Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

tatasone tsundum cikin 'yan kauye bata San komaiba daga zuwa dandali sai taya kawayenta Fulanin dasuke zama a kauyen kiwaon shanayensu.
Tsabagen karfi dajin naci tuwon dawa na kangare har siyanfada takeyi.

Za'ai girkin engayu adakinsu zata fitar suyi musaye da 'yayan makota wai bata iya cimarba ,itadai tasha fate da sugar ba manja,dan gauda,tukurkusu dadai sauransu don haka tataso kakkaura gidirgir kakkarfa da karfi kamar shara'a uwa wani namijin

Tunda yaya tahaifi da namiji bayan dogon zangon da ta kwashe ba haihuwa ,shikenan gori ya ishi mama binta ,wai sune da gida ,waye waye......

Wataranar sallah ce kaf yaran mama sunzo da yaransu duk mazajensu suka kawosu,basuyo abincin sallah ba saboda nisa amma sun kawo buhunhuna da gallons na mangyada da manja da komai namahadin girki.

Mama wayayyiyace don haka dasauri tadaura babban tukunya taraya masu girki dayaji tsokokin kaji,tahada masu lafiyayyen kunun aya dayaji madara ta aika akaje zuntu aka nemo mata kankara tasaka aciki
Ta wanke lafiyayyun plates ,warmers da spoons tagoge ,tazuba komai tashimfeda dardumanta na alfarma datayo a saudiyya tashirya masu komai a falonta
Suka baje kwansu da kwarkwatansu,sukaja gara cikeda barkwanci da wasa da dariya kamar zuri'a daya

Takaici kam habaici dayada magana mama sun shata, ko kusa taki ko zuwa su gaisa saboda bakin ciki

mazan da zasu tafi,kowa da kudinshi na albarka,Rafa Rafa sule yaya ba tasamu ba,yooo basuma San da itaba.

Fitonsu keda wuya tajawo murhu tahada wutankara tafara mulla tuwo,tana wake wake: "duniya rawar 'yan matane na gaba yakoma baya"
Sarai sumama sun gane mai take nufi amma bawanda yatankata
Cikin sa'a saiga daidai daita tashigo a keken almajiran gidansu data ara

"6ii6itttttttt!!!
abani waje kar nayi 6anna,akaudakaya harnayi kutubal dashi alkur'an....."
Hango yaya tatakarkare tana tuka tuwo,kawai sai ranta ya kissima mata ta roreta da fada

Kewaye ta da murhunta tashiga yi da keken "agafara ba birki Yaseen"wani gigir,gigir tashiga yi da kan keken kamar zata duro ta jikinta,raba mata hankali yasoma yi jiri nadibanta,ga hucin tuwo,ga wuta gakeke da ke wuliwuli akanta.

" ke dan iyayen ki bar nan" tafada tana zare idanuwa

"Hajiya nakwalla shugaban aiki maza tukesa Tass,din vamusan guda...don dole ki tuke katon tukuny mu danna .....wooooo 'Yar aiki ke daya daya dagake saidanki sanusi mai kan jaki.....kinaji zaki kwashe ki kawo mana"

Yo kanta tayi dagudu zata daketa ,tako zille ta watsar da keken ckan tukunyar ,yako 6are cikin wutan,ji kake cuuuuiuuu!!!


"Wayyo jama'a gudunmawa ta shekarmun da tuwo" tasa hannu aka tana kwarara ihu ,cikinta ba kululu na azababben yunwa.

Lankwashe murya indo tayi sannan tayi maganar da karfi ,yanda kowa zaiji a aza indon keda gaskiya

"Wayyo yayan mu saida nace maki ba burki ....kiyi hankuri bari naroko maki abincin en birni dakin mamanmu" tadaddalo mata ido tana mata gwalo da dariyan sak'e

"Saidai ki roko wa uwarki dinmu bamuyi gadon rokoba" tanayi tana matsowa kusada inda take

Tsalle tayi taje kofar fita waje"haba Yar tsohuwa ,tarrr nake kallon ki.....kije jira zamanku da yunwa dan aradu babana yau famfo zammai ga abinci gida baxai asaran kudi yabakiba......hahhhhh yau wata zataga malaikan mutuwa azzallaruruwa me wukaken azaba kala dubu"tafalla aguje tabar gidan



