Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[29/01, 10:09 PM] Mom Islam Ce: 🤦‍🤦‍♂️🤦‍♂️🤦‍♂️🤦‍♂️🤦‍♂️🤦‍♂️🤦‍♂️
*NIDA YARINYA*
🪂🪂🪂🪂🪂🪂🪂🪂

_Zainab Habib /Mom islam_

*Bismillahir rahmanir rahim*






https://www.wattpad.com/user/momislam2020?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends


1-2
yarinya ce ƴar kimanin shekaru goma sha huɗu na hango , zaune take a bakin ƙofar wata tsohuwa tana karkaɗa ƙafarta , tsohuwar dake zaune a cikin ɗaki tace "Ramu maza kije ki karɓo min fatari na idan Adamu ya ɗinke "cikin tsiwa Ramu tace "ka jiki dai ke baki da aiki sai aikan mutane ,ni yanzu ma zanyi kwaskwarima in fice "riƙe baki tsohuwa tayi kana tace "ke karki kawomin rashin arziƙi ,ubanki ma sai in aikeshi yaje balle ke "miƙewa Ramu tayi kana karkaɗe koɗaɗɗen zaninta tace "idan yazo kya aikeshi nikam dandali zani ".

Tsintsiyar dake bakin ƙofa ta wurgawa Ramu tana cewa "shegiya irin Dije irin tsiya ,baku san mutunci ba ,tsohuwa ta rariko Ramu da gudu taci karo da wani dutse tayi tuntuɓe ,Ramu dake tsaye tana jiran tsohuwa ta zo gurinta ganin ta faɗi yasa ta tu tsirewa da dariya tace "bani da alhakinki har da tafawa , a hankali tsohuwa ta rarrafa ta miƙe tana ɗingishi tace "shegiya irin tsiya kin yiwa Dije "oho dai kindai faɗi sai ki koma ɗaki "Ramu tace "tana tuntsirewa da dariya ta fice .

Tafiya taci gaba dayi tana yi tana ranguwaɗa harda yarfe hannaye taci karo da wani mai kwsar kwata , toshe hanci tayi taci ɗammara kana tace "jibeka zankaɗeɗe da kai amma ka ƙare a kwasar kwata ?" saurayin ne ya kalleta a kai kaice kana yace "ke dan uwarki ni kike gayawa haka ?"lura da tayi idanunsa sun juye alamar yana shaye shaye ya sanyata cewa "an faɗa mai shan giya kawai "ajiye baron dake gabansa yayi ya zubo da gudu , mai makon ta miƙe hanyar da take bi sai ta dawo hanyar gidan tsohuwa , da gudu ta shigo tana cewa "tsohuwa ki taimakeni zai kasheni "tsohuwa da ta gama kiɗimewa ta turo ƙofa da ƙarfi tana cewa "ya kasheki "dan Allah tsohuwa ki buɗe wlh ya biyoni "ya kasheki "tsohuwa ta faɗa tare da hayewa gadonta mai rumfa , fitsari Ramu ta saki a wando ƙafafuwanta har rawa suke tana ihu , wani wawan cafka yayi mata kana yace "ubanwa kike zagi ?"cikin suɓutar baki tace "badai ubana ba "buge mata baki yayi kana yace sai uban wa ? ya wanketa da mari ta riƙe gurin a hankali tace "Allah ya isa "waro ido yayi kana yace "waye wai ubanki ne ?"cikin tsiwa tace "kaje ka dubashi "tsohuwa dake ɗaki ta ɗaga murya tace "wlh kaci ubanta dama maganinta irinka mahaukaci "bugu ɗaya yayiwa ƙofar ta buɗe ya faɗa ɗakin da gudu yana cewa "ke gyatuma ki iya bakinki wlh zan mugun saɓa miki "nayi shiru "tsohuwa ta faɗa tare da toshe bakinta , mai kwasar bola yace "dena kallo na "cikin sauri ta sunkuyar da kai yace "tari naji kinyi sai na buge bakinki "Ramu dake bakin ƙofa tana jin diramar da sukeyi ta sanya dariya mai sauti tare da cewa "yau a dandali akwai labari mai daɗi ,ta fice da gudu .

Fitowa yayi ya tsaya a tsakar gida yace "wlh idan na kama jikarki sai nayi mata dukan tsuguna kaci doya "wlh kayi mata dukan sumewa ma "tsohuwa ta faɗa tana gwalo ido ,ficewa yayi cikin tafiyarsa irin ta ƴar shaye-shaye .

Tsohuwa najin ya fice ta nunfasa tare da yakice ɗan kwalin kanta tana fifita "wanan yarinya kwai masifa ,taje ta tsokano min tsuliyar dodo yanzu da naɗamin duka ai dana shiga uku ,tsohuwa ta faɗa tana share ragowar hawayen dake idonta.

Tunda Ramu ta fita take neman tsokana ,duk wanda tagani ko sa'an waye tsokanarsa take , wasu manyan sun bari a yarinta ke damunta wasu kuma basa ƙyaleta , cin karo tayi da wata budurwa tana waya a kusa da gidansu ,kasancewar gidan tsohuwa da nasu babu nisa , har zata wuce sai ta dawo da baya ta kalli budurwar ta tuntsire da dariya kana tace "jiran saurayinki kike ?budurwar dake yamutsa fuska tace "jiran ubanku nake "a'a'a ,Ramu tace "tana riƙe baki sai kuma tace "badai ubana ba sai dai naki "budurwar zata bita da gudu ta arce tare da yi mata gwalo ,cizon yatsa budurwar tayi cikin takaici tace "Allah yasa ma babyn nawa bai zo ba da wanan shegiyar yarinyar sai ta yarfani ,wata ƙila ma ta fallasani tace "aron kayan nayi, tana cikin magana wata mota Sharon fara mai gilashi tayi parking a kusa da ita , washe baki budurwar tayi kana tace "baby har ka iso ? leƙowa yayi yana yi mata murmishi yace "na ɗauka ma nayi miki laifi sbda ban fito da wuri ba ? "uhm ai baka laifi babyna ,budurwar ta faɗa tana kashe masa ido , buɗe murfin motar yayi tare da fitowa a hankali yace "dole in jinjina miki sarauniyar mata ,sunyi nisa a love Ramu ta taho a hankali da kifiyarta a hannu ta sace tayar motar tare da rugawa da gudu inda bazasu ganta ba .
Saurayin ne yace "Saudat ina sonki so mai tsanani bansan ko kema kina yimin irin son da nake yi miki ba?, lumshe ido budurwar da ya kira da saudat tayi kana tace "ai ni a tunani na Abdull soyayyar da nake yi maka tafi gaban kwatance, jin daɗin kalamanta ya sanyashi kamo hannunta ya buɗe murfin mota ta shiga shima ya shiga mazaunin driver ya tada mota , mamaki ne ya kamasa ya buɗe murfin motar ya fito tare da kallon tayar motar a fili yace "innalilahi wa'inna ilaihir raji'un , fitowa Saudat tayi ta kallesa tace "wai meke faruwa ne babyna?"tayar motar ce ta sace kumafa lafiya nazo da ita ai kin gani ma ko ?Abdull ya faɗa cikin ɓacin rai "to bari a kirawo masu gyara man ,Saudat ta faɗa tana shirin kama hanya ,Abdull da ransa ya gama ɓaci ya ɗauko wayarsa ya rufe motar da key yace "ki koma gida ni zan tari napep in hau ,ba haka taso ji ba daga gareshi sbda taso ya tafi da ita tunda duk zuwa yana yi mata kyauta mai tsoka gashi yau babu ko sisi kuma bashin kayan dake jikinta taci bata biya kuɗin ba , gani ranta a ɓace ya matso kusa da ita a hankali yace "Saudatu ki kwantar da hankalinki idan ganina ne da zarar munyi aure kin dinga ganina kenan ,murmishin yaƙe tayi lokacin daya fara tafiya a zuciyarta tace "ancema tunaninka nake ni tunani na daban ,ya zanyi in biya bashin da ake bina ?"ganin yayi nisa yasa ta yin gudu kaɗan-kaɗan har ta cim masa yana tare mai napep, baby yanzu tafiyar kenan ?Abdull dake shiga napep yace "insha Allah ba lallai gobe ma in dawo ba ,sbda zani Abuja wata ƙila nayi one week ma a can ,gabanta ne ya bada dumm a fili tace Bana ƙaunar muyi nesa da juna ji nake kamar in bika,murmishi Abdull yayi kana yace "ina dawowa sai maganar auranmu kisa ranki a inuwa.

Cikin jin daɗin kalaman nasa ta juya da sauri tayi hanyar gidansu tanajin wani irin farinciki a ranta , tasan tabbas ta auri Abdull to hatta ƙawayenta tayi musu zarra sbda tarin dukiya da mahaifinsa ya mallaka kowa yasan da zamansa.

Ramu na isa gida ta tarar da ƙannenta a zaune su biyu ,da Hajara da mariya , Hajara zatayi shekara uku yayin da mariya take da shekara ɗaya a duniya amma tana tafiya ba sosai ba , tsawa tayi kusa da mamanta tace "Lami ni a gaskiya na daina zuwa gidan tsohuwa ,yau ma sata ta laƙa min "waro ido mamar tata tayi kana tace "dan ubanki ban hanaki zuwa gidanta ba ?"tunda bazata fasa aibanta minke ba"Baba daya fito daga bayi hannunsa riƙe da buta yace "ina cikin gidan kuke zagarmin uwa anya kuna neman zaman lpy kuwa ?, Lami data cika tayi fam dan ita a rayuwarta ta tsani dangin mijinta bare ita kanta uwarsu, cikin gyatsina baki tace "ai tayi abin a faɗa ne da batayi ba baza'a faɗa ba "a fusace baba yayi gurin da Ramu ke zaune sbda suna haɗa ido ta ƙyal-ƙyale da dariya marar sauti ,baba yayi kanta da gudu yana cewa "ƴar kan uba wlh ke kin zamo fitinanniya ya bita da ubangudu , zagaye gidan ta farayi ta jefo sanda kusa da ƙafar baba -baba ya faɗi timm ya fara ihu yana cewa "wayo Allah Lami ɗagani "wata wawuyar dariya Ramu ta daki harda rawa tana zaro harshe , Lami na ganin abun kamar wasa ta ƙyaleshi bata ma juya ba bare ta san halin da yake ciki , juyo muryar Ramu tayi tana cewa "Lami baba na kuka wlh harda hawaye "ido waje Lami ta juya tare da miƙewa ta nufi gurin baba cikin tausayawa kamar ba yanzu suka gama faɗa ba tace "mai gida dan Allah ka tashi "baba dake jin ciwon da kwankwason sa keyi masa babu halin masifa yace "ɗagani -dagani"to Lami tace "kasancewarta mai ƙiba sosai ta fincikosa ya miƙe ,kasa tsayuwa yayi murya irin ta wanda yaji jiki yace "kaini ɗaki "tsaki Lami tayi kana ta sureshi , Ramu dake rakuɓe ta ƙunshe dariya jira take taji baban nata ya suɓuto ta sa dariya , ganin an kaishi ɗaki lafiya ta fice waje tana kuka.

A wata fale falen katifa ta jefashi ya saki ihu tare da cewa "wlh inhar Allah ya tashi kafaɗa ta saina yi miki hukunci dai-dai da laifinki "Lami dake girgiza dama ƙirs take jira tace "sai me ?ni wlh nama gaji da zama da kai tunda baka da amfani sai wajen cin abinci ,baka fita nemowa ,kullum nayi sana'a ribar a gida take tafiya "gumm baba yayi har ta fice bai sake magana ba ,yasan dai gaskiya ta faɗa.

