Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

YAR BARIKI
Littafi na daya 1 complet
Na Rufaida Omar
Ebook created by Shuraih 99%
Published @ www.hausaebooks.com.ng


'YAR BARIKI

©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)

(01)

Kayataccen hotel ne na shak'atawa. Mafi akasarin mutanen dake zaune a farfajiyar wajen matasa ne da yawansu kuma 'ya'yan masu hannu da shuni ne. Mutane ne daga kabilu iri iri,ya had'a da larabawa da turawa uwa uba hausawa da fulanawa. Kowanne sha'anin gabansa kawai yakeyi ba ruwan wani da wani.

Lokacin k'arfe bakwai na daren alhamis. Daidai lokacin ne wata matashiyar budurwa sanye da siket wanda ko cinyoyinta bai gama rufewa ba da wata shegiyar riga wanda dashi da babu duk d'aya domin rabin jikinta daga saman wuyanta da kuma cikinta duk a bayyane suke. Kanta yasha gashin doki,ta tufkeshi da manya manyan ribbons har uku,maimakon tufkar ya kasance a tsakiya sai ya zamana a gefen b'arin kanta na dama. Fuskarta sai shek'i takeyi gata sarauniyar kyau. Lebban sun sha jan baki. (Nayi kyam rik'e da alk'alamina ina duban irin takalmi mai tsinin dunduniya dake sanye a kafarta tare da mamakin yanda bata ko tsoron ya karya mata k'afa. Ganin zata b'acemin ya sanyani watsar da tunanina nabi bayanta a guje yayin dana bar Hanne cillare a bayana tana cillara k'afafuwanta wanda hakan ya tunomin da Kayan moh...(Hasken Idaniya..na tagwayen marubuta...lol).

Cikin takunta mai sanya zuciyar dukkan wani d'a namijin da yayi kicib'us da ita motsawa take tafiya bata tsaya ko'ina ba sai gaban teburin wasu 'yan mata su uku wadanda duk cikinsu suma babu mai shigar arziki.

"Sexy angel"

Cewar wani bature dake zaune a kusa dasu, ya lumshe ido saboda wani irin k'amshi da ya busoshi. Bata ko kalleshi ba saidai ta murmusa saboda ta karanci da ita yake. Tsinken sigari ta janyo ta sanya a bakinta kafin tayi amfani da lighter ta kunna.

"Baby wallahi mutuminki yayi fushi,munkai (30mins) zaune tare dashi yana jira yaga b'ullowarki amma...."

Wacce aka kira da sunan Baby,ta dakatar da ita ta hanyar watsa mata kallo da shanyayyun idanuwanta,kafin ta fesar da hayak'in sigarin. Cikin zazzak'ar muryarta tamkar sarewa marar tashi sosai

"Ya kamata by now ace kin fahimceni sosai Manal, banason a dunga yimin karan tsaye a sha'anina ok? Da nasan ya bar nan da babu abunda zaisa nazo ."

Tana gama fad'in haka ta mike da niyyar tafiya,baturen nan ya katse mata hanzari

"Excuse me."

Bata ko kalleshi ba tayi gaba tana karkada jiki. Manal ta dubi yan matan nan kafin taja tsaki

"Zaman me mukeyi kuma? Saiku tashi mu wuce tunda 'yar mulkin tayi halin nata. Ta sanya muzo mu jirata,tayi mana rashin arzikin."

'Yar bak'ar cikinsu ta bugi tebur daidai lokacin da baturen nan ya katsesu da tambayar lambar wacce suka kira Baby. Harararsa sukayi kafin su bar wajen. Akan hanya bak'ar ciki wato Dalal ta ja tsaki

"Guy dinnan baisan wacece Baby ba da baiyi gigin tambayarmu lambarta ba."

Manal ta tab'e baki

"Kowane gayu idan ya tashi baby,baby. Sai kace muma ba mata bane. Ji fa yanda guys din wajen nan suka bita da kallo tamkar ita kad'ai ce mai abun kallo a jiki. Naga muma dai muna da dirin jikin nan da kyawun fuska ko? Me tafi sauran mata ne?"

Hibba wacce tun soma maganarsu batace dasu uffan ba ta saki dariya a daidai lokacin da Manal ke kokarin bud'e mota. Wannan yasa duk suka kalleta da alamar tambaya na me kuma ya bata dariya haka?

Hibba ta cigaba da magana

"Kuna b'ata lokacinku wajen had'a kanku da Baby Tasleem. Wallahi tayi mana zarra,ku nifa tunda nake a rayuwata ban tab'a cin karo da gogaggiyar 'YAR BARIKI ba wacce komai nata daidai da fushinta ke burgeni ba kamar Tasleem. Ta cancanci a kirata baby domin wallahi ku kanku kun sani daidai da mayuka da turarukan da take amfani dasu abun kallo ne. Ai samun guy irin KB wanda zai tsaya maka akan komai wanda ko mijinka sai haka abu ne da mai matukar wuya. Abu na gaba da zai k'ara tabbatar maku ita d'in ta dabance,ba kowane shara take mu'amala dashi ba. Wallahi komai muk'ami da kud'in mutum idan har bai yiwa Tasleem ba toh koda yafi kare naci karan kanku ne kunsan ba kulashi zatayi ba. Wannan sai mu."

Ta k'arashe tana 'yar dariya,inda ta k'ara k'ular da Manal da Dalal. A fusace Manal ke tuk'in har suka haura titi suka fita daga hotel d'in na Tahir. Kwarai su ukun sun kasance amininan baby saidai suna matukar kishin yanda ta fisu da komai,ta k'etaresu a harkar bariki. Haka Hibba tayi ta dariya tana k'ara b'ata ransu.

*******

Baby Tasleem bata tsaya a ko'ina ba sai kofar gidan KB. Hon d'aya tayi,maigadin yayi azamar wangale mata k'ofa sanin ko wacece ita ga maigidan. Da gudu ta shiga harabar gidan ta faka motarta ta fito. Cike da yanga ta nufi cikin gidan kai tsaye.... ..!






'YAR BARIKI

©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)

(02)

Tangameman falo ne,yasha kayan k'awace k'awace,b'ata lokaci ne tsayawa kwatanta kyawu da tsaruwar falon. Daga can wata 'yar kusurwa kuwa, matattakala ne wanda zai sadaka da sauran sashen na dake cikin gidan.

Baby bata b'ata lokaci ba ta haye saman kanta tsaye bata dire a ko'ina ba sai a falon da ta hakik'ance zata tarar da Kb. Fitilun wajen a kashe,ta lalubi makunninsu ta kunna,saidai wayam babu shi. Tana shirin fad'awa d'akinsa ne taji an rungumota ta baya. Ta d'an rufe ido kafin ta bud'esu tana murmushi yayinda ta k'ara damk'e hannuwansa tana murmushi. Tana jinsa ya d'ora hab'arsa akan kafad'arta bata iya hanashi ba.

"Kina sane da laifin da kikayimin ko?"

Ya fad'a daidai saitin kunnenta yanda ita kad'aice zata ji. Ta lumshe ido,cikin muryarta mai sanyi tace

"Laifinka ne, meyasa bakayi calling dina ba kafin kabar wajen? Na biya nasha mai ne shine dalilin jimawata. Kaima kasan banason yin nesa dakai."

Matashin saurayin da bai wuce shekaru talatin ba,bak'i saidai bak'insa mai kyau kasancewarshi d'an hutu,yana da kyawunsa daidai misali. Da ganinshi kaga cikakken namiji. Shine dai wanda aka kira da KB(Kabir). Ya saki Baby yayi gaba zuwa bakin firij dinsa,kofi ya dauka a saman firij din yana tsiyaya lemun da baya rabo da shan shi(barasa). Sanye yake da kayan bacci na(pyjamas),sai lokacin ya k'arewa Baby data zauna saman kujera kallo tun daga sama har k'asa kafin ya saki murmushi mai burgeta. Ta kauda kanta daga dubansa tana mai lumshe ido

"Kallon nan yayimin yawa,a rage."

Yayi 'yar dariya kafin ya dawo ya zauna gefanta

"Mamaki kike bani aduk lokacin da kikace bakyason nesa dani Baby,alhalin nasha gayyatarki zuwa Abuja inda acan nafi jimawa nan kuwa sai weekend,ke ma kin sani. Baki tab'a amincewa da hakan ba Baby,(I don't know your reason.)"

Ta tab'e baki kad'an kafin ta sakar mishi wani shu'umin kallo,baisan lokacin daya saki baki yana kallonta ba cikin shauk'i matuk'a.

"Kanason maimaita magana KB,munyi maganar nan yafi sau goma. Na sanar dakai dalilina,bazan iya binka ba domin banason shiga tsakaninka da iyalinka. Aduk sa'ilin da kake garin nan,nikam taka ce, muddin ka cire k'afa ka koma Abuja,ka zama ikon Yasmeen. So please mubar zancen banaso,daga yau kada a k'ara maimaicinta."

Kb ya cigaba da kurb'ar barasarsa yana dubanta cike da mamaki,ya za'ayi wacce kw ikrarin tana matuk'ar sonshi amma har ace bata kishi da matarsa. Wannan wane irin so Tasleem keyi mishi ne?"

Ta katse mishi tunani da salonta mai rikirkita tunaninsa,babu shiri ya mance a duniyar da yake.

******

Baby bata bar gidan KB ba sai washegari da yamma bayan ya cikata da kud'i. Nan ma da yayo mata rakiya kamar kada su rabu. Suna tsaye a wajen fakin,yana rike da ita a jikinsa inda yayi mata iznin zab'ar mota d'aya cikin tsadaddun motocinsa dake k'asan rumfar ajiye motoci. Saida ta kammala duban kowaccensu kafin ta zab'i
bak'ar (Mercedes Benz C300). Ya yafito direbansa da hannu,yayi mishi nuni da motar ba tare da yace uffan ba. Direban ya gyada kanshi cike da ladabi kafin ya fice. Can ya dawo d'auke da mukullin ya mik'awa ogansa,KB ya karb'a ya damk'awa Baby suka sakarwa juna murmushin kafin ta had'a mukullin da hannunsa ta sumbata.

"Thank you my soul,sai had'uwa na gaba."

Ta k'arashe tana mai kanne mishi ido d'aya. Baisan lokacin daya d'aga mata yatsunshi ba saboda duk lokacin da yake gaban Tasleem,mantawa yakeyk da komai sai ita. A gaban idonshi tayi ribas taja motar. Maigadi ya bud'e mata ta fita.

Akan hanyarta tasha kwanar shiga sultanroad taji anayi mata hon babu kakkautawa. Da fari ta dauka bada ita ake ba,saida ta rage sautin kid'an dake tashi ta k'ara duba side mirrow dinta,tabbas Honda civic dinnan ita take bi,a yanda ta lura da yacce fitilunta ke kawowa su dauke a lokaci guda tasan ita d'in akewa magana. Baki ta tab'e ba tare da tayi niyyar tsayuwar ba ta k'ara k'aimi wajen gudun da takeyi. Saidai me? Rikitaccen hon d'in da mai motar nan ke cigaba da danno mata ya fusatar da ita. Ala dole ta taka burki a ta tsaya,wannan ya sanyawa mai motar dake biye da ita taka burkinsa babu shiri gudun kada ya goga mata. Bata da niyyar koda fitowa daga cikin motar balle kuma mai shi ya samu damar cewa wani abu. Tana karkad'a yatsunta jikin sitiyari idanunta naga madubi tana duban motar ta bayanta. Bakin ciki ya turnuketa ganin an tsayar da ita sannan ba'a da niyyar fitowa balle kuma ayi magana. Takaici bai gama cika Tasleem ba saida taga motar nan tayi ribas tayi U turn ta koma baya. Wani wawan zuciya
daya taso mata batasan sadda ta juya ba itama ta bi motar. Gudu mai motar yakeyi,itama gudu take. Saidai abun bakin cikin suna zuwa danja ya b'ace mata domin kuwa yana ficewa kafin ta karaso aka dakatar dasu. Ta bugi sitiyari don bakin ciki,hakanan ta koma hanyar da ta nufa cike da bakin cikin yanda mai motar da batasan ko wanene ba ya raina mata wayo har haka.....!
'YAR BARIKI

©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)

(03)

A fusace ta wuce su ta fada kan kujera tana huci kafin ta janyo kwalin sigarin dake ajiye saman center table din,wanda da wuya ka rasa shi a wajen. Ta zari d'aya ta soma zuk'a.

Manal,Hibba da sauran abokan watsewarsu maza da mata duk suka bita da kallo cikin rashin sanin tak'amaiman dalilin fushinta.

"Baby ke da wa?"

Cikin murya irin na wacce ta sha kwaya,Hibba ta tambayeta. Ta kauda kai tana fesar da hayak'i,kafin ta sanya hannu ta cire tufkar da ta yiwa kitsonta na gashin doki,ya zubo har kafad'unta.

"Uban waye ne? Ina zan sake samun damar cin karo da mai motar nan?"

Hibba ta dubi Manal wacce tayi filo da cinyar abokin watsewarta,Manal ta tabe baki inda ta juyar da kanta gefe don kuwa zuwa yanzu kishin Baby fal cike a zuciyarta. Wani d'an karambanin aka samu ya kai hannu da niyyar tab'a fuskar Baby,batayi wata wata ba ta mik'e ta wankeshi da mari gami da nunashi da yatsa.

"Ba kowane tsami ne yake da damar tab'a jikina ba! Daga yau ina mai gargad'inka ka nisantar da kanka daga gareni if not..."

Tayi kwafa ba tare data k'arasa ba ta dauki mukullin mota da jakarta ta haye sama.

Dariya gayun suka sanya mishi,wani dake can gefe yana kokarin jona socket jikin TV ya d'ago mishi hannu

"Sorry Baaba,wannan fa babban goro kake gani sai magogin k'arfe. Ka kiyaye a zauna lafiya."

Wanda aka kira da baaba ya shafa kumatunsa yana murmushin takaicin marin da Baby tayimishi kafin yayi kissing hannunshi

"Me takeji dashi? Kud'i ko kyau?"

"Babu wanda bata ji dashi,kasan babu abunda zaka nuna mata don ubanka.Da kud'inka tsohonka kake tutiya,ita kuwa harkarta har da sa'annin ubanka da gayu irinmu da suka dame tsoffinmu a kud'i da komai Baby gogayya take dasu."

Baaba ya jinjina kanshi yana murmushin da shi kad'ai yasan manufarsa kafin yayi wuf yabar wajen. Suka k'ara sanya dariya,banda Manal wacce takeji tamkar ta tashi da kifawa Musty mari yanda yake ta kod'a Baby. A fusace ta mike zaune zatayi magana saidai ta fasa sakamakon kid'an da ya cika ko'ina na gidan. Nan wasu suka mik'e suka hau casu alhalin ga kiran sallah can na magrib yana tashi a masallatan unguwa.(Allah Ya shiryemu,amin.)

Baby tasleem kuwa tana shiga d'akinta wanka tayi na musamman ta fito ta k'ara mulke jikinta da mayuka da turarukanta tsadaddu kafin ta shirya cikin wata gown mai tsaga a gefe gefenta,tun daga gwuiwa har k'asa. Ta k'ara gyara gashinta,ta fesheshi da Hairsprays kala kala. Kafin tayi zaman shafa jan farce a yatsunta kalar skyblue(wato kalar gown dinta). Ta kwashi awa kusan uku gaba daya yayin wankan da komai nata na shiri. A lokacin da take jiran bushewar faratan nata ne,Dalal ta turo k'ofa ta shigo. Itama ta had'e cikin riga da wando matsastsu masu bin jiki. Sai taunar cingam takeyi na yan bariki ta rike k'ugu tana duban Tasleem wacce kallo d'aya tayi mata ta madubi bata k'ara dubanta ba.

"Zaki gidan Momi ne ko muyi gaba?"

Kamar bazatayi magana ba,har ta k'ular da Dalal.

"Kuje,zan biyoku. Hibba ta jirani mu wuce tare."

Harararta Dalal tayi kafin tayi gaba tana jan tsaki yanda Baby bazata jiyota ba. Ta iske Hibba cikin shiri zaune a saman mota

"Hakimar tace kiyi jiranta ku taho tare. Munyi gaba,kinsan Momi batason a b'ata lokaci."

Hibba tayi murmushi domin tasan yanda Momi ke ji da Baby ko don masu gidan ranar da take kai mata a kowane sati,domin nata kyautar ga Momi yafi na dukkansu yawa.

"Kada ku damu kuyi gaba."

Manal ta bud'e wutar hon,da azama Dalal ta shiga suka tafi. Basuyi mintuna da barin gidan ba,Baby ta fito cikin takunta na jin ita d'in ta isa tana tafe ko'inanta yana rawa,tana amsa waya tamkar bataso. Hibba dai kallon ikon Allah takeyi,har ta soma zargin kodai Baby 'yar wata basaraken ce? Haka tayi ta kallonta ita kuwa batasan ma tana yi ba,mota ta bud'e ta shiga ba tare da ta cewa Hibba uffan ba. Don kanta itama ta bud'e gidan gaba ta shiga. Minti uku da soma tafiyarsu,Hibba ta fahimci da shahararren mai kud'in nan Baby take waya, wato Alhaji Ridwan Naira. Gudu takeyi kasancewar dare ne,hakan yasa tafiyar mintuna talatin,sai gashi minti goma sha biyar ya kawosu gidan MOMI......!
'YAR BARIKI

©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)

(04)

Falo ne babba,cike yake da matasan mata da manyansu. Kowacce tana ji da kanta da ganin tafi 'yar uwarta. Wacce aka kira fa Momi tana hakimce a saman kujera mai zaman mutum biyu ta kishingid'a tana cin tuffa. Kallonsu takeyi d'aya bayan d'aya fuskarta dauke da murmushi. Kowaccensu tasha shiga ta alfarma,saika rantse wani shagalin akeyi. Daidai lokacin Baby ta sanyo kai,a bayanta Hibba. Matasa da yawa dake mutanenta ne,suka hau jinjina da ihu

"Shegiya Baby,manya a baku naku daban."

Ta sakar musu murmushi mai bayyana hak'ora tare da mimmik'a musu hannu suna cafkewa. Manyan kuwa gaisheshu tayi kafin ta isa ga Momi wacce ta zuba mata ido tana murmushi. Hannu ta dunkule,alamun jinjina

"Na gaida uwata,ranki ya dade tuba nake."

Momi ta ja hannunta ta zauna da ita gefanta tana dariya ga hakoran Makkah farare a hakoranta biyu na gefe da gefe.

"Bakya laifi gareni baby."

Daga haka Momi ta juya don soma abunda ya tarasu. Magana ce aka cigabansu a harkokinsa. Ta kara gargad'insu akan su kiyaye kada su bari ciki ya shiga jikinsu koda wasa. A karshe ta dubesu sosai

"Maganata ta karshe ku sani, babu aure a tsarinmu. Nasha sanar maku koda ya kasance zakuyi auren,toh fa baifi na wata uku ba kin fito. Auren ba talaka ba,mai hannu da shuni,ki tabbatar kin tatso mana mai yawa kafin ki datse igiyar auren naki. Wannan shine jawabina. Batun balance kuma,ina jiranku babu wacce batasan acc.no. dina ba."

Haka suka jima suna tattaunawa kafin taro ya watse,Momi ta dubi Baby wacce tayi haramar tafiya. Lokacin karfe sha biyu da mintoci

"Baby baby,kodayaushe tauraruwarki kara haskawa takeyi. Ba daga kananun ba,daidai da manyan suna son mu'amala dake. Ina kuma ga an lek'a ga Hajiyoyinmu duk da dai kin nuna wannan baya kanki yanzu."

Baby tayi murmushi ta girgiza kanta

"Momina kenan,me zanyi da jinsi irin nawa? Wannan babbar kazanta ce, wannan dinma da nakeyi fatana nan gaba na daina."

Momi ta kyalkyale da dariya tana mai dafa kafad'ar Baby

"Babu ranar da wannan fatan naki zai tabbata kuwa,zan maki uzuri da alama bakisan alfanun jinsi ba sai nan gaba."

Baby tayi murmushi mai had'e da jan numfashi

"Ba halina bane,baya daga abunda nake sha'awar aikatawa. So,in sha Allah bazan tab'a bin wannan hanyar ba."

"Ja'irar kaya,ashe har yanzu kinsan da sunan Allah? Toh ba laifi muje zuwa."

Abun sai ya bawa baby dariya,ta d'an dara kafin ta mik'e tayi hanyar fita

"Momi kenan,na barki lafiya."

******

Mutum ne matsakaici,mai dogon fuska,yana da matsakaicin hanci saidai akwai magana(idanu). Girarsa a cike kuma bak'i wuluk,kamar dai yanda sajensa da gashin kansa yake. Fari sol,zubin Fulani.
Zaune yake a ofis yana aiki akan Laptop. Hankalinsa gaba d'aya ya tafi ga aikinsa,kallo d'aya zakayi mishi kasan yana hutawa. Daidai lokacin aka bud'e kofar gami da yin sallama. Ba tare daya kalli mai sallamar ba ya amsa ciki ciki kasancewar ransa a b'ace yake dashi. Ya k'araso da fara'a ya zauna

"An gaida mutumina,ba fad'a mai ya kawo gaba kuma? Ace har ka iso garin nan saidai don rashin mutunci ko waya bakayi domin sanar dani ba sai a bakin kanwarka na tsinci labarin."


'YAR BARIKI

©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)

(05)

Har ya gama maganarsa baice mishi komai ba. Ganin haka ya buga tebur wannan yasa shi watsa mishi wani irin kallo kafin ya karkato yayi juyi da kujerarsa yana fuskantarshi. Fuska a daure yace

"Kana da kunyar takowa ofishina bayan wulakancin kayimin?"

Cikin rashin fahimta,KB ya zuba mishi ido kafin ya tambayeshi

"Me kake nufi wai Haris? Nifa bansan takamaiman laifin dana aikata ba."

Ya dubeshi kadan kafin ya girgiza kai

"Jiya,(around 6:00pm),na had'u dakai anan wajejan sultan road. Saidai abun mamaki nayita hon baka tsaya ba saida kyar,karshe ma don rainin hankali kak'i fitowa daga motar. Saidai a yanda ka nuna yanzu ya tabbatar min ba kaine cikin motar ba saidai tabbas lambar motarka ce. Na soma tunanin direbanka ne,toh a gaskiya ka chanja direba,domin bakayi dace ba wallahi da zan ganshi zai sha mari ne...."

Kb ya katseshi

"Tsaya don Allah,gayamin menene ya faru?"

Haris ya labarta mishi,ya k'arashe da cewa

"Mercedes Benz dinka ce, kada kaso kaga gudun da direbanka ke...."

KB ya katseshi a kunyace

"Oh,Baby ce a ciki fa."

Haris ya yamutsa fuska

"Who the hell is Baby?"

Kb yayi murmushin basarwa

"Wata cousin d'in Mamina ce,ta ari motata ne tun kusan (last two days.)"

Haris ba don ya yarda ba,sai don kawai bai fiye bin kwakkwafin abunda bai shafeshi bane,ya gyada kanshi

"Ok."

Daga haka suka bar zancen suka fad'a hirarsu.


DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment