Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

zuwa wata private school mai kyau da tsada.



rayuwarta ayanzu Takoma tamkar Mara komai da kowa tunda Dama Abbansu shine abokinta datake iya zaunawa suyi fira da dariya,yaji damuwarta da duk abinda take ciki,



Yanzu duk bame mata wannan Dan haka ahankali Dole tayi qawa daya Nabila a makaranta wadda da ita kawai taye Yar fira yanzu.





Dukkanin nau'in bauta na aikin gidan sai ya sake rataya a wuyarta musamman da bikin Anty maryamah ya gabato gashi dangin umma wasu tun rasuwar abban suna gidan,



hatta girkin abincin yanzu Umma ta fara horar da ita akan yinsa harma ta sakar mata gaba daya,

tun tana yi Maryamah na kushewa bataci har hannunta ya nuna a iya girkin.





Anfara bikin maryamah gidan yacika da dangin umma dawasu tsirarraku daga dangin mahaifinsu dasukazo daga qauye Kuma ahakan har akai aka gama Babu ma Wanda yayi noticing dinta amatsayin qanwar amarya Koda yaushe tana cikin aiki da aike Dan haka har akai aka gama ko zanin sabuwar atampa Bata samu Wanda ya Bata ta daura ba saidai Bayan bikin umma tabata kala hudu acikin tsofin kayan Anty maryamah din Wanda sunyi mata yawa sosai saida umman ta Bata dari uku takai aka rage mata take sakawa dayake kayan Anty maryamah din duk masu kyau ne sbd umman dakuma Alhaji Asad daya tsaya mata.



An gama bikin ne cikin kwanciyar hankali da bushasha don harkar ta masu arziƙi ce sosai kuma ya sakar musu naira sun yi yadda suke so,



Dangin Umma 'yan Cameron ne Dama Kuma duk wata riyar kudi sun iya Dan haka kudi suma suka hada sosai sukai mata wasu abubuwan na fita tsara duk da Babu abinda Alhaj Barr Asadullah din beyiba.



Amarya maryamah tabar gidansu ta tare a gidan mijinta aka bar daga umma sai Zainab wadda tun yanzu tafara hangowa kanta garari sbd rashin sanin saime Kuma Nan gaba.

#MAMUH#

#love

#sisters chldrn

#AMAL IDON NAIRA





*_ZAFAFA BIYAR_*



*RUMBUN K'AYA*🔥

Hafsat Rano



*DAUDAR GORA*🔥

Billyn Abdul



*IDON NERA*🔥

Mamuhgee



*A RUBUCE TAKE*🔥

Safiya huguma



*KI KULANI*🔥

Miss xoxo







Littafi daya---400

Biyu---600

Uku----800

Hudu-----1k

Biyar din duka----1200



ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN



0022419171

Maryam sani

Access bank



MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN



09166221261



🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪

*Ina yan uwa 'yan nijer?*

*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*



+22799643131



Littafi daya---450CFA

biyu---650CFA

uku----850CFA

hudu----1050 CFA

Biyar----1250CFA



*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*

*Thanks for choosing us*🔥

*_IDON NAIRA_*

_Mamuhgee_

_Arewabooks@Mamuhgee_

_ZAFAFA BIYAR 2023_







3

Wata biyar da yin bikin Maryamah Zainab ta shiga Ss1 alokacin Kuma Allah yabata ikon saukar hizifi talatin na alqur'ani daga Nan zuwanta islamiyya yafara qaranci sosai sbd ayyukan dasukai mata yawa na gida,



Barin Maryamah gidan memakon yasa Umma janta ajiki ko yayane dakuma samun saukin ayyuka sai hakan bai samu ba don kuwa Umma tsakaninta da umman umarni da aiki ne sai aikenta datakeyi kaman engine Sam duk nisan anguwa yanada wuya tabata kudin mashin ko a daidaita da qafa take zuwa wani lokaci idan nisan nada yawa sosai shine zata Bata kudin zuwa ta dawo da qafa.



Tariga ta saba aikin Bata mata rai hakama batajin qyashin yinsa,

Akan lokaci takeyin komai tunda safe Idan ta tashi aikine kaman jaka sai dare take samun damar kwantar da kafadunta taji sanyi sanyi ajikinta,



Shara,wanke wanke,wankin kayanta Dana umman,girki da sauran ayyukan komai itace hatta yankar farcen umman itace takeyi mata duk qarshen sati tareda tsifar Kai danma Bata iya kitsoba da itace zatayi mata har shi din.



Duk wannan bautar Batajin haushin umma sbd Bata rasa ciba ko sha hakama sitirar sakawa ana Bata kwancen maryamah ta rage ga karatunta tanayi Alh Barr ya dauke nauyin komai nasu Babu abinda suka rasa na Jin dadi duk da ita Yar kallo ce kawai.



Dangin mahaifiyarta mutum daya ya taba zuwa dubata so daya daga qauyensu

Koda yaga alamar batada gadon komai da mahaifinsu yabari aka raba sai ya tattara ya tafiyarsa batareda ya sake waiwayotaba Dan haka itama batasan Ina sukeba bare inda zata samesu kota sani batada ikon kanta sai abinda umma ta zartar akanta.



Maryamah nacika wata bakwai a gidanta tasamu ciki mai tsananin wahalarwa da laulayi mai wuya Dan haka hankalin ummanta ya tashi Dan kuwa tuni aka kwantar da maryamah din a asibiti gashi basa gari itada mijin nata suna Abuja Dan dawowarsu daga Umrah kenan suka tsaya Abuja sake hutawa kafin su dawo.



A wahale tayi sati daya a asibitin suka sallamota suka tattaro a ranar suka biyo jirgi suka iso gida.



Dawowarsu da washe gari umma ta tafi dubota acan ta wuni Dan haka sai kusan dare tadawo gida lokacin zainb tagama zaman jira a tsakar gidan harta shige daki bacci ya dauketa.



Rashin lafiyar maryamah yasa komai ya rikice a gidanta gashi masu aikinta biyu duk ta koresu sbd rashin tarbiya da nutsuwarsu gashi Alh Asad mai ilimin addini ne sosai Kuma har lokacin duk bayan sallar magriba zuwa ishai karatun addini sukeyi sosai shida malamansa a harabar gidan wani lokacin kuma a masallacin kofar gidan Dan haka idan akai sallar magriba bamai iya shigowa gidan sai bayan ishai.



Ayyukan gidan Dana rashin lafiyarta suka taru suka cakude gashi lafiyayan abinci ake fiddawa idan sungama karatu shida malamansa suci acan Dan haka ba shiri takira umma akan a nemo mata wasu masu aikin.



Kafinma a samo masu Aiki sai gata an sake kwantarwa a asibiti Dole umma ce taje tayi jinyarta a wani babban tsadadden private hospital Alh Asad ya ringa zuba kudi sosai ana kulawa da matarsa wadda itama yanzu koina haj maryamah ake kiranta dashi.



Kwanciyar Maryamah asibiti yasake tsananta ayyukan Zainab sbd itace take abincin safe driver yazo ya dauka,

Hakama tayi na Rana hakama tayi na dare,

Tun shekarunta Basu gama kaiwaba ta iya kusan komai daidai gwargwado.



Ranarda aka sallami maryamah suna kawo umma gida Basu wuceba tasaka Zainab hada Yan kayanta tasakata binsu sbd ayyukan gidan maryamah din dakuma kula da cimar maryamah daketa fama da laulayin zabar abinci.





Zainab batada zabi ko ikon kanta sai yanda akai da ita Dan haka jiki ba qwari ta debo Yan kayanta da Basu fi kala biyarba ta fito tabi driver zuwa gidan maryamah da Bata taba zuwaba cikin wata lafiyayar Jeep black data gama daukan sanyin AC.





Babban gida ginin masu arziki na zamani sai daukan ido yakeyi ga masu gadi har biyu a gidan Nan zainab taga sun shige ta tabbarda Nan ne gidan 'yar uwarta maryamah Dan haka Bata wani qure koina da kalloba ta sauke kanta tareda sauke numfashi sbd duk wani abu daya shafa maryamah baya baya takeyi dashi tareda nutsuwa sbd yanda alaqarsu take Sam idan ba gaisuwaba Babu abinda maryamah takeyi da ita Dan haka ko yanzu dinma sanyi jikinta yayi Tana tsoro tsoron idan maryamah din tasan da zuwanta da umma tasaka.



Har kofar shiga babban palon dazai sadaka da cikin gidan yakaita ya babbuga kofar tareda juyawa yabar gurin.



Yana barin gurin wata dattijuwar me Aiki da aka kawowa maryamah daga gidan hajjar Alh Asad ta bude kofar Tana kallon Zainab da a Dan fizge Tana diban kama da maryamah Amma ba'a ganewa Kai tsaye.



Shigowa sukai bayan Zainab ta gaida matar kanta a qasa..



Babban palon alfarma ne da kusan Babu abinda ya rasa na tsarin gidajen masu arziki,



Sanyin AC da qamshi tako Ina tashi yakeyi Dan haka sai jikin Zainab ya sakeyin sanyi Dan kwata kwata rayuwarta Bata taba zuwa irin guraren Nan ba.



Can hanyar kitchen aka nufa da ita matar tace ta jirata anan bara taje ta sanar da Haj maryamah din.



Saida Zainab tayi kusan mintuna ashirin agurin kafin Maryamah ta fito sanye cikin wata maroon jallabiya

Fuskarta da fatarta sai sheqi sukeyi tayi haske sosai taqara wani irin lafiyayyan kyau da kiba duk saita sauyawa Zainab din kwata kwata kaman wata balaraba.



Saurin sauke Kai Zainab tayi cikin girmamawa ta gaidata tareda yimata sannu da jiki na rashin lafiyar datai.



A kasalance cikeda mamaki maryamah ta amsa tareda kallon Karima tace ta wuce tabasu guri.



Maido kallonta tayi kan Zainab da kayanta cikin rashin son daga murya tace"



Keda waye kukazo?

Ina ummar?



Umma Tana gida

Itace tace nabiyo Wanda yakaita gida nazo nan.



Shiru maryamah tai Tana tunanin me umma ke nufi da hakan

Dan haka saita juya ta nufi palonta Dan Kiran umman taji meke faruwa.



Umma na daukar wayar Kai tsaye tace,



Me Zainab zatayi anan da kika aikota?



Ganin nayi masu aikin Nan idan aka biye halayensu haka zakiyita canjawa batareda kin samu yanda kikesoba gashi kina fama da laulayin Nan gwara ita din datake 'yar uwarki zata Miki duk yanda kikeso anhuta da neman kowace me Aiki Zainab zata iya duk wani aikin gidan..



Cikin tare zancen umman tace"



Umma kinsan aikin gidan Nan kuwa?

Ina zata iya sa,



Kina ganin girman gidan Nan ko shararsa zata iya,



Ga aikin abincin dare da ake fitarwa karatun Asad da malamansa,



Hakama umma zaginmu zaayi zaace na mun maidata 'yar aiki,



Duk ba bayan wannan Sam bana buqatarta kusa Dani umma kinsani banaso.





Cikin takaici umman tace"



Duk Wanda zaiyi magana yayi a bayana badai gabana ba Dan kuwa Babu mai iko da ita sai ni

Ni ubanta ya barwa amanarta hakama akwai wanda ya taba damuwa da ita ko kulawa da itane bayan mu din?



Idan bamu qaru da junaba to meye amfanin riqon nata danayi.



Rashin buqatarta a gidanki kuwa hakuri zakiyi ta zauna da itace kawai zatai Miki Aiki yanda kikeso ba qirsa koba komai ai mijinki ne me biyan kudin karatunta Dan haka Kuma kwa fanshe guminku anan.





"Umma to ke kuma wa zai dinga miki duk ayyukan da ta ke yi ɗin?"



Sai alokacin Umma ta sauke numfashi tana tausasa murya tace,



"Maryamah ko jiya da mu kai magana a asibiti na sake maimaita Miki cewan Cameron zan koma can gida cikin 'yan uwana tunda bani da kowa anan Kuma dai Tunda ba aure yanzu nakeyiba anan din gwara na koma can din cikin dangi shiyasama na sake yanke shawarar kawo Miki Zainab din Nan Dan Kinga bazan dauketa naje da itaba acan idan dangin mahaifiyarta sun sake zuwa ki miqa musu ita idanma basuzoba Tana samun miji ko wane iri ne aura mata taje nata gidan mijin kowa ya zauna lafiya shekenan.



Shiru kawai maryamah tayi sbd batasan abinda zataceba Kuma Dan haka sukai sallama kawai ta fito Kai tsaye tasa Inna Karima takai zainab Dan madaicin dakin dake hanyar kitchen Wanda masu Aiki yakamata su zauna anan Amma maryamah dayake batason qazantar masu Aiki dakin yanan sabonsa Babu me aikin data Taba zama acikinsa komai nasa na Nan sabo

masu aikin Kuma dakin boys quarters take kaisu Dan ko Inna Karima acan take yanzu hakan.



Dakin da aka bawa zainab qatuwar katifa ce aciki sabuwa da wardrobe sai madubi da toilet me girma sai Kuma zanin gado har biyu da daddumar sallah da fanka qarama ta tsaye sbd gidan koina pop ne Dan haka AC ne ako Ina Banda dakunan masu Aiki.



Inna Karima ta nuna mata ta saka kayanta cikin wardrobe



Inna Kariman ce ta shimfida mata bedsheet a katifar da kanta takuma share mata dakin tai mopping tareda wankin toilet din dayake tamkar dakin wani basarake sbd kyansa da girmansa.



Duk aikin da Inna Karima tayi mata tayi mata ne dan taga yanda akeyi ta koya tun yanzu din Dan a daukarta sabuwa me aikice aka kawo wadda zata karba ragamar tsaftace koina ita Kuma taji da aikin girki.



Duk aikinda Inna ta nunawa zainab din tagane Tunda Dama aikin wahala shine rayuwarta ba Wai sabon Abu bane.



Kitchen takuma janta can ma ta nuna mata yanda zatai wanke wanke a kitchen din tareda tsaftacesa.



A taqaice dai Tunda zainab ta iso gidan a ranar Bata zaunaba sai dare sbd aikin da aka fara tarbarta dashi gashi Bata Kuma ganin maryamah ba sai dare data fito tace zainab din ta dafa mata ruwan shayin datake dafo musu da suna asibiti.



Inna Karima ce ta kunnawa zainab din gas ta dafa mata aka Bata inda ta juye mata takai mata kafin suka kashe komai tareda rufewa itada Inna Karima kowa ya nufa makwancinsa.



Sallar ishai tayi ta kwanta take bacci ya dauketa Dan Dama ita data kwanta sai bacci sbd aikin datake wuni yi jikinta a gajiye yake Koda yaushe.



A gida akan tabarma take kwana saida maryamah tayi aure umma ta saida katifar maryamah babba ta siya mata wata Yar yololuwar katifa data gama sidewa Amma dadinta takeji ko ahakan ita,.

Ganin wannan babbar katifar baisa ta hau akai ta kwanta ba sbd gudun laifi ko zaqewa dakuma shakkar yiwa maryamah laifi da haka a kan tiles ta shimfida daddumar sallah tayi kwanciyarta har safe.



Qarfe 7 Inna Karima Tazo ta tadata suka fito Dan fara aikin gidan.



Shara tafara mai kyau

Ya goge komai cikin tsoro tsoron kada ta fasa ga jikinta dake faman Yar rawar fargabar kada tayiwa maryamah laifi da yanayin aikin.



Fes tayiwa koina saidai Kam yau saida bayanta ya amsa wahalar aikin daya bambamta Dana gidansu data saba,



Palo uku manya Manya da dakuna biyu da kitchen da corridors biyu da toilets ta share tai mopping takuma wanke Bayan goge gogen datai.



Kowanne gurin datai aikin girmane dashi Babu qaramin guri,.



Jin tayi bayanta ya riqe qyam kamar bazata iya miqewa daidaiba Amma haka ta miqe ta share babbar harabar gidan da kusan mota hudu yake dauka.



Ko data gama ayyukan tas bayanta da qugunta sun mata nauyi daqyar take iya miqewa tsaye daidai haka ta zauna kitchen taci abincinta da Inna Karima ta Bata Tana gamawa tayi wanke wanke tasake tsaftace kitchen din ta nufi dakinta.



Daqyar tayi wanka ta saka kaya tazo ta Dan kwanta take baccin wahala yafara daukan kenan saiga Kiran Inna Karima akan taje ta tattaro kayan dining idan su masu gidan sun gama breakfast.



Haka ta tashi taje tattara gurin tasake gyarawa Takoma kitchen tayi Wani wanke wanken tafara Taya Inna Karima aikin abincin Rana.



Wunin ranar ma Kam Bata sake samun zama ba sallah kawai ake barin taje tayi tadawo

Da yamma ma saida takuma sharar harabar gidan sbd karatun daren da akeyi.



Da daddare data kwanta tsamin da jikinta yayi ko bacci mai dadi data saba samu Bata samuba ranar.



Washe garima duk aikin datai a jiyan haka ta maimaitashi Dan haka ranar jikinta har kasa daka yayi da zazzabi ta kwana.



Haka aikin yakasa karban jikinta kusan kwanaki hudu kullum da zazzabi take kwana Amma harta Dan fara sabo da aikin jikin ne dai bai sababa sbd aikin yafi karfin shekarunta ga makaranta har lokacin maryamah batace mata komaiba akai ita Kuma Bata cika ganintaba kota ganta bazata iya Mata magana ba sbd shakka da tsoron Mata laifi.





Idan tace tana Bata gaji da zaman gidan matuqa ba ta yi ƙarya,

don kuwa duk aikin da ta ke yi a gidan Umma bai kai nan ba sbd ko gyaran ɗakunan da take yi a can girman falukan wannan gidan na Maryamah shi ne matsayin girman ɗakunan gidan Umma kaf ɗinsu



Duka gidan dakin Alh Asad ne kawai ba itace take sharewaba Amma kaf gidan itace mai share koina ta gyara



Har aikin kitchen da Inna Karima yakamata tayi kusan duk itace take Rabi sbd Maryamah wasu lokutan tafison aikin zainab na abinci hardai na marmari.



Sati biyu da zuwanta gidan ta fara sabawa da duk wasu bautan da ta ke yi

Umma kuma a satin ta haɗa komi nata ta ɗaga zuwa Cameron bayan ta zo har gidan Maryamah sun yi sallama da juna tayiwa zainab nasihar biyayya ga Yar uwarta tareda tunatar da ita batada kowa sai su Dan haka ta zauna ta Taya Yar uwarta aikin gidanta Tunda idanma batayiba batada gurin zuwa.



Zainab ta sha kuka sosai duk da cewa babu shaƙuwa tsakaninta da Umman amma sai tafiyar nata ya ɗaga hankalinta sosai sbd koba komai tafi Jin sanyi agurin umman tun rasuwar Abbansu sbd lokuta da Dama umman na Mata wasu abubuwan kulawa sabanin maryamah dako kallon fuskar juna basayi sosai,



Kwata kwata Babu shaquwa ko kusanci ko wata qauna a tsakaninsu Dan haka takejin da umman zata taimaketa da ta tafi da ita ko bautarce ta yarda acan tayiya yi Mata har tsufa yafi Mata zaman Nan din.



Bayan tafiyar umma da sati uku maryamah tayi barin cikinta Dan haka gidan duk suka shiga damuwa musamman maigidan gabaki dayama dauketa yayi sukai tafiya wata qasar aka bar su zainab masu aiki.



Bayan tafiyarsu ne zainab tasamu Takoma makaranta shima saida aka Kira Alhaji Asad din daga makarantar Yana can suka sanar Masa ta Dena zuwa shinefa yayi waya drivern gidan na kaita wata Rana Kuma da qafa take zuwa tadawo da qafa duk nisan kuwa sbd driver ganin yakeyi Mai aikice ita Amma tasamu shigar da ake kaita makaranta da mota Dan haka Wani lokacin yake shareta ya dauki motar ya tafiyarsa nasa sabgogin.



Karatunta da aikin gidan ya taru ya hade mata gabaki daya rayuwarta Aiki ya firgitata ga kadaici,



Sam bayan aikin wahalar hidimar gidan maryamah da hidmar maryamah din batada aboki Dan haka duk Takoma kaman wata nakasasshiya karatun ma yanzu sai ahankali Bata Wani ganewa zuwa kawai takeyi.

#MAMUH#

#SISTERS#LIFE#LOVE#AQEEL#AMAL IDON NERA#





*_ZAFAFA BIYAR_*



*RUMBUN K'AYA*🔥

Hafsat Rano



*DAUDAR GORA*🔥

Billyn Abdul



*IDON NERA*🔥

Mamuhgee



*A RUBUCE TAKE*🔥

Safiya huguma



*KI KULANI*🔥

Miss xoxo







Littafi daya---400

Biyu---600

Uku----800

Hudu-----1k

Biyar din duka----1200



ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN



0022419171

Maryam sani

Access bank



Shedarka ta 09033181070





MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN



09166221261



🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪

*Ina yan uwa 'yan nijer?*

*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*



+22799643131



Littafi daya---450CFA

biyu---650CFA

uku----850CFA

hudu----1050 CFA

Biyar----1250CFA



*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*

*Thanks for choosing us*🔥

*_IDON NAIRA_*

_Mamuhgee_

_Arewabooks@Mamuhgee_

_ZAFAFA BIYAR 2023_





4





*_MAAB LUXURY HOME_*🔥🔥



_ASSALAMU ALAIKUM JAMA’AR KWARAI.. JAMA’AR AMANA… JAMA’AR ZAFAFA… MASOYA KUMA MABIYA MASU ALHERIN SAYAN ZAFAFA A KODA YAUSHE BA GAJIYAWA…GODIA MAI TARIN DIMBIN ALBARKA DA FATAN ALKHAIRI AGARE KU.._



_KUNSAN DUK INDA ABUBUWAN ARZUKA SUKE MUNA SHIGA MU KURDA MU NEMO MUKU SU DOMIN JIN DADIN KU..🥰💕SABODA KU DIN NA GABAN GOSHINAN MU NE._



_TAMKAR KO DA YAUSHE.. YAU MA MUNZO MUKU DA WATA TSARABAR.. TSARABAR DUNIYAR KAYAN KITCHEN, DECORATIONS DA SAURAN SU… KU MARMATSO KU JI…_



*_MAAB LUXURY HOME_*

*_MAAB LUXURY HOME_*

*_MAAB LUXURY HOME_*



_KUN GANI KO? TO INA AMAREN? INA UWAYEN GIDAH INA YAMMATAN DA KE SHIRYE SHIRYEN SHIGA DAGA CIKI? INDA ZAKU JE KU KANKARO MUTUNCI KU DANDALO ARZIKI NA KECE RAINI.. INDA ZAKU WUCE RENI DA GANIN KASKANCI..INA MAZAN DA KE BURIN FARANTAWA MATAN SU DA ‘YAYAN SU DA KANNEN SU? _



_MAAB LUXURY HOME: RIGIJI GABJIN KENAN! WOHOHO WANI KAYA SAI AMALE KAN DAUKA.. MAAB LUXURY HOME : ALJANNAR KAYAN KITCHEN KENAN, INDE AKACE KAT TOH KARSHEN MAGANA TA KARE KENAN.. MAAB LUXURY HOME ; A NUMBER ONE STOP SHOP FOR HEAVENLY KITCHEN UTENSILS, HOME DECORATIONS AND MUCH MORE_



_ADIRESHIN MU: MUNA KAN TITIN AHMADU BELLO WAY, KANO STATE. ZAKUGA TAMBARIN DA MAAB LUXURY HOME.._



_DAN SAUKAKA MAKU FITA ZUWA SHAGON MU. ZAKU IYA ORDER AKAWO MUKU DUKKANIN INDA KUKE A FADIN NIJERIYA DA KETARE. _



_INSTAGRAM: @maabluxuryhome._



_FACEBOOK: @maabluxuryhome._



_KO KU NEME MU TA LAMBAR TARHON MU: 08034631010_



_KYAU! INGANCI! RAHUSA! ADADE ANA AMFANI DA SHI SAI KAYAN: MAAB LUXURY HOME_



_100% TESTED AND TRUSTED😍☑️_

______







********

Kasancewar maryamah nason kalolin abinci daban daban Kuma ta saba yiwa Alh Asad na Wanda ake fitarwa harabar gida da dare yasa ta Sanya zainab gurin koyan abinci Amma a online tareda siya Mata wata Yar tab wadda da ita take sake koyan komai.



Da farko zainab na Shan wuyar gane kan lamarin tab din gabaki daya kafin ma gane abinda take koya din

Amma sanin koyar Dole ce a gareta kaman yanda aikin tasani Dole ne itace wadda zata ringa yi har lokacinda Allah zai yanke Mata wahalar Dan haka ta ringa takura kanta tana dagewa gurin fahimta da koyon har Allah yasa ta Dan fara fahimta sosai.



Sbd yanda take tsananin kiyaye doka da shakkar keta kowace irin sharadi da iyakar da maryamah ta ajiye tareda dorata akai yasa yanda ta maida hankali da nutsuwa a gurin koyan girki da sauran ayyukan gidan ko karatunta bata bawa wanna kulawar da mahimmanciba.



Ahakan saida ta Dan dauki lokaci kafin ta iya gane kan tab din harma da abinda take koya din Wanda kullum da abinda take girkawa na abinda ta koya sai gashi tafara qwarewa musamman da Inna Karima Tana qara fahimtar da ita wasu abubuwan.



Ana hakan Maryamah ta Kuma samun wani ciki me laulayi sosai kala kala

hakan ya sanya Zainab sake zama busy da ayyuka sbd kusan yanzu idanba aikin zainab dinba daga Alh Asad har maryamah din basa son aikin kowa

Dan haka samun cikin yasa hidimar kulawa da buqatun maryamah suka ninkar Mata wata Rana ma ko makarantar Bata samun zuwa sbd tarin ayyuka.



Yanayin laulayin maryamah me wuya ne sbd yawan amai yake sata sosai Wanda yasa yanzu a wuni so uku ko so biyu take wanke toilet din dakin maryamah din bayan gyare gurarenda wani lokacin anan yake kufce Mata.



Samun cikin maryamah yasa zainab ta qarasa figewa kamar kamun yunwa sbd rashin Hutu.



Zainab bata ga amfanin Inna Karima ba a gidan don yanzu hutawa kawai takeyi girkinma an sakar Mata na Rana ne kawai ba ita keyiba sbd kafin tadawo makaranta tayi lokaci ya shige shi dinma Tana gamawa take komawar boys quarters ta shigewarta ita kuwa Sam hidimar Maryamah baya ƙarewa, bata da wani cikakken hutu sai idan dare yayi.



*******

Alh Asad a lokacinda ya fahimci karatun Zainab din Yana rawa sbd tsallaken kwanakin zuwa saiya Dan tsaya Mata a wannan fannin ya saka dokar zuwanta makaranta duk kuwa aikin datakeyi ya soke Mata na lokutan zuwa makaranta dole Inna Karima tadawo yin wasu daga cikin aikin da ake biyan Dan tayi.



Daga wannan lokacin tasamu Tana zuwa makaranta ba dauke Rana saida ayyukanta Kam Babu Wanda ya ragu suna nan yanda suke saidai kawai ace Allah ya kyauta.



Alh Asad mijin Yar uwar tata ne kawai zatace yake kulawa da ita amatsayin Yar Adam Kuma jinin matarsa sbd duk wata kulawa da abubuwan buqata shine ya tsaya Mata kaman babban Yaya kokuma tace kamarma mahaifi sbd ya Isa haihuwarta.



Yanzu rayuwarta takeyi a natse cikin tawakkali da rungumar wannan rayuwar sbd ta Gama yarda da hakan shine tata rayuwar.



Sam Bata damuwa ko Jin takaicin yin Aiki ko daya yanzu haka zalika ma jikin nata ya saba da wahalar batajin komai yanzu saima sake nutsuwa datayi akan komai.



Sai da cikin maryamah ya shiga watanni shida sannan Maryamah din ta sama sauƙin laulayin da ta ke yi Dan haka yanzu wasu lokutan hidmar maryamah din da sauki



Cikin Maryamah Yana cika watanni bakwai haihuwar gaggawa tazo Mata qarshe aka haife cikin Babu rai



Babban tashin hankali suka shiga daga alha Asad din har maryamah da Yan uwansama musamman mahaifiyarsa Amma haka suka fawwala ubangiji suka dauki qaddara.



Bayan wata biyu takuma samun wani cikin ko wata biyu bai rufaba shima ya bare,



A qataice saida ta dauki ciki so hudu duk ana rasawa kafin takuma samun Wanda ko wata biyu be rufa da samuwaba mijinta ya tattarata suka tafi India acan tayi renon cikin qarqashin kulawar wani likita har saida cikin yakai wata bakwai suka dawo sbd dukansu sunfi shaawar haihuwa acin Yan uwansu.



Bayan tafiyarsu maryamah zainab ta kammala karatunta na secondary

Kuma tafiyar tasu wani nauyi ne me girma ya hau kanta Dan kuwa duk hidimar kula da gidan da duk Wanda yake gidan kanta dawo Dan kuwa Jin tayi kaman anbar Mata wata gagarumar Amana gashi Sam a duniya Bata kaunar abinda zaisa tayiwa 'yar uwar tata laifi ko abinda zai Bata ranta sbd kaucewa damuwar abinda zaije ya dawo.



******

Lokacin da cikin Maryamah ya shiga watanni tara a lokacin ne Zainab haka kawai itama taji Ta kaunaci haihuwar anty Maryamah din da wuri musamman ganin yanda kusan kowa ya qwallafa rai a haihuwar da abinda zaa Haifa din.



Cikin na shiga wata Tara da sati biyu

Cikin dare naƙuda ya kama Maryamah Alh Asad ya wuce da ita zuwa asibiti bayan ta sha matuƙar wahala daf da asuba ta haifo yaronta me Kama da ita sosai kyakkyawa dashi Kuma lafiyayye babba dashi.



Ko kaɗan Zainab ba su san bikin da ake ba sai da safe da Maryamah ta kira wayarta ta shaida mata haihuwar tare da bata umurnin girka abincin breakfast da duk wani abinda ta ke buƙata ta sanar da ita cewa Alh Asad zai dawo su taho tare da ita zuwa asibitin sbd ba za a basu sallama sai zuwa can rana an sake tabbatar da lafiyarta da na Babynta.



Zainab sauke wayar daga kunninta tayi tana jin wani boyayyan farin cikin da tsawon wayonta batasan ta taba yinsaba,



can ƙasan zuciyartata jin wani irin ɗokin son ganin yaron Maryamah tayi haka kawai duk da tasan ita dashi saidai hange Amma Zataso abata shi Koda so daya ne ta Dan dauka Dan tasan ba lallai tasamu nata rabonba kila Dan bataga alamar zata samu tata rayuwarba idan ba Allah ya riga ya nufa ba.



Aikin da Anty Maryamah din ta bada umarnin ayi tafara a tsanake kaman yanda tasan Anty Maryamah din na buqatar komai.



Tana gamawa ta harhada ta shirya
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4

Please Login or Register in order to submit comment