Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

Matar Hariji Complete N ovel

Miqewa tayi da sauri ta daga kanta tana kallon me shigowar ya tafa hannu tare da tuntsirewa da dariya yace “kin dauka wannan raggon mijin nakine ko? Nifa ina mamakin yanda mace kamarki zaki tsaya kina auren wannan sullutun mutumin da baya iya biya miki buqatarki itafa mace tafi kowa yanci kuma tanada zabin daya dace da ita namiji dai har namiji a riga Amma a gado babu fuss sai jinkai da izza a waje, koda yake hakanma ni yayimin ya auromin mata babu ko sisina nayi mata ban ruwa kuma ta cikamin aljihuna da kudi hhhhhhhh!"
Suka kwashe da dariya ita kuma ta tsuke fuska tace “amma kasan nace maka kada kazo gdannan yau yayanka zai dawo kuma kasan cewa banason ya fahimci akwai alaqa tsakaninmu mu zauna a matsayin abokan gaba haka nakeso shirin ya kasance.



Dara² idanunsa ya sauke akan me tallan furar da ya tsayar ta dago da hardaddiyar hausarta tace “Kado ka hiya niman magana wallah in zaka shiya jaka hudu ka shiya in bakka shiya kuma ka bareshi dama kai ka cika son araha toni komi nawa mi tsadane kajima in hwadi maka"

Yanda take mgnr ne yayi bala'in bawa pillot Lameer dariya yayi murmushi yace “komanki me tsadane nikuwa idan babu damuwa mu buga wani wasa mana ki fadamin komai kikeso zanyi miki zan aureki kawai dan ki rinqa bani dariya ko sau daya kika bari nazo gurinki baki bani dariya ba zan sanya karnukan gdana su cijeki idanfa kin yarda"

Wani murguda baki Jiddoh tayi tace “hohoho aura kado mi akai akayika da har zan kasa baka dariya yo ko innarka da baffanka ai nabawa dariya kai bura ma kaji wani abu kwanaki da naje burni har wani me qaton ciki nabawa dariya bare kai dan tatsitsi dakai amma fah tsaya kaji ni bani auren kado kado bashi riqon aure saki a jininku shike yawwa kuma jauro Madi ma ya fika kyau gashi dan gayu har agogo fah yake sawa🤣🤣🤣

Sake gyara zaman hularsa yayi ya zuba mata maganadisun idanunsa yana qare mata kallo sama da qasa yace “nononki baiyi tsami ba ko?" Turo baki gaba tayi ta qara tura cokalelen dankwalinta gaba tace “yo nonon shanuwa idan yayi tsami ai saidai akai juji" dariya yayi da ganin bata fahimci me yake cewa ba yace “amma akwai ranar da nonon naki zaiyi tsami fah" wani tsalle tayi tace “ariyyy hege Kaɗo da muguwar alkaba'i kake idan nonona yayi tsami ai goggo kasheni takayi kai barima kaji ranar nan da mukaje dandali ana ajon auren me yar butta da tsalha da nashiga ina rawa kowa saida ya liqamin takarda"

Ɗan ƙaramin bakinta ya zubawa ido yana kallonta yarinyar kyakkyawa sai bambadanci daya dami rayuwarta miqewa yayi tare dayin miqa yace "kisamu leda ki juyemin a ciki zan baki jaka uku da rabi" miƙewa tayi ta zari qwaryarta zata tafi ya riqo hnnunta da sauri yace "tsaya mana Hauwa" sakin ƙwayar tayi jikinta ya dauki rawa ta zube a gurin ta fasa uban ihu ya saki bottle ɗin hannunsa yayo kanta yayi saurin rufe mata baki yace "ke kinada hsnkali kuwa JIDDAH uwar me nayi miki da zaki zunduma wannan uban ihun salon kisa yan uwanki su bugeni"

sake rintse idonta tayi ta zunduma ihu tana fadin "shikenan na mutu na lalace jiyannan goggo ta gama hwaɗi mami cewa idan kaɗo ya tabaka mutuwa kakeyi yanzu nima shikenan mutuwata tazo zan tafi inda Allah wayyoh ni goggo wayyoh ni baffa wayyoh ni Madi dan burni kaɗo ya cutamin shikenan walakiri zaya kasheni..."



Sauke Littafin : Dr. Bobby Complete Novel Document



Tsayawa yayi kawai ya zuba mata ido haushi baƙin ciki da takaici kamar su kasheshi baisan sanda ya fincikota ya hadata da jikinsa yace "badai tabaki nayi kike haukannan ba to na rungumeki na tsotsi bakinki ma yarinya sai ki jira mutuwarki kowanne lkc daga yanzu"



Bai damu da yanda ta bata jikinta da nono ba ya sake mannata da jikin motar ya matseta yanda ko hangenta baayi ya manna mta kiss a goshinta da lebenta ya sauke numfashi ya saketa ta kuwa zube a gurin shikuma ya zaro dubu biyu ya ɗora mata a cinyarta ya shige motarsa yaja yabar gurin itakam jiddah sake neman guri tayi ta kwanta bayan ta soke kudinta tana jiran mutuwarta don tayi imanin a yau kaɗó ya cusheta babu abinda zai hanata mutuwa.

Numfashinta ma ɗaukewa takeyi wai ta mutu idan ta bude idonta saita sunsuna rigar jikinta sai taji ƙamshin jikin kaɗo a jikin rigarta sai ta sake mutuwa taji ko zata dainajin ƙamshin turaren kaɗonta😄😃

Tananan kwance har masu kiwon shanun rugarsu suka fara dawowa idan taji tafiyar mutane sai ta qara kwanciya tayi luf ita a dole ta mutu idan suka wucce sai ta bude idonta tayi ajiyar zuciya tace “hege walakiri ya wucce baiganni ba"🤣

Kai harfa dare ya fara shiga Jiddoh ana kwance jikin ta qaura yayi la'asar qarshe dai ta tashi zaune ta takure a jikin wata bishiya tanata dan kukanta.

Baffanta ne yazo wuccewa yaci karo da qwarya yayi saurin ja da baya tare da ciro touch light dinsa ya fara haske haske can ya hangota a takure ya matsa da sanda gabanta yana ware Mata kallo Saida ya tabbatar itace sannan ya matsa kusa da ita ya hasketa tayi saurin dagowa tare da qanqame jikinta tana karkarwa tace “na tuba azara'ilu mazarin rai alqur'an bansan ya taba hannuna ba kuma ma har rungumeni yayi sumbaceni nidai yau mutuwa kala uku zanyi wayyohh Baffa zan tafi nabar ko harda Madi dan burni aradun Allah kado ka cuceni..."

Naushin da taji taji an sakar Mata a bakinta shine ya dawo da ita hayyacinta ta bude idonta ta saukeshi akan baffanta aisai ta zabura ta miqe da sabuwar rawar jiki tace “kaima Baffa ka mutu ne ashe zanci gaba da ganinka a lahira amma baffa ance a lahira baa zalumci meye yasa ka bugemin baki" fincikarta yayi yace “dama Yadammu ta hwadi mani cewa akwai wani kado da yake zuwa yake siye nononki kullum har yana qara miki kudi yanzu har takai ya hwara rungumarki yana sumbarki to alqur'an baki jamin abin hwadi a duniya ba a rinqa nunani da lebe muje wuro nijiyya ubanda yace ki rinqa hutta kina neman maza mazanma asararru irin kadawa su shusheki su tai su barki"

Figarta yakeyi da dukkan qarfinsu suna shiga ya watsata tsakar gdan fadi yake “Laure Ladi ku fito kuji abunda almurar diyar nan take aikatawa nan fa duk gida aka fito akayi cirko² ita kuma ta qara bajewa a dole itafa mutuwa take jira.

Gyaran murya Baffa wuro yayi yace “wato Laure kene kika lalata yarki da kanki yanzu gatanan ta hwadi miki abinda suke aikatawa da kado" salati aka hau yi ana tafa hannuwa fadi suke sun banu sun lalace wani uwar maqura da goggo tayi Mata ne yasata sake shiga hayyacinta tace “qur'anin ubangiji bani nace yayimin shine yayimin kuma nima har mutuwa nayi walakiri yaqi zuwa ya tafi dani da tuni na huta"

Buge bakinta goggo tayi tace zakici uwariyonki yar qaniya" Baffa ne ya daga murya yace “Tani kaje kace da Jauro mudi anjima inason ganeshi aradun Allah aure zanyi miki tunda ke bakyajin magana yau ki tsokano masunta gone ki tsokano manoma yanzu kin fara biyewa shiriritar kado to gara kowa ma da kado donni ko gaisuwa banso ta hadani da kado shashashan kawai"

___________Qarfe tara na dare ya shiga cikin garin Kano saboda tsakanin Kano da qauyen Alqalawa da nisa sosai don't qallah yakai kilometer 94.

Gdan iyayensa dake cikin unguwar Tarauni ya fara zuwa yayi parking ya fito ya qwanqwasa bayan yan mintina yaji ana zare saqatar gdan suka gaisa da maigadin yace “Alh kuwa yananan?" Shafa kansa yayi yace “Sai Hajiya dama tace idan kazo ince tanason ganinka"

Saida gabansa ya fadi don yasan Kiran mahaifiyar tasu ba alkhairi bane, hakanan yasa aka budensa get din ya shiga da motarsa yayi parking ya fita ya dauki ledojin da yasa aka yanko masa zabbi manya guda ashirin ya raba biyu zaikai gidansa daya daya kuma ya taho dashi gdan iyayen nasa ya shiga.



Da sallama aka amsa masa ya miqawa me aikin da take yankan apple ledojin guda biyu days zabbi daya qwansu ta tafi shikuma ya zauna tare da rusunawa yace “hajiya barka da hutawa"..........



Karanta Littafin : Macijine Shi Complete Hausa Novel



Wani mugun kallo ta watsa masa tare da yatsina fuska ta qara cokalo dankwalinta gaba tacr “wato kai Lameer bakajin mgn ko ban isa dakai ba jiya jiyannan mukayi muku sulhu da wannan yarinyar arziqin Mubaraka amma yau ma dake kai dan tsiyane Saida ka qara towai meye matsalarka ne kullum ku kenan a sulhu kamar qananun yara?"



Tattare girar sama data qasa yayi yace “yanzu dai qarata ta kawo miki kenan towai ita yaushe zata fahimceni ne yanzu ace matarka ta sunna ta kasa gane matsalarka to waye zai gane kuwa" daquwa ta watsa masa ta gyara zaman mazaunanta tace “qaniyarka dan kusun uwa taya zata gane baka yi Mata ban ruwa yanda ya dace har cemin tayi fah sai kayi wata baka nemeta ba idan kuma ka nemeta din saidai kabarta da ciwon mara dakayi kuruf kuruf na minti biyar ka gama oni Kandala qanwar maza anya wannan da ba mace zaayi ba kuwa aka manta akayima abin maza kai komai naka a sanyaye"



Wata uwar kunyace ta kama Lameer kamar qasa ta tsage ya shige shikam ya shiga uku da barbada a dangi tun yana boyewa iyayensa matsalarsa yau gashi Mubaraka ta tona masa asiri ta yaye masa zani a kasuwa shiwai wacce irin mace yake aure mara sirri bata riqe nata bama bare ta riqe na wani to waima yaushe ma sukayi auren ne duka duka har yanzu basu rufa shekara uku ba da yarsu daya amma duk ta tallatashi a dangi bayan shima bashi yayi kansa a hakaba hakanan ya tashi yaganshi bashida qarfin sha'awa.



Ruwa yaji Hajiya ta watso masa tace “soko sakarai tashi ka bacemin a guri nikam na haihi Ladidi da hula har mace take kawo qararta dubi jikinka duk wani farin abu ya bushe kamar wani Fadwah yar cikinka ma tahika natsuwa"

Kallon jikinsa yayi da sauri yana tunanin to meye a jikin nasa tunawa yayi da yanda suka rabu da Hauwa yar fillo dutse a hannun riga baisan sanda yayi murmushi ba tare da shafa kansa yace “nono naje siyo mana rugar Sambajo a garin Alqalawa wlh wata sokuwar yarinya Hauwa tayimin barinsa a jikina wai kawai saboda by mistake na taba hannunta a shirmenta wai goggonta tace idan kado ya tabata mutuwa zatayi"



Dariya sosai Hajiya takeyi tace “dada fillo bazai waye ba batasan kaima hakan take ba" fara'ar fuskarsa ce ta dauke ya tsuke fuska idanunsa ya kada yayi jajir yace “zan daina zuwa gidan nan Hajiya tunda nayi aure bantaba zuwa gdannan na tafi da farin ciki ba kullum sai kin fadamin kalma mara dadi akan lalurata Hajiya idan ban samu tausayi dajin qai a gurinki ba a gurin wa zan samu?"

Binsa tayi da kallo cike da sanyin jiki kuma fa mgnr dan nata haka take kamata yayi take kwantar masa da hankali tabe baki tayi tace “hotiho kawai"



__________Horn yaketa dokawa a gidan nasa kafin maigadin yazo ya bude masa ya shiga yayi parking ya dauki kayan dayazo dasu ya bude qofar parlourn ya shiga TV tanata aiki ga yarsa nan Fadwah tanata baccinta a saman kujera ita kuma uwar bata parlourn.

Iska ya furzar ya nufi qofar dakin ya kama jarmlock din amma sai yajishi a kulle yayi Knocking ya juya ya shiga kitchen ya nade hannun rigarsa ya fara jera naman da yazo dashi a ciki ya koma kan kayan miyan Suma yaji an bude qofar parlourn an mayar an rufe, to be kawo komai a ransa ba saboda zuciyarsa ta tafi tunanin Hauwa wanda ya addabi zuciyarsa cikin kwanakin nan ko kwanciya yayi itace da sakarcinta sukeyi masa yawo a kwanya saidai yayita zuba murmushi shi kadai gashi gobe zaiyi tafiya zuwa sounth Africa zaiyi missing dinta sosai.



Baiji shigowarta ba sai ji yayi ta bugeshi ta baya ta wucce ya dago manyan maganansa ya kalleta ta daga masa hannu tace “oh sorry mistake ashe ka dawo" murmushin kawai yayi ya matsa gabanta yace “naji saqonki na gode waike Mubaraka yaushe zakiyi hankali ne ki riqe mana sirrinmu kinsani fah nafi kowa son naga na zama jarumin namiji wanda bakeba zan iya gamsar da wasu matan ma amma ban samu wannan damar ba ya kikeso nayi don Allah kina gani kullum cikin neman magani nake kuma kin sani ko banyi sex ba Ina iyakar qoqarina naga na cire miki kewa amma komai nayi miki bakya gani saboda kawai wannan matsalar Mubaraka mata da yawa irin damarki suke nema sun rasa kinga ke ba rashin ci ba ba rashin sutura ba duk abinda kikace shine nakeyi miki Toni meye ya hana ki karbeni a yanda nake bayan kin sani abubuwa da yawa naki bayimin sukayi ba Amma saboda kada tawayar tayi yawa nake qyaleki yanzu idan baki rufa asirinmu ba a duniya waye zai rufa?"



Tabe baki tayi ta juye indomie dinta a flat sai yanzu ma ya lura da yanda gashinta yake a hargitse shi dama ba kirki ba, kafin yayi mgn tace “dallah malam kauce na wucce" matsawa yayi ta wucce har takai bakin qofar yace “yinin yau banci abinci ba Ina abinci na?" Ko kallon arziqi bai samu ba tayi ficewarta.

Ajiyar numfashi yayi ya dauki yourghut da cake ya fita ya nufi dakinsa dake sama abin takaici da mamaki dakin kaca² gadon harda danshi alamun baa dade da tashi akai ba ya ajiye yourghut din ya fara gyara dakin ya gama ya shimfida sallaya yaci abinda zaici ya miqe yayi wanka ya dawo ya dauki laptop dinsa ya fara aikace²nsa sai wajen daya sannan ya kwanta saime?



Zuciyarsa taqi hutawa da tunanin Hauwa da zarar ya rintse idonsa kallonta yakeyi matse jikin mota ya hade jikinsa da nata yana sauke mata kiss a kuncinta jikinta na rawa tunaninsa gabadaya ya karkata ya koma Rugar Sambajo qauyen su Jiddoh yasan dai bai barta da matsala ba tunda ya biyata kudin nononta da wautarta tasa ya zubar da haka ya kwana ko cikin baccinsa itace wai tana shafa gemunsa tana cemasa “I LOVE U My Lameer" shikadai yaketa zuba murmushi yana qara qanqame pillow.



Hodijam Jiddoh baiwar Allah wannan dare ta daku gurin goggonta har saida ta kumbura mata jiki saboda duka da muburgi fadi takeyi “ni zaki kunyata ki jawa abin hwadi a gari dan ubanki ki rasa wa zakike kulawa kuna shiga duhun dawa dashi yana lalubeki sai kado ashe da gaskene da Madi dan burni yashe yana ganinki kina kaiwa wani dan yankon kayi nono yanayi miki juyensa ya baki kudi da yawa, to daɗa Allah ya nunamin kuɗi har jaka goma a jikinki ɓingel wato kuɗi yake baki yake ƙwaƙuleki ko?"



Girgiza kai takeyi kamar zata tsinkeshi tana kuka jikinta na rawa goggo ta sake nufota tana cewa “kina yimun bayani ko sai nasha aradu ani gaton uwarki"

Jiddoh bata iya qaryaba cikin kuka ta zayyane musu komai suka rinqa sallalami da tafa hannaye suna hwadin “aradun Allah Jiddoh kin riqa qugunki ya isa daukan bindira tunda har kado ya hwara hwadi maki batun aure to kuwa ai dole baffanki yayi miki aure da Madi dan burni tunda ke shegiyar ya ce"



Wata wawura goggonta ta kumayi mata ta zauneta ta bare qafafunta tana kuka tana ihu ta dauki danyan tasshi ta murza Mata ta dagata tace “gobema ki qara bari Kado ya tabaki har ya dambusheki dau uwariyonki aurakiya kawai almura me idon agwagwa"

Habawa me Jiddoh zatayi banda kuka tumami da ihun azaba danyan barkono a gatonta sai tsuku yakeyi Mata ita kuma tanata dara tana tumami tana ihu da kuka me ban tausayi.



A haka goggonta ta cillo Mata bokatin qarfe tace “tashi dan ubanki kije rafi ki daukomin ruwa kizo kiyi wanka kiyimin wankin daudata ki sukole wadannan kayan naki bazan kwanta dake bukka dai ba babu tsarki yau sai kin qarar da ruwa buta goma"

Hakanan tana tafe tana talewa tana kuka taje rafin ta zauna a bakin rafi tanata rera kukanta taji an warce bokitin nata ta dago da sauri zatayi bala'i sai taga Madi a tsaye sai washe baki yakeyi yana turo harshe gaba yace “hegiya Jiddoh yau nayi miki burni ai ya nine nazo nace naganki da Kado a cikin duhun dawa kuna cicin tsuli kuma aradun Allah gobema na ganki kin qara kai mushi nono sai nayi miki sharri da yahi haka tunda ke bakyaji kuma kin rainani aradun Allah bindira ta tahi ta Kado qarhi kuma kizo muje bayan rafi a gwada ki gan...."



Qumm yaji an buga masa Abu a goshinsa jini ya balle ita kuma taja da baya da sauri tace “alqur'anin Allah kai tsinanne ne Innan qotai tayi asarar aihuwa shege dan durun uwa danma ka samu nace da Kado ka iya sa agogo to tunda kai Dan iskane na daina sonka ma na tsaneka na tsaneka hege bindirar ka din uwarka an hwadi muka di diyat iskace"

Damqota yakai hannu zaiyi ta qara jifansa da bokatin ta kwasa da gudu ta shige cikin duhun dawa tanata bubbuda qafa saboda zafin tasshin da takeji a qasanta har yanzu ta jima a gurin sannan taga yabar gurin ta fito da sanda ta kandami ruwanta ta dora akanta ta nufi cikin rugarsu takai tayi wanka ta wanke gidan dadin sosai Amma har lkcn zafi yakeyi Mata ta shafa versilin a gurin ta rinqa fifitawa har Allah yasa taji relief ta koma daki tayi sallah ta kwanta tanata juyi qasan zuciyarta cike da tunanin Kado tare dajin haushinsa na jamata dukan da yayi a fili tayi tsaki tace “Kado hege ne harda wani hmwah yayimin qaton kawai saikace Bandirawo Iro"............



Karanta Littafin : Abban Sojoji Hausa Novel



Washegari tun asuba ya tashi ya fara shirya kayansa cikin trouble bag dinsa kasancewar yasan Koda ya tashi Mubaraka ba lallai ta tashi ba zatace yayi wuri da yawa to shima baiyi yunqurin tashin nataba ya gama shirinsa tsaf ya hada tea dinsa yasha ya kira drivern office dinsa ya daukeshi zuwa airport kasancewar tafiyar bashi daya bane da sauran abokan aikinsa zasuje training din.



Yana zuwa babu bata lkc suka daga zuwa South Africa zuciyarsa cike da kewar parents dinsa da yar fulaninsa Hauwa da kewarta take neman zame masa jiki a wannan lkcn haka ya wanzu cikin wata irin rayuwa daya kasa gane wacce iri ce kullum zasuyi waya sau biyu da Mubaraka ya tambayeta lfyrta data yarsa Fadwah amma ya kasa daina kewar qasarsa ta gado musamman Rugar Sambajo.



____________Kwananta uku bata dauki tallan nono ba ko dandali ta daina fita duk a qoqarinta na karsu hadu da Madi dan burni yace zai sanya mata bindara tunda taji Indo qawarta da akayi Mata aure tana cewa bindira lubebiyace idan ta shiga bata iya fita saidai ta yayyaga mutum kuma idan ta tashi dane yake tunkudota waje.

Shiyasa take masifar tsoron bindira ita har kuka takeyi da tumami idan akace zaa kaita asa mata bindira, tana tafi tana yan waqoqinta taci uwar dammara abinka tayi kwalliya ta rambada kanta kile harda digon india a goshinta da kumatunta tasa kayansu na fulani shudaye tana tafe tana waqar “lula lulaye aluliya zani bikin andi aluliya" batasan binta akeyi ba saida tazo jikin wata bishiya kawai taji an dumbular mata nono an kwasa da gudu.



Aikuwa ta dora hannunta akan nononta tana ihu tana burgima tana hwadin “shikenan na mitu na lalashe dan innini na sun tabamin wayyoh Goggo wayyohhhh Baffa wlh bazan yarda ba saina taba nonon uwarsa nima" wasu yanmata ne guda uku sukazo wuccewa suka ganta a kwance duk tayi birgima tayi tumu² suka tsaya suna kallonta tare da tafa hannu sukace “Hamdi imboni Jiddoh meye hakadin?"

Miqewa tayi zaune tana karkade qasar data shiga cikin dogo baqin gashinta da ya mulku da manshanu tace “Qur'ani saina mulmulawa uwar Wanda ya dumbularmin Inninina Fura a gatonta"🤣🤣



Dariya suka kwashe da ita Lantana ta kalli Jummai tace “kiji doluwa to yau aka fara dumbular inninin naki naga cewa akayi har Kado kike bawa yakesha shiyasa sukayi girma sukayi ruguza ruguza haka"

Zabura tayi tace “kutmar dumadu naci hagu naci dama naci tattabatsinin kantalin baqoramar inyaniyar marurun tsohon gwailon uban wanda ya hwadi haka" kafin suyi wani aune ta hade kansu guri guda ta kama jibgarsu hagu da dama tana wani tsalle tana naushi ta ko Ina.



Suna ganin haka kowa yaci na kare ta kuwa rufa musu baya a guje fadi take.

Yau har bayan tsoho da tsohuwa suna doki doki sai nabi ƴa naci uwar galken ubanta Kaɗon dako mgn bata dameshi ba ina ya iya wannan iskancin shi banda sumba da qaquba babu abinda ya iya kuma qur'ani saina hwaɗí muhi bashi kawo lantarki gidanku"

Yanda suka rinqa gudun a daji abin abin dariya kuma sai qara rungume qirjinta takeyi wai kada a qara dumbular mata nono😁





Jitayi an riƙeta ta baya taja ta tsaya tana huci tare da waiwayowa zatayi bala'i sai tayi ƙasa luuuu saboda ganin yayanta lawan tasan ta kaɗe har rassanta rirriƙeshi tayi tana kuka tana cewa.

"Alqur'an bani na tsokalesu ba sune kawai ina kukana da burgimar tuba sukazo suka tambayeni meye yasani kuka nace adumbili akayimin shine sukace wai ai dama ance ina bawa Kaɗo nono na wannan na jikina bana shanuwa ba yanasha
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On MATAR HARIJI
avatar
ashiru-3

4 months ago

Reply

.

Please Login or Register in order to submit comment