Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

Ga ubangijin talikai daya bani ikon rubuta
wannan ta'kaitacan rubutu kan MATSALAR
JINNI. Ubangiji yadda kabani ikon farawa kabani
ikon kamalawa.Sa'kon godiya ga daukacin member na group d'ina MATA MASU AJI. Ubangiji ya 'kara had'a kawunanmu amin.



SADAUKARWA.
Gareku bazan manta karamcinku ba.
Teemah Cool
Safdeeq Cool
Maryam Idris Katsina.
Jamila Umar Katsina.
Aina'u Jega.
YABAWA.
Taurari cikin NAGARTA (NWA).
Ummu Fadila.
Miss Hafcy
Meesha Luv
Aunty YBK.
Aunty Chuchu.
Addah Jabo.
Beneziratu Ammar Saje.


JINJINA GA 'DAUKACIN MASOYANA.
Kaduna.
Katsina.
Narasawa.
Gashuwa
Kebbi
Kano
Da sauran jahohi ubangiji ya kara mana 'kaunar juna.Sadaukarwata gaba d'aya ga
TAURARUWATA ita ce MAHAIFIYATA ubangiji ya bani ikon kyautatta maki.


************
GAMUNAN DAI.
Hassana Muhammad Kano.
Hassana Zakariyya Shahada Kano
Hussaina Garba 'Danlami Kano.
Hussaina Zamfara.
Hussaina Kaduna Shantaly.
Hussaina Gashuwa Munayshat.
************


1-3
Cikin matsanancin gudu take wuce tsaunika tare
da tarin bishiyu, taka 'kayoyi take amma hakan
baya d'aya daga cikin abinda ya dameta, burinta
kawai ta tseremasa daga mummunan nufinsa a
kanta, cikin rashin tsamani ta taka wata
'katuwar 'kaya mai tsanani kaifi. Take ta 'kwala
giggitaciyar 'kara hakan yai dai-dai da
farkawarta. Cikin hanzari tabi 'kafarta da kallo
abinda yai matu'jar tsorata ta. 'Kayar data taka
a mafarki gata a tafin 'kafarta ga jini na bin
'kafafunta cikin tashin hankali ta soma waige-
waige. Shiru garin babu motsin bil'adama sai
kukan karnuka da tsuntsaye. A hankali takai
kallonta kan 'kofar d'akinsu cikin sakan guda
cikinta ya bada wani sauti. 'Kuuuuuuuuuu.
Cikin tsoro ta dinga ja da baya tare da karanto
duk adu'ar data zo bakinta. Ta runtse idonta ta
jiran 'karasowar 'KADDARARTA saidai ga
mamakinta sai ta tsinkayi muryar Mahaifiyarta
tana fad'in "Najwa me kikeyi baki kwanta ba?
Cikin sauri ta bud'e idonta. Sai ta saki ajiyar
zuciya. Cikin azama takaiwa 'kafarta bahagon
kallo dansan nunawa mahaifiyarta. Abin mamaki
da tsoro babu ciwo babu alamunsa. Nan da nan
ta nemi nutsuwarta cikin kaucewa kwataragin
daya dumfarota tace "Innarmu farkawa nai".
Cikin d'aurewar fuska tace " ina d'ankwalinki?".
Nanfa ta kama kame-kame sabida bama dashi
ta kwanta ba. Cikin fad'a mara sauti tace " wato
Najwa bakya jin magana ko ke kullum baza
agaya maki kijiba, kwanciya kai a bud'e ke ba
gwanar adu'aba sai anyi magana kice antakura
miki ko?". Cikin gunguni tace "Mantawa fa nayi".
Cike da mamaki tabita da kallo tana jinjina
taurin rai irin nata.Cikin nutsuwa take tafiya tamkar mai tausayi 'kasa, saidai zuciyarta cike da rud'anin mafarkinta na jiya tana jin kodai tagayawa Husnah kotai shiru. Can wata zuciyar tace " Ke Najwa yanzufa zamani ya sauya mutum ba'abun yadda bane, wani zaimiki kwance- kwance yaji matsalarki kawai dan yaji dad'in falasawa. Wani kuwa dan yaji dad'in yimiki gorine. Ki ri'ke matsalarki a ',kar'kashin zuciyarki da sannu ubangiji zai miki maganinta. Saidai ki ri'ki adu'a. Cikin farin ciki tai na'am da abinda zuciyarta ta fad'a.Kamar daga sama akaimata salama" Assalamu alaiki Gimbiyar mata". Shaidar mai muryar ne yasa ta d'ago cike da murmushi tana kallinsa cike da so da kuma 'kauna. Sai taji kaf damuwarta ta wuce. Amma miskilar saita maze. Mustapha yai murmushi yana dubanta yace,
"Najwa ina zaki cikin ranar nan?, ta ya mutsa
fuska alamun gajiya tace "gidan yaya Maryam
zani mijinta baya nan zan tayata kwana zuwa
jibi". Cikin jin dad'i yace "kice kwana biyu muna
tare"?. Ta gintse fuska "ba lallai bane tunda
kasan ra'ayin Innarmu shine nata". Yai ajiyar
zuciya " shikenan Najwa sai munyi waya". Yana
fad'ar hakan ya juya idonsa jajjir cike da
sassarfa. Duk sai ya bata tausayi, to amma ya
yakeso tayi ? Yasani sarai mudun ta sami labari
rayukane zasu 'baci a haka ta 'karasa 'kofar
ruwa cike da kasala. Tun daga soro Walid yake
oyoyo. Tilas ta aro juriya ta tari fara'arsa suka
shiga gidan. Da fara'a yayarta ta amsheta suka hau wasa da dariya. Cikin zolaya tace 'ina kuwa MUS'AB?". Take fara'ar data aro ta gushe. Kai tsaye d'akin da take sauka ta wuce ta barta anan shanye da baki. Tanata bambamin fad'a. Tana shiga kiranwayarta na shigowa jaka kawai ta ajiye ta wuce kan kujera. Tana karar wayar a kunnanta suka saki ajiyar zuciya lokaci guda.
Cikin tausasawa yace "menene?" Kai tsaye ta
amsa masa "babu komai hubbynah hope (fat an)
ka'isa gida lafiya"?. "Ba wannan ke gabana ba
Najwa dalilin ajiyar zuciyarki nake san ji, tai gum
tana juya lamarinsa a ranta tasani kad'ai ko
muryarta yaji yana gane yanayin damuwarta,
bale kuma ga rabuwar da sukai. Jin shiru yayi
yawa ya kira sunanta. "Najwah!!!!!!" Yar cigar
jikinta ta tashi cikin kasala ta amsa. "Na'am
hubbynah". " please menene damuwarki?".
"Mustapha kaine damuwata, kaine abinda ke
sani damuwa, ina duba yanayin da muka rabu
inajin araina ban kyautaba. Kobaka cancanci
SADAUKARWA ........"Ya'isa Najwa kinci abinci".
Duk saitaji haushin kanta wato shi 'ko'karinsama
cikinta, gaskiya inta auri Mustapha zata ga
tarairaya. Shigowar Yaya Maryam yasa tai masa salama. Bai matsa da sanjin daliliba ya katse. Zuciyarsa cike da tausayin rayuwarsu cikin azanci yace,
"KADDARARMU CE a hakan.
Haka ta 'karasa kwanakinta gidan cike da takura
sabida rashin samun jin muryar abin 'kaunarta.
Ranar da Abdul zai dawo tafi kowa murna da
zumud'i tun safe taimata aiki ta had'a kayanta.
'Karfe hud'u ya dawo gida, 'karfe biyar Najwa
taiwa unguwarsu tsinke. Tana shiga layinsu ta
saki sassanyar ajiyar zuciya sabida hango
'kawarta da tayi cikin sauri ta tarbeta suka shiga
gida tana fad'ar ",bestyna miss u more" ( ma'ana nayi kewarki da yawa). Cikin murmushi wanda ya zama al'adarta suka shiga gida.Inna na ganinta ta ta'be baki "wuuuu! Najwa 'yar nema wato har kin gudo ko"?. Ta turo baki " dole in gudo Innarmu aita saka aiki ba godi bare na gode, kuma kanayi ana hantararka". Duk sukai dariya Husnah ta jata d'akinta suna shiga tace "Mus'ab yazo sau biyu bakya nan, ya nemi numbarki Inna ta aiko na bashi, hope ya kiraki?.
Next Mustapha ya bani sa'ko anjima in munje
makarantar dare zan baki". Tunda ta soma
magana sai yanzu Najwa tai murmushi jin an
ambaci Mustapha . Cikin zolaya Husna ta d'aka
mata duka tai waje, aikuwa a guje ta biyota
kafin ta kamata ta kyalle. Cikin dariya Inna tace
"sababbu kun dawo zaku adabeni".
Cike da haushi ta cire d'ankwalinta ta suri buta
zuwa kewaye (band'aki), Inna kawai ta tsaya
taga gudun ruwanta, saidai bata da alamun
tsayawa ta daura. Cikin hargagi ta daka mata
tsawa." Keee! Najwa ina kalabinki? ('Dan kwali)
cikin basarwa tace "zan d'aura bari in fito". Bata
jira cewartaba ta shiga abinta. Mamaki ya kashe
Inna kwata-kwata Najwa bata jin tsoran fad'anta
mudin akan saka kalabine ko batun Mustapha
tun bata damuwa da lamarin harta soma
damuwa. Tana fitowa ta tareta da balbalin fad'a "wato ke Najwa bakyajin magana ko? Nahanaki zama babu kalabi kin'ki ji ko' uwa uba shiga bayi
babushi, waikin manta band'akine matattarar jinu amma kike 'kuga (saka) kanki ciki babu hijabi, wanda na tabbatar ko adu'arma da 'kyar idan kinayi". Inkin taka biron hanuna ya tanka haka Inna taita bambaminta Najwa tai biris.

Najwah Usmar Salis wadda abokanta suka fi kira
da Nus, d'iya ce ga Malam Usman marigayi tare
da Inna Hafsatu. Su shida iyayansu suka haifa
duk mata. Suna zaune a unguwar dandinshe
cikin 'karamar hukumar dala. Babbar yayarsu
Zainab na auran wani prof a gadon 'kaya
yaranta hud'u. Auwal da Sani da kuma Mahfuz
da Mahfuzaht. Sai mai bimata Saudat. Tana
zaune a unguwar tudun yola yaranta biyu,
Muhseen da Muhseenaht. Sai ta tsakiyar itama
yaranta biyu mai suma Fiddausi. Sai Ayshat ita
kuma tana 'kurfi tana aure bata ta'ba haihuwa
ba. Sai Maryam mai yaro guda tana 'kofar ruwa
sai autarsu Najwa. Mahaifinsu ya jima da rasuwa, tun suna yara. Rainansu da kulawarsu duk 'kar'kashin kulawar Inna Hafsatu. Innarsu macece mafad'aciya sossai. Bata san wargi (raini). Haifafiyar Kano ce unguwar 'kwali wajan gidan sarki hakan mahaifinsu haifafan 'kofar nasarawa ne. Tun bayan rasuwarsa danginsa basa basu wata cikakkiyar kulawa kasancewar shine bare cikinsu. Mahaifiyarsa ta rasu, tun tana kai yaran harta daina. Haka nan duk auran yaranta ita tai fadi tashinta babu taimakonsu. Macece mai zuciyar nema babu sanar da bataiba don rufawa kanta da yaranta asiri. Tana tsaya musu sui karatu kafin aure iyakarsu secondary inyaso inkinje mijinki na muradi kya cigaba. Itace yin surfe, wanki da sauransu. Harta gama auransu yaranta sai autarta Najwa.
Asalin iyayan Inna Hafsatu 'yan 'kasar Niger ne,
kyawawan fararren buzaye masu gashi da kyan
fasai. Doguwar mace sam'bal zubin Karas ba
d'ata ba. Cikin bayin da ake kawowa gidan sarki
aka had'o da mahaifiyarta anan ta had'u da
mahaifinta shima mutumin can ne kasan
cewarsu 'KABILA d'aya ba jinkiri sukai aure.
Inna Hafsat kad'ai suka haifa kyakkyawar mace,
shekarunta sha biyu akai wata annobar kwalara
suka rasa rayukansu. Hakan ya sa Usman yake
tausayinta har ya juye zuwa so ansha fama
kafin auransu saidai ikon Allah. MATAR
MUTUM....hausawa sukace wai 'kabarinsa. Duk
cikin yaranta Najwace ta d'auko komai nata.
Dan haka ina keji da d'iyarta.
Tunda ta gama aurar da yayyanta sai hankalinta
ya kwanta, Najwahce kad'ai gabanta. A da
yaranta makarantar gwamnati suke, amma ganin wadata da bud'i daga ubangiji tare da taimakon surukanta. Najwah na gama primaryn makara huta ta sama mata gurbin karatu a gora
academic. Najwa ta tashi cikin so da kulawar
yayye uwa da mazajan yayyanta. Kullum cikin
samun gata da kulawa take. Saidai duk cikin
yayyunta tafi shiri da Maryam dan haka tafi
zuwa gidanta. Sui tsiya sui dad'i sabida Maryam
akwai tsokana. Duk cikin yaran Innarsu Maryam ita ta kwashe halin Inna, akwaita da fad'a ammafa kan gaskiya batasan raini. Najwa bata da 'kawa ko daya sai ma'kwafciyarsu mai suna Husnah, 'kiriniyarsu iri d'ayace saidai akwai kwanyar nacin karatu. Ga masifaffiyar tsokana akwai wata al'adah guda d'aya da Najwa keda ita wadda kullum takesa su sami sa'bani da Inna.............

'Dabi'ar Najwa itace yawo a tsakar gida babu
d'ankwali, ko banda'ki zata bata damu ta
d'aurashi ba. Ga yawan shigar kaya masu shara-
shara ko matsatsu. Duk lokacin da tai hakan
sukan haura sama ita da Innarta. Hakan kan
'kona ran Najwa ganinta yadda take da gashi har
tsakiyar bayanta bai kamaci tasa kalabiba. Uwa
uba 'yan ajinsu na fasa mata kai idan akazo
exfection.
Najwa irin matan nan ne dogaye masu fad'in
',kugu da cikar 'kirji hakan yasa duk suturar data
saka take mata das gata chaculate colour mai
haske. Kalar da ba a siyanta komai kud'inka.
Tun tana 'karama take fama da'ita tayi dukan
duk a banza har zuwa girmanta. Hallayarta na
ba'kanta ran mahaifiyarta sossai,tun tana
'karama har yanzu da takai matakin shekaru sha
biyar, komai nata ya kara kyau da girma, kullum
cikin nuna mata kuskurenta take amma abu yaci
tura. Mus'ab matashin saurayine dan bayan layinsu tun Najwa na jss one yake 'kwa'kwar santa, saidai Innarta tace saitayi karatu. Yace yaji ya amince zai jira. Najwa ta tsani Mus'ab kullum ta ganshi wani mugun abu takeji ya taremata 'kirji. Zagi kuwa yana shansa lodi-lodi. Tasha saka yara su sace masa tayar kekensa d'an tsura ta basu lada. Wata ranma ita da shakiyiyyar 'kawarta suke zuwa. Tun bai saniba harya ganosu. Najwa na jss 3 wani ba'kon al'amari yasoma giftawa cikin rayuwarta mai cike da mamaki da ban tsoro.
Wasu irin mafarkai take masu tsananin ban
tsoro, wasuma ta kanjisu ajikinta suna matu' kar
wahalar da'ita tare da rikita tunaninta. Da fari
taso sanarwa Innarta saidai tana tsoron tayar
mata da hankali. Gashi mafarkin yana sata
kokwanto ta kanji anya a kantane koko a kasin
hakan. Tsanar Mus'abu ta cigaba da yad'uwa a
zuciyarta harzuwa lokacin data had'u da
Mustspha.
Najwa ta tsinci kanta cikin yawan mafarkai
barkatai. Lokuta da dama ta kanyi mafarkin gata
a harabar wani babban gida yara 'kanana suna
zagaye da ita. Kota ganta rungume da jarirai a
hannu. Kota ganta tana tana feeding (shayarwa)
d'in jarirai. Lokacin tana jss three, sai ta maida
abun tamkar wasa. Tana matakin Sss one ne,
ubangiji ya had'ata da Mustapha a hanyar
makarantarsu wato 'kofar ruwa. Mustapha
nitsattsan saurayine mai tsantseni da Ibadan.
Tunda ubangiji yasa ya d'ora idannunsa kan
Najwa ubangiji ya jarabceshi da 'kaunarta. Tun
yana kkakaucewa har yai shahadar ',kuda ya
isar da sa'kon zuciyarsa. Najwa macece mai san
soyyaya da kulawa hakan yasa cikin 'kan'kanin
lokaci Mustapha yai nasarar samun soyayyarta.
Cikin 'kan'kanin lokaci sukai wata irin sha'kuwa
mai wuyar fassaruwa. Kullum tafito zuwa
makaranta ta 'kofar gidansu take wucewa, yana
zaune ya dakkonta (jiranta) in kuwa ta wuce
zaimata fatan alkhairi ya shiga gida. Wasu
lokutan ya rakata sch yana tsokanarta yanai
mata wa'ka.
Najwa fara kyayyawa, matata abar sona.
Babyna ina sanki Kuma kema nasan kina sona.
Inmunyi aure musha 'kauna ke zan miki wanki
duk dan 'kauna.
Zanmiki wanke- wanke harma da goyo sabida
'kauna.
Ira-iran kalaman Mustapha kenan, ya iya salon
sace zuciyar mutum. Najwa najin dad'in al'ka
dashi gashi mudun zasu zauna hira saita 'karu
dashi fanin addininta da all',amuran rayuwa. Irin
mazan da ake buri kenan arayuwa. Ubangiji
kabamu mazaje nagari.
Mus'ab hankalinsa ya tashi ganin kwata-kwata
hankalin Najwa baya Kansa. Hakan yasa yasoma
yiwa Inna Hafsatu 'barin kud'I a fakaice batare
da sanin Najwa ba. Inna Hafsatu hankalinta ya
tashi ganin yadda diyarta ta karkata kai ga
Mustapha, batare da laifin komaiba. Mugun
tsanarsa takeji a ranta. Abinda bata saniba
matsalar Najwa ce ta haddasa hakan, saidai
rashin kula ya hanata fuskanta.
Zagin yau daban na gobe daban, Mustapha yana
da hakuri da juriya, bai taba d'aga kai ya kalli
Inna da batunba. Sau tari zaizo gida amma Inna
ta hanata fita. Yaya Maryam tafi kowa assasa
lamarin sabida basa shiri da gidansu Mustapha
kan mijinta Abdul nasan 'kanwarsa Farida.
Kasancewarsu akwai ma'kotaka saitai amfani da
damar dan 'kuntattama danginsu.
Mahaifin Mustapha ya jima da rasuwa, daga shi
sai 'kanwarsa da mahaifiyarsa. Yana kyautatta
musu sossai ya kamala karatunsa na NCE
da'kyar. Yanzu koyarwa yake a wata nursery
dake kusa dasu mai suna HASMAH
INTERNATIONAL SCHOOL PRI- NURSERY AND
NURSERY AND PRIMARY. Balaifi yana samun
albarka. Bai zauna hakaba yana koyarwa a
makarantun dare guda biyu magarba da isha
mai suna UMMU SAMHAT TAHAFIZUL QUR'AN
da kuma MADINATUL AHBAB.




Kwanci tashi babu wuya gurin ubangiji al'amura
sunka cigaba da faruwa masu dad'i da akasinsu.
Ana hakan kwatsam Mus'abu ya aikowa Najwa
kyautar waya sabuwa dal. Wadda mahaifiyarsa
ce da kanta ta kawo kyautar kasancewarta
aminiyar Inna. Wannan yasa Inna ta 'kara san
Mus'ab sossai. Da farko Najwa ta'ki amsar
wayar amma data gayawa Husnah tuni ta shirts
mata hanya mai 'bilewa. Da sassafe ta tashi
cikin shirin zuwa makaranta taima Inna salama
ta wuce zuwa gidansu aminiyarta suka rankaya.
Tafe suke suna tad'i (hira) su biyu cikin
nutsuwa da sanyin rai Najwa tace" aminiyansi
jiyafa 'kolo ya kawomani waya 'kirar gione
amma ban kar'bata tana gun Innah". Cikin
masifa Husnah tace " gaki dai kamar wayyayiya
kina neman yin kwa'ba, banda ke ai wayar wata
hanyace ta 'karfaffa ala'karki da Mustapha". Tai
jim alamun tunani, can ta saki murmushi
'kayatace wanda yasa dimple d'inta motsawa
tace "gaskiya Husnaty ke mission ce, aikuwa
hakan zanyi walahi, in'kulle a d'aka ina waya da
hobby a Inna nayin magana nace 'kolone". Gaba
d'aya sukasa dariya dai-dai lokacin suka 'karaso
bakin geta d'insu suka shiga makaranta.
Najwa alla alla take a tashi makaranta taje ta
amshi waya. Ana kuwa tashi kai tsaye tayo gida
ko Husnah bata tsaya jiraba. Kasancewar rana
ta take haka ta taho tana zumud'i tazo gab da
layinsu akwai wata 'katuwar kuka mai koguna da
yaw a a kan layin anan idonta yai katari da wani
kyakkyawan farin mutum yanai mata murmushi,
da farko taji ya birgeta dan yaimata yanayi da
hubbynta amma daga bisani saita lura jikinsa
duk gashine kuma kasansa maimakon 'kafaffu
aaaa jikin micijine. Cikin sassarfa ta bar gurin
tana waiwaye yana d'aga mata hannu. Wajan
shiga gida tai karo jikake 'kumm ta 'kwala 'kara
nan da nan Innarta ta fito tana tambayar ba'asi.
Tuni goshinta yayi lukuni abinka da farar fata.
Cikin sauri tasoma mulmula mata, suna shiga
gida tana zumud'in fadar abunda ta gani. Saita
samu kanta da tsanani tsoro domin mutumin
kemata barazana yana tsiratatta da wata
sharbebbiyar wuka. Luf tai ajikin Inna tana ajiyar
zuciya. Uniforma ta cire ta d'aura zani still babu
dankwali ta shiga bandaki ta watso ruwa
abunta.
Tana nan zaune Husnah ta shigo, tana
bambamin anbarota saitai turus ganin lukuni a
fuskarta, ga wani uban tagumi data rafka, cikin
tsoro ta girgizata ajiyar zuciya tai lokacin data
dawo daga tunani. " bestyna meya sameki" "
bigewa nai tafada cikin bagararwa" " wannan
tunaninfa?". Take abinda ya faru ya dawo mata
ta bud'e baki zatai magana sai bakinta ya'ki
magana tashin hankali kawai saitasa kuka "
Besty nima bansaniba walahi bansan abinda ke
damuna ba". Husnah tai musmushi duk zatanta
Innace ta hana wayar ko garin zumudinta ta
fasa musu kwai kawai saita shiga ciki taiwa
Inna dad'in baki ta am sonata wayar ta
hadamata komi tadangamata tajata d'akinta.

Suna shiga ta dubeta da yanayin kulawa. "
bestyna menene damuwarki? Zatona
Mustaphane kuma kinsamu hanyar jinsa what
next"?. Cikin jimami ta bud'e baki zata bata
labari amma hakan ya gaggara. Kawai sai
Husna ta Samara number Mustapha dake
wayarta ta dana kira. Lokacin da kiran ya shiga
yana niyyar shiga masallaci saiya share kiran.
Ganin shiru bai d'agaba yasa Husnah taimata
salama tare da lallashinta ta wuce gida.
Najwa tai ajiyar zuciya ta kwanta kan katifarta
ya illahi wazata tunkara da batun. Mustapha
yana fitowa masallaci yai karo da wani ba'kin
'kadangare ya kawowa babban yatsansa cafka
cikin nutsuwa ya furta" hasbunallah". ' Bat ya
'bace babushi babu lamarinsa. Cikin rashin
kuzari ya 'karasa kan benci ya zauna. Wayarsa
ya zaro ',karama mai sau'kin kud'i mai suna G-
best ya kira numbar d'azu. 'Karar wayar ita ta
dawo da Najwa daga dogon tunaninta cikin
nutsuwa ta d'aga tana murmushi, tana jan jelar
gashinta. Jin muryar juna ya haifarmusu da
nutsuwa domin rabansu da juna tun had'uwarsu
a zuwanta gidan yayarta. Cike da kulawa yace "
Najwa yanajiki wani sanyi- sanyi?". Hawaye
yabiyo kuncinta tace " bakomai Hubbyna hope
kana lafiya ya jikin Mama"?. Cikin sar'kewar
murya yace "aa'a Najwah ban aminta ba".
"Hmmmm! Kafi 'karfin komai a gurina ka yarda
banda damuwar data wuce ka". "
To nagode Allah yabar 'kauna inajin dad'in
hakan sai dai zuciyata zafi Najwa inajin kamar
kin 'boyemun ne. Inasan inji nasamu sanyi inajin
kamar idona zasu zubar da hawaye
hmmmmmm! Kicema Inna ina gaisheta, ki dinga
yi mana adu'a".
Sunyi shiru na mintina, ya kauda shirun" ina kika
sami waya naga ba layin bestynmu bane?". Dum
' kirjinta ya buga bazata iyayi masa 'karya ba
kawai saita gaya masa gaskiya. Jikinsa yai
sanyi duk yaji babu dad'i amma yasani
sarewarsa na nufin sarewarta. Sarewarta na
nufin bijirewa mahaifanta, bazaiso hakan ba
baimata adalciba inyai hakan ba santa yake ba
cikin murmushi yace .
" Najwa You make me smile for no reason
whatsoever, you make me laugh at the unfunny
things, but most of all, you make me love you
when I shouldn't be loving you". Bai jira cewarta
ba ya katse kiran. Cikin nutsuwa tabi wayar da
kallo tanajin dad'i mara misaltuwa. A fili ta furta
"Mustapha ina 'kaunarka". Bazaki aureshiba inko
kin sureshi kina tare da bala'i da masifa.


Cikin yanayin damuwa Mustapha ya ajiye wayar
hannunsa. Zuciyarsa nasan gargad'insa abisa
matakin daya ke shirin d'auka. Saidai yana ganin
hakan shine dai-dai. Yana tashi gida ya nufa da
salama. Farida dake wanki ta amsa masa da
kulawa tanai masa kirarin dake sashi murmushi.
"Angon Aunty Najwa sai dubu ta taru"
mahaifiyarsu ta kallesu cike da murmushi
tanaiwa ubangiji godiyar samun nutsattsun
'ya'ya.
Cikin ladabi ya zauna ya gaisheta, kansa a
sunkuye tace " mai sunan manya ya akai?
Bakinka akwai magana". Yai murmushi ya sosa
kai "mama dama maganar yarinyar can ne".
Sarai ta fahimceshi amma saita bagarar da
zancan" ban fahimtaba Mustapha wacce
Kenyan?". "Mamanmu Najwah nake nufi". Cikin
murmushi tace "to ya akayi ko sunce mu
mutsane?". "A'a mamanmu nine dai nake ganin
dacewar hakan sabida takai matakin aji biyar".
"Hmmmmm! Ban'ki ta takaba amma baka ganin
zamui musu riga Malam masallaciba,
kasancewar basu but',kaci hakan ba?". "Insha
Allah ba matsala". Da haka suka rufe zancan.
Da yamma mama ta shiga gidan liman
ma'kocinsu ta shaida masa bu'katarta tasan
nemawa Mustapha aure tare da wasu cikin
abokan mahaifinsa. Sun amshi batun hannu biy-
biyu ana sallahr isha'i suka d'auki hanya bisa
rakiyar mustapha. Saidai kash sunyi takaicin
abinda suka riska, domin Inna taci mutuncinsu
tas, tare da shaida musu sati mezuwa zata
Karl'bi kud'in auran 'yarta.
Sun dawo jiki a sanyaye basu 'boyewa
mahaifiyarsa komai ba, tai musu godiya sossai
tare da yiwa Mustspha nasiha. Najwa tayi kuka
kamar ranta zai fita, washegari taiwa gidan Yaya
Zainab tsinke tun daga soro to soma gunjin
kuka, da 'kyar ta lallasheta tai shiru tare da
yimata bayanin lamarin. Zainab tai jigum tana
jinjina batun kaf yaran mamansu babu wanda
taiwa auran dole to miyasa zata soma a kan
Najwa?. Cikin jimami tace "anya ba laifi kukai
mata ba koke ko Mustaphan?". "Walahi Aunty
baimata komai ba kawai na rasa shin 'KIYYAYA
CE KO SON ZUCIYA Innarmu keyiwa
Mustapha?". Ha'kuri ta bata ta nuna mata
d'akinta "shiga ki wanka duk wani hargitse". Ba
musu ta shiga tai wanka ta kwanta. Sallahr
azahar tai kasancewar d'aya ta gota, tana
idarwa batai adu'aba ta cire abayar gashinta ya
bazo tabi lafiyar katifa ta kwanta.

MAFARKI.
A hankali ta riski kanta a wani daji mai tsananin
duhuwa da koguna, babu abinda takeji sai wani
irin 'kugi da gurnani, a hankali wasu halitu suka
fara bayyana masu launin ban tsoro, kawunansu
manya kamar me, saidai jikinsu na majizai. Can
taji ana 'kwalamata kira Najwa! Najwa!! Najwa!!!
A rikice ta juya tana waige-waige. Karaf ta
had'a ido da fuskar da baza ta mantattaba,
saidai wannan karan sa'banin wancan ne,
maimakon murmushi fuskarta a d'aure take
tamau cikin 'karaji yace " kali nan" a d'imauce
ta juya Mustapha da Mus'ab ta gani wasu
manyan hallitu sun d'add'auresu hannu, cikin
tsananin rud'ewa tai nufin zuwa gur in amma
wasu sar'ko'ki sun mata mugun d'auri ta bud'e
baki tana kuka tana magiya kan ya sakesu. Cikin
murya mara dad'in sauti yace " Najwa waya
gayamiki anayiwa ASHIQ kishiya? Kina neman
cutar dani na'ki JINSINA sabida ke, amma ke
kina neman gujemun, nasanya hijabi tsakaninki
da duk wani JINSI inba nawa ba. Da bana
samun matsala dake shiyasa bana bayyana
kaina a gareki, amma zuwan wan an
BIL'ADAMAN kinsoma yimun taurin kai ko
shimfid'ata nai 'kokarin kiranki saiki kauce
yarana sundaina samun kulawarki. Cikin masifa
Mustapha yace "kai la'anan Allah" cikin jin
haushi ASHIQ yakai masa duka da takobinsa
amma sai wani haske yai sama da mustapha
take takobin ya sauka kan wuyan MUS'AB. A
firgice ta farka tana fad'ar MUSTAPHA!!!!!!!!!!!.A
tsorace takaiwa jikinta bahagon kallo wani
mugun bugawa yai das-das-das sakammakon
abinda ta gani ku biyoni danjin wai me Najwa ta
gani?.
Cikin tsananin razani ta soma duban kusan
da'ita zahiri jinine a jikin rigarta da gefan gadon.
Kanta yai muguwar sarawa ga wata muguwar
fad'uwar gaba. Da sauri Zainab ta shigo tana
tambayar "lafiya Najwa kike 'kara haka kina
kiran Mustapha?". Saita 'kan'kameta tana fad'in
"Aunty kingani" tana nunamata jikinta. Take
Zainab ta tureta tana nuna tsananin jin haushi
"gaskiya Najwa kinfiya abin haushi, period d'in
kikewa wannan wula'kancin?". Cikin rudani ta
furta " Aunty ba period nai ba, kiduba fa sossai".
"To gayamin mekikayi?". Bud'a baki tai da niyyar
bata amsa gam baki ya kulle cikin bagararwa
Zainab tace." Hmmm! Shiga ciki ki gyara jikinki
banasan shirme, koni d'in ba'kuwarki ce?". Take
ta fice ta bar d'akin. Jikinta yai sanyi, tana fita
d'akin ya gauraye da wata irin hargowa
hhhhhhhhhhhhhhh "Najwa kinyi kuskure tunda
kikesan BIL'ADAM zakija na dasawa kowa
tsanarki, zan tozartaki a duniya, ki kasance dani
ni kad'ai zai fimaki kwanciyar hankali". Cikin
kuka Najwa ta bud'e baki zatai magana
fuuuuuuu iskar tabar d'akin. Cikin hanzari ta
d'auki wayarta ta kira Mustapha kira d'aya ya
amsa muryarta na rawa tace "Mustapha! Take
tsigar jikinsa ta zuba ya amsa "ya akai Najwa?
"Lafiya 'kalau kake"? Ta fad'a murya na rawa jin
a yanayin da take yasashi cewa. " Cool Najwa
menene duk kin rikice ne?". Cikin jimami ya
saita kanta "dama........dama" saita kama kame-
kame. Murmushi yai yace "

Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3

Please Login or Register in order to submit comment