƙabila ta baza suyi shiru ba. Kuma
babban sarki Ururu Kuyurussa'ayi yayi mana katanga
daku..." Yana magana yana karkarwa, kuma ganin cewa
Uznu baya saurarensa kawai sauri yake ƙarawa yasa tsaya
ya kasa ƙarasa abinda yake faɗa tare da fara karkarwa.
Uznu na ƙarasowa yasa takobinsa ruwan toka ya tsarge
aljani Jidaime gida biyu. Aljanin yai wata ƙara mai
firgitarwa, inda daga bisa ya fara narkewa izuwa toka
yana murmushewa.
"Da kasan da tsakanin da akai mana da baka tunkare ni
ba. Ko ba komai ina da hujja idan aka je gaban babban
sarki Ururu Kuyurussa'ayi." Uznu na magana yana goge
takobinsa.
Sannan nan take ya ɗau Armad ya ɓace daga wannan filin
gasa.
___
A can gefe guda kuwa sarki Deniz Iluru da dakarunsa
suna tsaye suna kare duk wani hari da yayo kan ƴan kallo
a lokacin da ake wannan fafatwa tsakanin Uznu da su
Armad.
Duk da kuwa cewa tunda Uznu ya buɗe idonsa dukkan
ƴan kallon suka sume, amma bayan da aka gama komai
hankali ya dawo jikinsu saida hukumar yaƙin garin tayi
amfani da rahoton ƙarya na cewa girgizar ƙasa ce tasa
aka tsayar da gasar wannan shekara. Amma ta ƙarƙashin
ƙasa sarki Deniz Iluru ya rubuta ƙara izuwa fadar Ururu
dake ƙasa ta biyu mai kula harkokin Jinzidal akan su
hukunta Uznu Ururu saboda cikas ɗin daya kawo a gasar
Jinzidal ɗin. Cewa kuma suna fata ai musu adalci.
To haka dai aka kawo ƙarshen wannan gasa ta Jinzidal ta
wannan shekara.
____
To ALLAH ya kawo mu ƙarshen Jinzidal. Yanzu zamu shiga
wani sabon sashi na wannan littafi. Duk mai tambaya ko
kuma wani abu da bai gane ba a babika 50 da suka wuce
ya rubuto a comment.
Nidinne dai Shuraih Usman inkiya
99%
Daga taskar magajin wilbafos
MAGAJIN WILBAFOS
Marubuci: Dr Abdullahi Muhammad Ibrahim
Babi na 52: Dordor mai waka
Post by: Shuraih Usman
@shuraih 99%
www.facebook.com/hausaebooks
.
Daga:- Taskar Magajin Wilbafos
Doron ƙasa na huɗu
Shalkwatar Mayaƙan Ururu
____
Sahu-sahu ne na mutane ɗai-ɗai har sahu ɗari, kowanne
ɗaya daga cikin wannan sahu yana ɗauke da mutane
guda ɗari. A taƙaice dai mutanen dake cikin wannan sahu
su dubu goma ne. Dukkaninsu na sanye da baƙaƙen kaya.
Babu mai ko magana acikinsu. Kai ko tari babu maiyi.
Dukkanin wannan mutane ba kowa suke jira ba illa
kwamanda Uznu Ururu. Uznu Ururu dai yaje ƙaro ilmi a
jami'a mafi girma a duniya dake bisa doron ƙasa ta farko.
Jami'ar da ake kira da Namibiya da yaren Aldurish na
Ururu. Saboda daɗewar da yayi nema baya nan suka
shirya masa wannan gagarumar tarya.
Amma bisa mamaki Uznu yana bayyana kawai tsayawa
yayi kimanin daƙiƙa ɗaya, inda ya kyaɗa musu kai
alamun jinjina sannan yai ɓangaren inda ofishinsa yake.
Koda yake baza a iya kiran wajen na Iznu Ururu da ofishi
ba kaɗai, tunda iya girman wajen kaɗai yakai wani ɗan
ƙaramin gari. Sannan kuma ga shirye-shirye na
musamman na al'amura da suka shafi Izza da ake
gudanarwa a wajen. Kusan zaka iya cewa duk wani
sinadari da za'a iya samu a ƙasa bakwai akwai a wannan
ɓangare na Uznu Ururu, kasancewar shi ɗin yawanci
kayansa daga doron ƙasa ta farko yake tahowa dasu.
Amma dukkanin wannan abubuwa basu suka dami Uznu
ba, a yayin da cikin sauri ya shige wani ƙaton ɗaki na
bincike-bincike inda yana shiga ya turo ƙofa ya rufe,
tunda dama babu kowa acikin ɗakin. Sannan ya zaro
wani ɗan irin Ayrid na musamman daga aljihunsa ya
karanta wasu ɗalasimai, wanda nan take wannan Ayrid ya
fara ƙara girma yana girma har saida ya kai girman ƴar
ƙaramar ƙofa, inda nan take wannan irin Ayrid yai aman
Armad ta cikin wannan ƙofa.
Uznu ya fizgi Armad ya kwantar dashi akan wani ƙaton
taburi na aiki. Sannan kuma ya fara karanta wasu
ɗalasimai wanda suka saka wani farin haske ya fara cika
ɗakin.
Nan take wasu Rauhanan aljanu guda biyu, ɗaya mai
ƙaho ɗaya mara ƙaho, suka bayyana, suna bayyana suka
zube a gaban Uznu, kana gani kasan alaƙar dake
tsakaninsu bata wuce ta bawa da ubangidansa ba.
Uznu ya amsa sannan ya fito da wasu fararen takardu
daga aljihunsa guda biyu ya miƙa musu. Sannan ya fara
jawabi da cewa, "Kunga wannan shi ne karo na biyu da
muka shigo da Littafin takobi wannan ɗaki acikin shekaru
ɗari da suka wuce, saboda haka haka ina fata zamu
kiyaye duk abubuwanda suka sa a wancan lokaci bamuyi
nasara ba."
Ya kalli aljanin mai ƙaho daga cikin guda biyun yace,
"Kalkutu kasan mai zakai."
Sannan ya juya izuwa mara ƙahon, "Kaima Netti kasan
meye aikinka."
Uznu ya ci gaba da bayani a yayinda wannan aljanu biyu
suka nutsu suna saurare, "A bisa bincike na na gano cewa
Littafin-takobi yana da rai yana kuma da hankali nasa na
kansa. Kawai dai ba irin yadda mutane da aljanu suke ba.
Kuma ta hakan nema na gano cewa indai akwai ma'aboci
Ururu a waje to Littafin-takobi bazai taɓa baƴyana kansa
ba. Kuma hakan ba abin mamaki bane tunda shi wanda
ya samarda Littafin takobin ɗan adawar gidan mune na
Ururu.
"Saboda haka a lokacin da za'ai wannan aiki dole ne ya
zamanto bana kusa da wannan yaro, in ba haka ba
wannan Littafi bazai taɓa bayyana kansa ba.
"Sannan kuma a wani binciken da muka gudanar a
jami'ar Nimibiya mun gano cewa wannan Littafin ya zaɓi
ƴan zuri'ar Wilbafos har a karo biyar daga cikin karo
bakwai da ya taɓa zaɓar wani. Kuma shima wannan
yaron daya zaba ɗan zuri'ar wilbafos ɗinne. Amma
babban abinda zaku riƙe ku kiyaye shi ne, Littafin-takobi
yana bayyana ya taimaki waɗanda ya zaɓa. Saboda haka
hanya ɗaya da zamu tabbatar ya bayyana shi ne mu
tabbatar da cewa mun azabtar da wannan yaro ta
kowacce hanya ƙololuwar azabatarwa tayadda Littafin zai
fito da kansa ya taimakeshi. Da zarar ya fito kunsan
abinda zaku yi na gaba, saboda haka ku fara aiki.
"Zan shiga shalkwata na fara shirye-shiryen sarrafa
wannan Littafi tayadda kuna zaƙulo shi kawai aiki zamu
fara akansa. A tafiya ta zuwa doron ƙasa ta farko na samu
dama na tattautana da Babban ɗan sarki Kuyurussa'ayi,
yarima mai jiran gado Níwajítu Dúmaƙísu Kuyurussa'ayi.
Kuma ya bada koyon bayansa ɗari bisa ɗari akan abinda
muke niyyar yi da wannan Littafi. Saboda haka lallai sai
mun tabbata munyi nasara a wannan karan."
Bayan Uznu ya tabbatar da cewa aljani kalkutu da Netti
sun fuskanci halinda ake ciki sai ya fita ya barsu domin su
fara aiki akan Armad.
________
A can wani sashin duniya dake ɓangaren Ikwatora na
doron ƙasa ta shida kuwa wata mace ce kwatsam ta
bayyana cikin jini kuma a sume. Lallai kana ganinta zaka
san gab take da mutuwa, kuma lallai idan ba'ai wani abu
akanta ba, to babu makawa mutuwa zatai. A tsakiyar inda
wannan mace ta bayyana kamar wata daula ce ta Dordor
launi-launi. Domin kuwa duk inda ka duba su zaka gani.
Babu gida gaba babu gida baya a wannan daji da take,
babu kuma abinda kake ji sai kukan tsuntsaye da
maganganun jinsin halittar nan da ake kira da Dordor.
To kamar masifar da wannan mata take ciki bata isa ba,
sai kurum wasu daga cikin Dordor dake wajen suka
hange ta. Ai kuwa nan take manyansu suka fara isa wajen.
Amma bisa mamaki kowanne Dordor idan yazo ya
shanshana wannan mace sai kawai yai tsaki ya juya kai ya
tafi. Kuma dukkanin waɗannan dordor da suke zuwa
kanta suna da kai sama da biyar. Kuma kowannensu fatar
jikinsa nada launi na daban. Babu kuma wanda keda Izza
ƙasa da ɗari biyar acikinsu. Lallai koda wannan mace na
cikin hayyacinta bata ishe su kallo ba.
To abu ne dai sananne a duniya cewa Dordor mai kai
biyar zuwa sama shi ake cewa Babban Dordor, sannan
kuma babban Dordor baya cin naman halittar da Izzarta
bata kai ɗari biyar ba. Saboda haka dai ga dukkan alamu
wannan mace ta taki sa'a.
Sai dai kuma ana haka bayan waɗannan manyan Dordor
masu kayika da yawa sun bar kanta sai ga wani Dordor
nan mai kai biyu ya gabato, yana tafiya a hankali kana
ganinsa kasan a yunwace yake. Tun daga nesa ya hangi
wannan mace ya kuma fara murmushi da kansa na
dama, sannan kuma yana dariya da waƙa da kansa na
ɓangaren hagu.
*Abinci ya samu
Yau yau abinci ya samu
Abinci har da kalace
Abinci ya samu
Abinci ya samu*
Haka dai wannan aljani ya wanzu yana gudu-gudu sauri-
sauri yana waƙa har ya isa inda wannan mace ke kwance.
Abune sananne ansan cewa jinsin fararen Dordor sha'irai
ne ma'abota waƙa, kuma sukan rera waƙa musamman a
lokacin da suka samu abinci.
Hakan nema yasa waƙa taƙi ƙarewa a bakin wannan Farin
Dordor wanda kaf komai a jikinsa fari ne fat tun daga
gashin kansa har zuwa fatar tafin ƙafarsa.
Dordon ya miƙa farin hannunsa wanda yafi farar-ƙasa
fari ya juyo da fuskar wannan mace. Sannan ya zaro wata
ƴar ƙaramar wuƙa daga aljihunsa da niyyar ya fara
yankar naman wannan mace yana kaiwa bakinsa-na-
waƙa. Amma kafin ya fara komai ya ɗaga hannu ya fara
da addu'a, "Godiya ga ubangijin daya jefowa da farin
Dordor naman bil-adama. Muna fata gobe ma a bamu!
Ameen!" Wannan Dordor ya shafa wannan addu'a
sannan yai azama wajen fara yankan naman jikin wannan
mace.
Idan ka kalli fuskar wannan mace zaka ga ba wata bace
illa Nusi ƙawar Armad wilbafos, wadda kwamanda Uznu
Ururu yai cilli da ita aka nemeta aka rasa tsahon lokaci.
Nidinne dai Shuraih Usman inkiya
99%
Daga taskar magajin wilbafos
MAGAJIN WILBAFOS
Marubuci: Dr Abdullahi Muhammad Ibrahim
Babi na 53: Bakar guguwa
Post by: Shuraih Usman
@shuraih 99%
www.facebook.com/hausaebooks
.
Daga:- Taskar Magajin Wilbafos
___
A kowanne yanki na Ikwatora dake kowacce ɗaya daga
cikin ƙasashe bakwai na duniya, akwai wani tsibiri wanda
shi ne waje da ma'abota wannan yankin suke gani a
matsayin tsarkakakken waje. Wannan tsibiri shi ake cewa
Tsibirin-guguwa.
A duk bayan kowacce shekara sittin wata guguwa mai
ƙarfin gaske na tasowa daga Tsibiri. Wannan guguwa ita
ake kira da Baƙar guguwa. Duk lokacin da aka fara ta
akanyi watanni kamar biyar ana yinta, kuma anyi ittafaƙi
wannan iska tana da ƙarfin da zata iya tarwatsa duwatsu
da ƙarafa da al'amudai komai girmansu.
Amma acikin wannan guguwa ake fitarda shugaban da
zaiyi mulki a kowanne shashi na ikwatora a shekaru sittin
masu zuwa. Hanyar kuwa mai sauƙi ce, duk wanda yake
so ya tsaya takarar wannan kujera saiya fito ya kuma
tsaya a tsakiyar wannan guguwa har tsahon wannan
watanni biyar, indai aka kammala iskar duk wanda yai
ragowa shi ne zai zama shugaba a wannan sashi na
Ikwatora har tsahon wasu shekaru sittin masu zuwa.
To amma mulki dai bashi kaɗai ne abinda ake muradi ba
a shiga cikin wannan guguwa ba. Babban abinda ake
muradi shi ne sadakar baiwa da ake acikin wannan iska.
Babu wata irin baiwa a duniya ko kuma wani sihiri ko
kuma wata fasaha wadda baza a iya tsinta ba acikin
wannan iska ba. Sabida haka nema wasu sukan siyar da
ransu su shiga duk da kuwa sunsan cewa ƙarfin Izzarsu
bai kaiba, amma saboda kwaɗayin wannan baiwa da ake
samu.
To wannan dai shi ne kaɗan daga cikin Tarihin wannan
sashi na Ikwatora inda a dai-dai wannan lokaci Nusi take
kwance rai a hannun ALLAH tana jira Dordor mai kai biyu
yayi layya da namanta.
Sai dai kuma kash, lallai naman Nusi yafi ƙarfin wannan
Dordor, domin kuwa a dai-dai wannan lokaci ne aka fara
busa wata sarewa wadda duk wanda ya rayu a sashin
Ikwatora yasanta. Sarewar da take nuni da cewa lokaci
yayi. Wato shekaru sittin sun kewayo kenan.
Ai kuwa wannan busa tana isa kunnen wannan Dordor
yai tsalle gami da cilli da wuƙar dake hannunsa, sannan
ya taka a guje. Bawai shi kaɗai bama, duk wani Dordor
dake wajen babu abinda yake face gudu izuwa maɓoya.
Tunda dama a wannan lokaci tuni lissafi ya cika, kuma a
kowanne lokaci ana jira ne kawai aga baiyanar wannan
guguwa. Hakan nema yasa a lokacinda Nusi ta bayyana ta
iske manyan Dordor suna tsaye cirko-cirko a wannan
waje.
Ba jimawa da fara wannan busa sarkin dake mulki a
wannan lokaci wanda ya kasance Dordor ne mai kai tara
ya bayyana sanye cikin kayan yaƙi. Kowanne ɗaya daga
cikin kayikansa tara yasha kwalliya ta kayan yaƙi. Lallai
kana ganinsa kasan ya shirya saiya koma kan wannan
mulki. Izzaraa kaɗai shekaru dubu bakwai da tamanin ce.
Sannan kuma fatar jikinsa da komai na jikinsa Ja ne.
Sai dai kuma amma bawai shi kaɗai bane, akwai sauran
zaratan tsofaffin Dordor da mutane ma'abota Izza wanda
suma suke neman wannan muƙami da kuma baiwa da
za'a raba a cikin wannan baƙar guguwa.
Babu wanda yake cikin filin nan wanda Izzarsa bata kai
dubu biyar ba acikinsu, sannan kuma babu wanda baiyi
shekaru samada da hamsin yana shirin wannan rana ba
sai mutun ɗaya. Wato Nusi kenan.
Ba jimawa gari yai duhu, ko tafin hannu ba'a gani, sannan
kuma daga bisani Baƙar guguwa ta fara sauka. Sadaukai
suka fara fitowa da shirye-shiryensu da suka tanada.
_______
Babu wanda yasan taƙamaimai maike faruwa acikin
wannan baƙar guguwa, domin a duk bayan shekaru sittin
mutun ɗaya ne kaɗai yake samun nasara, shi kuma tarihi
yazo cewa indai ya bayyana abubuwan da suka faru aciki
to duk wata baiwa daya samu zai nemeta ya rasa.
Hakan yasa sai dai kawai ka samu shaɗi faɗi, amma
taƙamaimai babu wanda yasan maike faruwa.
To haka dai wannan iska taci gaba da wanzuwa tsahon
lokaci, wata ɗai-ɗai har wata biyar. Sannan daga bisani ta
fara lafawa. Inda alƙalan kowanne yanki suka fara fitowa
domin suga wane ne sabon sarkinsu.
Saida aka ɗauki wasu kwananki ukun cir, sannan komai
ya lafa gari yai haske. Alƙalai suka gabato cikin filin da aka
gudanar da wannan gasa. Amma bisa mamaki maimakon
su tararda sarki sai suka tararda da sarauniya.
Wata mace ce mai kyawun sura baƙar fata. Tsaye take
riƙe da kambun nasara wanda duk wanda yaci nasara
yake samu. Babu alamun ciwo ko rauni a tattare da ita.
Kana ganinta kasan ta cika jaruma irin ta mutanen farko.
Idanunta suna fitarda farin hasken mai ɗauke da Izza
abar girmamawa. Abin aljabi wata ƴar ƙaramar tukunyar
dinare ce a hannunta na dama, sannan kuma a hannunta
na hagu wata ƴar ƙaramar bishiya ce mai yawan koren
ganye.
Amma da dama zasu fi yadda dani idan nace babban abin
mamakin shi ne wannan sarauniya ba wata bace illa Nusi.
Wannan alƙalai suna ganinta suka zube a ƙasa cikin
gaisuwa da biyayya.
To wannan dai shi ne abinda ya kasance da Nusi bayan
rabuwarsu da abokinta Armad wilbafos.
____
A can cikin fadar Ururu kuwa yau ankai wata biyar kenan
aljani Kalkuta da aljani Netti suna azabtar da Armad duk
domin Littafin takobi, amma babu labari. Tuni hankalin
Arnad ya gushe yafi sau ɗari yana dawowa. Amma a
kowanne lokaci sai dai aljanun su ƙara ƙarfin azabar da
suke yi masa.
Tuni Armad yaci alwashin kashe wannan aljanu guda biyu
da danginsu da kuma Uznu Ururu. Yayi kuma alƙawarin
lallai bazai mutu ba saiya ɗau fansar abinda sukai masa.
Idan kuwa a sakamakon tsare shi da sukai anan babarsa
ta mutu, to lallai saiya kashe duk wani ma'aboci Ururu
sannan zai huce.
Ana cikin haka ne Armad yaga watarana wannan aljanu
guda biyu sun shigo wannan ɗaki. Suna zuwa suka ɗaure
shi, sannan suka rufe masa fuska suka fice dashi daga
cikin wannan ɗaki sannan suka ɓace sukai yamma.
___
To ko ina suka tafi da Armad?
Nidinne dai Shuraih Usman inkiya
99%
Daga taskar magajin wilbafos
MAGAJIN WILBAFOS
Marubuci: Dr Abdullahi Muhammad Ibrahim
Babi na 54: Cinikin Bayi
Post by: Shuraih Usman
@shuraih 99%
www.facebook.com/hausaebooks
.
Daga:- Taskar Magajin Wilbafos
Aljani Kalkútu da aljani Netti na keta hazo suna tattauna
al'amuran da suka shafi wannan yaro mai suna Armad da
suke azabtarwa.
Aljani Netti dai shi yake magana a wannan lokaci, "Babu
abinda ba muyiwa wannan yaro ba amma littafin takobi
yaƙi fitowa. Yau wata biyar kenan, indai abu sunansa
azaba a duniya to munyi masa shi, amma babu labari. Ni
ina ganin shawarar da shugaba Uznu ya bayar tayi dai-dai
amma kai naga hankalinka bai kwanta ba."
Kalkutu yai kyaran murya gami da kallon Armad wanda
ke ɗaure a bayansa ya ce, "Eh.... Haka ne, amma kana
ganin siyar dashi a matsayin bawa shi ne zaisa Littafin-
takobi ya fito. Kada ka manta da irin azabar da muka
gana masa. Ai ina ganin azabar da mukai masa tafi azabar
siyarwa a matsayin bawa."
Netti ya gurgiza kai tare da cewa, "Eh da wannan dan
wannan, amma koma dai mene ne yadda aka umarce mu
haka zamu yi. Zamu je mu siyar dashi a matsayin bawa ga
ɗaya daga cikin sarakunan Jinzidal ɗinnan. Sannan kuma
zamu ci gaba saka ido a kansa har illa mashaALLAH, har
sai sanda Littafin ya fito. Wataƙila idan yaji azabar bauta
Littafin ya bayyana."
Haka dai suka ci gaba da tattauna yadda suke shirin
siyarda Armad a matsayin bawa.
____
Ranar sha tara ga watan goma na kowacce shekara, ita ce
ranar da aka tana da domin yin gagarumin taron da za'a
gabatar da dukkan bayin da aka samo ta hanyar gasar
Jinzidal. Duk wani mai iko yazo ya siyi abinda yake so.
To kamar dai yadda aka sani sarakunan Jinzidal guda
biyar sune suke gudanar da wannan ciniki, kuma sukan
rarraba wajen gudanarda wannan gasa a kowacce
shekara a tsakaninsu. Idan wannan shekara a ƙasar
wannan sarkin akai, wata shekarar sai aje ƙasar wani
sarkin. To a wannan shekara a ƙasar sarki Rafiya ake
wannan taro.
Sarki Rafiya ɗaya ne daga cikin sarakuna biyar na Jinzidal,
kuma yana da iko akan miliyoyin mutane da kuma
ɗaruruwan ƙasashe.
Wajen da aka
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment