Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

karta kashe shi. Abun ya daure wa su Umma kai amma banda ni domin ni nasan komai. Allurar bacci akayi masa ba wuya ya koma barci doctor yace Insha Allah nan da awa biyu zai tashi. kuma zai farka ne cikin natsuwa. Sai a lokacin muka dan kwantar da hankali. Umma ta kira Abban shi ta gaya masa ya farka haka nima na kira gida na fada musu ance nan da awa biyu Habib zai farka. Kafin lokacin tuni Family din biyu an hallara. Kamar yanda doctor ya fada awa biyu na cika Habib ya fara bude ido a hankali. Sannan ya yunkurq a gajiya ya tashi zaune. yayin da su Abba suke taimaka masa. Waige-waige ya hau yi yana cewa bata nan karfa ta zo ta kashe ni". Abban shi yace "Wace ce kuma zata kashe ka din". Habib yace "Indo Fatalwa mana dan Allah kar ku bari ta zo". Abban mu yace "Fatalwa kuma? Habib lafiyan ka kuwa". Yace "Eh Abba a hayyacina nake da idona na ganta duk ciwukan jikina ita taji mun wallahi bata da imani". Kallon kallo mutanen wajen aka shiga yi kafin Habib ya fara bada labari yace........,..............


Koma dai me yace ni kam na gaji yaseen a nan zan tsaya. Tunda Habib aka sambada bani ba.lol


https://www.facebook.com/groups/1232550283531628/







↫ NI DA FATALWA! ↬

{gajeran labari}

Part {10} *The end*

@KINGBOY ISAH


*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*

♥♡❥ ALFAHARI DAKU NAKE MASOYAN LITTAFAINA A DUK INDA KUKE. NA GAIDA MASOYAN ALJANA KURIYYA DA KANWARTA MARIYYA NA LITTAFIN MIJIN ALJANA. DA KUMA MASOYAN ALJANA SAFURATU TA LITTAFINA ALJANAR FATIMA. BAN MANTA DAKU BA MASOYAN SMASHER NA LABARIN ALJANA CE. GA KUMA MASOYAN FATALWA INNA INDO GAISUWA NAKE. KU KASANCE DA NAKU KING BOY ISAH MAI GURIN NISHADANTARWA FADAKARWA AND WA`AZANTAR DA KU A KO DA YAUSHE.❥♡♥

Habib ya fara da cewa. "Karfe shida da rabi na dawo daga wajen aiki. Abun mamaki ina zuwa kofar gida sai naga gidan a bude. bayan kuwa nasan Khadija da tsoro ba zata iya barin gida a bude ba. Bayan na saka mota cikin gida sai na shiga falo inata sallama amma shiru ba khadija. Hakan yasa na shiga cikin daki a zatona ko tana ciki ne amma sai ban ganta ba. Na tura ban daki naga nan ma a bud bata nan. Nan take zuciyata ta hau suya. Wato khadija har tana da ikon fita daga gidan nan ba tare da izinina ba? Lalai zata dawo ta same ni. A zuciya na fadi haka cike da kunar rai. Na ajiye jakar dake hannuna bayan nayi wanka na dawo falo Abun haushi har lokacin Khadija bata dawo ba dare kuma ya farari domin bakwai da rabi. Na fiddo wayata na kira number khadija amma sai ji nayi waya tayi ringing a kusa dani wato a nan ta bar wayar. na dauka hade da yin tsaki a zuciya nace yaushe Khadija ta fara bin gidaje yawo gashj har dare yayi bata dawo ba? Ni a zatona batayi nisa ba tundq ta bar gida a bude kuma ga wayarta ma a gida. Haushi da takaici suka ishe ni jira nake kawai Khadija ta dawo domin ta karbi hukunci. Dan kwanciyar da nayi ne barci yayi gaba dani. Ina fara barcin nan Kuwa na fara mafarka na abu tsoro kala kala. Ji nayi ana daddabata ana kiran sunana alamun tashina ake daga barci. Bude ido da zanyi sai ganin wata mumunar fuska nayi mai ban tsoro wata mace mai sanyi da bakakke kaya doguwar riga. hakan yasa na kwalla ihu kafin in tashi zaune na nema matar sama da kasa na rasa. Lokacin na lura da an kawo wuta. Kirjina yana bugawa domin na tsorata sai dai ina tantama matar nan a mafarki ne na ganta ko a farke. lokacin na kara kiran khadija amma sai ji nayi shiru kamar maye yaci shirwa. Na lashe wayata karfe tara da rabi. nan take haushi yq kara rufe ni. wato Khadija bata dawo ba har yanzu
Tashi nayi naje kitchen na dakko bredi da juice na zo na kunna kallo na fara ci. Ana cikin haka naji an bude kofar kitchen da karfi ina waigawa naga wani bakin abu ya shiga kitchen din a guje ya rufe kofar. Cikin gaggawa na tashi na bude kitchen din na leka ko'inq Amma banga kowa ba. Na fito yayin da na dawo sai gani nayi babu biredin da nake ci juice din dake cikin jug ma babu an dauke sannan na duba ni da nake kallon MBC 2 sai gani nayi an maida ni mbc Bollywood abun ya ban mamaki sosai. zaunawa nayi naci gaba da kallo ko minti biyu ba ayi da zamana ba naji ana kwankwasa gida da karfi. tun daga falo na fara fadin waye? waye jira a bude ma?. Ina zuwa na bude sai gani nayi wajen wayam ba kowa. Ana cikin haka naga wani abu baki kamar doki ya nufo ni a guje. ba shiri na mayar da gidan na kulle na koma ciki a razani. Naje wucewa kawai naji an tada mota ta ina lekawa naga wani a ciki na dauka barawo ne hakan yasa na dauki wani icce dake kusa dani kafin in zagaya na bude motar sai gani nayi ba kowa kuma motar ta kashe kanta. Ana cikin haka sai ji nayi an kure volume kallo da nake yi a falo da gudu na karasa ciki amma sai banga kowa ba. Na dauki remote na rage. Lokacin fa abun ya fara bani tsoro. Ina cikin kallo naji an dungure ni ta baya na juya da sauri banga kowa ba. Nan take kuma sai naji wani iska mai karfi ya shigo cikin falon ina jiyawa naga fankoki ne suke gudu kamar zasu cire. na tashi a rikice nakashe su. Kukan dan jariri naji a cikin dakin da muke kwana tsoro ya fara ziyarta ta a lokacin a hankali na nufi dakin ina lekawa naji shiru jaririn ya daina kukan. Kai in takaice muku labari ban sama hutu ba har wajen karfe dayan dare abubuwa ne suke faruwa na ban tsoro makamantan wannan. karfe biyun dare ina zaune a falo domin sam na kqsayin barci har kwantawa nayi amma sai naji ana kirqn sunana a falo. na fito kumq banga kowa ba. Ina zaune sai gani nayi kofar falo ta bude wani iska mai karfi ya shigo isakan ya farq rikita abubuwan daki marar nauyi irin su labulaye da sauran su. kujerar dake saitin kofa naga ta matsa da kanta kamar an ture ta. yayin da naga tayas din wajen ya fara banbarewa. bayan ya gama fashewq can sai gani nayi an zuro hannu ya hudo ta karkashin kasa. Tuni tsoro ya kamani na fara karkarwa. dayan hannun ya karq hudo kasa ya fito hannu ne mai dogayen yatsotsi gq farcina dogaye suma can jimawq sai gani nayi kan mace ya hudo mai matukar ban tsoro. Idonta daya ya kwakware gefan fuskar ya rube wasu irin tsutsotsi na yawo. Hakoran kuwa bakikirin sai wani abu yake zuba daga cikin bakin. Nan take matr nan ta kaure da wata irin dariya mai firgitarwa wanda gaba dayan dakin ne ke amsawa. Ni kam tuni na fara karkarwa sai dai kuma kamar an rufe bakina nq kasa yin addu'ah kuma na kasa tashi in gudu. Sai dq matar nan ta gama fitowa daga cikin kasa gaba daya sannan ta mike tsaye ta dage kai sama ta kyalekyale da dariya cikin muryarta marar dadi ta fara magana.
"Kai Habib ka sani kayi kuskuren kama gidan nan gidan haya domin yau matar ka ta jawo ma silar ajalinka. Ni ce nan *Fatalwa Aisha Indo* kuma nan gida nan ne. Ba wanda ya isa ya zauna a cikinsa. Yau matar ka khadija tayi yunkurin kashe ni sannan ta gudu. Na bita domin in kashe ta amma sai dai gidan da ta shiga akwai tsari shiyasa ban shiga ba. Tunda kuwa nayi alkawari bazan karya ba yau sai na kashe ka". Tana fadar haka ta bushe da dariya Na mike cikin karfin hali nace "Karya kike shedaniyar aljana ki sani kinyi kadan kuma baki isa ki kashe ni ba. Sannan yanzu...". Kafin in rufe baki sai gani nayi kan Indo yayi jawur alamun taji haushi tayi nuni dani da hannunta nan take wani haske ya fito ya dauke ni ya rada da kasa. Kafin in mike ta sake daga ni da asiri irin nasu aljannu ta kama wulwulawa dani tana dakani jikin bango. Ana cikin haka ne na ruga da gudu daki na samu sa'ah na rufe dakin. ina tunanin na tsirq amma sai gani nayi ta ratso ta cikin bango. Nan take taci gaba da wahaltar da ni har wajen karfe hudun dare. Sai sannan na samu na fara addu'ah da kuwa kamar bakina ya kulle na kasa addu'ah. Har tayi mun jina jina. Tana ji na fara addu'ah sai ta fara wani irin ihu ta farq daukana tanq bugawa da kasa. Tana cewa in daina addu'ah Amma naki a haka ne ta sa wani irin haske ya daga ni sama na rabu da kasa. Lokacin kuw na karanta ayatul kursiyyu da la'ilafi na tofa mata. Sai ji nayi t saki ihu wuta ta kamata sai ci take da wuta. Ni kuma ta sake ni a lokacin ne na fado kasa kaina ya fashe ban sake sanin a ina nake ba sai yau da na farka nq ganni a nan asbitin". Kowa na cikin hospital din yayi tsananin mamaki. nan take aka kama yi mana barka ni da Habib. Abba yace inyi hakuri da rashin fahimta ta da yayi. Nace ba komai Abba. Bayan sati guda Aka sallami Habib daga Asibiti domin yaji sauki sosai. Muna komawa gida yasa akaje aka kwaso duk kayana dake wancan gidan na fatalwa Habib yaje sukayi lissafi da mai gidan aka biyashi kudin wata goma domain bqmuyi wata biyu a gidan ba.
Da ya tashi kama mana gida sai da ya nema na tsakar gari sannan shima sai da ya tabbatar nan kusa da mu bq makabarta. Watarana muna hira nace "Habib ya labarin Inna Indo fatalwa shin ta mutu ne dq wutar ta kamata ko kuwa?". Harare ya watso min yace "please karki sake tuno min da wannan Indo fatalwa din". Da jin haka na bushe da dariya......

TAMMAT BI HAMDULILLAH..

A NAN NA KAWO KARSHEN LITTAFIN NI DA FATALWA. KUNJE YADDA TA KASANCE TSAKANIN INDO FATALWA DA KHADIJA AMARYA. ABUN TAMBAYAR A NAN SHIN INDO FATALWA TA MUTU NE TA BAR GIDAN KO KUWA TANA NAN? NI DAI BAN SANI BA AMMA DAI GIDAN YANA NAN WANDA YAKE SO ZAI YI SABON AURE ZAN MAI JAGORA HAR GUN KAI GIDAN DOMIN YA KAMA HAYA. KUNGA SHI ZAI GAYA MANA INNA INDO NA NAN KO KUWA.LOL

MASU JIRAN *FESHIN JINI* DA *NI DA YAYA SAIFI* IN SHA ALLAH BAZAN SAKE WANI NOVEL DIN BA SU ZANCI GABA DAYI TUNDA YANZU NA SAMA YAR AKWALAR WAYATA. LOL


MASU SAN FESHIN JINI KO NI DA YAYA SAIFI DAGA FARKO ZAKU IYA BIYO NI TA WHATSAPP DOMIN IN TURO MUKU AMMA DOCUMENTS NE. GA NUMBER WHATAAPP DINA 08096831009. AUTAN MARUBUTA NAKU KING BOY KECEWA A HUTA LAFIYA

https://www.facebook.com/groups/1232550283531628/



An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels


Book Chapters
Chapter 1Chapter 2
Chapter 3

Please Login or Register in order to submit comment