Vote
Share
Comment
[8/19, 10:13 AM] Haisahhtttttt💅🏻: 👠👠💅BAGIDAJIYACE I👠👠💅🏻


*©️HIKIMA WRITERS ASSOCIATION*
*(Home of peace, joint entertainment to educate and enlighten our readers)*


Dis page ix dedicated to you my fanz 😍😍😍 indodo tace namiqa mata jinjinar ta gareku👍🏻 Allah ya bar kauna da zumunci🤝🏻

I reserve your comments my fam ,zanbisu daya bayan daya,ahankali zaku fara jin reply dina serially inshaallah,daga next update
amma sorry wasufa acikinkune , masu sharhi kadai zansa saboda groups din da yawa.
masu mun fatan alkhairi kuma da addu'oi kuma bazan mance dakuba zanware maku page na musamman in jero sunayenku, bayan next update.inayinku irin totally dinnan❣️💯



Written by
Hassenart



Litattafan marubuciyan
RAYUWAR AFREDARH

QASAITATTUN MATA

RAMUWAR GAYYA

_And now_

BAGIDAJIYACE


*littafina na kudine dashi da ramuwar gayya, anabiyar kowani daya #200,ake turowa ta katin MTN zaki turama wannan number 09065990265*
*Saiki screen shot a matsayin evidence ki turo,ko kuma zaki iya rubuto numbern katin ,ki turama numbern saman dai*


*Free page7️⃣~8️⃣*

Gidansu kawarta rahane tatafi,da sallama tashiga gidan kamar 'Yar arziki,ta gaida innansu rahane dake tuqe tuwon dare.
"Hannu innah ,shin rahane ko tana hiki?"
"Eh tana ciki ,tana shirin tafiya tallen gyada"
Cikin dakin takutsa kai batareda takuma cewa komaiba

"Kawalliya romon danga, kece haka se tsatso kyau kike abinki ?"

"To aminiya abun ai duk sirrine daka tsami nayi din wallahi innayi wanka ciwo nakeyi.... (Hikiciffff,atishawa tayi sannan tace)wasa da ruwan sanyi" tafada tana maida 'Yar kwallan da yazubo mata sakamakon tarin da takumayi
"H'ummm lallai zanzo inhana mamanmu yimun wanka dakanta,kinga nima sai ,inayin irin naki....mene kikace sunansa?"
"Daka tsami,eh daka tsami sunansa kenan... Bake ba tsamin rana...bare kije talle aki saya"
"Hakane fa kawalli li, muje kar dare yemana a waje mama tayi fada"
Saida tagama shirga hau kanta a fuska nan tafito rangandau fuska yasha dige digen ba'ki baki dal da janbankinda 24hours ,angoggoga janvakin asaman idon maikon hambakin ya hade Dana kwalli. Sallama sukayi ma inna suka tafi,zuciyar inna fal murna domin duk ranarda rahane tafita da indodo tas kayan su,ke karewa.
Jerawa sukayi suna tafiya duk yaran da yagansu saidai ya canza hanya don ko da kuskure yaro ya biyo ta wajen su ,saidai kaje fahhh!,ta kafta ma da mari .
Suna isa dandali ,rahane ta aje gyadarta a wajen masu sayarwa,itakam indodo Ku tsawa cikin gantsara,gantsaran 'yan mata tayi dasuke fili da samarinsu suna rawa,tana shiga kowace maison kanta da mutunci tayi waje, itakam ko ajikinta don tasaba haka ake mata ,ita aganinta hakanma isuwace.

"Masu hid'i canja Mani,wannan baiyi mun ba"
Rawa takeyi duk Wanda akasa ta iya rawarsa tana rawar tana bin wa'kar
"Kin gani kin gani kwalelarki,shegiya 'Yar banza" tamaimaita wa'kar data canja masa ma'ana kadan daga k'arshe tareda shako wuyar wata da ke daga kusa da ita tahankada ta wajen filin.aiko saurayin ta yazaburo kan indo,tsalle daya, tayi tafita filin tafara gurza kafarta a turbayen wajen k'ura yaringa tashi fuuuuuu! Take wajen ya hautsine.'yan kida suka hau tattare kayan su ,suna Allah ya isah don sunsan ,sin rasa kasuwar ranar.

Cike da barazana da cika baki tahau yiwa kanta kirari,koya tsorata yakyaleta .kirjinta na dukan taratara ,yau kam karyana takare inani ?,ina wannan rusheshen basamuden " da wannan zancen zucin takarasa gabanshi, kanta tsaye" Waye yace dani baniba,shima ince dashi bashiba,saini tururuwa mai idon zalinci,taboni kaga tarandangi saini dakalin majina ahauni a zame, saini....."
"Ke yimana shiru kinjiko?" Yadaka mata tsawa,"ke kin zama mana annoba a gari ,mai kike taqama dashine?....yauto zanci ubanki inga abunda zai faru!"

Wani kururuwa ta dauka da kaf saida 'yan filin suka arta da gudu har budurwan da akeson taremawan ,can nesa suka tsaya yau su sha kallo ,kodai amauji bakin muguwa suji dad'i,ko kuma ayi mai lilis susha kallo .
"Kucasu arna kucasu,Ku casu bamai rabaku" aka dauka yimasu waka don a kara gingering dinsu

"Tab yaro bakasan halin indodoba yoo, kaidin ka yimun kadan a danbena,ai ina hada jiki da kai kwashe mun k'arfina zakayi tassss!, kagako baka isa ba" takarasa maganar tana ja da baya,zuciyar ta na rayamata ta arce.

"Aini abun kunyane indanbe dake saidai in lallasaki" yajuya yazugo tafasan bayan su

daka tsalle tayi tatimu a kasa"Nasama Ku d'auka za'a taba maku god'iya"tafadi cikeda sadakarwa.

Abun tsoro ,kawai zai akaji karan bulalai ya kacame wajen ,aka shiga zubama saurayin,ihu yake kwarara wa,yana burgima akasa yana soshe soshe,amma saukan dukan akeji bamai dukan.....

Haba a matukar rude indo taci hanya ta dibi kasa ta watsama kafar tata,"kafa mainaci banbakiba?kimun gudun da baki taba yiba" fil ta b'ace kamar barewa.

Tana barin wajen aka dakanta da dukansa jikinsa rudu rudu duk ya farfashe ,kowa watsewa yayi sai masu balain abota daahine suka rakube daga nesa daya yasoma magana
"Iluwa tashi don Allah, Yaseen kaima danaka, Dana gani babu tambaya kasan yarinyar nan tasuce,don ni tun ranar Dana soma ganin ta raina taraya mun. 'Yar ruwace to 'ya kyau haka....du Allah wata rana Ku kare mata kallo zakuga yanda kalolin jikinta kesauyawa....abunda yafi muzueawa sarauta Allah ido ,don Allah baya dauka ka banza"

Daya kuma ya maida kallon sa sama "Ku kuke ganin mu bamu muke ganinku ba,agafarcemu muntuba,minbi Allah munbiku....kuskure irin haka bazata kuma faruwa ba"

Duhun darene suka farga yasoma riskarsu ,su kadai awajen

"Iluwa ko ,ka tashi wallahi ko mu barka afadansu,mutafi" suka juya zasu tafi ,ai a sittin ya mike ,d'afff yaji kamar an zare radadin dayake ji a jikinsa,tsabagen tsorata.




Koda indo tadawo gida sad'af sad'af tashige dakin su tawuce 'Yar gadon ta .ta kwanta

Anty amina ne ta hango kafarta bututu da kura kamar wacce tayi kwab'in k'asa
"Mun shigesu Aisha kece haka?... Ji yanda sababbin kayan ki suka koma? Ji kafarki?...tashi don kaniyarki ,kije kiyi sallah"

Sum sum tamike ta. Fita kamar mutuniyar kirki,yo ita kanta tsoron kanta takeji,gani take uwa a mafarki

"Ciftsi Ameenah kinganta kuwa ai ta cika botiki tai wanka tukum,don wannan najasace ,bazata yi sallah a hakaba"Cewar anty fatima

" mtseww laifin mamane,abani ita tayi sati biyu a wajena ,wallahi saita kintsu...to ina bazasu bakaba"

Sai anan mama takada baki tace"wallahi nabaku go ahead, kutafi da ita ,ita kenan ba tabar tsoho ba bare yaro?, Sam baki biyo halinaba,yanzu kujira zakuji yanda gidan zai hargitse itada yaya....nidani ne bazan ringa biyewa jikan cikina ba.da in sun fara ana zuwa ,yanzu bamai zuwa bada hakuri"

"To algungumai,gulmata kikayi ko,ai yau zata gane shayi ma ruwane,ina me idon mayun take?"
Dasauri anty Fatima taboyeta a bayan kyaure
Tagama waige waigenta,bata hango taba ta shige d'akinta ,tana 'yan zage zage,bawanda yace mata cikanki

Anty faty dakanta taje tayi mata wanka ta tsaya akanta tana alwala tana gyara mata. Har tagama suka shigo daki.


********************

Zau maganar fadan iluwa da indo yacika gari kowa yaji bai musawa yasan zata aikata,don abunda takeyi,inba shafar jinnuba bameyinshi bai ciwon jikiba. Amma ita kullum kamar kara Mata lafiya akeyi

Ganin sauyin data gani a fuskokin kowa lamarin yakuma burgeta ,tataka kowaye,bamai tankata.duk abunda ke faruwa ,bawanda yasani a gidansu har yayyenta suka gama kwanakinsu suka koma don tace bazata bi ameenaba,ranar dazasu tafi tunda tasha ruwan kunu ta arce,ba Wanda yakuma ganin keyarta sai dare lokacin tuni driven kowaccensu yazo ya kwashe su.

Wata makociyarsuce takira yaya gefe,watarana sunje gidan rasuwa, tagayamata rad'e rad'in da akeyi akan indo wai ba mutum bace,saida takoro mata labari kaf ,sannan yaya ta d'age hanci ta rangad'a gud'a
"Wohoho Allah matubi,Ku shashashun inane?, indonce aljan ?, tabdijam yanzu naji nasamu lasisin jibgarta da hujjah"

"Adaibi a hankali innan sanusi donko lamarinta ba karya cikinsa, don yanzu haka iluwa nanan yana jinya....."

"Bayin Allah, kuyiwa Allah kufita daga waje ,komaji da rad'ad'in rashin damu kayi....."
"Dubu daga kinganmu a gidanki shine har zaki koremu?" Yaya tafada cikeda jin haushi

"An koreku d'in inbanda rashin kamun kai yazakizo gidan mutuwa,kina mana gud'a ?...Yaseen 'Yar uwan zamanki na kokari dake,don ma tanada mai maganin ki akusa ,bacin haka dakin cutarda hakurarran baiwar Allah"

Ainan bakin yaya yafara tururi,bakin cikinta daya,anyabi kishiyarta anzageta,cikin kumfar baki tahau bala'i .da kyar mata suka rabasu ,don suna daf da dakuwa.
don itama abokiyar fadan babayabace.
nan dakyar aka jata suka fitar daita daga gidan.


Wayyo ina wuta tawatsawa mama binta da indo, nan komai yakuma jagulewa,kullum cikin bala'i gidan yake ,don yaya tana cewa tak!
Inbai gamsarda indo ba ,saita ramamasu.

Ana haka indo da sanusi suka gama primary, ba laifi tafara kokari don takan dauki na Ashirin haka cikin su sittin.
Kuma alhamdulillah tasama admission a makarantan day maza da mata na zuntu.

Akuma hutun datasamune ta shirya kayanta anty faty taturo ,aka dauketa taje tayi masu Hutu kafin sigama registration.




Vote
Share
Comment
[8/19, 10:13 AM] Haisahhtttttt💅🏻: *👠👠💅🏻BAGIDAJIYACE👠👠💅🏻*



*©️HIKIMA WRITERS ASSOCIATION*
*(Home of peace, joint entertainment to educate and enlighten our readers)*


Story and written by✍🏻
Hassenart
☎️090- 659 -902 -65


*Basai na maimaita kaina ba ,littafin nan na kudine #200 ne kacal zaki turo mun ta wannan number 09065990265, VIP kuma #300 na katin MTN, kibiya kudinki don more karatun littafin ki a tsananki*
👏🏻



*Free page9️⃣~1️⃣0️⃣*



Saida tashake Ghana must go biyu taf ,dakaya .tunda tashigo dasu cikin motar gaba daya annurin fuskar idi driver ya dauke,sakamakon tsamin kayan datti da warin ajiya da yagauraye kamshin turaren motar saida tazo har tashiga motar metatuna oho!, tafara jijjiga hannun budewa,tana shirin karyeta,azabure idi ya zagayo ya bude mata,ranshi fal takaici,don inba cin akan aikinta yazo wannan garin da ba abunda zai hana ya jibgeta kamar Allah ya aiko sa,k'wafa yasoma yi sannan ya d'an
Sassauta murya yad'an rankwafo cikin motar ta windon waje"hajiya yadai,ko akwai abunda kika mantoshi ciki ne"da lalatattan hausanta tasoma bashi amsa"uhm'u uhmum rahane,k'awar arziki na manta bamuyi sallama ba hine ,yanzu ta hwad'o mun a rai ,kaga yazamammun tilashin wuya nadubo ta"wani malolon abune yazomar makogoro ya toshe,dakyar ya iya maida yawun bakinsa,bayan yad'an kauda kansa, jin wani irin mak'ak'in warin kore fet din bakinta dake barazanar d'aukemasa numfashi don inbaicikaba k'ila ta shekara batayi brush ba. Yinaji yana gani takuma fita a motar ta arta cikin unguwa ,ba'ajimaba saiga su tareda wata matashiyar yarinya da zasuzo sa'anni duk'u duk'u da ita ,k'afa bako takalmi.har gaban motar ta rakota"indona wazai ringa taremun fad'a inkin tafi" wani wawan tsawa tadaka mata"keeee!, to saiki gayyato uwarki tatare maki,tukunama waike dak'ik'iyar inace,na'aza nan nagama baki shawaran yanda zaki daki banzaye,yanzu kinamun maimaici ,salan inje zaria intarar 'yar farfesun nawa yagaji da jirana yahuce ya sandare....malama dan janye tsumman jikinki saura karki kwaso takalmi kisa kibari indawo insameki hakan"
"Wohoho! Indo waike wannan kawarkice ko 'yarki,kitsahirta mata hakamana ,ke kuma da azaban kwadayi 'yan uwanta dakike gani yasakike like mata tana maki gori da wulakanci..." Yayace tafito daga cikin gidansu ,jin karad'in indo dayacika layi,tafito taga dawacce takeyi.
"Ahayyye ,cas lallai,inbaka mutuba ,ba zaka daina ganin abun haushiba ,kekuma asuwa?, karuwa a masallaci?" Idi driver ne da kuluwa suka dauki salati atare "indo nice karuwan?" Mere baki tayi,bako d'ar aranta "ohoo tanan kika biyo to kilan hakanne...malam zakaja mato mutafi ko in kwashe tsummokarai nane inkoma ciki? " jinjina kai yayi cikeda gajiyawa ikon Allah "hajiya kiyi hak'uri d'an yau se allAllah shirya" baibi takan surutanda kuluwa tacigaba dayiba,ba kwama bare fullstop ,tasai fad'an tsaf ,don tuni rahane tasulale ,don tasan indo na jin zuciya zata fincikota tajibga.
Wuta yabawa motarshi yaci hanya ,yanbin kwazazzabon hanyoyin,duk in yashiga inzai fito saidai kaji k'ummm! Indo tak'ume , nan zata haujaraba bazata yi shiru ba zatajita takuma wani k'umuwar,zagi kam drivern nan yasha ta har sukafito titin zuntu.
Goshinta duk sunyi k'ulayen azaba,shikam duk tsiyar datake cikanki baice mataba. Basuyi nisa da tafiyaba ,barci ya sureta bata tashi farkawaba saida suka shigo Zaria.
Mik'a tayi tahau mitsike fuskarta da kwalliyar kwalli da janbaki datayi ya hade da zufa yayi dameji tadawo kamar aljana bakaganin komai sai farin kwarar idonta.
Tunda ya hango idonta tamadubin dake kusa dashi yake guntse dariya duk wannan kwalliyar haukan yadame guri guda,bata wani damu da murmushi dayake yiba .tsaki tamayi"mtseewwww,Allah yara bamu da motsatse"
Kanzil veceba saima shan kunu da yayi, shan kwana roundabout din p.z din da taga yayi a maimakon adauki hanyar hanwa shi ya tsoratar daita,shalll taga driver yadauki hanyar shiga GRA din gadan gadan,awani zabure ta k'walla mai wani gigitataccen k'ara a kunne , dagudu yataka wani wawan burki ,sakamakon kambin motar da ta nemi kub'ce masa a hannu. Aguje yayi parking a gefen hanya.
"Hajiya lafiya dai?" Tsaki tayi tafara babballa masa harara kamar aljana
"Ina fa lafiya zaka kaini inda za'ayi gandar kaina,kahe kai, in d'an yankan kaine,inbahakaba meyakawo mu nan,muda zamu unguwarsu.... Yo kodai kadauka bansan wuri bane,kana wani wuri wuri da ido kamar ifiritu,ja'iri tsokan kaina yafi karhinku ank'ur'an..." Takaicintane yacika mai zuciya don dai idi driver badai fushi ba
"To dan gidanku ,yanxu ya kikeso ayine?ko kibari inban kaiki gidan su hajiyanba daganan saiki nema hanyar matsera,dan inkika sake mun ihu aka saina karairayaki nawatsa ma karnukan layin nan Yaseen"
"Iyeee!, wata kan anty tasan kuna cin naman mutane,tokodai harda wannan mijin nata,dama ni tini nad'ibiya masa ayar tambaya, wannan talliyar kan nasa kamar na yahudu da nasara,to mujed'in inga dame kuke tak'ama,koka d'auka zan firgitane?, to aradu k'wank'waman kaina sunfi k'arfinka..."figar motarshi yayi a mugun zuciye,zuwa cikin GRA din ,don duk ak'agare yake ,yak'osa yakaita yahuta da jarababben surutunta maras kan Gado
Adaidai wani mahaukacin gida,taga drivern yana karkata akalan motar ciki,horn yayi tareda kokarin shiga harabar gidan bayan ankwaye get d'in. Wani hamshakin gida mai cikeda furanni da bishiyoyin kwakwa tagani yacusa kan motar ciki,sojoji birjik acikin gidan.tsurewa tayi take tahau sunbatu" lahaula walakuwata,ya bagabaga ya kilu ,wabillahi labinnasi ...idirisu ina zaka kaini ne? Daga wasa...aradun Allah wasa nake maka,mama na sona araye...nabi allAllah nabika ka maidani gida nafasa zuwa gidan su fatsiman..."
"Kinfasa,gayyato mitsa mitsankan naki? Bagidaji kawai to har gaban dodon tsafinmu zankaiki ,sai naga ya zuk'e jinin jikinki zanfita" nan yashiga da motar wajen adanasu,yayi fakin yafito "fito haka nan nace" zare gwalagulan idonta tashiga yi,hawaye na diga
"Yaseen banfita,saidai kakirasunan..." D'age kafad'arta sama yayi"to ki tazama ni kinga tafiya ta"
Daidai nan ta hango anty faty cikin shigar dandatsatsiyar leshi,sai walainiya takeyi ta hasken rana.
K'uri tayi da idanuwanta cikeda tantaman in antyn tace.da dariyarta takaraso ta bude mata kofan"autanmu sannu da hanya"ja dabaya tayi saurin yi su Hassana da Hussaina ma suka juya a zabure cikeda taraddadi,kwalla ma idi kira tayi
"Idi mai yafaru ne,ko iskantane suka bugeta a hanya?" Sauke wahalallan ajiyar zuciya yayi
"Kamar kinsani hajiya,naci wuya a hanya ,kar ala naimaita"
"Allahu sarki ,gaskiya naga fuskarta kamar daddawa sai dango takeyi ga jirwayen hawaye faceface.... Topah ya zamuyi kenan" zaraf Hassana tasoma magana "mommy akira kakkarfan kurtun can Joseph mana,sai yadauketa ashigo daita daga ciki"
Indo datun d'azu take jab'e kamar kayan wanki ba uhm bare um'um rungume da tarin kayanta ,jin an anbaci soja yasa tazabura tafito a sittin .hanyarda mom suka fito tanufa a tsiyace,karo tayida kakkarfan kirjin wani dake tunkaro cikin compound din,tipp tafadi 'kasa cikeda jin jiki................
Wani kakkausan muryane yasoma amsa kuwa a kunnenta
" Waye wannan? Hassenorh wata bagidajiyace wannan? "




Like
Vote
Share
Comment
[8/19, 10:14 AM] Haisahhtttttt💅🏻: *👠👠💅🏻 BAGIDAJIYACE👠👠💅🏻*



*©️HIKIMA WRITERS ASSOCIATION*
*(Home of peace, joint entertainment to educate and enlighten our readers)*



Story and written by✍🏻
Hassenart
☎️090 -659 -902 -65


*Dedication*

*Wannan page din sadaukarwane gareku masoyana,🌹🌹 kuyi duk yanda kukaso dashi mallakinkune,saikunso wani ya karanta. 'yan groups d'ina masu nuna mun tsananin 'kauna ta hanyar turo mun zunzurutan comments 'dinku ,masu karamun k'warin gwuiwa,nima ina sonku kamar raina*
*•••HASSENART FANZ GROUP •••*

*•••RAMUWAR GAYYA/BAGIDAJIYACE COMMENT BOX•••*

*•••RAMUWAR GAYYA FANZ GROUPS1️⃣&2️⃣•••*

*My warm regard tareda jinjinar bangirmata baxai tab'a yankewaba agareku HASSENART NOVELS PAID GROUPs 1 & 2. Koban fad'aba kundaisan ance babbar masoyinka shine Wanda zai baka kudin shi don ya nishad'antu da labarin ka,don haka nima inayinku totally alqur'an🤪💯*


~*Littafin kudine books d'ina wato RAMUWAR GAYYA da BAGIDAJIYACE, only #200 na katin mtn .sai kuma idan VIP kikeso #300 ne shi,zaku turo katin ta wannan number 09065990265.*~
~*Hajiya karki biyoni inba biya zakiyi ba ,don aradun Allah zan blocking d'inkine nan take👌*~



*Free page 1️⃣1️⃣~1️⃣2️⃣*



Kecewa da dariyar 'keta su Hassana sukayi har suna duk'ewa a wajen don sunsan dai batazo gidan a sa'a ba tunda Allah yayi mata gamoda farouq.


girgiza kai mom tayi,sannan tawaigo tak'are ma umar da indo kallo.

"Umar wannan yarinyar dakake gani
Kanwarmuce,itace autarmu..."

Dafe k'irji yayi kamar Wanda yaga abun tsoro "mum,wannan abar ?...jitafa kamar bugun aljannu,nifa dafari na'aza gamo nayi...tabdi lallai wannan inhar kanwarkice,amma zama daku baisa ta gogeba tabbas ba k'aramar cikakkan BAGIDAJIYACE ba..."

Murmushi mum tayi don ita batafaye son hayaniyaba.jinjina masa kai kurum tayi
"In boy yazo katambayeshi relationship d'in dake tsakanin shi da ita"

Mikewa indo tayi cikeda masifa jin ankirata da bagidajiya tayi mai k'ur da dakwadakwan idan uwanta uwa na mayu,ai dasauri ya kauda fuska,donshifa rod'i rod'i yaga tana masa a ido ,tuni ya soma ganin jirijiri.
"Malam bar ganina haka ,kazata kanwar lasace,to kwarankwatsa nasaba danbe da shirga shirgan mazan k'auyenmu dagani sai guntun fatari ,bare kai me kamada tsinken sakace wani korekore dakai zibun cutar shawara, don haka kashiga cikin hankalinka inkuma saimun gwabzaneto"

Tsuru yayi mata da idanuwansa kamar yana hango wani najasa ajikinta. Kanzil yakasa cemata

"Hahahhh cabd'i yau yaya ba magana ne ?...gakafa ga indo,Ku d'ab kafta musha kallo don Allah" Cewar Hussaina kenan.

Juyowa yayi a mak'uran zuciye don gidanku yaushe nafara wasa dake ne?...bar wajen nan kar na b'arar dake" simsim tarab'e tawuce ciki. Hassana ma bin bayanta tayi dasauri don tasan yana iya zanesu yanzunnan .dama ita tuni mom tashige cike tabar su anan
Dawowa takan indo yayi datayi tsaye akansa tana jijjiga jiki
"Ke kin d'aga mun takalmina kinban waje nawuce kokuwa?k'afa kamar na tsinnaka"
Jan zogala zogalan kafarta data take masa takalmi tayi ta hankad'a masa takalmin gabanshi,tana faman ballare ballare tareda murguda masa baki.

"Mtsewwww,Toni me zanda takalmi nan har ake mun tsawa kansa ,takalmi sai kahe na hilanin garin mu"
tajuya tashige ciki,sai ya ??tana saka k'afarta a cikin falon da sauri tayi saurin dawo da kafarta wajen ,nan tasandare tsaye daga bakin k'ofa
"Ya rasulullahi manzan tsarki,jama'a inane hanyar dakukabi Nene?kut macizzai🤔"
Dakatawa da tafiyar farouk yayi da azamansa yadawo wajenta ,d'an nesa da ita ya tsaya,cikeda zullumi, yana toshe hancinsa yana k'arewa rafkeken falon kallo
" ke ina macizan?" Bata bashi amsaba saida ya zauna ,dab'as tayi a kasan varendarn tukuna.sannan ta bude baki hagaga tasaki 'katon hamma ,barufe baki bakomai tana gama hamman ta hau tofi da yamu tagefe,jikake tuftuf!

Jiyoda kansa tad'aya barin yayi,sannan yasake mata magana cikin tsawa tsawa
"Ke wai bakiji mai nace bane?"
Zare d'ankwalin kanta tayi zuwa gaban goshi tahau Sosa gashin kanta da akaima kitso 'Yar Hausa(two hands) tsabar dadewa har ya daskare baka iya ganin tsagon kitson,sai uwar k'ura kamar an barbad'a,wani hamma takuma yi harsaida tayi hawaye cikinta yabada kukan"k'uuuuuu" saida tashafa cikinta sannan tace "mai rogo....uhnm ,wai mekahe,macizzai ko?To eh maccizzai mana ni ,narasa ta inda sukaine, suka wuce ta wagga waje,sufa sukayi ne...yayane oho..."
"Ke wai macizan ?" Yafad'i a matuk'ar rud'e .Tab'e baki tayi
"malam bari inmaka gwari gwari,don naga kai din kamar bagidaje kake jinka... Tambaya nake ,shin ta ina ake shiga gidan saman Canne?...don dai kaga kasarnan kwalba ne,tekune menene allahu a 'alamu"tawatsa hannuwanta a siket din jikinta ,yaraffff.

"Mtseww ,nikike kira ma da bagidaje? Kodayake ba laifinkibane,tunda ga tayil kina kiransa teku?kaini wata jarrabtane yasameni ma,natsaya nake daka tataki?"

Juyawa yayi zai tafi,ai asittin tadank'o rigarsa."bawan Allah temaka muni kasadani da d'akin fatsime,kahin sanyin wajen nan yamaisheni k'ank'ara,bakajiyo ihun cikina daganan?....to Yaseen ko Karin safe banyi ba zumudin zanzo inci farfesu.....ko ka kwatantamun yanda kuke haye wannan wajen"

Daura hannu a goshinsa yayi kafin yafincike rigarsa dakyar
"Kedakata,wai wajena ne kikazo?, to bara inkira boy yazo yashigar dake"
yana magana yana maida numfashin wuya don tsamin jikinta ne yaji yana yin k'urin sashi amai,wayarsa yaciro yayi dialing wani number,ringing biyu aka d'auka

"kai haidar kana inane? ....ka Yiwa girman Allah kazo karabani da wata halittar....eh gamunan anan main door...tom"

k'arar k'ofar wani glass shi yadawo daita duniyarmu.bayan talula dunuyar tunani......

Takowa aliyu yayi da sauri fuskarsa fal fara'a
"A'aaah indororos ne yau a gidannamu?"

Kyar tayi mai idonta nakan sawayensa, saida ya karaso kusada su ta sauke numfashi,
"Gadanga ,karka gaya mun gurin nan ba tekubane?naga ka keto lakadan"

"Haba indo ,tayil dinne yau tazama sabo a wajen ki? "

"Ohooooo,kace mun sumuntin turawa,to ai naga wannan harda ratsin ciyawoyi,gashi kuma ina kallon idanuwa ta ciki.....shi yasa nakid'ima,gidan nakune kamar na masu cinkai..... "Umarne ya tsinketa ta hanyar cema aliyu yawuce shi.

" hmmm d'an daudu Allah yakiyaye hanya kayi mun taimakon....Allah yabaka macen kirki Irina"
Kwashewa da dariya,haidar yayi"aboki kace kazama d'an daudu"fusata yayi yajuyo a hargitse kamar zai kaimasa hanb'ari

"Kai karka gaya mun badadi kajiko?"
"Toohh,lallai katunzura dayawa,to ke indo me kika gani a jikinsa kikecemasa d'an daudu? (Yafada yana kamo hannunta sama)....sai anjima inanan shigowa.... Yanzu dai bari inji da bak'uwata"fita yayi cikeda takaicin wannan bagidajiyar indon .

Itakam indo sakin jiki tayi tafara kwararo mai surutu,ransa fal dariya badamar yi don gaba d'aya tazama kamar wata dodanniya.dakyar ya taitayota suka
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3

1 Comments On BAGIDAJIYACE
avatar
abdulkadir-lawan-yusuf

2 months ago

Reply

Tsarin labarin yayi

Please Login or Register in order to submit comment