Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[12/1, 3:22 PM] +2348037420816: https://chat.whatsapp.com/IpsParMb6dOBXLpns86N2u

°°°°°°°°° _*AMEENATOU*_
_('Yar Kaka)_


*NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼*

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.```
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

*https://www.facebook.com/106494781436168/*

_RUBUTAWA_
_*Xayyeesherthul-humaerath*_

_SADAUKARWA_
_*Nura Sada Nasimat, Allah ƙara Daukaka Oga.*_

_*Domin Farincikin ki kawar arziki irin albarka Ameena Abubakar*_

_NOBLE WRITERS ASSOCIATION ABAR ALFAHARI NA,NA GAIDAKU DUKA,SON SO FISABILLAH🤍_

_*LITTAFINA NA KUDINE NAIRA DARI UKU⚠️*_



*FREE PAGE-1/2*


Wata tsohuwa ce zaune akan kujera 'yar tsugunno tana tankad'e garin masara, a cikin wata 'katuwar 'kwarya.
"Oh! Ni Indo, ko ina Ameenatu ta tsaya ne? A ce tun almuru mutum ya fita har yanzu shiru."
Shiru ta yi kamar wacce ake fad'awa amsa, wani gutun tsaki ta ja ta ce,
"Ni ma na cika mantuwa halin Ameenatu sai dai wanda ba da shi Ibro da Hansai suka haifeta ba, yarinya sai ka ce rainon kaka."

Tankad'enta ta ci gaba hankali kwance, ba tare da damuwar komai ba har ta gama, ta mi'ke ta shiga madafa. Kamar wacce aka jefo ta shigo a guje ta bi ta kan 'kwaryan ta yi d'aki, baki bud'e tsohuwar ke kallon garin da ke zube a 'kasa, sannan ta bi sahun 'kafafunta da kallo, tana shirin magana ta ji sallama daga zaure, tana tsaye a inda take ta bada umarnin a shigo, ta hau 'ko'karin tattara garinta da ke 'kasa.


Ganin mutanen da suka shigo yasa ta d'agowa tare da mai da fuskarta alamun ba wasa, mutune biyar ne sai 'kananan yara 'yan ganin 'kwaf, Tumba mai awara da 'yarta, sai Halliru Mai Kaji, sai wata yarinya da namiji, jikin yarinyar sai zuba yake da manja, sama-sama suka gaisa, d'ayan namijin ne ya ce,

"Mun zo ne domin Ameenatu."

"Uhm ina sauraronku."

"Uwar yarinyar ta aiketa ta kai man ja gidan Sahura doguwa, ta had'u da Ameenatu a hanya, ba laifin zaune tsaye ko kwance ta juye mata shi a jiki bayan ta d'ura mata shi a baki."

Kallon yarinyar ta yi wacce a jiki da tsayi ta linka Ameenatu, nuna ta yi daga sama zuwa 'kasa ta ce,

"Ke kina shirgegeyiya haka kamar buhun siminti ta ya jikata zata yi miki wannan aika-aikar? Kin kwaso wasu 'kafufuwanki kamar fatanya da wannan jemamman tsohon naki kun zo sharrin dai da kuka saba yi ko? Toh ahir d'inku kurwar jikata ko harararta maye bazai yi ba ballantana ci, kai kuma Halliru fad'i naka."



"Zuwa ta yi kamar mutuniyar kirki tana taya Ni aiki da fira, ashe ta sa 'kawayenta su d'ebarmin 'kwayaye, sai da ja'irar yarinyar ta tafi na ga 'barnar da ta yimin."

Halliru Mai Kaji ya kai 'karshen zancen yana haki kamar ya zai sha'ko wuyar Tsohuwar, kallon Tumba da ke cika tana batsewa ta yi ta ce,

" ke ma fad'i kar ta kasheki."

"Ni ai sai na ga fitinanniyar jikar taki ta fito tukunnan."


Ta fad'a tana kallon yarinyarta, wacce goshinta ya kumbura ya yi lemon tsami, ba ta iya bud'e idonta saboda yashin da aka watsawa idon, ga bakinta na jini, fuskar kanta ta canza kammani, kakka'be hannnuwa Tsohuwar ta yi ta ce,

"Ameenatu dai bata nan, sai ki fad'i abin da ke ranki ko ki had'eye abarki."

Dukansu kallon shatin 'kafafuwan da ke zane a 'kasa da gari suka yi, ba sa tantamar Ameenatu tana ciki tana jinsu. Baki bud'e suka maida dubansu ga Tsohuwar, wacce ta 'kara tamke fuskarta.

"Uhm ke fa nake jira, ina da abin yi fa, in ke baki da aikin yi to Ni ina da shi."

Ta fad'a tana kallon Tumba, sannan ta waiwaya ga Halliru ta nunasa da yatsa ta ce,

" Ban ta'ba ganin mutumin banza ba irinka, tsabar rashin mutuncin ka kalli tsabar idanuna ka kira jikata da ja'ira, to babu ja'ira a zuri'ata sai dai ka gani a kanka, da kake maganar sun daukar maka 'kwai, dad'ina da bad'i saurin zuwa, zakkar da baka fitarwa ita suka fitar, ka godewa Allah da ba kazar suka d'auka ba, da kuka kwaso jiki kuka zo so kuke na biyaku, ko kuma na kama marainiyar Allah na jiba kamar jaka, to ba da Indo ba, na daina zubin adashin da babu d'auka ballantana riba, da a ce iya gaskiya kuka fad'a da na biya, amma sai kuka yi rashin sa'a harda sharri a maganarku, dan haka ko gaban Hashimu Mai Gari zaku je ba Baballe Mai Unguwa ba ku je, ku ce Ni Indo Saleh 'kawar wasan 'kasar uwarsa Lantana Sabi'u nace ba zan ba ku ko sisi ba, ku wuce ko fitarmin a gida gayyar tsiya tun kafin nayi muku rashin mutunci, kun ci sa'a yau bana jin rashin mutunci da surutu da kun ga tsiye da ta uwayenku ja'irai."


"Wallahi Inna ki ji tsoron Allah, wannan ba gata kike yiwa Ameenatu ba, a ce yarinya ta yi laifi ba za ki hukuntata ba sai dai ki goyi bayanta, wannan ba gata bane."

"Na daketa saboda gani tsinanniya ko? Na ce na daketa saboda gani tsinanniya ko?"

Gaba d'aya zaro idano waje suka yi ciki mamaki, bud'e baki Halliru ya yi da nufin kare kansu ya ce,

"Inna ba haka muke nufi ba fa, tunatarwa ne dai muke miki."

Wani kuka Tsohuwar ta saki,sai kace wacce aka ce wani nata ya mutu, cikin kukan ta ce,

"Bayan kun kirani da tsinanniya sannan kuma kuka ce min ma'karyaciya, ko iyayenku ba su isa su kira Ni da wad'annan sunayen ba ballantana ku 'kananan 'kwari, bari na nuna muku cewa ku din kananan kwari ne."

Ta'baryar da ke aje a gefen turmi ta d'auko, sanin halin Inna ya sa kafin ta jiyo sai dai ta ga takalma.

"Ai da kun tsaya kun ga 'karshen rashin mutunci marasa mutunci kawai, ke kuma ja'irar sai ki fito ai."




Lekowa tayi a hankali sai da ta tabbatar sun tafi kan ta fito tana kyalkyala dariya.


Taɓe baki Kaka tayi kan ta ce, "Kin ganki nan da wuya kamar mariƙin lema da ma na bari sun jajjaga mun ke ai na huta."


"Yoo su jajjagan mana wa aka ma asara? Kece za ki yi kuka wallahi bani ba,na ga ranar ma ban da lafiya kuka kike ehee sai in mutu ma kowa ya huta tunda kin gaji da ganina kuma ma."



Zaro ido kaka tai kan ta tallafo kan Ameenatou , "Kin ga rufamun asiri bar maganar mutuwar nan, yanzu je kiyi wanka kin ga rabonki da wanka tun shekaran jiya."


"Aradun Allah ba zan ba sai kace wata 'Yar ruwa,ni kifi ma na ke sha'awar ci bara in kira Furera da Lantana muje gun tumbiɗa mai kifi."


Daura hannu akai Kaka tayi.

"Oh ni Indo Allah Na Gode ma da ka bani Ameenatou yanzu duk abun da ki kai yau bai isheki ba sai kin karo wani?"


Ameenatou ta fara tafiya tana tsalle-tsallenta , "ki aje mun ruwan wankan inna dawo zan yi,bara muje gun Alhaji tumbiɗa mu dawo aheee kifi dadi wallahi zan rago miki kar ki damu Babar Maman Ameenatou Indo."


Har ta fita ta dawo aguje.

Sai da Kaka ta firgita.


"Ke lafiya? Me yafaru kuma?"


Buta ta dauka tana nishi, "Wallahi kashi nake ji, kashi zanyi wayyo kashina kar ka fito."



Tsaki Kaka ta yi, "yo ni na zata ma karshen duniyarce tazo ai irin wannan gudu." Ta ci gaba da shararta tana yan wake-wakensu na da.


Ameenatou kuwa kamar an shuka dawa a bandaki tunda ta shiga kusan minti talatin ba ta fito ba.


"Ke Ameenatou na ce ko Barci kika soma a bayinne?"


"Eheeem, eheeem kaka yasin kwan nake kasayarwa."


Sai da Ta kusa Awa daya a bandaki kan ta fito tana nishi.

"Tab wallahi naci kwannan da yawa ni kaina warin yadameni,gidansu Furera mu ka je muka dafe kwayayenmu mu ka cinye su tas." Ta karasa maganar tana kyalkyala dariya.


Kaka ta ce, "kyaji da shi dai."


Ameenatou sai da tazo gaban kaka sannan ta sake mata tusa mai bala'in wari ta fice aguje tana dariya, "Kaka kema ga rabon ki."


Rike hanci ka ke tayi tana masifa, "zaki dawo gidannan ki sameni wallahi sai na rama, har ni za afadawa tusa? Mu da muke adashenta ina jiran ki ba kaffara sai na rama tusar nan zaki sha mamaki."


Ameenatou na fita.......



A ci gaba ko a tsaya?

In ga ruwan sharhi jama'a🤸‍♀️

22/10/2021

_LITTAFINA NA KUDINE DUK MAI SO ZATA TURO DA KATIN 300 TA WANNAN NUMBER 08103080717 SANNAN TA MUN MAGANA AWATSP TA NUMBER KO KUMA ATURA TA ACCOUNT 1453215759 Aisha Abdullahi Sani Acess Bank, THANK YOU OLL,SHARE& COMMENTS FISABILLAH🥰_

_*Urs Xayyeesherthuo🤍*_
[12/1, 3:22 PM] +2348037420816: https://chat.whatsapp.com/IpsParMb6dOBXLpns86N2u


°°°°°°°°° _*AMEENATOU*_
_('Yar Kaka)_


*NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼*

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.```
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

*https://www.facebook.com/106494781436168/*

_RUBUTAWA_
_*Xayyeesherthul-humaerath*_

_SADAUKARWA_
_*Nura Sada Nasimat, Allah ƙara Daukaka Oga.*_

_*Domin Farincikin ki kawar arziki irin albarka Ameena Abubakar*_

_NOBLE WRITERS ASSOCIATION ABAR ALFAHARI NA,NA GAIDAKU DUKA,SON SO FISABILLAH🤍_

_*LITTAFINA NA KUDINE NAIRA DARI UKU⚠️*_



*FREE PAGE-3*

_*XAYYEESHERTHUO FANS CLUB ARADU SHARHINKU NA TAHIYA DANI🤣🥰💃💃INA YINKU IRIN SOSAI DINNAN*


Taci karo da mai tallen alewa.


Tsayawa tai kamar kamila.

"Ina kwana Baba mai alewa?"


Washe baki ya yi,yana "lafiya yar nan,na nawa za abaki?"


"Ni fa da yawa ina so daman kakace ta ce in siyo za ta yi sadaka."


Mai alewa son kudi anji banza.

Tuni ya sauke alewa kasa yana washe baki, "ma sha Allah ki ce yau bani ba wahala anyi an gama duka zan bar miki jaka biyu."


Ameenatou ta washe baki.

"Tab ni dai sai dai in zaka bari jaka daya ai sari zan yi ma."


"Haba yar nan alewar fa ba wani riba duka kudinta kenan."


Ameenatou ta ce, "Shikenan, Shikenan to wallahi na fasa siya." Ta karasa maganar tana kokarin tafiya.


"Haba 'yata ayi haka kuwa? To zo na bar miki jaka daya da rabi,bara ajuye miki aleda."


(Alewar da dukanta ba ta kai na jaka dayan ba ma amman dan son zuciya za a saida jaka daya da rabi,hhhh Alhaji baba anga bati adole za ama 'ya wayo)



"Yawwa to zubamun aleda nikam sauri ina yi kar kakata tamun fada."


"Yi hakuri yar nan yanzu ma kuwa zan sa miki."


Mai alewa harda yar wakarsa yana murna yau ya ci ganima ya zuba aleda tare da mika mata.

"Yawwa yammata bani kudin to."

Kallon cikin ledar tayi kan ta ce, "to rufe idonka ni karka kallemun kudina da yawa kaka tace kar inna ciro kudi gaban mutune."


Rufe idon ya yi yana , "Yo ai da gaskiyar kakarki duniyar nan ce yanzu sam ba yarda."


Kallon tai ta tintsire da dariya.

"Aradu alewar nan taka kwai zaki."


"Bari kawai 'yar nan ai kadan ma kikaji sai kin sha farar can Aradu har wani gardi take."


Yana cikin maganar nan ta zame jikinta ahankali tana dariya.



"wai baki gama ciro kudin bane? Ha'ah wannan kaka taki kwai wayo Aradu zan fa bude idona ni kam."


Shiru dai ba alamar motsi bare maganar Ameenatou.


Bude idon da zai yi ba alewa ba Ameenatou ba kudi.


Suman tsaye ya yi yana.

"Ina ki ke ne? Wai ina ki ke ne? Ince yau gamo nayi da aljana,na shiga uku kudina ."

Zama ya yi awajen kawai ya fara kuka wiwiwi.
Majina na bin hawaye.

Lekosa ta yi tana dariya.

"Wayyo cikina,ji tsoho na kuka, wayyo Allahna."
Kara lekasa tai tana shan alewa tana dariya.


Alhaji Baba mai alewa kuwa kukansa yake yana, "Allah ya isana wallahi,muguwa ja'irar yarinya,Ba zan yafe ba,wallahi ba zan yafe ba koma Aljannarce."


Ganin yaki tashi yasa Ameenatou fara ihu tana.


"Kai Malam,Kai Malam na ce kai Malam." Cikin murya mai tsoratarwa.


Waige-waige ya fara ko zai ga inda ake kiran na shi ammman ina sautin magana kawai yake ji batare da alamun mutum ba.


Ci gaba da magana tayi, "ka bar mana gida,na ce ka bar mana gida in ba haka ba ina daf da shigewa jikinka na fadama zan shiga zan shiga."


Nan da nan cikin tsoho duri ruwa kan kace miye ya fara fitsari a zaune.

Da ta kuma wata kara bai san lokacin da ya zura da wani mugun gudu ba.


AMEENATOU na fitowa dan dariya har da rike ciki tana kwantawa, mussamman inta kalli gun da ya yi fitsari.


Gidan su Furera ta shige tana shan alewarta da yar wake tana dariya.


Innar Furare gwanar kwadayi ta ce, "Ah Ameenatou me aka samo mana ne?"


Murguɗa mata baki ta yi kan ta ce, "Alawar Aljanuce na tsinta a hanya in kuma za ki sha to."


Zaro ido Innar Furare tai , "tab yi hakuri Ameenatou wallahi na koshi ni tsoron Aljanu nake."


Ta kalli Furera , "Ke Zo muje gun tumbiɗa dan wallahi kifi na ke son ci."


Furera ta ce, "Haba Ameenatou dazu fa kina gani da kyar muka sha yanzu in aka kama mu fa."


"Ke dallah bana son iskanci in an samo ma wa yafi ci ina kece da shegen baki kamar sabuwar akuya zauna kar kije ita ma lantanar bani zuwa gidansu Amma ku sani bani ba ku agarinnan kowa ya kama hanyar gabansa,banziya mai idon agwagwi."


Furera ta ji Maganar rabuwa Da Ameenatou tuni ta yi karamar murya, "Goggo Ameenatou dan Allah kiyi hakuri kinji,kar azo tafiya binni ace bani."


Washe baki Ameenatou tayi domin ba abun da ke faranta mata rai fiye da ace Goggo uwa uba kuma ayi maganar birni.


"Kin ci sa'a wallahi yarinya, Allah raya min ke mu sha biki a birni yasin,hhh jeki kiramun Lantus tun yanzu zan mai da ku yan gayu kan Kawu Audu yazo kai mu binni ke Fures ita Lantus."



Lantana zata fita Ameenatou ta ce, "Dalla dawo wawiya ba ki ce mun kin gode ba."


"Na gode Goggo Ameenatou."


"Yawwa yi sauri kuje ku dawo aradu yau tumbiɗa zai sha yasa."


Bai fi minti biyu ba kuwa sai ga Fures da Lantus an shigo.


Ameenatou ta ce, "yawwa wallahi ku goyani mutafi tunda Jiddah matar police ma kawayenta goyata suke."


Ba yadda suka iya haka suka saba Ameenatou abaya tana shan alewarta suna gani ta hana.

"Fures wallahi kibar hadiye yawo ma dan ba sammiki zan ba,ke kam kinyi gadon kwadayi wallahi innarki kamar kuda yaga suga haka take."


Ba abun su tanka ba ta ce asauketa ba ita ba su.


Suna isa gun tumbiɗa Ameenatou ta sauko tana , "Yaya Tumbiɗa wallahi kaf garinnan ka fi kowa iya suyan kifi,har mafarki na yi jiya fa inaci."

Washe baki tumbiɗa ya yi kan ya ce, "Yoo ai na jima da sani kin ga fa har yan binni zuwa suke saye."




Jansa da hira ta fara tana ɗiba Lantana na karɓa.

Duk atunaninsu tumbiɗa bai san me suke ba.


Tumbiɗa irin lutayen mazannanne karfafa masu kirar samudawa.


Sai da ya bari suka diba son ransu suna kokarin fita ya janyo kofar shagon.


Ameenatou ta ce, "Yaya Tumbiɗa zamu tafi ne fa."


Dariyar mugunta ya fara.

"In kinga kun fita agidannan to na maidaku kifaye ne na gasa na siyar."


Jikin Ameenatou ya duri ruwa.

Su Lantana kuwa hawayene kawai ke kwarara.


Tumbiɗa ya ce, "dake Zan fara Ameenatou ina tunaninki duk ban san me kuke mun bane,gani banza ko? Maza zo nan inna maidaki kifin na ga yadda za ki ci ai."


Ameenatou ta gama tsorata baba mai alewaa kawai ta tuna sai ga fitsari ita ma ya fara kwararowa, can kuma ta ce, "Yaya tumbiɗa ba ka ce kana sona ba rannan? Wallahi zan aureka kaji."


"Dagaske zaki aureni?."

Ehmna na fada jiki na rawa.


Washe baki ya yi,"yawwa to ku tafi da kifin da kuka diba duka ga kari ma sai na zo mu zanta ko Amaryar."

Ita ma ta washe baki , "eh sai kazo."


Tana amshewa suka fice adari .

Dan neman Jaraba ta dawo tana, "tumbiɗa mai tumbin giwa wallahi karya nake ma ba zan aureka ba,tab ji ka fa kazami kullum wari wallahi bana sonka wayo na ma ysin." Tana gani ya taso ta zura aguje tana mai gwalo.

Biyota ya yi tana gudu yana yi gashi shi jiki ba kadan ba har tsayawa kallonsa take tana dariya.


Gajiya ya yi ya tsaya yana haki, "zaki sani wallahi ba abun da zai hanani aurenki agarinnan nan da sati daya."


Turo masa baya tai tana.

"Fada ma Duwaisatu ba dai ni ba."


Furera da lantana kuwa sun jima da isa gidan kaka.

Tana shiga suka fara dariya.

Kaka ta ce, "Ya naji zarni wake zarni acikinku kuma?"


Ameenatou ta kalli su Lantana, "wallahi in baku bar mun dariya ba kwalelanku kifinnan,Kaka nice na yi fitsari kuma wallahi ba zan cire kayannan ba jiya fa nasa tab, Tumbiɗa ne ya turfamu ban san sanda na sake masa fitsari ba."

Sallamar da akayine ya katse ma su magana.

"Kaka ga shi kawu Audu ne ya kirawo waya akawo miki."

Amsa tai tana , "to fa Malam Audu da yammacinnan Allah sa dai lafiya."

"Shallo,shallo na ce kana ji na ko?"


"Ina Jinki Inna,ina wuni ina gajiya ya aiki."


"Yoo ni ka daga murya wannan abu naku ba wani nake ba,ehhh fa muna lafiya ya iyalan gidan fatan duk lahiya?"


Ameenatou ta ce, "Kaka kice abawa Okul Al-ameen zan ji muryarsa."


"Toh toh Audu abawa Al-ameen Yar uwarsa na son jin muryarsa."


Dadyne ya mikawa Al-ameen wayar yana "ga shi Ameenatou za ta ma magana."


Rai bace ya karba dan yasan in yaki karba yanzu zai jawa kan shi jidali Yar da bai taba gani ba ta nanike masa.

"Shallo Okul ka mun magana kaji."

Al-ameen ya ce, "kina lafiya?"

Bai jira ta amsa ba ya datse wayar tare da mikawa Dady yana ba network,jin tsanar yarinyar yake ji har ransa mara dalili duk da cewa bai taba ganin ta ba.


Ameenatou kuwa ta dage sai magana take taji shiru

Kuka ta fara, "Kaka ni wallahi ban gama jin muryarsa ba abun ya dauke ni akiranmu shi ni wallahi ban yarda ba."

Birgima ta fara yi akasa tana akira mata Al-ameen

23/10/2021


_LITTAFINA NA KUDINE DUK MAI SO ZATA TURO DA KATIN 300 TA WANNAN NUMBER 08103080717 SANNAN TA MUN MAGANA AWATSP TA NUMBER KO KUMA ATURA TA ACCOUNT 1453215759 Aisha Abdullahi Sani Acess Bank, THANK YOU OLL,SHARE& COMMENTS FISABILLAH🥰_

_*Urs Xayyeesherthuo🤍*_
[12/1, 3:23 PM] +2348037420816: https://chat.whatsapp.com/GeuRcMbmDGuHPBZu4928K8

*IN KINA NA FARKON KAR KI SHIGA WANNAN PLS🙏*


°°°°°°°°° _*AMEENATOU*_
_('Yar Kaka)_


*NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼*

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.```
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

*https://www.facebook.com/106494781436168/*

_RUBUTAWA_
_*Xayyeesherthul-humaerath*_

_SADAUKARWA_
_*Nura Sada Nasimat, Allah ƙara Daukaka Oga.*_

_*Domin Farincikin ki kawar arziki irin albarka Ameena Abubakar*_

_NOBLE WRITERS ASSOCIATION ABAR ALFAHARI NA,NA GAIDAKU DUKA,SON SO FISABILLAH🤍_

_*LITTAFINA NA KUDINE NAIRA DARI UKU⚠️*_



*FREE PAGE-4*


Kaka ta karbi salular tare da mikawa Halliru, "ka ga karba abun ka."


"Haba Ameenatoun Kaka kiyi shiru kin ji zaki kara waya da shi anjima na tabbata Audu zai ƙara kira, kin ga jarumar jikata ba ta kuka sai dai tasa ayi ko?"



Ameenatou ta girgiza kai, "Amman sai har in Zaki goyani inyi barci ni."


Kaka ta wage baki, "ina ni ina daukan buhun sumunti?"

Nan da nan Ameenatou ta kara bajewa akasa , "To ni wallahi mutuwa zan yi in baki goyani ba."


Kan kace me Kaka ta dauko zani ta saba gardiyar jikarta abaya.


Tamkar wata jinjira tai lum abaya.

Su Lantana kuwa sun zama yan kallo ba abun suyi magana ba cibi ya zama kari.


Daga karshe ma Ameenatou cewa ta yi , "Kuma tafi gida wallahi dan ba cin kifinnan za kuyi ba kwalelanku ehee naga ai Tumbiɗan cewa na yi ina son shi, munafukai ku bar mana gida."


Dukkannunsu sai da sukai wani hamshakin hadiyan yawo domin ransu ya gama biyaws Amman ba yadda suka iya.


"Munafukai ku fice mana wallahi."


Haka Ameenatou ta korasu ba dan sun so ba


Suna tafiya kuwa ta dirka abayan kaka ta fara damkar kifi.




"Oh ni Indo Sale Ameenatou anji kunya da rowa ni da uwarki kam ba haka muke, yanzu dai sammun ladan goyo nima."



"Ysn,ysn,ysn dan dai ina sonki ne amman da bazan sammiki ba ."


Dan ficil kamar kuda ta gutsiro ta mikawa kaka, "ga shi dai amaida mugun yawo."


"Yoo ina zan sa wannan? Aiko hanjin wuyana ba zai shige ba."


Ameenatou ta ma kaka wani kallo kan ta ce, "bani,bani abuna nace tunda kin rena."


Tuni Kaka ta zurma abaki tana mamula dan ta san halin Ameenatou sarai zata iya kwace

Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6

Please Login or Register in order to submit comment