Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

inda na samo shi ba?".

sai a sannan ta ɗan ɓata rai ta zauna kan turmi tana yimin kallon tuhuma ta ce"ikon Allah ke kuwa a ina kika samo wannan kuɗin me yawa haka?gaskiya kasuwar yau ta yi ƙyau sosai."

ɗan yatsina fuska na yi sannan na ce"wani mutumine ya haɗu dani a hanya shine ya bani kuɗin sannan kuma ya ce inyi sadaka da sauran".

na faɗi hakan ina kallon ɓangaren da mahaifina ya ke,idanunsa a rufe kamar me bacci,na lumshe idanuwa na inajin wani irin raɗaɗi a cikin zuciyata,ban sanda hawaye ya shiga sakkomin ba,sai ji na yi Amma na cewa.


"Ai wannan cinikin yanzu kasuwa zanje in saro kayan koli don mu ƙara jari,idan wannan ya tashi ki gyara mishi jikinsa ni ns tafi,ta nuna mahaifina da hannu a ya yinda ta ke saka mayafinta don fita,babu neman izini babu komai haka Amma ta saka mayafinta ta yi tafiyarta kuma tana bani sallahun wai idan ya ɓata jikinsa in gyara masa.

Kuka na shigayi babu ji babu gani don yadda zuciyata ta ke ta faman raɗaɗi sosai,ina Allah wadai da hali irin na mahaifiyata Amma.
Ko babu komai ai bai kamata ta ce in kula dashi ba saboda zai iya fitsari a zaune har ma da kashi,kenan ni ya kamata in ga tsaraicin mahaifina a wannan shekarun nawa da basu gaza sha huɗu ba,duk da a nahiyarmu ta ruwan kanya,da wuri a ke yiwa yara aure saboda mu fulani ne na usul.


Ni kaɗai na ke ta maganganu na babu mai bani amsa a haka na tashi na fara gyaran gidanmu ina cikinyi,na ga kamar alamar mahaifina ya buɗe idanunsa ƙwalla ta cika ƙwarmin idanuwansa tana ta sakkowa.


Jiki na a sanyaye na ƙarasa kusa dashi ina sharemai hawayen nasa,ya juyo ya kalleni yna son yimin magana amman bakin baya fitowa sosai,don bakin ya yi gefe gaba ki Ɗaya,kuka na fashe dashi kamar raina zai fita a tsugunnan da nake,da Ƙer ya ce"mama na ki daina kuka kinji insha Allah Zanji sauƙi kinji Inna woru na".

Ƴar dariya na yi na sunkuyar da kaina zara zaran gashin idona ya jiƙe da hawaye,ya tambayeni ina Amma na ce mishi bata nan,sai naga yana kiciniyar tashi alamun ya yi wani abu yana son a wanke mishi.

Ganin hakan da na yi na taimaka mishi na ɗebo ruwan na zuba mishi na rufe mishi suturarsa ya saka ɗayan hannun yana wankewa abin tausayi.
Tunda Amma ta ce ta tafi kasuwa bata dawo ba sai bayan isha'i bata bi takan mahaifina ba ta ɗora girkin dare babu ko magi a ciki ta zuba mana ni da ƙannai na muka fara ci,ita kuwa daman tazo da tsire da kuma gurasa na kasuwa ta cinye abinta,mahaifina ma wannan abincin yaci mara magi.




Kash!duniya kenan mata muji tsoron Allah mijin da ka ke saka ran zama dashi har a gidan aljanna kuma ka ke neman aljanna a wajensa amman kuma ka ga gara kyauta ta masa,Allah ka bamu ikon kyauta tawa mazajenmu Amin.
Amir yana zaune yana cin abinci amman hankalinsa baya kan abincin saboda tsananin tunanin wannan yarinyar da ya gani ɗazu gashi bai tambaye ta gidansu ba?yanzu ya ya zaiyi tunda ya ke bai taɓa jin son wata ƴa mace irin son da ya kewa wannan yarinyar da ya gani a ƙauyen Ruwan kanya,amman insha Allah kafin ya tafi zai nemi wannan yarinyar don yana ji a jikinsa matuƙar bai aure taba komai zai iya faruwa,yana cikin wannan tunanin Amira ta kirawo sa matarsa.


Yana ɗauka ta fara kuka tana cewa"Abban safna tun jiya muna asibiti safna bata da lafiya numfashinta ya ƙi saituwa har yanzu don Allah kadawo Kadawo".


da sauri ya ajje wayar hankalinsa ya yi matuƙar tashi a ranar Amir ya koma duk ya rame saboda tashin hankali.


A ranar Safna ta ce ga garunka nan Bayan Amir ya koma😭.. . .






*miss green ce*
*🌈DARASI!!🌈*


BOOK 1

✨Rabiatu Bashir
Ummu maher(miss green)🍀💚


*@Wattpad link*

https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333?utm_source=android&utm_medium=com.gbwhatsapp&utm_campaign=invitefriends


*@Arewa book link*

https://arewabooks.com/chapter?id=62a48949772e179ad6e54443


*SIRRINKI👂🏻*

Ki zamo mai suturta jikinki kada ki fita ƙariyatun ƙasiyatun,ki zamo mai lulluɓe jikinki.Allah karabamu da cin wuta Amin.

14/15


"Ammi don Allah ki daina kukan nan, da saka damuwa aranki abinda yaya Ammar ya ke buƙata a wajenki kawai addu'a ya kamata ki dinga yi masa,damuwarki za ta haifarwa da Yaya matsala sosai aruyuwarsa,don haka ki share hawayenki ki yi masa addu'a insha Allah Sakinat sai ta girbi abinda ta aikata miki,don raba ɗa da uwa ba ƙaramin abu ba ne."


"insha Allah auta na daina kukan nan daga yanzu".


dariya Khalisat ta yi sannan ta ce"Ammi a kullum idan na tuno wacece Sakinat a cen baya abin har mamaki ya ke bani,kamar ba ita ce ƴar aikin ki a baya ba,kucaka ƙazama."

dariya Ammi ta yi wanda ya fi kuka ciwo tana tuno wacece Sakinat a ba ya.






*Asalin labarin Sakinat*



kamar yadda Khalisat ta faɗa Sakinat mai aiki ce a gidansu tun zamanin mahaifinsu yana nan kafin daga bisani kuma ya yi hatsari ya rasu.


Sakinar ƴar asalin maiduguri ce a cen aka haifeta ita kaɗai ce awajen mahaifinta tun tana ƙarama mahaifiyarta ta rasu,bayan mahaifiyarta ta rasu ne suka koma garin adamawa anan kuma riƙonta ya koma gun yayar mahaifinta.

Yayar mahaifinta ita ce ta kai Sakinat wajen aiki da kanta don ta ce tunda taƙi talla dole ne ta yi aiki,gidan farko da aka kaita yaron gidan ya yi mata fyaɗe daga nan kuma suka jo ne da yaron gidan don kullum Sakinat tana ɗakinsa,duk sanda
Za suyi mu'amala sai ya bata wata ƙwaya ta hana ɗaukar juna biyu,sakinat kuwa bata san ko na me ye ba don ba tada ilimin da za ta gane.
Kwatsa rannan mahaifiyar yaron ta gansu ta yiwa Sakinat korar kare,daga nan ta koma gidan yayar mahaifinta mai suna Abuwalle.

Abuwalle mace ce mai shegen son kuɗi da son duniya don haka babu daɗewa ta samo wa Sakinat aiki a gidansu Ammar.
Tun ranar da Sakinat ta fara aiki a gisansu Khalisat Ammar ya dawo daga tafiya daga ƙasar germany,Tun da Sakinat taga Ammar hankalinta ya tashi don kyaunsa da nutsuwarsa ba ƙaramin dagula mata lissafi ya yi ba.

Ta rasa yadda za ta yi da rayuwarta don ko kallo bata ishe sa,ko mopping ta ke idan ta hangosa ɓuya take saboda matuƙar ta gansa to fa zuciyarta ta yi ta bugawa kenan,har sai ya bar wajen da kusan awanni sannan za ta samu damar fitowa don cigaba da aiki.

Ammi ba macece mai takura ba saboda ba ta ɗaya daga cikin matan da ke wahalar da ƴan aikinsu ba,saboda macece mai mutunci da kuma karamci.

Ana cikin haka ne Sakinat ta fara wani irin ciwo,idan ciwon na ta ya tashi har aman jini ta ke,babu shiri Ammi da Alhaji Muhammad Lamiɗo wato mahaifin su Ammar suka kai Sakinat asibiti.


Tashin farko bayan likita ya gama gwaji ya ce ai Sakinat tana da ciwon zuciya,adinga yi mata duk abinda ta keso saboda idan ba haka ba ciwon ba zai warke ba.


Hankalinsu ya tashi sosai bayan sun dawo gida shima Ammar ya dawo ganin da Sakinat suke tare ya yi gaba zuwa cikin babban farlon gidansu,yana zama sai ga su Ammi sun shigo.

Suka saka Sakinat a gaba da tambayar abinda ya ke damunta kai tsaye ta ce ita Ammar ta ke so. . . ..




Kuyi haƙuri wani busy ne shiga ne👏🏻👏🏻👏🏻👏🏻.



*Miss green ce*
*🌈DARASI!!🌈*


BOOK 1

✨Rabiatu Bashir
Ummu maher(miss green)🍀💚


*@Wattpad link*

https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333?utm_source=android&utm_medium=com.gbwhatsapp&utm_campaign=invitefriends


*@Arewa book link*

https://arewabooks.com/chapter?id=62a48949772e179ad6e54443


*SIRRINKI👂🏻*

Mu yawaita tunawa da mutuwa yin hakan zai rabutar damu duniya da lahira.Allah ka tsaremu daga shiga wuta Amin.
--------------------------------

18/19


Maganar ƙarshe da mahaifin Ammar ya faɗa shine"Ammar kada ka wulaƙanta wannan yarinyar kada ka juya mata baya,don kaga bani da rai,kada ka taɓa rabuwa da ita ma'ana ka saketa matuƙar ka saketa to ka saka a ranka babu ni babu kai."


wannan maganar ita ce ta ƙarshe da ya faɗa ya fara wani irin tari mai sarƙe maƙoshi daga nan rai ya yi halinsa,babu irin kukan da Ammar bai yi ba na rashin mahaifinsa ga abu goma da ashirin wai kada ya yarda ya saki Sakinat,shi ya rasa me yasa ma ƙwata2 ko kallonta ba yasan ya yi,yadda kasan wata mujiya haka take a wajen Ammar amman ya zamar masa dole ya fara sakin jiki da ita ko don nasihar mahaifinsa.



Bayan wata biyu rannan Sakinat tana zaune suna hira da Ammi,aka yi sallama da gudu Sakinat ta rungume Falmata ƙawarta ta yarinya ta,sosai taji daɗin zuwan Falmata don tunda ta yi aure ko dangin mahaifiyarta basu zo ba,don basu san ma ta yi auren ba.


Kalle2 Falmata ta shiga yi sosai irin kallon tsaf ɗinnan,Ammi sai kallonta take tana mamakin hali irin na wannan baiwar Allah.


Sai da Sakinay ta ɗan dunguri Falmata sannan ta dawo cikin hayyacinta,tana harar bayan Sakinat don gani take Sakinat bata dace da wannan gidan ba ita ce ta dace dashi,don haka ko ta halin ƙaƙa sai ta zauna itama a wannan gidan kuma ta fitar da ƙawarta Sakinat.


Tunda Falmata tazo gidan babu abinda take sai zuga Sakinat akan cewa wai tsabar baya sonta har yanzu yaƙi ya kaita gidanta ya barta a gidan iyayensa,wani lokacin kuma ta ce kinga gidansu kamar aljannar duniya ko ina gwanin sha'awa,duk yadda akayi komai shi yake a gidan kuma yana jin maganar mahaifiyarsa.


