Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

nasiha akan su yaqi shedan su tsarkake zuciyoyinsu duk da yasan tana taimakon hafsatu da wasu ayyukan kamar yadda ta ke wa uwarta duk ranar girkinta,

Zata tayata ayyuka da dama Amma Babu wata doguwar magana shiyasa itama hafsatu Bata takurawa Maryamah din da magana sbd tasan ko ahakan yarinyar tanada tarbiya sosai tunda ko kallon wulaqanci bare rashin kunya batai taba mataba.



Tana kwashe kayan ta kai madafin ta aje ta dawo ta wuce ɗan ƙaramin ɗakinta ta kwanta ba bacci za ta yi ba wayarta ta ɗauka Android me arhar kuɗi wanda Abban nata ya siya mata ta hau chatting sai wajen 11:30pm ta kashe wayar ta kwanta don tana da lactures ɗin safe 8 za ta bar gida.



Washe gari karfe takwas daidai Maryama ta fito cikin shirin fita makaranta tana sanye da riga da zani da suka amsa jikinta ta yafa mayafi me Dan girma sbd Maryamah ba laifi tanada ilimin addini sosai hakama tanada irin yanayi na rayuwar uztazan Yan mata.,



Baƙace Maryamah amma kyakykywace sosai tanada jiki Mai kyau da kyakkyawar fuskar Mai kyau itama.



A falon nasu ta samu Abbah da su Ummanta suna kalacin safe ta tsuguna ta gaida su gaba ɗaya a jam'i tana ɗauke idanunta daga duban sashin da Amarya Hafsatu ke zaune ta zauna daga gefen Ummarta ta zuba kunun tsamiya da ƙosai ta fara ci.



"Maryamah ƙarfe nawa za ki dawo daga makarantar yau?"



Abbanta ya tambaya idanunsa a kanta, sai ta ɗaga kai ta dubesa tana amsa shi da cewa,



"Ƙarfe biyu Abbah."



Malam Adamu ya gyaɗa kai yace"



Madallah, Ga kuɗin motarki na kwana biyu zan baki don tafiya Lokoja ya kamani sai jibi zan dawo idan Allah Ya yarda.



Ya yi maganar yana zura hannu ya zaro kuɗin ya miƙa mata

Maryamah ta amsa kuɗin ta yi godia tana cigaba da cin abincin har ta kammala Ta yi wa Abbah da Umma sai ta dawo ta fice daga falon.



Bayan tafiyar malam har kusan yamma tana dakinta Bata fitoba

Ta muskuta tana sake rintse idanunta kewa da kaɗaicin rashin abokin hira ko wanda za ta yi walwala tare da shi na sake danne zuciyarta

ta buɗe idanun tana janyo radio ta kunna don shi ne abokin hirarta idan Malam ya fita kasuwa ko idan ya yi tafiya baya gari gaba ɗaya don sam bata iya fita zaman falo sabida gujewa ɓacin rai da kallon ƙasƙanci daga abokan zaman gidan.



Wannan shi ne kalar irin rayuwar da Hafsatu ke yi a gidan Malam Adamu tun da ya auro ta shekaru biyu da suka wuce har kawo yau da take ɗauke da cikin watanni bakwai Sam Ummar Maryamah da ita kanta Maryamah basu taɓa nuna cewa akwai lokacin da za su amsheta da daraja,

Basa zaginta basa komai hakama basa Shiga sanbarta,



Anty hadeeza kuwa Sam batayi Mata kallon mace ma take gani bare harta dauketa kishiya ko cikakkiyar mutum ma,

Ita ko Maryamah tsakaninta da ita gaisuwar safe ce idan ta gaidasu a tare da iyayenta sai sallama idan tashigo guri hafsatun na gurin.



Hafsatu abin na damunta ƙwarai gashi Malam ba mai son shige shigen gidajen maƙwafta bane bare ta yi ƙawaye waɗanda za su dinga ɗebe mata kewa Mace ɗaya ce dattijuwa da ta saba da ita me suna Iyah me ƙosai ita ma ɗin ita ke shigowa gidan ba Hafsah ke zuwa nata gidan ba kwana biyu ma tayi tafiya ta tafi can garinsu shiyasa bata da abokin hira sai dai ta shige ɗaki ta kunna radio ta yi ta saurare.



Ƙarfe biyu Maryama ta shigo gidan tana tafiya tamkar ba za ta taka ƙasa ba sabida gajiya ta wuto matsakaicin tsakar gidan nasu ta shigo zuwa falon gidan Cikin sa a tana sanyo kai cikin falon idanunta ya sauka akan Hafsatu da cikin jikinta ta yi saurin kawar da kanta ta raɓa Hafsatu za ta wuce sai Hafsatu ta yi ƙarfin halin kiran sunanta,



"Maryamah"



cak ta tsaya ba tare da ta waiwayo ta dubi matar uban nata ba



Hafsatu ta sake cewa,



"Don Allah ki taimaka ki amso min batir a shagon nan kusa damu don Allah!"



juyowa gaba ɗaya tayi ta zube idanunta akan Hafsatu ta kalleta kamar ba za amsa kuɗin ba sai kuma ta karba batareda tace komaiba ta raɓata ta fice don zuwa yi mata saƙon.



Ajiyar zuciya me sanyi Hafsah ta sauke tana jinjina irin wannan halayya ta Maryamah gashi ita Kuma kaman mayya Allah ya saka Mata kaunar maryamah din cikin zuciyarta.



"Gashi!"



Shine kalmar da Maryamah ta furta da muryarta me nutsuwa lokacin da ta shigo cikin falon tana miƙawa Hafsatu manyan batira biyu da ta siyo mata.



Karba tayi tana cewa,



"Na gode Maryamah."



Daga haka dukkansu suka shige ɗaki ba tare da Maryamah ta sake furta ko da kalma guda ba.



*********

Bayan watanni biyu cikin Hafsatu ya shiga watan haihuwa wata ranar asabar da misalin ƙarfe shida na safe naƙuda ya kamata aka kaita asibiti.



Bayan ta sha matuƙar wahala ta haifo kyakykyawar yarta mace fara da ita babu in da ta baro kamannin Hafsatu tamkar an tsaga kara.



Malam Adamu da maƙwafciyarsu Iyah me ƙosai dattijiya me shekaru hamsin su ne ke tsaye daga bakin labour room ɗin suna dakon haihuwar Likitar ta fito ta sanar da su an sauka lafiya tare da miƙa musu Babyn wacce aka naɗeta cikin showel da kayan sanyi farare ƙal

Hannun Malam Adamu har rawa ya ke yi lokacin da ya amsa jaririyar yana ƙare mata kallo wani irin ƙaunar Yarinyar na huda zuciyarsa Ya yi mata addu'a tare da miƙawa Iyah ita yana kutsa kansa cikin ɗakin da aka fito da Hafsatu bayan an gama kintsa ta ganinta cikin ƙoshin lafiya ya sanya shi yin hamdala da jin ƙarin farin ciki mara misaltuwa.



Bayan sun dawo daga asibiti zuwa gida ne Iyah ta wanke jaririyar tas Aka sake naɗeta cikin kayan sanyi sai a lokacin Umma da Maryamah suka shigo ɗakin don ganin Baby.



Maryamah tun kallon farko dataiwa babyn taji jikinta na neman sanyi sbd haka kawai taji kaman qaddarartace aka haifo Mata.



Hadeeza ma bayan ta gama ƙarewa jaririyar kallo ne ta aje ta tana duban Hafsatu ta miƙe tana cewa,



"Allah shi raya mana ya baki lafiya."



Daga haka ta fice daga ɗakin ba tare da ta sake cewa komi ba maryamah na bayanta.



Bayansu hafsatu tabi da kallo ƙwalla na taruwa a idanunta sbd tana kaunarsu Kuma tana Jin inama Suma zasu Dan kaunaceta su dukan zuciyoyinsu su huta da wannan zaman quncin dasukeyi su dukan.



"Hafsatu ki yi haƙury da halin abokiyar zamarki da ƴar mijinki ki rungumi ƴarki ta zama abokiyar hirarki da shawaranki idan Allah ya raya miki ita Ba lalle sai kowa ya soka a duniya za ka rayu ba

bai zama lallai sai waɗanda ka ke tare da su sun nuna maka ƙauna ba

ki godewa Allah ba cutar da ke suke yi ba kawai dai basa shiga sha'aninki ne kuma basa maraba da ke a cikin gidan Kuma Inshallah wataran hakan ma saikiga ya wuce Kun zauna cikin walwala kaman baayiba

don haka ki yi haƙury tunda ke ma gashi Allah ya baki rabo sai ta zama abokiyar ɗebe miki kewa."



Iyah ta yi maganar tana duban yadda hawaye ke gudu a idanun Hafsatu

ta cigaba da rarrashinta da kalamai masu daɗi har sai da ta tabbatar Hafsatu ta samu nutsuwar zuciya.



Kwanakin da suka biyo baya gaba ɗaya Iyah ce ke shigowa tana hidimar kula da Hafsatu tunda bata da kowa a garin Kano bata da wani sauran gata da dangin da za su iya yo tattaki tun daga Adamawa su kula da ita ba.



Ranar suna Jaririya ta ci suna ZAINAB sunan mahaifiyar Malam Adamu da ta jima da rasuwa ba wani taro aka yi sosai ba daya wuce maƙwafta da jama'ar arziƙi da ya ke huɗɗa da su a unguwar Sabida shi ma zuwa ya yi garin Kano don kasuwanci, amma asalinsa ɗan Lokoja ne ba shi da ƴan uwa sam a garin sai dai abokan kasuwanci da maƙwafta kawai.



Iyah ita ta dinga kulawa da Zaynab da Hafsatu har suka gama wanka

sam bata taɓa gajiyawa ba tamkar jikarta ta jini haka ta ɗauki Hafsatu shiyasa Hafsatun ke jin cewa bata da tamkar Iyah don ta maye mata gurbi da dama waɗanda danginta na jini ne kawai za su iya mata hakan.



Har kawo wannan lokacin da suka gama wanka koda wasa Maryamah bata taɓa shiga ɗakin Hafsatu ta ga ƙanwarta Zaynab ba tun ɗaukar da ta yi mata ran da aka haifeta bata sake daukantaba saidai lokuta da dama idan Hafsatu tafito da zainab din haka zata ringa kallonta tanajin rashin nutsuwar zuciya.

Daga Iyah sai Malam Adamu su kaɗai suke nuna soyayyarsu ga Hafsatu da jinjirarta Zaynab harsun Saba.



Watannin Zainab shida da haihuwa ciwo me zafi ya kama Hafsatu aka wuce da ita asibiti kwananta tana jinya Ubangiji ya amsa rayuwarta ta bar jaririyarta Zaynab.



Faɗin irin tashin hankalin da Malam Adamu da Iyah suka shiga ba zai faɗu ba, don rumgume gawar matarsa ya yi yana kuka me asalin motsa zuciyar duk wani me saurarensa.



Har aka kai Hafsatu makwancinta Malam Adamu baya cikin hayyaci da nutsuwarsa tun yana kuka da idanunsa har ya koma na zuci wanda yafi na fili illah.



Daga Hadeeza har Maryamah mutuwar Hafsatu ya doke su matuƙa sbd halayenta masu sanyi da hakuri duk da kusan su dukan sunada hakr sosai sai dai lokacin da aka watse zaman makoki sai kowa ta koma sabgar gabansa Iyah me ƙosai ita ce ta sanar da Malam Adamu cewa za ta riƙe masa Zaynab har zuwa lokacin da za ta cika shekaru biyu ko uku sai ta bashi abarsa ya baiwa matarsa riƙonta Sabisa ta san Hadeeza ba za ta raini Zaynab a yanzu ba Ranar Malam Adamu yayi sabon kukan rashin hafsatu dukkanin ƙauna da soyayyar da ya ke ma Hafsatu sai ya dawo kan Zaynab har ma da ƙari.



A kwana a tashi Zainab tafara wayo yar kyakkyawa da ita da kamanninta na uwarta na sake bayyana matuƙa kamar yadda kullum kwanar duniya ake sake ninka ƙaunarta a zuciyar Malam Adamu Koda wasa Umma da Maryamah basu taɓa cewa za su shiga gidan Iyah su ga Zainab ba tun Iyah na mamakin ƙarfin halinsu har ta daina ta cigaba da kula da Yarinyar har ta cika shekara guda tana gudunta ko'ina Duk in da suka shiga da Zainab sai an yabi kyawunta shiyasa Iyah ke dagewa wajen yi mata addu'a sabida gudun bakin mutane.



Zainab na cika shekaru biyu da rabi Iyah ta tattaro kayanta ta dawo ma Malam Adamu da ƴarsa hannunsa domin ta so cigaba da riƙon Zaynab amma sai aka aiko cewa mahaifiyar Iyah babu lafiya dole za ta tafi jinyarta acan gida ƙauye Hakan shi ya tilasta dawo ma Malam Adamu da riƙon ƴarsa Zaynab hannunsa wannan ne kuma ya zama silar da riƙon Zainab ya dawo hannun Umman Maryamah wacce daga ita har Maryamah ba su taɓa nuna so ko qi wa zainab ba.



Kasancewar Malam Adamu tsayayye kuma jajirtacce a gidansa shiya sanya Umma ta kasa cewa ba za ta riƙe masa Zainab ba

Don haka ba don ranta ya so ba ta amshi riƙon Zainab.

##MAMUH#

#LIFE#

#LOVE#

#SISTERS

#CHILDREN#



*_ZAFAFA BIYAR_*



*RUMBUN K'AYA*🔥

Hafsat Rano



*DAUDAR GORA*🔥

Billyn Abdul



*IDON NERA*🔥

Mamuhgee



*A RUBUCE TAKE*🔥

Safiya huguma



*KI KULANI*🔥

Miss xoxo





Littafi daya---400

Biyu---600

Uku----800

Hudu-----1k

Biyar din duka----1200



ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN



0022419171

Maryam sani

Access bank



MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN



09166221261



🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪

*Ina yan uwa 'yan nijer?*

*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*



+22799643131



Littafi daya---450CFA

biyu---650CFA

uku----850CFA

hudu----1050 CFA

Biyar----1250CFA



*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*

*Thanks for choosing us*🔥

*_IDON NAIRA_*

_Mamuhgee_

_Arewabooks@Mamuhgee_

*_Zafafa biyar 2023_*







2

A hankali Zainab tafara girma tare da samun kulawa daga wajen Abbansu Malam Adamu wanda duk wata hidimi na Zainab shi ke yi tun dawowarta gidan Dan Zamanta a hannun Umma Hadeeza ya zama sunane kawai sbd bata san duk wata wahalar kulawa da ita ba sai idan Malam ɗin ya fita kasuwa ne kaɗai ta ke yi mata abinda ta ga za ta iya, amma daga wankan safe zuwa shiryata da bata abinci da duk wata hidimarta Malam ɗin ke yi da safe kafin ya fita sauran Kuma zatayi abinda taji zata iya Wanda bazata iyaba Maryamah tayi iya Wanda taji zata iya itama,

Idan ya dawo zai tadda tana buƙatar wani sabon gyaran haka zai zage ya sake mata wanka ya sauya mata shiga sannan su haɗu aci abinci yana bata abaki sbd bazata iya ci da kantaba.



Maryamah bata taɓa janyota a jikinta ko sau ɗaya ba bare ta hidimta mata,bata taɓa nuna so ko qi akan Zainab dinba yanda ta yi treating mahaifiyar Zainab lokacin tana raye haka take treating Zainab ɗin

Hasalima ko sakin fuska daga gareta Zainab bata gani sai ya kasance ma tsoron Maryamah ya shigi Zainab ɗin ta yadda ko kusa da Maryamah bata son zuwa Dan gwara mahaifiyar Zainab din da batada irin kamewar fuskar Maryamah sosai.



Ummar ma sam bata janyota a jikiba saidaj Bata kame mata fuskarta sbd ganin bazatama iya wahalarda kanta da daure dauren fuska da damuwaba akan jinjirar yarinya hakama ba wani boyo ta fifita soyayyar ƴarta akan Zainab sosai da sosai Shiyasa Zainab din tun shekarun nata Basu wani tasaba gane batada uwa kuma ta taso da tsoransu da rashin sakin jiki da su har tayi girman fara zuwa makaranta saidai Abbansu na dawowa tana walwalarta da farin cikinta sosai kaman kowanne yaro.



Rashin kulawar umman Maryamah akan Zainab baya damun Malam kaman rashin kulawar Maryamah akanta da rashin shaquwa ko kaunar junansu..



Abin Yana tsananin damunsa da basa tsoro sbd Maryamah ita kadaice Yar uwarta dasuke jini daya yake Kuma fatar ta zamewa Zainab din gata idan sun hade kansu a gaba har zuriarsu,

Fatansa burinsa su zama tsintsiya madaurinsu daya har tsufa da zuriarsu,

shiyasa yake jin damuwa akan halin ko inkula da rashin kulawar Maryamah din akan Zainab.



yayi faɗa yayi nasiha har ya gaji ba wani sauyin arziki ya hakura ya zuba musu ido tare da cigaba da inganta rayuwar tasu da adduar hadin kansu su dukan.

Karshe dai kasa hakuri yayi ya dauko tsarin zaunawa dasu biyun idan har Yana gida to Yana tareda Maryamah din da Zainab Yana fira dasu tareda jansu a jikinsa sosai ko hakan zaisa kauna da shaquwar dayake fata su shiga tsakaninsu.





Umma Kuma tana ganin Zainab tafara girman da zata iya wasu ayyukan saita raba musu aiki wanda kusan ayyukan Zainab din sunfi na Maryamah yawa a cewar Maryamah karatunta yafi wahala tunda har yamma take kaiwa ita Kuma Zainab yanxu nema take Shirin shiga secondary.



Kafin ta tafi makaranta da safe sai tayi aikin shara da wanke wanke kafin ta tafi hakama tana dawowa sallah da kawai takeyi saita Kuma shara da wanke wanke da wasu Yan ayyukan ta wanke uniform dinta kafin taci abinci ta wuce islamiyya.



Tana qara girma kuwa hatta wankin umman da Maryamah ce keyi ya dawo kanta

Maryamah ma umman tayi tayi tabarwa Zainab wankinta taringa yi Amma tace Sam Bata buqata sbd ita irin mutanen ne da idan basa son abu ko kaunarsa to ko wahalardashi basa iyayi sbd kadama komai ya hadaka dasu shiyasa ko aikin wahala Bata damu data bawa Zainab din tai mata ba saida idan batanan umma tabawa Zainab wankinta Amma indai tana Nan Bata so itace takeyin abinta.



Rashin sabo da haniya da rashin abokin hira a gida da bata da shi sai ya kasance Zainab din ta taso a miskili batada surutu ko rawar Kai ko makamancin hakan shiyasa ko a makarantar boko da islamiyya batada qawa ko daya Kuma daidai gwargwado tanada qwaqwalwar daukar karatu hakan ya qarawa malam qarfin zuciya akanta da sake dauke ido akan rayuwar dasukeyiwa Zainab din tunda Basu cutatar da itaba Kuma Basu fito sun furta mata qiyayyaba Kuma lurada qaunarta dayake bayyanarwa da tausayinta shike sake neman dagula Yar qaramar zaman lafiyar da akeyi a tsakaninsu sai kawai yaringa binsu da adduar shiriya su dukan har umman

Kuma tunda dai Zainab din na fira dashi harda dariya sosai ba laifi hakan ma Allah ya shirya masa su gashi dama Sam umma Bata taba yimata horon yunwaba abinci ake Bata yanda ya isheta tunda ubanta ke kawowa.



Maryamah tagama karatunta tuni harta gama service dinta aiki takeson farawa Amma abban nasu yaqi amincewa sbd shekarunta sun qanqanta da fara wannan rayuwar Dan hakan yabawa manemin aurenta damar fitowa ayi aurensu saita fara aikin nata acan.



Barr Asadullah Muhammed Ismail shine Wanda yake neman maraymah din da aure tun Bata gama karatu ba,



Shima tuzuru ne sosai Dan ya jima Yana aiki batareda yayi aureba harya fita cikin layin samari,



Babban lauya ne me zaman kansa hakama Dan kasuwar gaske Wanda ya Tara abin duniya maana arziki sbd gadon arziki da kamfanona dayayi daga mahaifinsa tsohon minister kafin ya rasu haka su din asalin ya kogi state ne aiki da kasuwanci ya dawo dasu arewa.



An sanya ranar auren Maryamah da Asadullah watanni uku masu zuwa Dan haka umma da abban nasu suketa Yan shirye shiryensu sbd su din bawai masu kudi bane rufin asiri ne kawai gashi gidan arzki Maryam din zatai aure sbd sosai dangin Asad suka fara hidima suna barin dukiya a harkar auren.



Zainab tafi kowa shedan son da Maryamah kewa Asad sbd Bata taba ganin abinda yake saka Maryamah farin ciki da walwala harma da bayyanuwar hakorantaba gurin bayyanarda farin ciki irin a ambata sunan Asad wanda suka jima tare Dan haka har cikin ranta sai itama take farin ciki da bikin auren.



Haka Umma kullum ta zauna Batada zance me dadi saina irin daula da arzikin da Maryamah zata shiga a gidan auren,

Alfahari takeyi sosai akan auren me kudin da 'yarta zatayi abun har Yana sirkawa da kaman gori ga Zainab wadda batama San bambamcin rayuwar aure gidan me kudi da me rufin asiriba Dan haka ita Sam batasan da ita akeba sai aikin hidimar wahala datake fama dashi kullum.





A ranar alhamis Babu makarantar Islamiyya wankin kayan umma tayi da nata harma dana Abbansu

Tana gamawa tayi wanka ta shiga dakinsu ta shafa Vaseline ta saka atamparta doguwar riga tana cikin saka hijib zata fito taje Aiken umma taji sallamar maza a tsakar gidansu Dan haka ta qarasa sakawa da Dan sauri Dan fitowa taga masu sallamar sbd Dama itace me fitowa tarban baqi Koda yaushe...



Jin sallamar maza yasa yau har umma da Maryamah dake dakinta suna magana tasowa suka fito dukkaninsu kusan a tare..



Idanuwansu ne suka sauka akan Malam Adamu da ake shinfiɗewa kan tabarman da Zainab ta shimfida tun kafin tayi wanki,



Umma ce tayi saurin ƙarisowa wajen tana duban mutanen da ke gyara masa kwanciya akan tabarman cikin matsanancin firgici da tashin hankali ta ce,



"Lafiya me yafaru da shi ne haka?"

Me nake gani haka kamar jini a tufafinsa?

Innalillahi.





Cikin wainda suka shigo dashi dinne makabtansu ya dago ya duba umman a sanyaye da mutuwar jikin tausayin malam din yace,



"Wallahi hatsari ya samu akan hanyar dawowarsa acan bakin junction na layin Nan wani me mota ya kaɗesa akan mashin ɗinsa sosai

kuma shi me motar ya gudu abinsa shi ne muka ɗakko sa zuwa gida kafin akawo motar da isyaka da akaje Kira..



Umma da su Maryamah cikin matsanancin tashin hankali da tsoro suke kallonsa



Zainab tuni hawaye suka fara gangaro mata cikin matsanancin tsoro da tashin hankali da tausayinsa,



Umma da Maryamah jikinsu rawa kawai yake dauka

Umman ta buɗe baki kenan za ta yi magana wani matashi ya shigo da sallama yana cewa,



"Ku fito da shi ga motar isyaku nan za mu kaisa asibiti"



Sake daukansa sukai suka fita akai asibiti dashi umma da Maryamah suka rufa musu baya cikin adaidaita aka bar Zainab din ita kadai a gida tana neman fashewa da kukan firgici da tsoron kada wani abu yasamu abban nasu.







Har aka kira sallar magriba su Umma basu dawo ba bare taji a wani hali Abban ke ciki,

Ga tsoronta sai qaruwa yakeyi musammam ganin har aka fita da abban hancinsa da kunnuwansa jini sukeyi Kuma iya ko magana ba bare budu ido ya kallesu.



Sai ana kiran sallar Isha'i su Umma suka shigo gidan Umma na kuka sosai kaman mayafinta a hannu

Maryamah kuwa ko ganin gabanta batayi sosai sbd tashin hankali tafiyar kawai takeyi kaman me koya.



hakan ya sake ɗaga hankalin Zainab da ke zaune har lokacin a tsakar gida tana zare ido cikin rashin sanin abin yi,

Murya na rawa tace"



"Umma ya jikin Abbah?

ya yi motsi ya farfaɗo kuwa?"



kamar Umma ba za ta ce komi ba sai kuma ta tuna yadda Abbah ke ta kiran sunan Zainab ɗin lokacin da ya farfaɗo

sai ta juyo murya na rawa itama tace,



"Da sauki ya farfaɗo amma yana jin jiki, ga idanuwansa ance daya ya fashe"



Hawayen Zainab ne suka qara gudu jikinta yaqara daukar rawa a tsorace tace"



Umma dan Allah akaini can na kwana gurinsa inason ganinsa Dan Allah umma...



Kasa tankata umman tayi suka wuce sukabarta tsaye tanajin tashin hankali da tsoro na shigarta,

Abbansu kawai takeson gani itadai ko hankalinta zai kwanta,

Ita ko a kwancen ne tanason tagansa.



Ganin duk sun shige bamai kulata Dole ya hakura ta shige itama

Haka gidan yayi tsit kaman gidan ba kowa sbd damuwa

Su umma Kuma sunacan suna rankon sallolin da basuyiba a asibiti.





Misalin ƙarfe takwas na safe Umma na tsaye a kitchen tana ƙarisa zuba farin kokon data Dama Dan zuwa asibitin duk da malam Kam yai nisan da ba iya Shan kunun zaiyiba Dan harsuka baro bai farfadoba Amma Kuma gwara takai din Koda Allah zaisa asamu sauki ya iya farfadowar,



Zainab ce ta shigo kitchen ɗin ta gaida Umman tana tattara kayan wanke wanke zata fitar tayi batareda umma takalletaba tace"



Kibar aikin kiyi Shirin makarantarki Dan bazan iya jiran ki gamaba kafin na fita yazu nakeson isa asibiti rufe gidan zanyi idan kin dawo kinyi



Dan dakatawa tayi ahankali daga tattara kayan cikin sanyi tace,



"Umma yau ba za ni makaranta ba, ina so aje da ni in ga Abbah."



Kallonta umma tayi zatai magana sallamarsu Malam hamisu maqocinsu da isyaku ya katseta sai ta yi saurin fita ba tare da ta bi ta kan Zainab dinba sbd isyakun shine ya kwana a asibitin Bata saniba ko jikin ne kokuma sallamosu akai.



Kallo daya tayiwa fuskokinsu take ta fahimci mugun sakon da sukazo dashi saidai Bata gama yardaba Dan haka qafafuwanta dake rawa ta dago ahankali tana qarasowa tsakar gidan murya na rawa a harde cikin rudewa tahau cewa,



"Ina kwananku?"



Maryamah da zainab ne suka fito kusan lokaci daya suma suna gaida su malam hamisun Wanda bai tsaya Jan lokaciba ko Jan ransu ya sanar dasu malam Adamu dai lokaci yayi rai yayi halinsa ya rasu qarfe hudun asubar yau..



Dan gyara tsayuwa umma tayi daqyar ta iya tattaro yawu ta hadiye a makoshinta tace"



Malam ya rasu????????



Gyada Kai isyaku yayi yana sauke kansa qasa sbd babu abinda zai iya cewa shima sbd mutuwar malam ta dakesa Dan mutumin arzikine mutumin jamaa.



Zubewa Maryamah tayi a qasa tana neman sumewa sukai kanta isyaku na zuma mata ruwa suna Basu hakuri sbd take kowannensu ya rikice da kukan tashin hankali da firgici mai tsanani.



Zainab kuka takeyi sosai mai sauti sbd asirinta yafi na kowa tonuwa rasuwar mahaifinsu.



Cikin qanqanin lokaci a yada rasuwar malam din cikin anguwa da Yan uwa da abokan hulda

Take aka fara shigowa ana rarrashinsu umma dake kuka kaman rayukansu zasu fita.



Ahakan akai janaizarsa aka kaisa makwancinsa.



Alh Barr Asad shine kusan jagoran zaman gaisuwar malam din tunda shine tamkar 'dansa yanzu tunda baida 'da namiji hakama ba wasu dangi sosai dazasu zauna.



Haka aka share zaman makokin tsayin kwanaki bakwai Zainab na cikin ƙunci da rashin walwala gaba ɗaya ta sake zama wata shiru shiru bata magana abinci ma sai an matsa mata ta ke iya cin kaɗan ta ce ta ƙoshi Bata da aiki sai na kuka duk idanunta sun zurma ta fita a hayyacinta gaba ɗaya,

ga rashin me rarrashi ga rashin gata da ke kewaye da ita,

dama ƴan zaman makokin ne ke janta ajiki da bata baki yanzu an watse babu kowa daga ita sai su Umma da sam basa bi takan ta suma takansu sukeyi tunda rasuwar ta shafi kowannensu ba ita kadaiba,



Ahankali lokaci yaja har akai kusan wata biyu da rasuwar Dama bikin maryamah din an daga sai umma ta fita takaba Dan haka tuni kowa yaci gaba da rayuwarsa,



Bebar musu gadon komaiba saina gidan dasuke ciki Wanda bawani gida bane babba Dan madaidaicine Kuma bama ginin zamani bane.



Zainab taci gaba da zuwa makaranta dayake Daman ta gwamnati ce batada wata wahalar shaani kafin daga baya ko sati batai da komawa makarantarba Alhaji Asad ya sauya mata makaranta
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3Chapter 4

Please Login or Register in order to submit comment