Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

RANA DA WATA
Littafi na biyu 2
Na abdulaziz sani madakin gini
Typing:- Shuraih Usman
Post:- Shuraih 99%
Part A
.
.
Lokacin da su tsohuwa shafhila suka shafe rabin sa'a suna tafiya a wannan daji mai dauke da mugayen maridai masu cin bil'adama, sai suka zo wucewa ta gaban wata katuwar tukunya wadda aka girke ta da wasu manyan itatuwan wuta suna ci ganga-ganga
.
Yayin da suka ga haka sai sabitul agadawur yayi masu nuni da hannunsa alamar kowa yayi shiri da barin yin wani motsi
.
Tsohuwa shafhila tana ganin wannan katuwar tukunya,sai hantar cikinta ta kada, sai ta koma tsakiyar wannan ayari, tana mai tsananin lura da sauraren dukkanin wani motsi dake tashi a wannan lokaci
.
Ahaka har suka shafe rabin sa'a suna tafiya batare da sun hadu da wani abu na cutarwa ba,
Kwatsam ba zati ba tsammani sai suka ga wadansu maridai masu tsananin yawan gaske sun tare masu hanya ba damar wucewa
.
Su dai wadannan maridai sun Shuraih Usman inkiya Shuraih 99% kasance dogayene suna da tsawo wanda ya kai kamu arba'in, idan mutum ya tsaya a gabansu sai kaga kamar wani tsauni ne a gabanka
.
Koda su tsohuwa shafhila suka ga wadannan maridai, sai wani wanda yafi kowa tsoro acikinsu ya kurma wani uban ihu da dukkanin karfinsa saboda tsabar kidimewa da razana da yayi sa'adda yaga wadannan maridai
.
Lokacin da wannan matsoracin yayi wannan ihu, sai gaba dayan wadannan maridai suka juyo tare da barin wawason da suke akan wadansu mutane shida da suka kamo, suna juyawa ai kuwa sukayi arba da ayarin su tsohuwa shafhila
.
Take sai wani maridi dake kusa da wannan mai tsoron yai saurin sa hannunsa mai kamar shafcecen shebur ya dauke shi ya jefa abaki yana taunawa,
.
Sa'adda maridin ya dauki she, sai ya kasance kamar ya dauki wwani dan karamin tsuntsu ne, al'amarin daya dugunzuma su tsohuwa shafhila da su sabitul agadawur kenan.
Ai nima shuraih Shuraih 99% sai da na tsorata ainun
.
Suka kidime kowannnensu jikinsu ya kama karkarwa maridin daya jefa matsoracin nan abakinsa ya taune, ya hangame baki yana wata irin hamma wadda ta haddasa wata guguwa ta bayyana mai karfi tana daukar duk abinda ba shi da kwakkwaran nauyi
.
Sannan yace da wata irin murya mai kamar rugugin hadari,
"Hakika wadannan mutane sunfi duk wadanda muke kamawa zakin nama,saboda haka mutafi dasu a kowacce rana mu ringa karyawa da su har su kare"
.
Lokacin da su tsohuwa shafhila suka ji haka, sai gaba danysu hankalinsu ya tashi, nan take sai manyan sadaukai da jaruman dake tare da su, suka zaare takobi da niyyar su afkawa wadannan maridai ayi ta takare
.
Koda ganin haka sai daya daga cikin maridan ya bushe da dariya yana mai tsuntsirewa akas, sannan yasa hannu ya rarumi mutum goma daga wadannan Shuraih Usman inkiya Shuraih 99% sadaukai da jarumai yai wurgi da su, bisa ga dole kowa ya nutsu aka daina samun masu taurin kai a cikinsu
.
Batare da bata wani dogon lokaci ba sai wadannan maridai suka tasa keyar ayarin su sabitul agadawur zuwa wani katon kogon dutse wanda dama anan ne suke aje duk wanda suka kamo
.
A lokacin da aka kaisu wannan wuri sai suka iske wadansu jarumai majiya karfi su hudu a daddaure da wata katuwar igiya wanda sai mutum dari su hadu ba tare da sun iya koda tsinka rabin ta ba
.
Maridan suka kebe ayarin su tsohuwa shafhila daban ba tare da sun hada su da wayannan zaratan jarumai ba , sannan suka mirgino wani katoton dutse suka toshe hanyar da ake shigowa wannan katon kogo
.
A wannan lokaci ne nadama da dana sanin wannan tafiya tazo wa gaba daya ayarin, tsohuwa shafhila tafi kowa razana da kasancewar wannan lamari, take ta tuna Shuraih Usman Shuraih 99% mai typing yayanta wadanda suke tsananin gaba da junansu wadanda saboda ta samu hadin kansu ne ta sayar da dukkanin kadarorinta ta taho da niyyar ta sama masu hanyar da zasu san cewa sufa yan uwa ne na jini
.
Kuma su hada kansu wuri daya ba tare da sun kara nuna tsana da matsananciyar gabar dake tsakaninsu ba
.
Kashe gari da safe sai ga wadannan maridai sun shigo , suka debi mutun dari daga yarinsu tsohuwa shafhila zasu tafi dasu koda suka zo kan tsohuwa shafhila sai wani maridi ya kura mata ido yana kallonta
.
Al'amarin dayai matukar tayar mata da hankali kenan, batare da yace da ita komai ba sai kawai suka fita tare da wayannan mutane da suka deba a matsayin kalacin su na wannan safiya
.
Yayin da wadannan zaratan jarumai dake daure cikin igiyya , suka ga tashin hankalin da su tsohuwa shafhila suka shiga sakamakon zuwansu wannan waje da suka Shuraih Usman inkiya Shuraih 99% fidda rai da ci gaba da rayuwa, sai daya daga cikinsu wanda ake kira da suna zahakim yai magana da murya yadda duk wanda yake kogon dutsen zaiji ya fara da cewa
.
"Yaku wadannan mutane ku sani da zaku yadda da wata shawara da kuwa mu da kuu din nan mun kubuta daga sharrin wadannan maridai"
Yayin da tsohuwa shafhila da sabitul agadawur da sauran mutanen da ke tare da su , sai tsohuwa shafhila tayi saurin amsa masa tana mai cewa
.
"Me zai hana mubi ko wace irin shawara ka zo mana da ita koda kuwa hakan daidai yake da halakarmu gaba daya, kasancewar zamanmu a cikin kogon dutsen nan shima halakane"
.
Koda zahakim yaji wannan bayanni daga bakin tsohuwa shafhila sai yayi murmushin karfin hali yace da ita, Shuraih Usman inkiya Shuraih 99%
.
"Mu hudunnan da kuke gani yau kwananmu tara a cikin wannan kogon dutse, kuma wadannan maridai sun kasa cinyemu ne saboda dalili daya, nalura akwai wani maridi daga cikin su wanda yana da matukar tausayi da jinkai, baya sin ganin ana halaka mata ko kadan, atakaice ma zai iya bujirewa sauran maridan ya yakesu idan suka dage akan cewa lallai sai an halaka mata a wannan kogon dutse
.
A gaban idonmu yazo ya kubutar da wasu mata dake tare damu a lokacin da aka kamamu, kasancewar wannan dabi'a ta wannan maridi, ina mai tabbatar maku da cewa lallai zai dawo garemu ayau dinnan da dare, saboda wannan tsohuwar da kuke tare da ita
.
Sai ku kwance mu tun yanzu domin da zarar ya shigi muyi masa kwab daya mu halakashi, sannan mu tsre kafin gari ya waye munyi masu nisan da ba zasu taba cimmana ba"
.
Koda zahakim yazo nan a zancensa Shuraih Usman inkiya Shuraih 99% sai gaba daya suka amince da wannan shawara tasa , sai kuwa suka taru gaba dayansu kowannensu ya zare takobin da ke tare dashi, suka kama aikin yankan wannan katuwar igiya da aka daure wadannan zaratan jarumai
.
Sai da suka shafe fiye da sa'a biyar sannnan suka smau nasarar tsinke duk igiyar da aka daure su, take kowannensu ya mike tsaye sukayi wata doguwar mika, zahakim kasancewarsa musulmi sai yai godiya ga Allah daya kubutar da shi daga wannan dauri, ya kuma rokon ubangijinsa daya kubutar da shi daga sharrin wayannan maridai masu cin naman mutane
.
Haka kuwa akayi bayan dare ya raba sai ga wannan maridi ya mirgino wannan katon dutse da aka rufe kofar shigowa kogon ya shigo ciki, sannan ya maida ya rufe yana yan dube dube,
.
Adai dai wannan lokacin zahakim da sauran jaruman dake Shuraih Usman inkiya Shuraih 99% tare dashi, suka zare takobins dake tare da su suka yunkura da tsananin shammata, kafin wannan maridin ya ankara , sai kawai yaji sun kai masa sara da dukkan karfinsu
.
Take sai zahakim da wadannan jarumai sukaji kamar sun sari karfe , su duk suka zube a kas, wannan mariidi yasa hannu ya dauko tsohuwa shafhila daga inda take, sannan ya zahakim da bille can gefe daya
.
"Nazo a gareku ne ba da niyyar na cutar da daya daga cikinku ba, ku sani daga yau zan kauracewa wannan daji da muke ciki, na rantse da iyayena babu abinda zai same ku muddin kuna tare dani, sai na kubutar da ku bazan bari daya daga cikin yan uwana su samu sa'ar sake kamaku ba
.
Hakika maridan nan yan uwana sun cutar dani saboda sun kashe matata dana fi so aduniya fuye da komai,
Akan wannan daliline na daura damarar kubutar da duk wata mace kasancewata ina mai tsananin Shurraih Usman inkiya Shuraih 99% tausayawa rayuwar mata , kuma zan taimaka maku sai inda karfina ya kare " yayin da su tsohuwa shafhila dasu jarumi zahakim suka ji wannan batu, sai wani farin ciki mara adadi ya lullubesu, nan take gaba dayansu kowa yasa ran zai samu biyan bukatar abinda ya fito nema
.
Daga nan babu wanda ya kara cewa komai sai kawai wannan maridi ya ture wannan mulmulallen dutse da ake rufe kogon
Sannan ya fara fita daga bayansa tsohuwa shafhila ta biyo bayansa,
Sannan gaba dayan sauran mutanen da suka rage suaka bi bayansu zuwa waje suna masu tsananin lura da kowane motsi da ke tashi a wannan waje
.
. *** .
Lokacin da huzainu ya tabbatar da muddin yayi sake tofa wannan runduna ta sadaukai masu siffa irinta zuhaisa zasu iya gamawa da shi farat daya, sai ya fusata da fushi irin wanda bai taba yin irinshi ba take Shuraih Usman inkiya Shuraih 99% duk wani gashin jikinsa ya mimmike, dantsensa suka dada kumbura kamar zasu fashe, yai wata kururwa da tsananin karfin muryarsa, wadda gaba dayan dajin ya girgiza da amsa amon wannan kururuwa ta sa
.
Sannan huzaini ya sake daidata rikon takobinsa yaci gaba da saransu babu ji babu gani, aduk lokacin daya yunkura ya sari daya daga cikin sadaukan , sai dai kawai kaga ya tsarge ta gida biyu,
.
Dada yawaita suke da zarar ya kashe su, haka nan ma sadaukan masu siffa irinta zuhaisa dada karuwa suke fiyeda farko
.
Da zabbabu yaga abin ya nemi yafi karfinsa, sai ya kasance aduk lokacin daya yunkura yasa takobi dakai sara a tsakiyar sadaukan, sai yayi kalmar shahada tare da kai saran a tare
.
Sai ya kasance duk wadda ya sara bata da wowa, haka nan kuma babu wadda zata tashi ballantana ma su dada yawaita awannan lokacin
Kai nafa gaji da typing, amma dai barin dan kara jajircewa Shuraih Usman Shuraih 99%
.
Koda zabbabu ya fahimci haka sai ya dada zage dantse yana mai kai sara a kowane yanayi cikin kwarin guiwa da jarumta , cikin wani dan kankanin lokaci,
.
Sai daya kasance zabbabu ya samu nasarar kashe da yawa daga cikinsu sa'adda huzainu yaga irin yadda zabbabu yake kashe su, yana karanta wata magana da ambata wata kalma da baya fahimtar komai yake fada, da tafiya tayi tafiya sai huzainu ya rika ambatar kalmar da yaji zabbabu yana ambatawa a lokacin da yake kai sara ga wannan sadaukai masu siffar zuhaisa
.
Ai kuwa sai yaga shima yana samun nasarar tsargesu suna kamawa da wuta su kone kurmus su zama turbaya ba tare da wata ta samu sa'ar tashi ba
.
Huzainu da zabbabu suka kasance suna masu tsananin kai sara da suka cikin zafin nama da sadaukantaka, bayan dakika dari biyu da hamsin, sai ga shi huzainu da zabbabu sun samu nasarar kashe gaba Shuraih Usman inkiya Shuraih 99% dayan sadaukan babu wanda ya tsira daga cikinsu
.
Zabbabu ya dubi huzainu yana mai murmushi, kafin daya daga cikinsu ya damar cewa daya komai, sai kawai sukaji an kyalkyale da dariya, take huzainu ya gane muryarta, zuhaisa ce nan take ta bayyana a gabansa tana mai nuna sa da yatsa
.
"Kada kayi tsammanin ka samu nasara ka gama da wadannan sadaukai dana hada ka da su kayi zaton cewa ka rinjaye ne, wannan ya kasance shine mataki na daya daka haye daga cikin matakai miliyan dubu dana dauka a kanka
.
Ina mai rantsuwa da darajar iyayena, a karo na gaba ba zaka samu nasarar tsallake matakin da zan dana maka ba koda zaka hada kai da duk jaruman duniya gaba dayansu"
.
Yayin da zuhaisa tazo nan a zancenta, sai kawai ta bace ba tare da saurari wani lafazi daga dan uwanta huzainu ba,
.
.
Yo anan zan tsaya Daga naku Shuraih Usman inkiya Shuraih 99%
Mamallakin shafin hausaebooks
Da keffians News Teller
Sai mun hadu a part 2RANA DA WATA
Littafi na biyu 2
Na abdulaziz sani madakin gini
Typing:- Shuraih Usman
Post:- Shuraih 99%
Part B
.
.
Lokacin da zuhaisa ta bace sai zabbabu ya dubi huzainu yace dashi,
"Yakai jarumi huzainu hakika ba karamar kiyayya ke tsakaninka da wannan yar uwa taka ba , kasancewar naga tana neman halakaka ta kowwace hanya .
.
Ina mai kyautata zaton ta hada kai da manyan bokaye hatsabiban gaske, saboda haka nake shawartarka daka biyoni izuwa kasata wadda can na tabbata zuhaisa bata da ikon shigowa har can da niyyar ta cutar da kai"
.
Koda huzainu yaji haka sai yace da zabbabu
"Yakai zabbabu ka sani bana shakka kojin tsoron duk irin makircin da zuhaisa zata shirya mani, ka sani zuhaisa ta kasance tun muna yara kanana bama ga maciji da ita, har izuwa lokacin da kowannenmu karfi yazo masa daga nan kuma sai muka shiga farautar juna da son hallaka juna
.
Hakika zuhaisa ta kasance azzaluma mara tausayi Shuraih Usman inkiya Shuraih 99% ko kadan wannan shine dalilin daya sa ba ma shiri da ita sam, saboda na zamo mutum mai sanyin rai da taimako ga mutane mara gata a kasarmu, hatta mahaifiyarmu bata jin dadin irin wannan matsananciyar gaba dake tsakaninmu, amma na daukarwa kaina alkawarin duk lokacin da zuhaisa ta sake zuwa gare ni a bisa mummunar aniyarta a kaina , sai na halaka ta ba zan taba bari taci gaba da rayuwa ba muddin tana nan kan bakarta"
.
Daga nan suka kama tafiya cikin daji zabbabu yana mai yiwa huzainu jagora har suka dauki hanyar da zata sada su kasar gayyar inda a yanzu zabbabu yake sarauta
.
. *** .
Dawwara yana tafe kan wani ingarman doki yana mai tsananin tsala gudu kamar zai tashi sama , baya saurarawa komai a wannan muhimmiyar tafiya tasa,
.
Tun bayan da boka gayyar yaga ma shiryasa ya ba shi wata alkyabba ta tsafi yasa sannan SHurarih Usman inkiya Shuraih 99% ya bashi wasu guraye ya daura su a dantsensa, sannan ya kama tafiya baji babu gani wanda ayanzu ya shafe kwanaki arba'in yana tafiya batare daya hadu da wani mugun abu ba kan hanyarsa
.
Dawwara ya daukarwa kansa alkawarin cewa duk rintsi da tsanani ba zasu taba hana shi yaje kogon darul yamzin ba, don dauko wannan hatsabibin zoben zinari da boka gayyar ya labarta masa ba
.
Lokacin dawwara ya fahimci yabar nahiyar kasarsu ya shiga wani yanki daban inda babu yadda za'ayi a samu wanda ya sanshi
Dawwara yana cikin tafiya akan hanyarsa sai yazo wucewa ta wata kasa mai girman gaske, take dawwara ya kayatu da wannan kasa nan da nan ya ayyana a ransa cewa bari ya shiga wannan kasa ya yada zango kafin wayewar gari ya dan huta yaci gaba da tafiyarsa,
.
Lokacin da dawwara ya shiga wannan kasa sai ya tarar dukkanin mutanen kasar sun taru a wani Shuraih Usman inkiya Shuraih 99% katon fili daka shata layi, sarki zaftalaru ibini barbushe, yana zaune akan karagarsa ta mulki yana kallon duk abinda yake faruwa a wannan fili
.
Wasu karti ne majiya karfin dantse da murdewar jiki, wani kato daga cikinsu zai tsaya ya mike hannayensa sama , sannan sai wasu karti su ashirin suyi ta dukansa ta dukansa tsawon rabin sa'a batare da yayi koda gezau ba, sannan sarji zaftalarutu ya sa abashi dukiya nai tsananin yawan gaske ya koma gefe daya
.
Lokacin da dawwara yazo wannan waje sai masu gadi suka tare shi suka hana shi ya karasa wannan fili daa wadannan karti suke tada gwanjinsu ana basu dukiya mai tarin yawa, yayin da dawwara yaga haka sai ya fusata matuka, take ya sa dokinsa ya rika banke dakarun yana kusantar wannan fili,
.
Dawwara bai tsayay ba sai da kure a tsakiyar filin saboda karfin dokinsa daya Shuraih Usman inkiya Shuraih 99% sakarwa linzami batare daya bukaci ya tsaya
.
Sarki zaftalarutu yaji hayaniya ta yawaita sai ya hango dawwara yana ta aikin bangaje masa dakaru , al'amarin daya fusata shi kenan, sai ya bada umarnin cewa a tsaya da wannan gasa ta fada da ake gabatarwa ya daka wa dawwara tsawa ya ce dashi
.
"Yakai wannan mahayi, daga ina ka ke kuma me ya kawoka cikin birni na da har kake bangake mini dakaru alhalin sun haka shigowa inda ake wannan gasa ta fada tsakanin karti majiya majiya karfi ga shi kuma ka kasance baka da siffa irinta jarumai ma'abota karfin damtse"
.
Sa'adda sarki zaftalarutu yazo nan a zancensa sai dawwara ya gyara zamansa akan doki hankalinsa a kwance yafara magana cikin takama da jin cewa shi wani ne
.
"Banzo wannan kasa taka da niyar nayi musayar kalamai da kai ba yakai Shuraih Usman inkiya Shuraih 99% sarki ma'abocin zafin rai da shisshigi" yayinda dawarra yazo nan a zancensa sai kawai yaga wadannan karata majiya karfi sunyi masa kawanya kowannensu yana ta dukan kirjinsa suna tada kwanjinsu sarki zaftalarutu ya kyalkyale da dariya sannan ya dubi dawwara yace dashi
.
"Tunda tsautsayi da karar kwana suka sa ka shigo wannan fili batare da an umarceka ba sai kayi fada da wadannan karata idan kayi nasara kansu shi kenan, izan kuwa ka kasa tabuka komai hakika yau sai dai uwarka ta haifi wani ba kaiba"
.
Sa'adda sarki zaftalarutu yazo nan a jawabinsa sai ya koma ya zauna akan karagarsa ta mulki ya harde kafafuwansa yana mai kallon yadda dawwara zai kare tsakaninsa da wadannan karata
.
Dawwara ya sauko daga kan dokinsa ya fuskance su yana mai nazarin wadannan karata da duk motsi na su, kamar an Shuraih Usman inkiya Shuraih 99% umarci wadannan karti sai su duka saukayi kukan kura da wani mai zafin zuciya dake kan gaba , ya fara dunkule hannu da niyyar ya zabtarewa dawwara baki ya zubda masa dukkan hakoransa,
.
Koda dawwara yaga tahowar wannan hannu zuwa kan fuskarsa sai ya bari sai da hannunsa ya tsakumi wannan kato yai hajijiya da shi ya watsar dashi wani ya sake taso masa shi ma yayi saurin tararsa tun kafin ya iso gareshi ya daga shi gaba dayansa sannan yai wurgi da shi
.
Cikin dakika dari sai gashi dawwara ya watsar da fite da rabin wadannan karti, batare da sun samu sa'ar koda zunguransa ba, al'amarin da ya matukar burge sarki zzaftalarutu kenan, yaga dawwara ya kasance bashi da siffa irinta sadaukai, amma gashi ya kasance yana mai watsar da karata majiya karfin damtse wadanda daya daga cikinsu ma baya kwatanta aikata wannan aiki da wannan bako yazo daga wata kasa Shuraih Usman inkiya Shuraih 99% ya aikata musu ba
.
Sai kawai sarki zaftarutu ya cika da tsananin mamakinn wannan lamari na dawwara nan take sai ya ga ai yanzu ne ya samu dama da zaiyi amfani da dawwar domin cikar burinsa da ya dade yana hada wannan gasa saboda dashi
.
Nan take sarki zaftarutu yai umarni ga dukkan mutanensa da dakarunsa cewa kowa yatafi abinsa wannan gasa ta kare kenan,
Dawwara ya cika da matukar al'ajabin faruwar wannan lamari, sai ya dubi sarki zaftalarutu da niyyar yayi magana
.
Sai sarki zaftalarutu ya daga masa hannu alamar su kebe akwai abunda zasu tattauna akansa, koda suka kebe sai sarki zaftalarutu ya sake duban dawwara dakyau yana mai sake nazarinsa ,
.
Lokaci da dawwara yaga irin wannan duba take sai ya aiyana aransa koda wannan sarki yayi niyyar ya cutar da shi, hakika sai yake shi ya kasheshi da gaba dayan jama'arsa
Toh nine dai Shuraih 99% ke typing umje zuwa wai .....
.
"Kasani yakai wannan bako mai girman sha'ani na dade ina hada wannan gasa daka tarar anayi anan kasar tawa ne saboda wata bukata ta dana dade daita a raina ban taba fadawa kowa ba, kuma ko su mutanen wannan kasa tawa basu san dalilin daya sa nake hada su fada da juna ba, wannan ni kadai ne na sani sai kuma kai yanzu da zan sanar dakai kasancewarka jarumi uban jaruman wannan kasa tawa
.
A cikin gidan sarauta ta akwai wani dogon daki da mahaifina yabar mani wanda tun mutuwarsa yabar wasiyya da gargadi agareni kan cewa kada na sake nace zan shiga wannan daki sai bayan mutuwarsa da shekaru goma
.
Hakika yau wata tara kenan da cikar shekaru gima da mutuwar mahaifina "sarki zaftalarutu ya gyara zamansa sannan yaci gaba da cewa
.
"Saboda haka nake so ka shiga wannan daki ka gano mani kome ne yake tsoratar dani aduk lookacin danayi yunkurin Shuraih Usman inkiya Shuraih 99% sannan sai acigaba da hajijiya dani ana bugani adukkan bangwayen dake wannan dogon daki har na ga kawai an watsoni waje a sume sai bayan wani dogon lokaci sannan na farfado
.
Yakai wammam jarumi ina mai neman hadin kanka daka shiga cikin wannan daki tare da gano min meye mahaifina ya aajiye acikin wannan daki da har ya gargadeni da kada na fadawa kowa da kuma kar na sake na shiga har sai bayan cikar shekara goma"
.
Yayinda sarki zaftalarutu yazo nan a zancensa sai dawwara yace dashi,
"Kabani dakika dari zanje nayi
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3

Please Login or Register in order to submit comment