Da ya ke Sakinat sokuwa ce sai maganganun Falmata suka fara tasiri aranta har ta fara ganin ayanzu za ta iya fito na fito da Ammi don tun ba yau ba tana ganin irin abubuwan da Ammar ya ke wa Ammi,yana matuƙar girmama maganarta don har yafi jin maganar mahaifiyarsa da ta mahaifinsa.


Acikin satin Ammi babu irin rashin kunyar da ba ta gani ba awajen Sakinat kuma ta lura Falmata ce ke ƙara zugata,don haka duk sai ta watsar da su ta cigaba da sabgoginta,don dama Khalisat tana boarding Ammar kuwa ya yi tafiya zuwa ƙasar England wani aiki.



Ƙwanan Falmata biyar ta haɗa kayanta don tafiya gida,ta tambayi Sakinat ina ne ɗakin Hajiya,babu musu Sakinat ta nuna mata ta ƙwanƙwasa alokacin Ammi tana azkhar.
Ammi ta buɗe mata ta shigo tana gaida Ammi,ta amsa tana mamakin ganinta bata gama mamakin ba ta jiyo Falmata tana ce wa.


"Da man gida zan tafi shine na ce bari inyi miki sallama sannan in faɗa miki wata magana don nasan baki sani ba,lulluɓin biri aka yi muku.


Da mamaki Ammi ta ke kallonta tana mamakin hali irin na Falmata na munafurci,wato don taga ƙawarta ba ta nan shikkenan sai kuma ta yi gulmarta.


"Hajiya Sakinat fa kafin ta auri ɗanku sai da aka cire mata ciki har sau biyu,kuma wallahi har yanzu bata daina bin maza ba".


da sauri Ammi ta ɗaga mata hannu sannan ta ce cikin tsawa"get out in my room".


da sauri Falmata ta fito har tana haɗa hanya tana da na sanin zuwa wajen Ammi don yadda kasan zaki haka ta juye mata.


Akan hanya suka haɗu da Sakinat sannan ta rakata har bakin gate,tana mamakin sauyin Falmata lokaci ɗaya.




Ammar yana dawowa Ammi ta sakashi a gaba da ya tafi da Sakinat sabon gidansa na Abuja,babu yadda ya iya haka ya tafi da ita ransa baiso ba.



Wannan tafiya itace ta zamewa Ammi wannan mummunan tabo a rayuwarta don tun daga ranar Ammar bai sake zuwa wajen mahaifiyarsa ba,don tun bayan komawarsu da Sakinat ta ga Ammar ba ya ko kallonta ballan tana ta saka ya yi mata magana.

Da kanta ta nemi Falmata suka haɗa kai aka raba tsakanin ɗa da uwa Ammar da Ammi.







*Cigaban Labari*

*Fahima*
-------------------

A yanzu Amma ta matsamin wai acikin mane ma na wai in fito da mutum ɗaya don ita ta gaji da kallona babu aure,abin har mamaki ya ke bani don har yanzu ko shekara sha biyar ba amman ake min zancen aure.


A cikin masu sona aƙwai wani Alhaji Tasi'u mai nera,shine wanda Amma tafi don yana matuƙar jiƙata da kuɗi.


Ita kuwa Fahima ta yi mugun tsanarsa don mutumin mugun ɗan iska ne duk ranar da yazo sai ya nemi daya taɓa jikina ni kuma in ƙi yarda.

Kuma kamar maye gobe ma sai ya dawo,kuma a ƙalla ko da baiyi shekara hamsin ba to kaɗanne.




*miss green ce*
*🌈DARASI!!🌈*


BOOK 1

✨Rabiatu Bashir
Ummu maher(miss green)🍀💚


*@Wattpad link*

https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333?utm_source=android&utm_medium=com.gbwhatsapp&utm_campaign=invitefriends


*@Arewa book link*

https://arewabooks.com/chapter?id=62a48949772e179ad6e54443


*SIRRINKI👂🏻*
Kada ka aikata wani laifi ka ɗauka Allah baya ganinka idan kai baka ganinsa to shi yana ganinka.Allah katsaremu da cin wuta Amin.

16/17

. . .Wani Mugun kallo Ammar ya wurgawa Sakinat da ke lafe a jikin Ammi,sannan ya kalleta cikin wata muguwar tsawa yace"i hate u!i said i hate u!"shin ana soyayya dole ne,me zanyi dake kucaka ƙazama mara class,ni kuma in rasa wacce zan aura sai ke? Stupid girl kawai mssttttt".

Ya buga wani uban tsaki ya haye upstair don gani ya ke idan ya cigaba da kallon wannan mumu girl ɗin komai zai iya faruwa dashi,ƙarshe power ɗinsa na soldier ya motsa ya shiga jibgarta.


A hankaki Alhaji Muhammad Lamiɗo ya zauna ya kalli Sakinat ya ce"tashi ki koma ɗaki ki kwanta kinji Allah ya yi miki albarka".

da sauri Sakinat ta tashi kamar daman ta matsu ta tashi ɗin,Ammi tabi bayanta da kallo ta ce"Alhaji yanzu ya ya ka ke ganin za ayi"?.

"Insha Allah komai zaizo da sauƙi amman kafin nan zanyi shawara zuwa ko gobe fatanmu Allah ya tabbatar mana da alkhairi.


***

Ammar yana ɗakin motsa jikinsa yaji a jikinsa kamar ana kallonsa,da sauri ya juyo,Sakinat ce tsaye a kansa ta lu-la duniyat tunani,wata uwar tsawa ya buga mata ita kuwa tana cen kogin tunaninsa yadda gashin ƙirjinsa ya ƙwanta luf luf gwanin sha'awa ruwan gumin jikinsa ya jiƙa duk beauty ɗin skin ɗinsa abinka da ƙyaƙƙyawa sai ya yi wani ƙyau mai ɗaukar hankali.
Wani banzan kallo ya yi mata a karo na biyu sannan ya tashi ya yi tafiyarsa.
Sakinat ta bisa dana mujiya kamar za ta haɗiyesa tsabar so da ƙaunarsa.


"Ammar!"Alhaji muhammad ya faƊi sunansa cikin babbar murya ya ce"me sunan manya Ɗazu misalin Ƙarfe uku da rabi na rana an Ɗaura aurenka da wannan Yarinyar Sakinat abisa yardar waliyyanka da waliyanta don har garinsu na je muka taho da babanta".


Kansa a sunkuye tun da Alhaji ya fara magana baice komai ba,don iyayensu sun yi matuƙar ƙoƙari wajen basu tarbiyayya,idanuwansa sunyi jawur sosai jijiyoyin kansa sun tashi ruɗu ruɗu,ba Ammar ba hatta Khalisat sai da taji wani iri har a cikin zuciyarta.


Tunda Ammar ya Tashi daga wajen mahaifansa kai tsaye motarsa ya hau ya fita,wayarsa ya ɗauka ya kirawo Aliyu ringing na farko ya ɗaga yana tsokanarsa da ango don ɗazu yaji komai na game da auran da Dad ɗinsa ya yi masa.


Banza Ammar ya yiwa Aliyu ya cigaba da shaƙiyancinsa har ya yi shiru sannan Ammar ya ce idan har ka gama ka sameni a hill&vally.

Waje ne kyakkyawan waje wanda ya tsaru,an ƙawata shi da followers da bishi yu kala kala,ga sanyi da ni ima ta ubangiji,mutane da dama suna zuwa wajenne saboda shaƙatawa,ko kuma hutawa saboda zuciyarka ta samu reliep.

Yana zaune yana ta kallon ruwan da ya ke ta zubowa ta cikin ƙasa,shima wajen an ƙawata shi sosai gwanin ban sha'awa.

Tunani kawai ya ke yi a game da makomar aurensa shi da wannan mummunar yarinyar,sam ba irin kalar Sakinat ya ke buƙata a matsayin matar aurensa ba,gaba ki ɗaya ma dai ya tsani yarinyar sosai,har bai san adadin tsanar da ya yi mata ba.


Yana zaune kiran Amir ya shigo wayarsa ya ɗaga a hankali kamar ba soja mazan fama ba,nasiha mai ratsa jiki Amir ya dinga yi mai a game da auren da mahaifinsa ya yi masa,kada ya bijirewa mahaifansa ya yi abin da suke so wataran zai tsinci haƘurin a gaba.


Tnx kawai ya cewa Amir sannan ya kashe wayarsa saboda tsabar haushi,don shi haryanzu bai yarda zai tsinci wani alkhairi a gurin wannan fush girl ɗinnan ba.
Ammi ma ta rasa mai yasa tunda Mijin na ta ya yi mata albishir da ɗaura auren Sakinat da ɗanta ta tsinci kanta a mai mummunan faɗuwar gaba ta rasa me ya ke yi mata daɗi,ba wai auran ta tsana ba a ah kawai zuciyarta ce bata aminta dashi ba,musamman yadda taga Ammar gaba ki ɗaya ya canza alokaci ɗaya,ta tsani abinda zai ɓata ran Ammar tana yi masa wani irin mugun so da tausayinsa a matsayinta na mahaifiyarsa,Allah kaɗai yasan irin zaman da zasuyi shi da yarinyar,amman koma dai menene tana roƙon Allah ya kawo sauƙinsa cikin ruwan sanyi.
Sannan tana yi masa fatan samun zaman lfy . . ..

"Tunanin me ki ke yi Zulaihat"?.
da sauri Ammi ta cire tagumin da ta yi ta yiwa mijin na ta murmushi don kada ya fuskanci halin da ta ke ciki.


Murmushi ya yi sannan ya ce"Zulaiha na sanki tun kafin ki kai shekarun haka shekararki 14 aka auramin ke alokacin ni kuma ina da kusan talatin kuma ina matsayin soja a wannan lokacin,ki kayi haƙuri ki ka zauna dani a halin da na ke ciki na yaron soja don kowa yasan halin zuciyar soja awannan lokacin harma da yanzu,to me yasa ki ka kasa haƙuri akan wannan auren dana ɗaurawa ɗanki?aƙwai abubuwa da yawa dana duba kafin in haɗa wannan aure ba da ka na yi saba,wannan yarinyar ba tada gata sai Allah akan ɗanmu ta kamu da ciwon zuciya fa?idan ƴarki ce zaki so hakan ya faru da ita?to kinga ba zaki so ba."


Tun daga nan Ammi bata sake haɗe ranta ba kullum cikin yiwa ɗanta nasiha ta ke,tare da addu'ah.



Tafiya ce ta kamasi zuwa bauchi garin aminin Alhaji Muhammad,da ammi za aje amman kuma sai ta ce ta fasa tana da buki,da Khalisat da Sakinat aka yi tafiyar sai Alhaji don shi uban gayyar Ammar yana Abuja.
Innalillahi wa inna ilaihi raji'un.

Aranar bayan sun tafi kan hanya sukayi hatsari aka nufi dasu asibitin da ke kusa,shi dai Alhaji abin sai addu a,Sakinat da Khalisat kuwa ɗan kukkurjewa ne kawai.


Aka kirawo su Ammi a waya cikin tashin hankali tazo,yadda taga mijinta abin sai addu'a,ta kirawo Ammar tana kuka ta ce yazo ta faɗa masa halin da suke ciki,kai tsaye daga Abuja ya taho hankalinsa a tashe.

Da ƙer Alhaji ya fara magana yana yiwa Ammar nasiha akan Sakinat,kuka kawai Ammar ya ke na ganin halin da mahaifinsa ya ke.



*Miss green ce*
*🌈DARASI!!🌈*


BOOK 1

✨Rabiatu Bashir
Ummu maher(miss green)🍀💚


*@Wattpad link*

https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333?utm_source=android&utm_medium=com.gbwhatsapp&utm_campaign=invitefriends


*@Arewa book link*

https://arewabooks.com/chapter?id=62a48949772e179ad6e54443


*SIRRINKI👂🏻*

Mu yawaita hailala da istigfhari yin hakan zai ƙara kusan tamu da ubangiji.
----------------------------

20/21

Sakinat ce a zaune tana waya da Falmata, kana ganin Sakinat kasan ranta a ɓace ya ke ta ce"Falmata yau watanmu biyar da zuwa wajen bokannan amman har yanzu banji wani chanji ba da zaisa in gane ina da ciki,abin yana damuna Falmata ni dai idan babu hali kawai mu chanja wani bokan kawai ina ganin zaifi ko"?.


shiru Falmata ta yi tana mamakin hali irinna Sakinat don duk bin bokaye irin na Falmata bata ka ma ƙafar Sakinat ba,ko da ya ke Sakinat ta yi mata zarra a fannin kuɗi dole ta fita fitowa gari.


"Eh aƙwai wani boka da na ke tunanin zai iya wannan aikin wanda matuƙar ya yi miki aiki to fa shikkenan,zaki ganki da ciki a jikinki ko da na aljanu ne kuwa".


da sauri Sakinat ta ce"haba Falmata ya zaki ce wai ko da na aljanu ne,idan na samu cikin aljanu ai an samu matsala lafiyayye na ke son haifa".


Ƴar dariya ce ta kusa kufcewa Falmata don tasan duk wannan yawon da suke yi ba lallai ne ta haihu ba,don tun tana budurwa ta gama zubarda abinda tun a waje".


Ƙalubale gareku ƴan mata ku daure ku riƙe mutuncinku domin shi mutunci madara ne,kuma daga inda namiji ya yi amfani da ke ko da ciki bai shiga ba to kin gama cutar kanki,gwara duk rintsi ki daure ki kaiwa oganki(mijinki)budurcinki na ƴa mace,wallahu a 'alam.


Nan dai Sakinat da Falmata suka shirya zuwa har Ghana wajen wani tsohon mushriki don Sakinat ta samu Haihuwa,washe gari da wuri suka ɗauki hanya don ma jirgi zasu shiga sai Accra(Ghana).


Sun sami layi sosai don haka suka jira har layinsu yazo,suna shiga Sakinat ta fara toshe hancinta don wani irin mugun warin da wannan mushrikin bokan ya ke,Falmata ta riƙe hannun Sakinat tana janta don ta daina rufe idon,don idan bokannan ya zuciya zai iya gamaw dasu duka ya shanye musu jini.
Tun kafin su faɗi abinda ya kawosu Bokan ya fara faɗa musu duk abinda suke so ayi musu,ya janyo wani glass yana nuna musu abinda ke ciki.

Wata yarinya suka hango kyakkyawar Bafulata na suka hango yarinyar ba za ta wuce 13zuwa14 ba,cikin tsoro Sakinat ta ce"boka wannan kuma wacece?menene haɗinmu da ita?"

cikin sauri bokannan ya buɗe mushen bakinsa ya ce"ita wannan yarinyar ita ce za ta kawo ƙarshen matsalarki."





Alhmdh.


Anan na kawo ƙarshen book 1,kuma na gama free page idan ka tashi biyan kuɗinka ka neme ni ta wannan number.


07068606171



Ga
Details

*Littafin na kuɗi ne ban yarda ki karanta mun baki biyani ba,Gamai buƙata n cigaban labarin zai biya ₦300 normal* group...Vip group
₦500... Special₦1k....zaku iya Turo da katin MTN ta wannan number 07068606171
ko kuma ku tura ta wannan account number 2212328303
RABIATU BASHIR
Zenith Bank.

*Miss green ce*

An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2
Chapter 3

Please Login or Register in order to submit comment