Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

 *⋆☆A ZATO NA...!☆⋆*


*⋆©Jeedderh Lawals⋆*




*☆⋆01⋆☆*





Assalamu Alaikum wa Rahmatullah. Muna kara godiya da taruwarku a wannan zaure mai albarka, ina fata Allah Yasa mu gama lafiya kamar yadda zamu fara lafiya.

Littafin 'A Zato Na' mallakin wadda ta rubuta ne, ba'a yarda wani/wata su canza kowace irin suffa ta wannan littafi ba.

Muna fata zaku rike mana alkawari, ku kuma rike mana amana. Allah Yasa mu dace.
_Da sunan Allah Mai Rahma Mai jin Kai'_





'Kirr! Kirrr!!'...

Karan daya ziyarci kunnena kenan lokacin da na danna lambar wayar kawata Janan. Bata dauka nan take ba, sai da yayi kara kamar sau biyar.
Kafin ta dauka hakurina ya gama karewa, saboda haka tana dagawa, ban bari ko sallama tayi ba na tare ta da; "wai dallah can malama me kika tsaya yi ne kin tsaida mutane?".

Tace "jeez girl, bi a hankali mana. Ina jiran Anty Raheemah ne ta dawo kafin in fita".

Na ja dan siririn tsaki, "kawai ki fito ki bar mata gidan a haka mana. Ba maigadi yana nan ba?". Janan tayi ajiyar zuciya, "kin fa san abinda ya faru last time da nayi haka. Tace an shiga an mata satar kudi da jewelries, kuma dole sai da Yaya Bilal ya biyata sannan aka zauna lafiya, bana son abu makamancin haka ya sake faruwa". Nace "sai kiyi ta zama ai ta mayar da ke maigadinta. Ni dai wallahi idan baki zo nan da mintuna goma ba ko? Sai dai mu hadu da ke acan kawai!". Ban jira ta kara cewa komi ba na kashe wayar na ajiye ta a gefena.

Browsing naci gaba da yi da system dina, sai da nayi kamar minti goma sha biyar kafin na kashe na ajiyeta a mazauninta. Janan na sake dannawa kira, tana dauka tace "gani nan don Allah, sarkin gajen hakuri kawai!". Na tabe baki ba tare da na damu da abinda tace ba, nace "better. Idan kin iso ki kira ni kawai mu hadu a main entrance" tace "toh".

Gadona na dan gyara kafin ta iso. Zuwa lokacin da Janan ta kirani, na gama kimtsawa. Na dauki gyale na nada shi a kaina yadda ya zagaye rabin kirjina da bayana, na dauki wayar hannu, purse da flat din takalmi ruwan goro kalar veil dina da zanen flower da yake jikin doguwar rigar gown ta atamfa da na sa, na zura shi a kafata. Aylah, roommate dina na yiwa sallama na fita.

A bakin hostel din Queen Amina dake cikin campus din ABU Zaria, na tsaya ina karewa wajen kallo cikin neman Janan. Ina kokarin kiranta a waya na hango ta acan inda ake parking motoci a gefen hostel din tana dago min hannu, murmushi na saki cike da murna da dokin ganinta na taka a nutse na tsallaka zuwa inda take. A tsakiyar wajen ta tareni, muka rungume juna cike da doki. Duk duniya, ita kadai ce naki jinta kamar wata yar uwata ta jini, kamar yadda nasan itama haka take a bangarenta.

Na kalli iNext din da naga ta fito daga ciki ina daga mata gira, "Ya Almu ya sake sabuwar mota ne hala?". Ta girgiza kai tana murmushi, "ina Almu na yayi arzikin sayen irin wannan abun? Yaya Bilal ne". Na dan zare ido cikin mamaki, "Holy Wow!! Yaushe rabon da in ga Yaya Bilal? Har na manta wallahi. Yau dai Allah ya nufa zamu hadu kenan!".
Tayi dariya da tasa dimples dinta suka lotsa, abinda yake burgeni da haliitar ta kenan. Tace "sosai ma. Allah ne yasa ban samu abin hawa da wuri ba, shine yace bari ya kaini tunda shima wajen FCE din yayi. Taho muje, muna kara makara". Na bi bayanta zuwa wajen motar.

Janan ta bude gidan gaba, ni kuma na bude baya muka shiga a lokaci guda, bakina dauke da sallama. Sansanyan kamshin freshener na cytrus da mix din strawberry ya doki hancina hade da sansanyan sanyin AC daya dumame motar. Muna tsakiyar watan May ne, saboda haka ba karamin zafi muke sha ba a garin na Zaria.

A nutse na gaishe da Yaya Bilal, ya juyo a kaikaice ya amsa tare da juyawa ya tashi motar muka bar wajen. Babu abinda na iya kararwa game dashi sai cewa faded jeans ne a jikinshi da T-shirt mai zanen zebra a jiki, sai sunglass da ya saka ya sakaya idanunshi.

A hankali yake tukin, tattausar kira'ar Sheikh Malam Minshawee tana tashi cikin suratul-Kahf, na jingina kaina da kujerar motar na lumshe idanuna, a can kasan zuciyata kuma ina bin kira'ar bi da bi. Yayin da a gefe guda, shi da Janan suke hira jifa-jifa. Har muka isa makarantar Kongo, inda zamu je, a bakin gate ya nemi waje yayi parking. Sai a baki-baki ma yayi parking din, saboda yadda wajen ya cika da mutane da ababen hawa. Muka mishi godiya muka fita, ya ja motar ya tafi, mu kuma muka tunkari gate din makarantar.

Ranar babban Shehin malami, ' Dr. Bilal Philips' yake zuwa yin wa'azi. Saboda haka, you can only imagine yadda wajen zai cika da mutane wai don ma na mata ne zallah. Duk da mun zo kusan mintuna arba'in kafin a fara wa'azin, da kyar muka samu wajen zama muka zauna.

Akan Matan da zasu shiga aljanna yayi wa'azin ranar. Kafin ya gama, jikin kowace diya mace dake wajen yayi sanyi saboda yadda ya dinga zano abubuwa da mu mata muke yi, muna tunanin ba wani abu bane, either ga junanmu ko ga mazaje da iyayenmu, alhalin abubuwan nan za su iya jagorantarmu zuwa wuta. Karfe sha biyu na rana aka gama wa'azin, saboda karancin abubuwan hawa da aka yi ranar, bamu samu mun koma cikin makaranta ba sai kusan karfe daya da rabi.

A dakina muka sauka, Janan tayi sallar azuhur, kafin ta gama ni da bana yin sallah na gama dafa mana jollop spaghetti. Bayan mun gama cin abincin, kan gadon muka hau, na kunna mana film din Pick the Stars, wani Korean Film, muna kallo. Bamu jima da fara kallon ba, barci ya daukeni.


"Na'ilah!".
"Uhmn?" na amsa cikin barci.

A hankali naji an kai tattausan hannu gefen fuskana an shafa cike da wani irin tenderness da yasa naji bugun zuciyata ya canza sosai. "I Love You, baby! So much!!".
Aka fadi a daidai saitin kunnena, cikin wata irin tattausar murya. A hankali na bude idanuna dake cike da barci, mutumin da ke zaune a gefen gadon da nake kwance, appears very blurry, bana iya ganinshi cikin rashin hasken dakin.

"Na'ilah?" naji ya sake kirana cikin tattausar muryarshi, na saki murmushi a tausashe ina amsawa, "uhmmn??".

"Na'ilah!!". Wannan karon naji an kirani da karfi. A gigice na tashi zaune, kaina ya bugu da bango. Da sauri na dafe wajen na maida kaina kan pillow ina hararar Janan dake zaune a gefena, tana kallona cike da alamun tambaya.

Harara na jefa mata tun karfina, cikin tsiwa nace "dallah can Malama meye haka, zaki katse min barcina mai dadi?".
Ta daga kafada, "maganganu kike yi cikin barci. Abin naki ya dawo ne?".

Na kara komawa kan katifar na kwanta, "Wallahi kuwa Jan. Yaushe rabon ma da inyi irin mafarkannan? Har na manta. Sai yau".
Janan tace "to sai ki kiyaye da addu'o'i dai. Is'haq yazo yana jirana a waje, bari in tafi".
Na duba naga yamma har tayi.

Na mike ina lalubar mayafi na, "muje in miki rakiya to!".

Ta tashi na rufa mata baya, dakin na rufe kasancewar abokiyar zama na bata dawo ba, muka sauka kasa ni da ita.
Har parking lot na rakata inda Is'haq yake jiranta. Ta bude gidan baya ta shiga, na maida mata kofar na rufe ina daga mata hannu, a haka suka tafi. Sai da na tsaya anan kofar hostel din na sayi yoghurt babbar roba mai sanyi sannan na koma daki.

Bayan na yi yan gyare-gyare da kimtse-kimtse na, arm chair na dauka na ajiye a gefen gadona na zauna, na dora laptop dina akan gadon na bude tare da cigaba da kallon da muka fara ni da Janan.

Sai bayan magriba Aylah, roommate dina ta dawo. Har zuwa lokacin ina kan system dina, ta min sallama na amsa, a gajiye ta zauna a gefen gadonta. Sai da ta huta, sannan tayi sallah. Taci sauran spaghetti din da muka bari ni da Janan.
Ni kam karfe bakwai tana yi, na kashe laptop din na mike. Kasa na sauka inda common room yake, na kalli serieses din da nake kallo a Zee World; Twist of Fate da King of two Hearts. Karfe tara na koma daki, ina zuwa shirin kwanciya barci nayi cikin riga da wando, na bi lafiyar katifa na kwanta.

Hira muka fara da Aylah, tana bani labarin abinda ya faru a wajen bikin da taje ranar. Wai mutumin mace ta biyu ce zai aura, wadda ta kasance kawarsu ce. Shine a wajen lunch party, matarshi ta farko taje da tawagarta, aka yi rashin mutunci dai yadda ya kamata.

"Dama duka yaushe ne Yayan su Afrah kawata zai sake aure, amaryar ta hadu da uwargidan a shagon saloon. Wallahi tsiyar da aka yi a wajen sai ta baki mamaki. Kaca-kaca suka yi wa juna. Bayan anyi auren kuma da sati biyu, ya dankarawa uwargidan nashi saki. Naji ance kusan watannninta biyu a gida, sai kwanannan ta koma".

Nayi ajiyar zuciya tare da girgiza kai. Abinda yawancin mata suke jin tsoro game da kishiya kenan, taje ta fitar dasu daga gidansu. Ko ta hana su zaman lafiya da miji. Ko ta zauna, haka zaka kare rayuwarka cikin tashin hankali, fargaba da takaici.

Aylah ta cigaba da cewa, "ni wallahi gani nake babu wani aibu game da wata kishiya. Ba abokiyar zama bace? Menene a ciki? Idan dai ka kwantar da hankalinka, tsaf zaku yi zaman lafiya da ita wallahi!'.

Na kada idanu, "baki san komi ba game da kishiya Aylah. Kiyi shiru kawai. Ina tunanin duk danginki babu wadda take zaune da kishiya ko?".
Ta daga kafada, "Anty Hanifa ce kawai, kuma suna zaune da ita lafiya lau".

A hankali murmushi ya subuce min, "to wannan sa'a ce tayi ba karama ba, ina gaya miki. Wallahi da tayi rashin sa'a, gabadaya sai ta girgiza family dinku saboda sanabe".
Aylah ta girgiza kai, "naa. Bana tunanin haka. Kada dai kice min, baki son kishiya Na'ilah?!".

Murmushi kawai nayi, na gyara kwanciyata tare da mata sai da safe.


Dare ya tsala matuka, yayin da barci ya gagari idanuwana. Zuciyata tayi wani irin nauyi, ji nake kamar an dauki wani gungumemen dutse an dora min a kai, numfashi ma sai da naji ya fara gagarata. A hankali na janyo wayata da headphone na hada, na kamo kira'ar Sheikh Malam Ahmad Suleiman na kunna. Idanuwa na lumshe a hankali, ina bin kira'ar a cikin raina.

To say that na tsani kishiya, is an understatement.

I despise her! Na tsaneta with all my being.

Tunanin zama da kishiya kadai a cikin raina, yana sa jinin jikina tafasa, zuciyata zafi kamar ana diga ruwan dafaffiyar dalma.

Allah Ya gani, bana son kishiya. Ina kuma da yakini a cikin raina, ko zan mutu tuzuruwa, sai dai hakan ta faru, amma ba zan taba zama da kishiya ba!!.

And why not, you might ask?!

A shekaru na bakwa a cikin rayuwata, na dandana zafin kaidi irin na kishiyar uwa, a wani unfortunate dare, da na kira 'bakin dare'.

Ranar mahaifina yake sake aure, kyakkyawar bafulatanar mata, fara doguwa, tsayi wanda ta tafi gabadayanta ta mike, babu lankwasa ko duk'awa, har yau ina mamakin dalilin da yasa Baba ya aureta.

Idan kyawune, mahaifiyata tana daya daga cikin kyawawan cikin danginsu, kasancewarta ruwa biyu, shuwa-arab da barbanci, yasa ta kasance mace daya tamkar dubu. Kyawu, ladabi, biyayya, iya girki, kwalliya, kada ma ayi maganar tsafta, don gani nake duk duniya, babu na biyun mahaifiyata a tsafta.

Saboda haka, dalilin auren Babana da bafulatana Ramata, kazamiya mara kira, still remains a mystery, yet to be solved to me.

Bana taba manta ranar da aka kawota gidanmu, ina ta murna an kawo min wadda zan kira Anty na. Masu kai amarya sun shigo da habaici, suka tafi da bakaken maganganu a bakinsu, duk mahaifiyata da abokanta yan dannar cinya suna jinsu, amma suka kauda kai kamar basu ji ba. Wannan abu ya bakanta musu rai.
Wata daga cikin kawayen Mama da ta kasa kau da kai, ta tanka musu. Ba bata lokaci suka hau zage-zage, kamar dama jira suke yi, ko kuma da guzirin zagin suka shigo. Da kyar aka ba Iya Lami hakuri, su kuma suka tafi.

Bayan tafiyarsu babu jimawa, suma yan dannar cinyar suka mana sallama suka tafi, suna ta kara ba Mama na hakuri. Ni kam ina zaune muk'u a lokacin, ina jiran Mahaifina ya dawo. Bai dawo ba har barci ya daukeni.

Can zuwa cikin dare, hayaniya ta tasheni. Ba wai kuma normal hayaniya ba, kukan mahaifiyata ne ya tasheni wanda nake jiyowa yana tashi daga can dakin Babanmu.
Kasancewar gidanmu dakuna hudu ne, biyu suna kallon biyu. Dakin Mama shi yake kallon na amarya da Baba.

Daga tagar cikin dakin Mama na leka, ina hangen ta tsugune a gaban Baba. Matar da aka kai mishi a matsayin amaryarshi, a zaune a gefenshi kamar zata hau cinyarshi, tana ta wani firirita. Ban jiyo abinda suke cewa ba, daga karshe dai na ga Mama ta tashi ta fado daki da sauri.

Babu bata lokaci ta hau lalubar mayafi, ta yafa nata, nima ta miko min nawa. Ina tambayarta 'Ina zamu je Mama?', amma saboda tsabar kuka da take yi, ta kasa amsa min. Hannuna kawai ta kama ta ja muka fita daga dakin.

A bakin kofa, mahaifina ne a tsaye, kamar wanda yake jiran ta fito. Muna fita, ya kamo hannuna ya rike. Har yau ina tuna maganganun daya fada mata clearly,
"Kada ki kuskura kiyi tunanin zaki tafar min da diyata, yadda itama zaki je ki koya mata rashin kunya da rashin mutunci ko? To ba dani ba, yadda kika zo gidannan zikal, haka zaki tafi!".

Wani kukan ya sake barkewa daga bakin Mama, cikin rishin kuka, magana na fita da kyar, tace "haba Malam, ta yaya zaka ce in bar maka yarinya yar shekara bakwai a hannun wannan azzalumar mata ta ka?".
Ina tunanin hakan shi ya kara tunzira Baba, ya bude baki ya hau zazzagawa Mama masifa kamar wanda yake amayo kalmomin. Ban taba ganin tashin hankali irin na ranar ba.

Tunda aka haifeni, ban taba ganin sa'insa tsakanin iyayena ba. Tun tasowata, iyakarsu kawai: 'Yana yi kaza, to. Yana kada kiyi kaza, to Malam'. Ganin wannan abu a ranar nan, was a first. And definitely not a good one.

Ina ji, ina gani, Mama tasa kafa ta bar gidan, Baba ya bita a baya ya rufo gidan. Bai ma kula da cewa ina kofar dakin Mahaifiyata daya gama ci wa mutunci a gabana ba, ya wuce dakinshi. Amaryarshi na tsaye a kofar daki tana jiranshi, yana shiga, aka maida kofar dakin aka rufe, ji kake garammmmm!!.

A hankali naja kafafuna da suke rawa, na koma cikin daki. Kan gadon Mamata na hau, na kwanta.
Karo na farko a rayuwata dana kwanta ba tare da na ji dumin mahaifiyata a jikina ba. Kullum sai na yi barci take tafiya dakin Baba. Sai dai kawai wani lokaci idan na tashi cikin dare, in ga bata nan.

Daren ranar barci sai barawo.

Washegari tun da safe na tashi, al'adar gidanmu ce. Na share tsakar gida tsaf, na kunna wuta a murhu na dafa ruwan zafi, kasancewar lokacin sanyi ya fara shiga. Na je nayi wanka, na koma daki na shirya.

Shiru ina zaune, ina jiran a fito a dora abincin kari, ban ga motsin kowa ba. Ganin karfe takwas tana neman shigewa, yasa na dauki jakar Islamiya ta na fita. Sai da na saka makulii na rufe dakin Mama, sannan na yi sallama a kofar dakin Babana.

Sai da aka dauki lokaci kafin aka amsa min, a hankali na tura kofar dakin na shiga. Baba yana zaune a gefen katifarshi, amaryarshi na kasa kusa dashi, tsabar kusanci har cinyarshi na gogar tata, nayi saurin yin kasa da idanuwana.
Karin safe ne a gabansu, shayi, libgegen biridi, soyayyen kwai, da indomie.

A nutse na gaidashi, ya amsa ciki-ciki. Ganin na ki gaida matarshi, yasa ya umarceni da in gaidata. Cikin tafasar zuciya na gaidata, ta amsa tana watso min wasu dogayen hakora marasa tsari, wai ita ala dole murmushi take yi. Bayan a hakikanin gaskiya, ko kare aka yiwa murmushinnan yasan cewa dole tasa aka kakaro shi.

Bayan nan zamana nayi ina kallonsu suna karyawarsu a nutse, sai daya gaji da ganina sannan ya tambayeni lafiya? Na bude baki ni kuwa nace mishi ban karya ba.
Ya yanko burodin gami da tsiyaya shayin daya sha hadi, yaje yanko kwai amarya tasa hannu ta kame, ta wani langabar da kai tana mishi magana kasa-kasa, ban san me tace mishi ba, na dai ga ya zare hannunshi ya miko min biredi da shayin, na sa hannu biyu na amsa.

Waje na koma, na zauna na shanye. Na dauraye kofin. Daya daga cikin al'adar Mama kenan da na dauka, sam bata barin kwano mai datti. Hatta da cokali idan tayi amfani dashi, a take a wurin take wankeshi.

Ban kara waiwayar Baba da Amaryarshi ba, na wuce makaranta abina.

Karfe sha daya na safe muke tashi daga Islamiya a lokacin, daga can na kan wuce gidan Kakannina, iyayen Mama. Malam Bako Kakana, babban malamin allo ne da yayi suna a ciki da wajen garin Gashua. Yana da tarin dalibai yara da manya da suka kasance a ciki da wajen garin Yobe baki daya. Kullum na tashi daga makaranta, wajenshi nake wucewa inje ya taya ni biya karatuna, ya kuma dora min nashi wanda muke yi, watarana acan nake tsayawa har lokacin komawarmu Islamiya da yamma yayi, bana komawa gida sai dai in koma makaranta daga can.

Ranar ma can na wuce. Bayan munyi karatun, anan nake jin cewa wai ya je ya samu Babana akan maganarshi da Mama. Wai Baban yayi fir yace wai shi bai kori Mama daga gidan ba, ita taga damar tafiya, anan nasan cewa lallai sake aure ya kan sa mutum ya canza halaye.
Ban taba jin Babana ya fadi abinda ba shi kenan ba, sai a lokacin.

A daren ranar da dare Mama ta koma gida. Tun daga wannan ranar, ko in ce tun daga ranar da kafar Ramata ta taka doron kasar gidanmu, bamu sake samun farinciki da kwanciyar hankalin da muka samu kafin tazo ba, har yau dake motsi...



*******


Karan alarm din dana saka ne ya tashe ni daga barcin daya daukeni. Jiya barci ya daukeni ban cire headphone din dana saka a kunne na ba, ban san ma yadda aka yi na cire shi ba, na dai hango shi a kasan gadona. Na kai hannu kasan filona na zaro wayar, dusu-dusu nake ganin komi saboda barcin daya cika min ido. Naga karfe hudu da rabi.
Na kan manta in cire alarm din da yake tashi na sallar asuba duk lokacin da nake fashin sallah.

Kashe alarm din nayi, na koma na sake kwanciya. Sai karfe shida alarm dina na biyu ya sake bugawa. Nan na samu na mike da kyar ina layi. Cikin awa daya, nayi wanka na hada abin kari. Yeah, idan zaku kira indomie da bakin shayi breakfast, to abin kari.
Lokacin Aylah itama ta tashi.

Babu wata kwalliya da na tsaya bata fuskata da ita, daga mai, hoda, da janbaki, bana kara komi. Sai a lokutan da basu cika faruwa bane nake saka jagira da kwalli.

Na janyo stool gefen gadona na zauna na karya, ina gamawa na janyo uniform dina farare tas na saka.
Dogon wando ne fari, da riga wadda ta kai har gwiwata, na daura farin dankwali a kaina bayan na cikuikuye dogon sassalkan bakin gashin kaina na daure da ribbon, sai na dauko karamar farar hijabi data tsaya a saman kirjina na saka.

Na dauki agogon hannu ruwan kasa mai haske na daura, a jikinta naga cewa bakwai da rabi ta kusa yi. Cikin sauri na dauki gyale mai yalwar fadi na yafa a jikina. Na dauki purse, wayar hannu da littafin da nake shigar da duk wasu bayanai na ilimin dana dauka a ranar da naje asibiti, cikin sauri na zura bakin toms a kafata, na yiwa abokiyar zamana sallama na fita har ina hadawa da dan gudu.

Ina zuwa, bus din da take daukanmu zuwa Kongo tana zuwa, don haka na bi jerin mutanen dake layi suna shiga ciki, bayan na biya kudin mota.

Karfe takwas da yan mintuna na sauka a inda na saba sauka. Daga nan acaba na hau, zuwa cikin unguwar Gyallesu, wani karamin public health centre nake zuwa aikin TP na. Karfe takwas muke farawa mu gama karfe daya zuwa biyu. Kowa dai yasan yadda dalibai suke da son yin latti, musamman a irin wannan lokacin da kasan cewa babu wanda zai kulle maka aji, ko ya hana ka attendance.

Duk da lattin da nayi, sai da na riga Janan isa. Ita wannan dama ba'a maganarta idan ana zancen latti, sam bata dana biyu.

Karfe sha daya da rabi muka tashi. Muka fita daga wajen ni da ita a gajiye, kuma cikin sanyin jiki. Babu ranar banza da ba zaka je
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment