Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

Murya yace "momy wannan abincin zai tsinkemin kunne"

Momy na daga parlo tayi dariya ta kalli Hamud kana tace "ga mutuminka can yana aikin daya saba"

Hamud yayi dariya kafin yace "momy wannan gurin ɗiban girki baya wasa"

Bayan ya kammala cin abincin ya fito hannunsa riƙe da tissue paper yana goge bakinsa,

"Acici mala'ikun tauna baki baya zama sai ya ci"

Hamud ya faɗa yana shafa sumar kansa ya miƙe yabar gurin.

"Daka tsaya mana da kaji amsa"

Lirwan yace yana kallon momy dake yi musu dariya.



Ƙarfe sha ɗaya suka shigo Kaduna, aka saukesu a television garej, suna tsaye masu napep da mashina sunata cewa "Hajiya tafiya ne?"

Hajiya Indo tace "mezai kaini hawa mota a wannan tashar, gara in fita bakin titi inhau mota nera ɗari,

Hanan tace "nidai yunwa nakeji ki siyamin koko da ƙosai"

Hajiya Indo ta zarewa Hanan ido kafin tace "ke wato har kinga fuskar cemin in siya miki wani abu? nima banci ba, kuɗin da kikaga na bayar kuɗin masu dashi ne na tattaro shine nayi kuɗin mota, ko Allah zesa mu yagi rabonmu"

Hanan tayi shiru bata sake magana ba,

Suna tsaye a bakin titi Bus tazo wucewa, Hajiya Indo tace "Kinkinau"

Matemakin mai motar yace "muje mota ta cika"

Suna shiga motarsu ta ɗaga sai zuwa Kinkinau, a bakin titi aka saukesu tsakaninsu da gidan babu nisa, Hajiya Indo ta miƙa masa nera ɗari, suka wuce.

"Abinda nake so dake shine, ki nutsu fa su gidan ƴan gayu ba'a yi musu hauka yanzu sai su miƙa mutum ga hukuma"

Hanan tace "ni wlhi duk inda zasu kaini su kaini indai zasu bani shayi da burodi"

Hajiya Indo ta maka mata duka tana cewa "ai bama zakiji abinda nake faɗa miki ba kenan?"

"Naji"

Hanan ta faɗa a fili, a zuciyarsa tace "yabi ruwa ai ba ibada bane".

A bakin wani haɗaɗɗen get suka tsaya, Hajiya Indo tayi nocking, mai gadi ya leƙo ta ƙaramar ƙofa yace "waye?"

Yana ganin Hajiya Indo ya washe baki kafin yace "Barka da zuwa banma ganeki ba, dan kin kwana biyu rabonki da gidannan"

Hajiya Indo ta washe haƙorai tama tare da haƙorin Kano wato na Makkah tace "Hajiya Rashidan tana ciki?"

"Eh tana ciki amma inajin fita zatayi dan tasani wanke mota ɗazu"

Hajiya Indo tace "to bari muyi azamar shiga"

Suka wuce ciki.

Da shigarsu gidan Hanan ta riƙe baki, sakamakon ganin tsarin ginin gidan da flowers ɗin da sukayi luf gunin sha'awa, daga can ƙofar da zata sadaka da parlon Hajiya Rashida akwai wasu flowers a gefe da gefen ƙofar a cikin wata roba mai kyau, kasancewar tsaftace gidan da akeyi yasa duk wanda ya shigo sai yace ,sabone alhalin matar gidan zatayi shekaru ashirin da aure,

Hajiya Indo ta rangaɗa sallama cikin ɗaga murya,

Daga can ciki aka amsa kafin wata yarinya ƙarama ta fito wacce batafi 8yrs ba, kanta yasha kitson kalaba yarinyar fara, tana sanye da riga da skirt ɗan kanti, sosai tayi kyau itama ɗin kamar Hanan mai surutu tace "su waye ku?, momy tana wanka tare da dadyna"

Hajiya Indo ta zato ido, a zuciyarta tace "banda tacewar iskanci wankan ya gagareta ita kaɗai har sai ta haɗa da gardin mijinta"

A fili tace "zamu jirata ashe kin daɗa girma?"

Yarinyar ta washe haƙoranta wanda rabi giɓi ne tace "sunana Munipa"

"Ai ban mance da sunan naki ba jeki ce momynki tayi baƙi"

Munipa tace "toh"

Munipa ta ruga da gudu taje bedroom ɗin momyn tace "momy wata mata tazo wajenki"

Hajiya Rashida tace "to kikace mata inayin me?"

"Nace kina yiwa dady wanka"

Hajiya Rashida ta buge mata baki tace "surutunki yayi yawa fa"

Abu Uzaifa yace "haba momyn Munipa har tayi abin duka?"

Tayashi shafa mai takeyi ta bari ta fice tunda yana goyon bayan abinda tayi,

Tana isowa parlo ta washe baki sakamakon ganin mutuniyar Tata Hajiya Indo, Hajiya Rashida tace "Barka ashe kina hanya? wlhi ko jiya sai da nayi maganarki"

Hajiya Indo tace "aiko dai, mun shigo garin naku"

Hajiya Rashida ta tafi kitchen ta ɗibo musu soyayyen dankalin turawa da ƙawai ta ajiye musu ta buɗe fridge ta ɗibo drinks ta ajiye kafin ta kawo musu plet tace "wlhi ko girki banyi ba"

Hajiya Indo tace "abubuwanne sai a hankali, dama ƴar aiki na kawo miki"

Hajiya Rashida tayi murmishi kafin tace "ikon Allah ni yanzu bana ɗaukar yara wlhi, tunda na ɗauki wata yarinya ƴar ƙauyen Kano tun tana kamar wannan" ta nuna Hanan, taci gaba da cewa, naketa yi mata hidima, wlhi data girma cemin tayi wai Abu Uzaifa yana birgeta shine jikina yayi sanyi"

Hajiya Indo tace "inna likahi kice yaran sun koma tabbatattu banda baƙin hali ba ina kai ina mijin uwar ɗakinka mai temaka maka"

Hanan taga dai ba'ace taci abinci ba, tayi jiran harta gaji, kasancewar bata jurewa yunwa cikin marairace murya tace "in..inajin..."

Bata ƙarasa maganar ba, sakamakon Hajiya Indo data galla mata harara,

Hajiya Rashida ta fahimci abinda Hanan ɗin takeso,

"Kici mana"

Hajiya Rashida ta faɗa tana kallon Hanan,

Jikin Hanan na rawa ta dinga loma da dankalin, saboda tsabar laushinsa har wani bata tsunawa, tunda taji ba irin na garinsu bane, dankalin Hausa.

Sunanta hira ashe har ta cinye ta kora da fanta ta gora, saukar gorar da Hajiya Indo taji ne yasata kalli Hanan ɗin, a tunaninta dataga kular a rufe ko ta rage mata ne, sukaci gaba da hira, har Abu Uzaifa ya kira Hajiya Rashida ta tafi gurinsa,

Hajiya Indo ta buɗe kula taga wayam babu komai, ga wata uwar yunwa dake addabarta tashi ɗaya, tama rasa abinda zata cewa Hanan ɗin tsabar haushi, sai tace "Allah zai sakamin, dan yanzu ina dukanki zaki taramin mutane, wlhi idan aka samu gidan aikin dazan kaiki sai na ciri ɗari biyar a ciki"

Hanan tayi gyatsa tana shafa ciki, wani abun haushi ma batace wa Hajiya Indo komai ba sai rarraba idanu da takeyi.

Rashida ta dawo hannunta riƙe da kuɗi ta miƙawa Hajiya indo,

"To abin arziƙi muka samu?"

Rashida tace "Dadyn Munipa ne yace abaku 3k"

Hajiya Indo tace "aiko mun gode Allah ya saka masa da aljannatul firdausi"

Hajiya Rashida tace "amin, na tambayeshu zan rakaku gidan ƙanwar Ummana idan kun gama sai mu tafi, ina tunanin ƙila ta ɗauketa tunda naga ma'aikatan gidan ana ɗibarsu da yawa"

Hajiya Rashida tace "to Allah yasa a dace mun gama"

Ta faɗi maganar tana hararar Hanan.

Munipa ta taho da gudu tana cewa "momy anata kiranki a waya"

Hajiya Rashida tace "shine sai kinyi gudu?"

Ta ƙarɓi wayar, tana shirin kamawa kiran ya katse, cikin sauri tabi kiran tana cewa "aikuwa ƙanwar Ummana ce"

Hajiya Indo ta fara adu'a ranta, Allah yasa a dace idan ba haka ba ta shiga uku dan kuɗin da ake bata ajiya ne ta tattara ta taho dasu, da taga su Hanan sunzo da babanta shine tace musu tana shirin zuwa Kaduna, shikuma mai mashin dama sunyi dashi zai kaita tasha domin taje anguwar bawa sarin ɗanyar masara, dayazo tace tasha ze kaita.

Hajiya Rashida ta ajiye waya kafin tace "gaskiya tace "a halin yanzu yaran da sukeyi mata aiki sunkai biyar"

Gaban Hajiya Indo ya bada rass ta fara tunano kuɗin mutane, tazo dubu huɗu zata koma Allah masani ko nawa ne, gashi dai sun sami dubu uku, aciki ma sai ta cire kuɗin abinci, dan idan taci gaba da dauriyar wannan yunwar zata faɗi,

Ƙauye••

Jiki a sanyaye malam Junaidu ya shiga gidan tare da tsoron masifar Inna meramu, bai ganta a tsakar gida ba, yasashi shigewa ɗakinsa a hankali, ashe tana ganinsa ta labule kasancewar ba me duhu bane,

Cikin masifa ta miƙe tare da fitowa ta faɗa ɗakinsa tace "wai kana nufin nice baiwarku da zan dinga shiga nemo wannan makirar yarinyar? kwanaki nace maka bin maza takeyi kace ƙarya ne, yanzu ai kaga tabbacin abinda nake gaya maka ko?"

Malam Junaidu yace "dan Allah ki ƙyaleni ƙafata tana zugi idan kinada man zafi ki bani in shafa"

"Inna Meramu ta riƙe baki, kafin tace "yau naga makirci irinna munafurci wato saboda bakasan a faɗi lefinta shine zaka dinga yimin wani irin magiya ko?"

To ɗazu Usaini ya aiko ƙanin mahaifinsa da kayan lefe tunda nayiwa baba Isiyaku magana har an karɓi kaya an kawo sadakin aure, nace musu da bakinka kace a aiwatar da komai, tunda naga ka tafi yawo, nasan zakayi farinciki da hakan yau nayi abin farinciki ban mu tafa?"

Malam Junaidu ya juya zai fice tace "ah ko abinda nayi beyi maka bane?"

"Eh"

Kawai ya faɗa tare da ficewa yana juya kai alamar rashin jin daɗin abinda ta aikata, shikuma yaɗau alwashin ko dubu nawa ya kawo Hanan bazata dawo ƙauyennan ba bare ta shiga gidan masifa insha Allah.

Acan gidan Usaini kuwa, da kansa yake shafen farar ƙasa a wani ɗaki daya gina daga can nesa dasu, hatta ginin ma da kansa yayi,

Matan suna zaune sunanta gulmarshi, Hauwa tace "nidai da akwai inda zanyi inbar gidannan wlhi dana bari, ban taɓa nadamar shigowa ba sai da ya zagemin iyayena jiya akan nayi miya da yawa, dan nasa kuɓewa ƙulli biyu, Ladidi tace "nifa kamar masifarshi a kaina ta ƙare kullum yazo kwanciyar aure dani sai kiji yana cewa wai bayajin daɗi"

Walhi gwara Iyami yana ji da ita sosai kodan bata taɓa aihuwa bane?"

Hauwa tace "nidai da nice Iyami wlhi guduwa zanyi banga amfanin zamana a gidannan ba, banda ƙaddara da kwaɗayi mezai kawoka?"

Iyami ta taɓe baki kafin tace "koni nagaji da zaman gidannan kawai dai ina zaune ne, yaushe naga ƙofar fita ma bare in leƙs in fice?, kudai muyi adu'a Allah yasa ya gyara halinsa ya tabbatar da abinda yake yi ba mekyau bane"

Usaini yana daga can gurin ginin amma yace "sannunku munafukai, baku da aiki sai yi da mutum wlhi idan na sake jin Muryar wata ita zata surfa gero mudu ashirin"

Ko wacce tayi gum, saboda sunsan inhar ya fad'i magana sai ya aikata,

Yaran ma idan sun haɗu a ɗaƙi basu da zancen daya wuce hakan duk da basu taɓa leƙa wajen ba amma suna san ganin ko meye a wajen.

Bayan ya gama shafen yace "Iyami kawomin ruwan wanka"

Iyami ta miƙe jiki na rawa taje rijiya taja ruwa takai masa banɗakin daya kasance zagaye da karare ta ajiye, ta mance batace masa ga ruwan nan ba yana fitowa ya watsa mata mari da kafcecen hannunsa ya wuce.

A gigice ta durƙusa a gurin, sakamakon azabar dake addabarta a kumatunta, tama godewa Allah dayasa babu kowa a cikin gidan bare afara magana akai, tayi ɗaki idonta na zubar da hawaye...!



Hello fans labarin yayi muku kuwa???

08141799224 Mom Islam

*WAKE ƊAYA💍*

MomIslam

_True life story_

*Arewabook@momislam11*

🆓 Page 4

Harya fito daga wanka taji alamun ajiye bokitinsa tana kuka, bawai kukan marin da yayi mata takeyi ba, kukan rayuwar ƙunci da rashin ƴancin kai shi takeyi,

Daga can bakin ƙofa yace "an ƙona manajan da nace adinga shafawa kuwa?"

Iyami tayi tsit kamar ruwa ya cinyeta, bai shigo ɗakin ba ya wuce nasa ɗakin yana sababi harda cewa "nakusa yin amarya sabuwa fil duk wannan iskancin da kuke yimin zaku dena"

"Usaini ka siyo mana man shafawa rabonmu da shafa mai wlhi bamace ga ranar ba"

Hauwa ta faɗa tana daga bakin ƙofar Usaini,

"Ke mekikaji nace jiya lokacin dana taraku dukkanku?"

Hauwa tace "oho ina naji tunda ba abinda ze yuwu ka faɗa ba"

"Da sauri ya fito yana gyara mazugin wandonsa yace "wato kuna nufin kunaso kufi ƙarfi nane?, wallahi nasha gabanku sai amarya tazo duk wani iskanci nasan zaku dainashi, ga Iyami nan ma da kwata-kwata shekarata biyu ne a gidannan kun koya mata tsuguddidi da rashin kunya"

"Nifa kaga ba shine ya kawoni ba ka bani man shafawa dan nasan a ɗakinka baza'a rasa ba"

Cikin zafin rai ya wanka mata mari kafin yace "yau babu abinci a gidannan ku rubuta ku ajiye, me ragowar kokon safe tasha da ƴa'ƴanta wacce batadashi tayi ta hamma"

Yana gama faɗar haka ya koma ciki,

Sosai ran mutan gidan ya 6aci sakamakon Hauwa data janyo musu masifar zama da yunwa, gashi yanzu har ƙarfe tara da rabi na rana,

Iyami ta fito jiki a sanyaye ta ɗauki manja ƙulli ɗaya, kasancewar komai ƙullashi akeyi a leda, manjan ma befi na nera ashirin ba, sbda a ƙiyasi befi cikin cokali biyu ba shine nayi abinci,

Iyami ta ɗibo karare ta haɗa wuta tasa kwanon da take soya mai ta soya manjan har sai da yayi fari kafin ta sauke, daya huce ta juye a roba ƙarama ta koma ɗaki.

Duka yaran sun taru kashi-kashi, Sahura da kasancewar Hinde ce budurwa a cikinsu, yasa ta tara yaran masu wayo tace "wai kuna ganin bazamu gwada fita waje ba watara?"

Sahura tace "wlhi baba bashi da Imani kalli fa inda yake dukan su Hauwa, Hinde ta taɓe baki kafin tace "ina sha'awar fita waje domin inga ko meye a wajenan"

Sahura tayi tsaki, kafin tace "ina gaya miki lefin baba kekuma kina cewa zaki fita waje, idan kin fita ina zaki kuma da wane idon zaki kalli baba"

Hinde ta lumshe kyawawan idanuwanta kafin tace "idan har Allah ya bani iko na fita a gidannan wallahi bazan dawo ba, ga gurin zuwa da yawa, gidan mahaifiyar baabata nan zani"

Sahura ta riƙe baki, tasan tunda Hinde ta fara aikata hakan to babu mamaki zata iya fitar, saboda Hinde wata irin yarinya ce mai saka abu arai, inhar kuma tasa abun a ranta sai ta aikata ko zai zamo matsala a gareta, ga kafiya ga taurin kai bugu da ƙari tanada kyau mai ɗaukar hankali, amma chocolate color ce, tanada matsakaicin baki, idanuwanta ƙanana masu kyau,

Sahura tace "nidai ina roƙonki idan zaki fita a gidannan ki sanarwa baba"

Hinde ta buge bakin Sahura kafin tace "idan na sake jin maka manciyar maganar nan wlhi sai na illataki kin Sanni kin san halina"

Sahura tace "naji babu wanda zan gayawa"

Barira wacce ta kasance mai shekara 15 tazo kusa dasu tace "me ake cewa ne?" Hinde da Barira suka harareta, bata da yawan magana shiyasa aka bawa Hinde girman saboda tsaurin ido irin nata,

Washe gari Juma'a, mutanen gidan sunata hada hadar girkin abinci tun bayan da suka gama dakan kunu aka sha suka shiga yanka kabewa wanan na gyaran shinkafar tuwo wannan na markaɗa tumatur wannan na kula da fannin girki haka sukeyi ranar juma'a, lokacin da aka sakko sun kammala girkin kowa an samasa a kwano ko wacce ta koma ɗaki, Hinde ta shigo ɗaki tabar gurinsu Sahura, Barira na ganinta tace "mekuma ya faru?"

Hinde ta taɓe fuska kafin tace "Baabata zan bar gidannan saboda kema ki fita a wannan rayuwar, da sauri Hauwa ta kalli Hinde saboda mamakin maganar da tayi, musamman da takeda ƙarancin shekaru,

Hauwa ta riƙe baki tare da kallon bakin ƙofa tace "Hinde karki bari mutanen gidannan suji wannan maganar saboda zasu iya gayawa mahaifinki"

Hinde tace "nifa yanzu bana tsoronsa kune masu tsoronsa"

Hauwa tace "ina tausaya miki inhar kika bar gidannan mahaifinki zai cutar dani bayan haka kuma tausayinki nakeyi idan yaganki a waje zai iya kasheki"

Hinde ta kamo hannun Hauwa kafin tace "idan na fita zan nemi gidan iyayenki ki gayamin ina ne?"

Hauwa ta fashe da kuka kafin tace "rabona da ganin wani nawa yau shekara goma kenan tun dana haifeki ko na aihu babu mai zuwa gurina"

"Baabata ki rubutamin duk wani abu na gidanku tunda kince kinyi karatun Arabia"

Jikin Hauwa na rawa ta ɗauko alƙalami tayi rubutu a wata takarda kafin tace "kina fita a ƙofar gidannan ki miƙe gabas sosai hanya ce anan ne zaki hangi titi, ga wannan ƙuɗin nayi ajiyarsa tun zuwana gidannan kinga ma sanyi ya fara kamashi"

Hinde tace "baabata idan ba'a karɓi wannan kuɗin ba zanyi aikin kuɗi insha Allah"

Hauwa tace "dan girman Allah karki zubar da mutuncinki a matsayinki na ƴa mace"

Hinde tace "nayi miki alƙawarin hakan bazai faru ba"

Hauwa ta ƙulle mata takardar a cikin jakar kuɗin tace "akwai wani malami yana zama a cikin masallacin juma'a kiyi masa magana kice ke ƴar Hauwa ce yarinyar Usaini mai gidan duhu"

Hinde tace "to"

Daganan sukaci gaba da shawarwari tana sake kwantarwa da mahaifiyarta hankali tace "naji baba yana cewa yau zeje Jos yana tafiya nima zan fita"

Hauwa ta share hawaye kafin tace "babu ƙofa a gidannan ko kinzo fita ƙofar zata rufe kuma ta cikin ɗakinsa take"

Hinde tace "nifa duk wannan ba damuwata bane"

Hauwa tace "Hinde kina bani mamaki baki taki komai ba kike cewa zaki fita"

Daga tsakar gida sukaji Muryar Usaini yana cewa "toni zan fita zanje Jas banda shashanci"

Babu wanda ya amsa masa, Allah ya temaka ma ba takalmin suke sawa ba bare ya gane su nawa ne a ɗakin, ya fice ba tare da ya shiga ɗakin kowa ba.

KD

Hajiya Indo da Hanan suna tafe a motar Hajiya Rashida zuwa gidan ƙanwar Ummanta, sannu a hankali suke tafiyar har suka isa anguwar Sarki, a bakin get ɗin suka tsaya tare da danna horn mai gadin ya leƙo ya koma kana ya wangale musu get ɗin, suka shiga, nan fa kallo ya koma sama, hausawa sukace shaho yaɗau Giwa, duk yawon Hajiya Indo bata taɓa ganin gida mai kyau irin wannan ba, ya haɗu matuƙa, Hanan kuwa sai rarraba ido takeyi, har Hajiya Rashida tayi parking suka shiga ciki, da shigarsu da sallama suka sami hajiyar tana zaune da wasu maƙudan kuɗaɗe a gabanta kan table, Hajiya Indo ta lashe baki a zuciyarta tana aiyana wannan kuɗi kamar baza'a mutu ba?"

Sai da hajiyar ta gama lissafi kafin tace "ƴata kune a gidan?"

Munipa taje da gudu ta faɗa kan hajiyar, Hajiya tace "ƙawata anata girma ga haƙora na cirewa"

Munipa tayi dariya tana rufe baki, bayan sun gaisa Hanan dake zaune akan kafet itama ta gaisheta, Hajiya Rashida tace "Hajiya dama wai yarinyar nance ake don sama mata aiki koda a gidanki ne idan zamu samu"

Hajiyar ta jinjina kai kafin tace "leƙa kitchen kigani wlhi ƴan aiki sunkai biyar a haka ma inasan in sallama wasu, bari a kawo muku ruwa"

Rashida ta sauke nannauyar ajiyar zuciya kafin tace "to ko hanya ta gurinki bazamu samu ba?"

Hajiyar tace "zaku iya samu tunda inada ƙawaye, zaki tafi da ita gidanki ne kokuma zaki barta anan duk abinda ya wakana sai a sanar dake?"

Hajiya Indo tace "to nidai duk abinda akayi amma yau nakeson komawa gida"

Hajiya Indo ta faɗi hakanne domin taji ta bakinsu shin me zasu ce?

Hajiya Rashida tace "a'a mu koma gida idan har aka dai-daita da masu ɗaukar Hanan ɗin sai ki tafi, abar Hanan ɗin anan"

Cikin jin dadi tace "to" sai kuma ta ɗaure fuska tace "to yanzu sai gobe kenen? duk da dai dayau da goben duk ɗaya ne a gurin Allah babu damuwa,

Sukabar Hanan anan gidan sukuma suka kama hanyar komawa gida,

Suna cikin tafiya Abu Uzaifa yakira Rashida a waya, tana ɗagawa yace mata ya dawo gida bayajin daɗi,

Rashida ta ƙara bugun mota jikinta a sanyaye suka ƙarasa gidan,

Koda ta wuce bedroom ɗinta bata ganshi ba, ta dawo palo ta nunawa Hajiya Indo ɗakin kwana kafin ta koma bedroom ɗinsa ta sameshi a kwance jikin ma yayi sauƙin dama ciwon kai ne,

A hankali ta isa gareshi ta rungume shi tana cewa, "babyna jikinne ko yayi sauƙi"

"Yayi sauƙi karki damu Alhmdulilah"

Hajiya Rashida tace "to yanzu me kakeson ci?"

"Tea kawai zaki haɗamin is ok"

Ta fice kai tsaye ta nufi kitchen ta zubo ruwa a flaks ta haɗa masa tea ɗin mai kauri kafin ta kawo masa yashs.

Acan ɓangaren Hajiya Indo kuwa, ta gaji tayi lilis sai kuma tunanin farauto zuciyar Abu Uzaifa ya fara kamata, a fili tace "gaskiya mijin Rashida yayi min kyau wlhi ina sonsa da zeyi ta biyu dani wlhi dana more da nafi ko wacce mace sa'a"

Ta runtse ido tana tuno ta ina zata sami phone number ɗinsa?

Ta rasa ta inda zata samu bare tabi hanyar, da wannan tunanin bacci ya kwashe ta har akayi kiran sallahar magriba bataji ba tana bacci,

Hajiya Rashida ta shigo tana sanye da riga da skirt na atamfa ya mugun matseta komai ya fito sosai ajikinta saboda yanayin zaman ɗinkin, tace "Indo ki tashi an shiga Sallah"

Indo ta miƙe ido yayi ja saboda bacci gashi bai isheta ba,

Ta kalli Rashida tace "to Nagode"

Rashidar na fita Hajiya Indo tayi tsaki mtsww tare da cewa "wlhi tallahi sai na mallaki zuciyar mijinki da izinin Ubangiji"

Tana gama faɗar haka ta buɗe toilet ɗin dake gefe a cikin ɗakin ta shige tayi alwalah ta fito ta shimfida sallahya ta kabbara Sallah.

Abin mamaki gari yayi duhu, duk da ba'a mamaki da ikon Allah, bata ta6a tunanin kwana anan gidan ba, ko lokacin da take zuwa, iyakacin ta bada ƴan aiki ta wuce.

Acan gidan Hajiya kuwa, Hanan ta sata magana kamar zata ari baki,

Lokacin da Hajiyar ta shiga Sallah tana dawowa ta samu Hanan a zaune akan fridge hannunta riƙe da DuDu drink, sha takeyi tana lumshe ido, hajiyar tace "dan Allah a gidanku ba'ayi miki faɗa ne?"

Hanan tace "wlhi ƴan gayu kuna morewa shiyasa bakwa tuna Allah...

Hajiya ta riƙe baki a fusace ta....!

Ya kunshi cakwakiyar cikin labarin, masoya ayimin afuwa inhar kuna comments zango gaba da posting

*ALBISHIRINKU MASOYA MAKARANTA LITTAFIN MOM ISLAM, IDAN BAKU MANCE BA A CIKIN LITTAFINTA MAI SUNA _Falak🍒_AN ZUBA RUWAN BASIRA DA HIKIMA GURIN SARRAFA LABARIN, MARUBUCIYAR BATA YI ƘASA A GUIWA BA TA SAKE KAWO MUKU LITTAFINTA WATO _Guntun Goro_SHIN KUNADA LABARIN JARUMAR DA JARUMIN CIKIN LABARIN KUWA?? KARDAI IN CIKAKU DA SURUTU LITTAFIN _Wake ɗaya💍_ YAZO DA ZAZZAFAN SALO WANDA ZAI RIKITA TUNANIN MAI KARATU, LABARIN _Hanan marainiya da gidan Usaini mai gidan duhu_SHIN KUNSAN GWAGWARMAYAR DA TAKE FAƊAWA A GIDAN AIKI, TANAYIN NASARA, MEYASA IDAN TA HAƊU DA PRINCE JABEER FATAR JIKINTA KE SAUYAWA KUWA? AMSARKU TANA CIKIN LITTAFIN _Wake ɗaya💍_KUNADA LABARIN LITTAFIN YA TAƁO YARUKA HAR GUDA UKU MUSAMMAN MA GIDAN YARBAWA DA AKE KWASAR GWARAMA?, LITTAFIN BA ANAN YA TSAYA BA HARDA SIRRUKAN ZAMA DA MAI GIDA INSHA ALLAH, MAZA KU GARZAYO DOMIN KARATUN FITACCEN LITTAFIN DAYA BAZA MEDIA, KARKU BARI A BAKU LABARI, MUNA YIWA MASOYANMU GODIYA A DUK INDA SUKE*

Gamsu neman ƙarin bayani ku tuntuɓi wannan lambar, 08141799224 Mom Islam takuce..



*WAKE ƊAYA💍*

MomIslam



_True life story_





*Arewabook@momislam11





🆓 Page 5



Hajiya tace "waye ya gaya miki bama tuna Allah?"

Hanan tayi shiru, sai Kuma tace "dan Allah zan roƙeki wani abu ki taimaka min Hajiya"

Hajiya tace "ina jinki"

"Rabona dacin nama wallahi tun sallar laiyya da aka yanka mana bunsuru"

Hajiya ta zaro ido kafin tace "kina nufin kinkusa shekara kenan?"

"Eh wlhi ki taimaka inajin kamar zan ciji mutane"

Ai da gudu Hajiya taje kitchen, ta ɗibowa Hanan nama cikin kwano mai murfi harda ruwan sha, Hanan ta sakko tana rawa tana tafi tana cewa "a haiyye zamuci daɗi, a haiyye munzo binni da ƙafar dama"

Ko uffan hajiyar batace mata ba ta shige ɗaki ta barta a gurin.

Rashida••

Ta kawowa Hajiya Indo abinci mai rai da lafiya, soyaiyyar taliya mai haɗe da kayan lambu a fili ma ta bada kala inaga a ankai baki?"

Cikin farinciki Hajiya Indo tace "Nagode Allah ya biya ki"

Rashida tace "Amin to sai da safe"

Hajiya Indo tace "to Allah ya tashemu lafiya"

"Ke ƴar gayu harda saka wasu tsinannun kaya sai kace wata roba a ƙauyen mu wai ita Binta tsirara, mtsw"

Sai kuma takai lomar abincin bakinta, lumshe ido tayi ta buɗe kafin tace "wai-wai ai sai ya tsinke kunne, barin samu leda insa naci a mota gobe"

Cikin sa'a ta buɗe loka dake gefe ta samu leda, ta raba abincin gida biyu kafin tasa Kashi ɗaya a leda taci ragowar.

Tana gama ci aka kira sallahar isha'i ta kuskure bakinta kafin tazo ta kabbara sallah, tana idarwa tayi adu'oi harda na mallakar Abu Uzaifa, daga nan ta ninke sallahayar ta bi lafiyar gado, a fili tace "ban taɓa jin jimamin rashin miji ba sai yau"

Ta runtse ido, nan da nan bacci yayi awon gaba da ita.

Acan ɓangaren su Hajiya Rashida tace "Please baby idan ka gama cin abinci inason muyi magana"

Abu Uzaifa yace "to momyn Munipa ina jinki"

Hajiya Rashida ta kwanto a kafaɗarsa kafin tace "uhm dama inason zuwa gobe idan Allah ya kaimu kakai wannan baƙuwar tamu tasha idan sun gama abinda sukeyi Please tanada kirki wlhi"

Abu Uzaifa yace "hamm Rashida kenan, nifa ban cika son ɗaukar mutane a mota ba gaskiya kice tahau haya"

Hajiya Rashida ta haɗe fuska cikin fushi tace "to ai naga na isa dakai tunda kai mijina ne shiyasa nace haka"

"To tunda kin matsa shikenan Allah ya kaimu goben"

"Please akwai wata tambayar ma"

Ya zuba mata ido yace "ina jinki"

"Meyasa bazaka dinga hutawa Weekend ba"

Abu Uzaifa yayi murmishi yace "zan huta wataran".



Ya kalli Munipa da tuntuni tayi bacci yace "Munipa iyayen surutu anyi bacci"

Washe gari.

Ranar ta kama asabar, an tashi da sanyi mai shiga jiki, tun bayan sallahar asbha da sukayi basu fito ba, suna rungume da juna cikin blanket, Hajiya Indo na taja bargo tanason azo a
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3Chapter 4Chapter 5

Please Login or Register in order to submit comment