Saudat na shiga gida ta sami Ummanta na tuƙa tuwo , tsaki tayi kana tace "kullum tuwo kullum tuwo wlh dole ciwo ya dinga kama mutane ,ayi abin arziƙi baza'ayi ba sai tuwo "zaro ido Umman tayi tare da cewa "gidanku nace , anyi miki dole kici ?to tun wuri ki rufamin baki "Saudat na tafe tana bubuga ƙafa ta shige ɗakinta dake ɗake ɗauke da tabarma babu katifa sai tulin tsummokara tai tsaki ,ta nemi kujara ƴar tsugunno dake gefe ta zauna tare da rafka tagumi tace "ni Saudatu na shiga uku ,mai zan cewa Habu tela oho ,ya bani bashin kaya gashi nayi masa alƙawari "faskekiyar wayarta ta ciro infinix hot 10 ta nemo number Abdull ring ɗaya ya ɗauka tare da sallama , cikin rage sautin muryata tace "babyna ka isa gida lafiya ? Abdul dake zaune a makeken palon su ya amsa da cewa "eh har na huta ma ga hajiyata ku gaisa "miƙawa mahaifiyar tasa wayar yayi ,hajiya ta ƙarɓa ta kara a kunnenta tare da cewa "ƴata ya gida ya sanyi "lafiya lau Saudat tace "ta kuma gaisheta sukayi sallama , tare da taɓe baki hajiya ta miƙawa Abdull waya ta miƙe tabar gurin , baki sake yake kallon hajiya har ta ɓace wa ganinsa ,sanan ya nunfasa tare da miƙewa ya wuce bedroom ɗinsa , zama yayi kan bed tare da cusa hannunsa cikin yalwataccen sumar kansa yana huci , a fili yace "nasani tabbas akwai gagarumin matsala a gabana ,hajiya bazata amince da auran Saudat ba sbda dalilin da bazan iya amincewa dashi ba , gagararsa zaman yayi ya miƙe tsaye yana zagaye ɗakin hannunsa na haɗe ta baya yana lanƙwasasu suna ƙara ,wata dattijiwa ce ta bankaɗo ƙofa cikin zafin rai tace "Abdull gobe zaka koma egypt wlh gara zamanka a can da tayar mana da habkalin da kakeyi ,wanan wace irin rayuwa ce minyi maka zaɓi tun kana ƙarami amma yanzu wuyanka ya isa yanka shine kake neman bijire mana ko ?"ran Abdull yakai ƙololuwa gurin ɓaci sbda ji yake kamar ya ɗora hannu a kai yana tsala ihu ko ransa zai yi masa daɗi , yana jin daya auri Fati gara ya zauna baiyi aure ba , sbda abubuwan da ya taɓa gani ido da ido har yanzu ya kasa ɓace masa ,wanan shine ruwa biyun tabbas ta zamo (zulwaja haini) ,dattijuwar dake tsaye tana balbala masa masifa , sai da ta gaji sanan tayi shiru tana jiran abin da zai ce , kusam mintuna wajen goma Abdull bai yi magana ba ,can kuma ya juyo ya fuskanci dattijuwar yace "Anti Ummi bance muku bana son Fati ba "nidai ku barni in auri wacce nakeso "au iyee ma ,ni zaka kalla kace wani wai inbarka ka auri.. to ka daɗe baka mutu ba ,aure babu fashi nan da sati biyu kai nan da kwana goma ma wlh auranka da Fati ya ɗauru "cikin matsanancin firgici Abdull ya kalli Anty Ummi dake faman sababi yace "anty kiyi haƙuri ki...,ficewa daga ɗakin tayi ba tare da ta kuma sauraronsa ba tace "sauran shawar wari ya rage gareka Abdullahi.
Tashin hankali iya tashin Hankali Abdull ya shiga har ma yake jin inama mahaifinsa na raye babu wanda ya isa yayi masa haka.

Ganin zaman da yayi ba shine mafita a garesa ba yasa shi miƙewa ya shiga toilet ,ruwan sanyi ya sakarwa kansa kasancewar garin da zafi ,tunda ruwan ya fara sauka a jikinsa ya lumshe ido hoton fuskar Fati yake gani da abinda ta aikata runtse idonsa yayi yana mai cewa "wlh an cuceni "lokaci ɗaya kuma ya kashe shower ɗin ya ɗaura tawul ya fito , zama yayi a kan gadonsa yana lanƙwsa hannayensa , jiyo rurin wayarsa da yayi ne ya sanyashi miƙewa a hankali ya isa kan tebur ɗin da wayar take , Sis Fatima ,sunan da yayi saving number ta kenan a wayarsa ya gani , ɗagawa yayi tare da kara wayar a kunnensa yace "ina jinki "Fati dake zaune a gurin cin abinci ta ajiye cokalin dake hannunta cikin siririyar muryarta mai ɗaukar hankali tace "brother na da fatan ka wuni lafiya ?"cike da miskilanci ya fara magana kamar an shaƙesa yace "Tima kizo gidanmu akwai maganar da zamuyi "cikin jin daɗi ta miƙe tare da ture kujerar data tashi a kai ta wuce gurin biyan kuɗi ta biya tabar gurin , motarta dake pake a gaban gurin cin abincin ta shiga tare da yi mata key tabar gurin , tuƙi take tana tunani iri-iri ,ta wani ɓangaren hankalinta na titi a fili tace "Allah yasa kalmar dana daɗe ina tsumayi zai faɗamin da wlh yau bacci sai Allah "tana isowa bakin tangamemen get ɗin gidan tayi horn mai gadi dake zaune ya leƙo tare ɗaga mata hannu ya buɗe ta shige , kai tsaye gurin ajiye motoci ta nufa tana ajiyewa ta wuce side ɗin su Abdull , Anty Ummi ta samu a palo sai hajiyarsa , har ƙasa ta tsuguna ta gaishesu kana ta koma kan kujera ta zauna , murmishi anty Ummi tayi kana tace "Fati ai mutumin naki yana ciki "cikin jin kunya fati tayi murmishi tare da miƙewa tace "shine ma ya kirani a waya "sai tayi gaba .

Anty Ummi ce ta kalli Hajiya tace "kinga munafukin yaro yana so yana kaiwa kasuwa ko ?"uhm ai yaranan sai Allah nifa dama nasan yana sonta gulmace kawai "Hajiya ta faɗa tana turo ɗaurin ɗankwali gaba .

Fati na shiga ta tarar da Abdul zaune a palonsa hannunsa riƙe da kofi mai ɗauke da lemun karas , yana sha yana juya kofin ..

Uwar gida ga yadda zaki haɗa lemun karas da kanki .

ABUBUWAN HAƊAWA

Karas
Citta
Sugar
Flavour

Da farko zaki wanke karas ɗinki ya wanku sai ki yanka karas ɗinki ƙana na ,ki markaɗashi a blanda sai ki wanke cittarki ki yanka ƙanana ki markaɗata a balanda tare da karas ɗinki , sanan ki tace kisa sugar da flavor sai kisa a frij yayi sanyi sosai , karas yana da amfani musamman ga lafiyar ido ma.

Sallama tayi a hankali kamar ba ita ce ta shigo da kuzarinta ba ,amsawa Abdull yayi tare da ɗago kai ya kalleta ,kallon shigar da tayi yayi riga da wando ne a jikinta na jins sai t-shet mai ruwan ƙwai tanada adon duwatsu a jiki ,a zuciyarsa yace "mtsew wanan rashin ɗa'ar har ina ?sai kuma ya nuno mata kusa dashi yace "ta zauna , zama tayi tare da kwantar da kanta a cinyarsa , cikin sairi ya ɗagata tare da cewa "bana son raini fa "muyi abinda ke gabanmu "kallonsa tayi da fararen idanunta alamar tana jinsa ,Abdull dake kallonta yace "dama abin da nakeson faɗa miki shine kicewa anty Ummi bakya sona "wani rass gabanta ya bada ta miƙe tsaye da sauri tare da cewa "na shiga uku brother dama kiran da kayi min kenan ?"cikin nutsuwa yake kallonta yace "eh sbda bana son ayi mana auran dole ke bakice kina sona ba nima bance ina sonki ba so mu yanke hukunci tun kafin a cutar da zuciyoyin mu "ido waje Fati ke kallon Abdull a zuciyarta tace "wai bana sonsa ?"sai kuma tayi murmishin yaƙe tace "babu damuwa yayana indai dan wanan ne zan faɗa musu insha Allah ta juya ta fice zuciyarta kamar an sheƙa mata ruwan zafi ,har ta kawo palo batasan tazo ba sbda tuƙuƙi da zuciyarta keyi , Anty Ummi dake zaune tana jiran fitowarta ta miƙe da sauri ta dafa kafaɗar Fati tace "ya akayi ne Fatima ?"murmishi ta gayyato ya ziyarci fuskarta kana tace "wlh lafiya anty "mai Abdull ɗin yace "miki ?"anty Ummi ta jefo mata tambaya ,Fati dake tunanin abin da zatace ta wuce kan sofa ta zauna tare da sauke nunfashi tace "wai wai... Hajiya data fito yanzu itama ta iso gurin anty Ummi tace "mai ke faruwa naji tana ta cewa "wai "a tare suka iso gurinta kamar sun haɗa baki sukace wani abun yayi miki ?"a'a Fati tace "lokaci ɗaya ta tsinci kanta da faɗar abinda zuciyarta keso tace "cemin yayi wai ya daɗe yana sona kuma nice matar da zai aura amma kar in faɗa muku "murmishi ne ya ziyarci fuskar Hajiya da anty Ummi tace "amma naji daɗi ashe Abbdul bazai watsan ƙasa a ido ba "ta ɗaga hannunta sama tana godiya ga Allah , tsabar farinciki Hajiya ta kasa magana ,sai jinjina kai da takeyi alamun daɗi ya kamata , miƙewa Fati tayi ta fice a dole wai kunya ce ta kamata , tana zuwa gurin da ta ajiye motarta ta ciza yatsa tare da cewa "nako shiga uku tabbas nida gidansu Abdull sai an kuma ganina ƙila sai ranar da aka kaini faɗa idan na zamo matarsa , kai tsaye ta shige motarta tana jimamin ɓaran ɓaramar da tayi .

Gidan su Saudat.
Saudatu dake zaune tunanin duniya ya isheta har an kira sallahar magrib tana zaune taji an turo ƙofar ɗakinta , Ummi ce hannunta riƙe da kwanon tuwo da miya ta ajiye gaban Saudat tare da cewa "tunda sallah ta gagareki to kici abinci " rai a ɓace ta kalli tuwon dawar dake gabanta tayi tsaki tare da cewa "nifa bazanci ba wlh da inci gara in kwana da yunwa bakina duk yai ta wari "Ummi bata ce komai ba ta fice tare da barin tuwon a ɗakin ta jayo ƙofa , Umma na fita yaro ya shigo tare da gaishe da Umma yace "wai Saudat na nan ?"eh Umma tace "yaron yace "wai tazo inji Habu tela "Saudat dake ɗaki ta zaro ido kamar an tare ɓera a rami tai sauri ta haye katifarta tana shirin janyo bargo tayi ɓarin miyar kuka , bata tsaya kula miyar ba ta luluɓe jikinta ta fara rawar sanyi , Umma dake waje tace "kai ka shiga tana ciki "to yaron yace "ya kama hanyar zuwa ɗakin Saudat , yana isa ya buɗe labule ya ganta kwance da alamun bata ada lafiya ,bai tsaya kulata ba ya fice , Umma ko sai kallonsa take
[29/01, 10:10 PM] Mom Islam Ce: 🤦‍♂️🤦‍♂️🤦‍♂️🤦‍♂️🤦‍♂️🤦‍♂️🤦‍♂️🤦‍♂️

    *NIDA YARINYA*
🪂🪂🪂🪂🪂🪂🪂🪂

_Zainab Habib/Mom islam_

Page 3-4

Tasan baya wuce cin bashin taje tayi ,Saudat na jin yaron ya fice ta yunƙura ta miƙe kana tace "Allah ya taimakeni wlh da an ritsani " miƙewa tayi ta fito tsakar gida tare da ɗaukar buta ta shiga bayi ,tare da alwalah ta fito tana shirin shiga ɗakinta babanta ya ƙwala mata kira yana tsaye a bakin ƙofar dakin mamanta , amsawa tayi kana ta nufi inda yake , kanta a sunkuye tace "baba gani "mahaifin nata dake tsaye hannunsa riƙe da redio ya miƙa mata yace "ki ajiyemin a ɗaki "to tace "dan ta ɗauka wani laifin tayi , tana shiga ta sami Umma na sallah ta ajiye ta fito.

Bayan rabuwar Ramu da Saudat bata zarce ko ina ba sai gidansu , tana shiga ta sami Lami tana tuyar waina , dama sana'arta kenan kullum da yamma tana yin mai ƙuli , da rawar jiki Ramu ta ƙarasa tare da kallon  Hajara dake riƙe da ƴar ƙaramar roba ,da alamu talla zata ,hararta Ramu tayi kana tace "Lami ance akai da dubu guda inji wani mai kuɗi "cikin farinciki Lami ta hau sauri har tana ƙonewa ta fara zubawa a wani babban baho   nata sabo ,tanayi tana ƙirgawa har ya kai na dubu ɗaya tasa gyaran guda biyar tace "Ramu ta ɗauka ...

INDA AKE YIN WAINAR FARAR SHINKAFA.

•Farar shinkafa
•Yis
•Sikari
•Gishiri
•Albasa

Da farko zaki wanke shinkafarki ki jikata a markaɗa ,amma ba lallai sai ta jiƙu ba ,sai ki zuba yis da gishiri dai dai misali ,sai a kaɗashi sosai ki sanyashi a rana ya tashi ki yanka albasa ,idan kinaso tayi miki ja tayi kyau zaki iya sanya suga ,sai ki nemi tandar suyan waina
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment