Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

๏ปฟ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

โคโ€๐Ÿ”ฅ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จAUREN YARJEJENIYA๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จโคโ€๐Ÿ”ฅ

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

it's rometic love storyโคโ€๐Ÿ”ฅ๐Ÿ’”


Story & written by mommyn fareesa

*GODIYA* godiya ga Allah S W A tsira da Amincin Allah sutabbata ga shugabanmu Annabi mohd S A W"yah Allah yadda na fara wannan book lafiya yah Allah kasa na gamashi lafiya"Allah kabani ikon rubuta Abinda ke daidai kuma me Amfani๐Ÿคฒ

*GARGAD'I* wannan litttafi k'irkirarran labarine ban yishi dan wata ko waniba idan yayi kamanceceniya da rayuwar wata ko wani Arashi ne"aguji sauyashi ta kowace siga sbd hakk'in mallakata ne.

Dedicate to All my fans ๐Ÿ’–๐Ÿ’”

BISSIMILAHIR RAHAMANIR RAHIM

free page 1&2

kaduna state

*Rimi clinic*!.......Aguje wata had'add'iyar mota bak'a k'irar Lexus X750 tayi parking"yayinda wasu motocin guda biyu suma sukayi parking bayan bak'ar motar"wanda Abayan kowace mota An rubuta *Amj big man*" motocin dake baya duk Aka bud'e , Atake wasu mutane su shidda duk suka fito suna sanye da bak'ak'en kaya Ajikinsu"k'atti ne majiya k'arfi"da Alama body guards ne"wani k'ato bak'i da bbu Alamar rahama Asaman fuskarsa yanufi gefen bak'ar motar me glass bak'i yabud'e back sit Aladabce"Atake wani ni'imtaccen mayen k'amshi me tsayawa Azuciya ya bayyana "kusan second 10 duk suna tsaye kafin wanda Aka b'udema motar yazuro dogayen santala santalan k'afafuwan sa waje"dake sanye da cover shoes coffee brown"cikin nutsuwa da izzah data zama halayyarsa ya ida fitowa dg cikin motar"ya had'e girar sama data k'asa bbu fara'a ko kad'an Asaman doguwar kyakykyawar fuskarsa"sanye yake da wondo coffee brown da milk d'in riga"yatsuke k'ugunsa da belt coffee brown..... *Abdallah mohd jibo kenan!* yong bolonia wanda Akemu lak'abi da BIG MAN" matashin saurayi me jini Ajika"kuma yaro d'an kwalisa......yatsina fuska yayi yana kallon Asibitin yashafa bak'ar sumar kansa dake salk'i sbd gyaran datake sha"kafin yadubi Agogon dake d'aure A damtsan hannunsa"k'arfe 10:12 am na safiyar yau talata"uffan becebe"yafara tafiyarsa cikin nutsuwa yanufi k'ofar shiga ciki"yayinda body guards nasa ke biye dashi"tun dg nesa mutane ke binsu da kallo kasancewar big man sananne ne Agun jama'a"dukda da yawan mutane na masa kallon me girman kai"kai tsaye room 11 yanufa"saidai yana isowa daidai bakin k'ofar shiga d'akin yayiwa body guards nasa Alama da hannu su jirashi karsu biyoshi ciki" dg haka yatura k'ofar room d'in yashiga"wasu nurses dake zaune nesa dasu suka bishi da kallo guda na fad'in "kai masha Allah! kamar shine ya hallaci kansa"duk wacce ta sami waccan guy d'in tagama sa'a Arayuwa"gudar tace"kedai bari Inda farine k'ilan za'a d'auka ba'indiye ne sbd kyau da cikar suman kansa.....big man besan ma suna yiba"cikin shan k'amshi yashigo d'akin yayi sallama tamkar bayaso"kamal na kwance samqn bed idonsa biyu And'aura masa drip"sai tj da junuid na zaune samqn fararen kujeru roba"suna ganin shigowar big man suka fara washe baki suna Amsa sallamar da yayi"wanda brown d'in lips nasa da sukaga sun motsa suka fahimci sallama yayi"junuid ne yatashi daga samqn kujerar dayake zaune yana cewa"Abokina ga gun zama ka zauna"saidai nasan daka san miye Ainahin musabbin ciwon kamal da baza kazo dubiya ba"yak'are maganar yana kallon big man"miskilin beyi mgn ba yadai bashi hannu sukayi musabuha yabama tj"sannan ya zauna kan farar kujerar yana danna waya......"Abokina barka da Asuba"cewar kamal"big man ya d'auki kusan second 5 kafin yadubesa" cikin k'asaitacciyar muryarsa me dad'in Amo da saurare yace"ya jikin naka?"Alhmdllh da sauk'i"zuwa Anjima zasu bani sallama"okay miye wai ke damun ka?"tj da junuid suka saki dariyar shakkiyanci Atare"big man yatab'e baki beyi mgn ba"kamal kuwa cikin kwantar da murya yace"pls Abokina my leemart na hanyar zuwa dubani"idan tazo yanzun karka mata tsawa ko kyaranta.....doguwar tsuka big man yaja ya mik'e tsaye ya aza doguwar k'afarsa guda samqn kujerar daya tashi"yana bin kamal da wani irin kallo cikin kausasa murya yace"ka bani mamaki kamal daka kwanta jinya sbd soyayya"Abin takaici kuma sbd wannan jaririyar yarinyar leemart"dg k'arshe kuma Ashe tanama sonka"yanzun bakaji kunyar kwantawa ciwo sbd wannan Abar y'ar cikinka ba??"na rasa me kuka d'auki soyayya ne"?yak'are maganar yana tab'e baki yayi shiru"tj dake murmushi yace"sbd kana yadda kakeso shiyasa baka san wahalar soba Abokina"yatsina fuska big man yayi yace"Allah yatsareni da nasan miye so"banida wannan lokacin na wahalar da kaina"kai kuma dakake cewar karna mata kaza da kaza"to tafiya zanyi yanzun"nazone dama na nuna maka nasan Abinda kake b'oyemun"saidai karka yarda muna tare dakai ka kulata"yada girmanku wajen k'ananun yara da sunan soyayya ku cigaba"ga manyan y'an mata masu hankali nan Amma ka tsaya sokonci wajen y'ar cikinka sbd jama kai raini"indama ka hak'ura zata nuna tana sonka koda baka furtaba"saika nuna zaka Amince da soyayyar ta sbd tana sonka..... yak'are maganar yana jan tsaki had'e da tab'e baki"kamal ya dubesa yana girgiza kansa yace"Hmm! Big man kenan"wacce kuke soyayya da ita sam baku dace da juna ba shiyasa bakasan miye Ainahin SO ba! kaso Asoka shine SO bawai kai Ake soba"ko kuwa kaine ke son ba'a sonka"karka manta ka fita daban Acikin dubu sbd kamalarka"ka saba mata na rok'on ka kasosu koka yi soyayya dasu koda bakaso"shiyasa kake ganin laifinah"karka manta leemart nada 18 yrs yanzun"Ahaka shine take k'aramar yarinya?"to nasanar mata Amma saita nuna bazata Amince ba shine zuciyata ta buga! daga baya kuma jiya bayan nasami kaina Anan ta kirani tayi ta nunamun tayi Accepting.....look kamal! kabarni da fad'amun wannan shirmen"cewar big man Aharzuk'e yanufi k'ofa ya fisgeta da k'arfi yafita yabar musu daddad'an k'amshin turarensa....kamal yaja Ajiyar zuciya yana fad'in wlh big man be dace da preety ba"hmm ! Idan ba itaba kana ganin Akwai wacce zata iya jure wulakancinsa harta Auresa??"saidai idan An sami wacce ke masa irin son datake masa ko?cewar tj"kamal yace"itama sbd abu biyu take sonsa"na farko dukiyarsa"na biyu kyawun kamalarsa kodan tayi fahari da hakan cikin mutane"Amma sam basu daceba"kamata yayi yasami wacce yakeso take sonsa ya Aura"Aikuwa wannan tatsuniyace! ita kanta preety d'in itace ke zuwa garden d'in nan su gaisa shima saida Amincewar sa"kiran sama saiya ya yadda inko ta kira zaiki d'auka"hakama idan tazo wajensa bashine yace" tasoba zai disgata ko Agaban waye kuwa"danshi Atsarinsa be zuwa tad'i"Arana kana iya samun miss call na matan dake cewa suna sonsa fin 20 kasani kaima"cewar junuid"kamal yatab'e baki yana tunanin tsatstsauran ra'ayi da muguwar Ak'ida irinta Abokin nasu wato big man"wanda yasan sarai junuid da tj sbd dukiyarsa suke tare dashi....yana wannan tunanin leemart da sa'ada sukayi sallama suka shigo d'akin"kamal ya Amsa sallamarsu cikin zumud'i yana fad'in babyn yaya Abdallah yau bakije skul ba ko?"sa'ada na murmushi tace"makara nayi wlh yaya kamal ko yayanma besan banjeba"ta k'are maganar suna zama"sbd su tj sun tashi dg kan kujerun"leemart dai kanta Ak'asa ta kasa nutsuwa sbd irin kallon da kamal ke jifar dashi"Akunyace suka gaidasu itada sa'ada"kafin sa'ada yarinya y'ar 13 yrs tace"Anty leemart zanje waje na jiraki"Amma karki jima kizo muje"kinsan yaya 12 pm yake dawowa gida"idan yagane banje skul ba dukana zaiyi"kanta kawai leemart ta gyad'a mata"sa'ada batayi mgn ba ta fice d'aga cikin d'akin sbd driver nacan na jiransu....

Alh mohd jibo shine mahaifin Abdallah"hamshak'in me dukiya ne"sbd tsohon ministern man fetir ne"kuma d'an kwangilane "yataka makamai masu yawa"hasalinsa d'an garin yola ne"kasuwanci yakawosa kaduna shida k'aninsa usman"Alh mohd kyakykyawan gaske ne farin bafulatani"ya had'u da jamilah Anan kaduna sukayi Auren saurayi da budurwa"suna matuk'ar son junansu"shekaransu biyu da Aure suka haifi d'ansu Abdallah"yanada shekara 3 Aka haifi mohd (khalifa)saidai Ana goyonsa yarasu"dg nan hjy Jamila bata koma haihuwa ba"har k'anin mijinta yayi Aure wato usman"bayan shekara 1 matarsa Aysha ta haifi d'an ta sadeeq bayan shekara 4 ta haifi y'ar ta haleematu Ana kiranta da leemart"cikin ikon Allah leemart nada 5yrs hjy jamilah(Ammi)ta haifi sa'ada"daddy da Ammi da Abdallah suka d'auki son duniya suka Azama sa'ada"wanda lokacin da Aka haifi sa'ada Abdallah nada 20yrs"shine da kansa yasaka mata baby"tayi bala'in shak'uwa dashi"tun kafin zuwan sa'ada duniya Ammi na fama da dangin daddy suna cewa" tagama dashi sbd irin soyayyar dayake nuna mata da kulawa"kwatsam shekara 3 da suka wuce daddy yazoma da Ammi da zancen zai k'ara Aure"lokacin sa'ada nada 10yrs"hankalin Ammi yatashi sosai dataga tuni be k'ara Aureba sai yanzun data fara tsufa"dan lokacin 48yrs gareta"wasu najin dad'i wasu najin bbu dad'i"haka daddy ya Auri tsohuwar bazawara balki"tazo da Agolarta hafsat Agidan"wanda ko wata ukku bata k'ullah ba Agidan daddy yasaki Ammi saki 2 "hankalin ta dana Abdallah yatashi matuk'a"kuma yak'i bata sa'ada"Abdallah yasiya mata had'add'en gida ta koma can da zama itada k'anwarta Anty wasilah wacce mijinta yarasu"Abdallah ya cigaba da kulawa da baby sa'ada"saidai yayima umma balki wata iriyar muguwar tsana"yakuma fahimci itace silar raba Auren Amminsa da dadynsa"dama can bbu ruwanshi da ita da kuma y'arta dake bala'in sonsa"umma balki kuwa dama da Asiri ta shigo gidan"takuma raba daddy da matarsa da Asiri"yanzun burunta shine Abdallah ya Auri y'arta"idan haka bata faruba to taga bayan Abdallah ta gaje komai"gashi Abin mamaki data samu ciki saiya b'are.....

Abdallah tun bayan yagama primary skul daddynsa ya fiddasa k'asar waje yayi karatunsa Acan sai yasami hutu yake zuwa nigeria"tun tashin Abdallah miskiline na gidan gaba"da iyayensa kawai yake sakewa sbd yataso d'an gata kuma d'an hutu"sai bayan An haifi sa'ada sannan Aka rage jidashi"Abdallah yakammala digree nasa na farko dana biyu duk Akan fannin kasuwanci"lokacin yanada 30yrs yadawo gida Nigeria da d'inbun nassarori"mahaifinsa yagina mishi camporny na buga furnitures na gida dana waje"bayan shekara 2 kuma yagina gidan man fetur, yabud'e super market kusan guda 3"Acikin k'ank'anin lokaci Abdallah yazama yong bolonia"yanzun yanada 34yrs Aduniya"shekara guda kenan da had'uwarsa da fatima preety"itama ubanta nada kud'i"preety Asali cikin tv da jarida ta fara ganinsa"kafin tayi k'ok'arin zuwa office nasa Amatsayin zatayi order d'in gado"daga nan ta Amshi number nasa tafara cusa kanta"shi kuma dama indai bakan kasuwanci kazo kuyi mgn ba zai iya zaman Awa guda bece maka komai ba"tun yana disgata da wulak'antata harta samu tashawo kansa"sbd har kuka da rok'onsa takeyi yasota"hakan yak'ara fasa kansa"yanuna mata zai iya Aurenta idan zataji dokokinsa"sbd daddynsa dama na matsa masa da zancen ya Ajiye iyali"preety tayi murna sosai da hakan"saidai mahaifinta yace"saita Ida karatunta kuma mahaifiyarta dabatada lafiya ta sami lafiya sannan zai mata Aure"dan komai sai anyima mamanta"Abdallah be damuba da preety tasanar masa"shi dama sbd daddynsa kawai zaiyi Aure"sbd shi mutum ne me tsananin biyayya ga mahaifansa.....
Abdallah da kamal tun suna yara suke tare har Abdallah yatafi ingila karatu"shi kuma yayi nasa karatun Anan"wanda kamal d'an jaridane yanzun yana Aiki gidan TV"yayinda tj shima da junuid duka Abokansu ne"sai bayan Abdallah yadawo gida Nigeria sukaga yadda yakoma suka nace masa"
Abdallah dogone wankan tarwada"kyakykyawan bafulatanin usuli"me cike da kyawun haiba da kamala"yanada bak'ar suma da manyan idanuwansa dayake yawan lumshesu"sbd tsabar cikan gashin girarsa har guda ta kusan had'ewa da y'ar uwarta"yanada dogon hanci dg k'arshe sai yayi d'an fad'i"lips nasa bown ne"be cika yawan mgn sbd dan beson yawan hayaniya"mutum neshi me tsananin kwarjini"yanada zuciya da saurin fushi"saidai beson raini"yanada manyan k'wanji sbd motsa jiki dayakeji"kuma irin murd'add'en jikin nan garesa duk gashi"idan kuwa yana mgn wasu har basuson yadena sbd dad'in muryarsa"mutane da yawa na masa kallon me girman kai"saidai yanada sauk'in kai ga wanda yasan halayensa"Abdallah nada halaye guda 3 masu kyau da mutane suka bashi sheda Akai"na farko yana sallah kan lokacinta"na biyu beyin k'arya zai fad'i gaskiya ko A gaban waye sbd be tsoro be shakka"sai Abu na ukku yana yin kyauta taban mamaki"Abdallah na shaye shaye sanadin b'acin ran rabuwar daddy da Ammi yafara"wanda tj da junuid sune silar fara shaye shaye sa" kuma iyayensa basu sani ba"lokacin da kamal yasani hankalinsa yatashi matuk'a"saidai daya fahimci beshan giya hankalinsa yad'an kwanta"yanadai yimasa nasiha Amma be dena ba"Abdallah be tab'a tsayawaba ya kalli wata y'a mace harya furta mata kalmar so"saidai shi Ayita cewa Ana sonsa yana disgasu"shiyasa beson miye soba"idan yaga namiji yarikice sbd mace ba k'aramin haushinsa yakejiba"musammun da yawan matan dake nuna masa ko baya sonsu to yayi k'azamar hud'da dasu"wanda hakane yasa yake tsanar masu cewa suna sonsa"junuid da tj dai basa zina Amma suna soyayyar shan minti.... Abdallah yahad'u tako ina Akwai izzah da nuna Aji Aduk Inda yashiga"be kuma d'aukar raini"sunan big man kuwa A jami'a friends nasa suka saka mishi shi....

**************
wani had'add'en garden ne na hutawa wanda da kaga wajen zaka tabbatar da if you're not in the first social class baza kazo wajen ba"ko ina Akwai grass carpet"zaune take gaban wani table"hand bag nata da wayarta na A Ajiye samqn table d'in"tayi shiru ta lula Aduniyar tunani"Iska na marecen yau laraba na kad'awa gwanin dad'i....gefen zuciyarta kuma tana jiran isowar k'awarta lawisa Awajen"kasancewar tana son zuwa nan wajen dan yana mugun d'ebe mata kewa"tana sanye da jallabiya bak'a ta yane kanta da mayafin"bak'in gashin dake gaban goshinta ya bayyana"babu make up a samqn farar fuskarta Amma haka be hana kyawunta bayyanaba" dan tanada kyau kamar Aljannah"kimanin kwana 4 kenan dataga wani guy Anan dg nesa"saidai har yanzun zuciyarta ta kasa mantashi da manta fuskarsa"dukda tanada wanda zata Aura nanda shekara d'aya da rabi"koshi batajinsa Aranta kamar yadda takeji dataga wannan guy d'in"d'ago kanta tayi sbd motsin mutane dataji"kowa nata harkan gabansa"wasu samari da y'an matan nata fira suna shan drinks ko ice cream"wasu kuma manyan mutanene suna maganar data shafi Aikinsu.......gabanta yayi mugun bugawa! sbd hango guy d'in datayi dg gaba yana tafiya" sai mutane wasu Abayansa wasu Agefensa suna biye dashi"kallo d'aya ta musu ta d'auke kanta......jama'a pls ku d'an koma d'aga can ciki sbd big man ya iso"kuma nan farko farko yafi yawan zama shida muta nansa"cewar wasu security's dake Aiki Anan"sosai Abin yabama *ummul khairy* mamaki"kud'i ta biya ta shigo wajen da sauran mutane"haka shima kud'i ya biya to Akan me za'a ce su matsa ?wayafi Anan wajen??"dukta tambayi kanta Acikin zuciyarta"batare data san wama Ake nufi da big man d'in ba"juyowa tayi da mamaki taga duk gaban tables d'in bbu mutane sun koma can gaba"sai ita kad'ai kawai....tj yaja tsaki yana fad'in ita waccan meyasa barata tashi ba bayan Ansanar kowa ya matsa??junuid yace"sbd tana tak'amar k'ilan tanada kyau ko?sam Abdallah be lura da ummul khairy dake zaune ba can nesa"saida yaji kalaman su tj sannan ya lura da ita"kamal yabisu da kallo sbd yafahimci suna k'ok'arin d'ora big man hanyar banza yadinga wulak'anta mutane"wanda shima jiya Aka bashi sallama yabiyosu nan d'ansu d'ebe kewa"kallo d'aya big man yamata yaji wani irin mugun haushinta"musammun daya lura ko Ajikinta tanama danna waya ma"bayan Ansanar kowa yatashi sbd raini shine ta zauna ga sa'an wasanta ko??"duk ya Ayyanah hakan Aransa yana cije baki"yana nufar table d'in da ummu ke zaune"wanda tun kafin ya iso k'amshin turarensa ya rigasa isowa"su tj na biye dashi"gaban ummu yafad'i data fahimci nan suka doso"saidai ta had'e rai sbd itama bata d'aukar raini"tana kuma tambayar kanta idan sun iso miye zasuyi mata to??"........cike da izzah da gadara Abdallah dake sanye da k'ananun kayan da suka masa masifar kyau yatsaya daga gefenta yanata cin magani"kamal ya kalleta ya kallesa"bbu wanda yayi mgn"cikin zazzak'ar muryarta tace"malamai bashi ko tara konaci ban biyaba da zakuzo kumin tsaye samqn kai??"ta fad'a cikin masifa"tj yace"ke dallah rufema mutane baki"kinsan gaban kowa kike ne?"ko kuwa bakiji Ance kutashi Anan ba big man ke zama nan waje Jen da mutanansa...ummu bata ko kalli gefen da tj yake ba"sbd lokaci guda taji wata muguwar tsanarsa"Abdallah ta kallah suka had'a ido"Atare k'irjinsu ya buga!"dukda yamata kwarjini taji kuma mugun shakkarsa Arabta Amma batajin zata iya nunawa"harara me rai da lafiya ta wurgo masa tana fad'in........โœ๏ธ

๐Ÿค”๐Ÿซฃ๐Ÿคซtofa ga Abdallah ga ummu khairy yaya kuke ganin za'a soma wasan??๐Ÿคฃ

Ad'aure azuba zafafan comments

Yi k'ok'ari ki biya naki domin adama dake Awannan doguwar tafiyar me saka zuciya nishad'i maza ki biya ta nan dan free pages 5 ne๐Ÿ‘‡
wannan book d'in nakudine
Normal grp 300
Vip grp 1000
Special people 2k wato 3pages in a day

zaku biya kud'in ku ta wannan acc number๐Ÿ‘‰2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK
Kituro shaidar biyanki what's app number d'ina 08100084251
300 kawai ake turo Kati idan bakida acc amma sauran payment d'in ta acc ne

banason transfer d'in Kati ko vtu photo d'in katin MTN zaki d'auka saiki turo dan Allah banda kiraโŒ

Y'an nijar kutuntub'i wannan n๐Ÿ‘‰ +227 88 01 90 50
Normal grp 500f
Vip grp 1000f
Special people 2000f

dan girman Allah da darajan iyayenki karkimun mgn idan baki shirya biyaba
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

โคโ€๐Ÿ”ฅ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จAUREN YARJEJENIYA๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จโคโ€๐Ÿ”ฅ

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

it's rometic love storyโคโ€๐Ÿ”ฅ๐Ÿ’”


Story & written by mommyn fareesa

wannan shafin nakine halak malak *fatima Ahmed shema*๐Ÿ’–๐Ÿ’“


free page 3&4

.......harara me rai da lafiya ta wurgo masa tana fad'in"malam lafiya zaka tasani gaba kana kallo??"tukunnah ma waye shi wanda wannan d'an koron ke zuzutawa haka?"inaso na gansa naji yanada wuta ko aljannah balle yasakani ciki??"kud'i na biya na shigo nan kuma sune kuka biya kuka shigo ko?to Akan me zan tashi sbd wani?"bbu wanda ya isa yakafamun doka Anan"ta k'are maganar cikin k'arfin hali da nuna ko Ajikinta"kamal yasaki murmushi sbd yaji yarinyar tayi bala'in burgesa data disga TJ tanuna kuma bata tsoron kowa"Abdallah ya kallah yaga bbu Alamar rahama Asaman kyakykyawar fuskarsa"yana dai bin ummu da wani irin mugun kallo.....ke !dakata karki gaya mamu maganar banza"ga big man nan Agabanki"zai iya b'atar dake da Ahalinki bbu Abinda zai ita faruwa"zakizo kina gayama mutane mgn son ranki"ko Anfad'a miki kinada Ajin dazai kulaki ne??"cewar junuid"kamal yace"pls ya isa haka"duk kace nace be tasoba"ta fad'i iya gaskiyarta ne"yaka mata muje ga kujeru can mu zauna dan banga Amfanin tsayuwarmu Anan ba"wani banzan kallo junuid da tj sukabi kamal dashi"yayinda ummu gabanta keta dukan tara tara "ranta yabata wannan kyakykyawan mutumin shine big man"tayi mamakin izzarsa da har yanzun beyi mgn ba yana dai tsaye yana danna waya"yayinda Acikin zuciyarta taji kamal ya burgeta sbd gaskiyar dayake fad'a"tana wannan tunanin ta d'auki hand bag nata da wayarta ta mik'e tsaye da nufin tabar musu wajen"saidai tanaso ta wuce shi kuma yana tsaye bbu dama dole saiya gyara sannan ta wuce"kamal kuwa yayi mamakin Abdallah sbd yasan be shiga sabgar mata"saidai ranshi yabashi kodai cin mutunci zaiyiwa yarinyar nan"wacce yaga Alamar tarbiyya da kamun kai Atare da ita"musammun dayaga bata damu ko rikicewa da ganin big man ba.....ka gyara zan wuce! sanyayyar muryar ummu ta katsema kamal tunaninsa"Abdallah ya d'auki kusan second 10 kafin ya d'ago kansa ya watsa mata manyan idanuwansa"Atake taji k'irjinta yabuga"ta d'aure fuska tana d'auke kanta"koma matsowa yayi dab da ita har tana jin hucin numfashin sa"subahanallahi! ta fad'a tana matsawa"K wawiya! yafad'a cikin daka tsawa"hakan be hana tattausan muryanshi bayyanah ba"kin isa ki tsaya ki gayamun mgn ki kuma wanye lafiya??"never idan kinyi wannan tunanin"yafad'a yana girgiza kansa yanuna ta da yatsa"dubeki shashasha jiki na d'oyi da tsami"Ayanzun zan nuna miki tabbas inada k'arfin iko"banida wuta banida Aljannah Amma zakisan inada k'arfin iko ga wanda yyi gigin shiga gonata"yafad'a yana jan tsaki kamar zai huda harshensa"ya zaro handkcheef ya tsoshe hancinsa"junuid da tj suka saki dariyar rainin wayo suna nuna ummu"yayinda body guards nasa suma suka kama dariyar"sauran mutane dake can nesa suna kallo Amma basusan me suke fad'a ba"wani irin yanayi na b'acin rai ummu ta tsintsi kanta Aciki"tana jin ba k'aramin muzantata big man yayi ba"batace komaiba saidai fuskarta bbu Annuri"bata kalli ko wannan suba tayi k'ok'arin tafiya"big man na yatsina fuska yasha gabanta"batace komaiba tayi dai tsaye.....big man kabar musu yarinya ta tafi mana"banga wani laifin data maka ba"Amma ka mata irin wannan wulakancin....kamal sau nawa zance kadena shiga Abinda be shafeka ba?"cewar big man cikin fushi"ummu tayi k'ok'arin koma tafiya.....caraf big man ya damk'i hannunta ya maidota baya"Afusace ta juyo ta tsinkesa da mari tana huci tace"idan kasaba rik'e hannun shashashu toni ba irinsu bace"I hate you!...tsit sukayi dg body guards nasa har zuwa su junuid sbd tsantsar mamakin Abinda yarinyar nan tayi"kamal kuwa beso haka ba sbd yasan big man bazai k'yaletaba"shi kuwa uban gayyar shafa kuncinsa yayi da girarsa ta dama yana wani irin mugun murmushin daya bayyanar da tsantsar kyawun halittarsa"wanda kamal daya gani yasan mugun Abu zai Aiwatar idan yana irin wannan murmushin"sannan kuma yana rik'e da hannun nata be sakiba yamasa wata iriyar damk'a ta mugunta....body guards nasa suka nufi ummu! kubarta"ya fad'a Anutse"ita kuma tanata kiciniyar k'wace hannunta"big man ya had'e rai sosai yana dubarta kamar yaga Abin k'yama yace"zasu barki ne dan ki kafa tarihin kin mari mutum kamata"bayan kina banza k'azama kuma kucaka! ina mai tabbatar miki da cewa" zakiyi nadamar dabaki tab'a yin irinta ba Arayuwar ki...Ai big man hukuncin daya kamace ta shine reping!cewar tj" gaban ummu yayi wani irin mugun fad'uwa ta zaro ido da Alamar razana Asaman kyakykyawar fuskar ta"innalillahi wa inna ilaihir raju'un! yanzun har Abin yakai haka Abdallah??"cewar kamal cikin fushi"kasan me suke shirin sakaka ka Aikata kuwa??.....saurin cika hannun ummu Abdallah yayi sbd cizon data gartsa masa"tayi k'ok'arin guduwa"Abdallah yadubeta da nufin yabita"kamal ya rik'e masa hannu"yana fad'in kasan illar Abinda kake shirin jama kanka"kanaso duniya tamaka wata fassara ne??"ka cikani kamal ko kuwa na rabu dakai har Abada"cewar big man cikin hargiwa yana watsama kamal mugun kallo da idanuwansa da suka rine zuwa jaa"saime Abdallah idan ka rabu dani?"sbd na fad'a maka gaskiya kace haka?"to bari kaji su da kake tak'ama dasu wata ran zakayi nadamar saninsu Arayuwarka"tunda suna sakaka hanyar banza.....wace irin banzar mgn ce wannan kakeyi haka kamal?"cewar junuid"kamal yaja tsaki yana fad'in ban saniba"yacika hannun
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4

Please Login or Register in order to submit comment