Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

ο»ΏRAMLAT YAR TSINTUWA
littafin Raheem S Jega
Ebook created by Shuraih Usman
Published at www.hausaebooks.com.ng


πŸ€πŸ’πŸ€
*RAMLAT"*
_Yar Tsintuwa_
πŸ€πŸ’πŸ€
*_Written BY raheem jEgsπŸ“š_*
*Da sunan Allah mai rahama mai jink'ai tsira da Amincin Allah su tabbata ga Khairul Anbiya wato Annabi muhd (S A W) ya Allah ka k'ara d'aukaka darajar masoyan mu bayayyananni da boyayye*
_NAYI WANNAN LITTAFIN NE DOMIN SANYA NISHAD'I DA FAD'AKARWA GA AL'UMMA ZARGI MUGUN K'ULLI "BANAYI BANE DANCIN ZARAFIN WANI/WATA BA IDAN KUMA KUSKURE YA BIYO BAYA ALLAHU GAFURRUN RAHEEM._
πŸ’ _RaMlaT_ πŸ’
*1_5*
*_( YOBE STATE )...._*_misalin Karfe 8:15am nasafe zaune yake acikin babbar Office d'insa ga wata shahararriyar Lapton agaban sa ba abinda yakeyi face dube2 akan wani DOCUMENT wanda dukkan wani sirri na tattalin arzikinsa da filayen sa campanoninsa da tsaresarensa duk yana cikin wannan document da yake bincike aciki,_
Amma abin mamaki duk wannan abin bashine gaban sa ba sai tunani da kuma tsintsar tausayin karamar 'yarsa da yabaro a gida wadda bazata wuce shekaru 5 zuwa 6 ba, "Alhj *Hisham A. Ahmad* kenan wanda yayi k'aurin suna Acikin jahar Yobe state.
Mutum nea mai kyakkyawar zuciya son jama'a kyautatawa da kuma kawar da azzaluman mutane bai d'auki duniya komaiba hakan yasa yakeda tarin mak'iya masu bibiyarsa akan su kawarda shi wannan shine dalilin da yasa akoda yaushe yake tausayawa 'yarsa domin yasan za'a wayi gari wata rana mak'iyinsa sun kawarda shi
Wannan shine.
_K'wankwasa kofar akayi a hankali yad'ago kai yace "YES wani Alhj nea yashigo cikin manyan kaya babu alamar fara'a a fuskar kallo daya zakai mada kagane mutum nea mai babbsn matsayi a gaunati a fusace ya jawo kujera ya zauna batare da ya jira anbasa iziniba suna fuskantar juna shida Alhj hisham. cikin gadara yake maganar sa,_
*Hisham wann shine karo na karshe idan har baka janye bakinka acikin maganar filin da ke k'auyen gurma ba wlh saika ga abinda ba dai2 ba zakayi da nasani akan taurin kanka dake cutarda kai,*
"Dakata honarable wann barazanar taku baxatasa na karaya na barku kucinye filayen marayu ba, ba filin gaunati bane hakk'in marayu nea bawani mahalu kinda zaisa nasa hannu don kucinma wata manufa taku dan haka kafita kabani guri yada yak'arasa maganr cike da tsawa.
_AFusace yamike ya kalli Alh hisham ya girgixa kai yanuna shi da yatsa niko? Yayi kyacci yafice daga office d'in afusace Excort d'inshi suka maramai baya_
Bai shiga motarsa ba, saida yajima yana waya naso injiyo abinda yake fad'a amma badama inyo kusa dashi irin Yadda naga yad'au zafi yayima Excort d'insa hannu alamar sutafi.
Misalin karfe 4:00pm Alh Hashim yadawo gd ransa a6ace yashigo palour yasamu kujera ya zauna tare da kwa6e babbar rigar sa,
Wata mata tafito daga d'aki d'auke da cup d'in juice a hannunta fara fess da ita tanufo inda yake ga alama itace matarsa,
"Alhj Lfy kuwa yana ganka ba kamar ynda nasaba ganin kaba' "uhm bakmai fa Hajiya "ina *RAMLAT* ya tambayeta
Shiru yabiyo baya kafin tace Ramlat tana d'aki tasa murya takirata amma itadai haryan xu hankalinta bai kwanta ba,
_Yarinya ce k'arama naga tafito daga d'aki cikin jajayen kaya kyakkyawa da ita ga gashin nan tamkar na indiyawa tanufo inda abban ta yake zaune cike da farin ciki da zuwa ta fad'a jikin sa ya d'ora hannun sa akan gashin kanta cike da so da qauna ba kowa bace wannan Illa_ *RAMLAT*
Anan ya dagota ya kalleta yayinda yaji wani tausayin ta yak'ara ratsashi bud'e bakinsa yace
"Yata kizamo mai girmama mutane kada kizalunci kowa idan mutum yasaka miki da sharri kibishi da Alkhairi kada ki wulak'anta kowa domin duk d'an Adam yanada baiwar da Allah yayi masa kuma aduk inda kika samu kanki kixamo mai taimakon Al'umma. Cikin maganrta ta yaranta tace
"Abbana zan iyayin duk abinda kace amma bazan taba d'aukar wulak'anci ba, murmushi yayi yace dakyau *RAMLAT* Allah yayi miki Albarka,
Ta kalli mamarta dake tace " mama kince idan Abba yadawo zamuje gidan tarihi d'auko mayafinki muje ba musu suka shirya suka fito suka shiga mota mai gadi ya bude kofa harza su fita ramlat tatuna da abin wasan ta wato babyn d'inta tace atsaya ta manta batazo da baby ba,
_Mama tace "keda zakije gidan tarihi mei zakiyi da baby acan kinga zauna yanxu baby nacan tana bacci kada kitasheta. 6ata rai tayi ganin haka Abba yayi reverse suka dawo tafito takoma gida ta d'auko babyn tana kawowa harabar gidan kamar antashi bom haka motar takama da wuta Abba da umma duk suna ciki.....))_
Tasaki babyn da ke hannun ta tanufi inda motar keci da wuta tana kiran Abbanta...!!!
Via OHWπŸ“±πŸ“š
πŸ€πŸ’πŸ€
*RAMLAT"*
_Yar Tsintuwa_
πŸ€πŸ’πŸ€
*_Written BY raheem jEgsπŸ“š_*
πŸ’ _RaMlaT_ πŸ’
*6_10*
_Iya Gaskiyarta tanufo inda motar keci da wuta tanakiran sunan Abban ta cikin murya mai karar gaske hawaye suka dararo a edonta tana kuka mai tsuma zuciya gata yarinya k'arama abin tausayi....))_
Jin sautin muryarta ne yasa 'yan dabar suka juyo da k'arfi sumar kansu ta yamutse fuskokin su rufe da wani bak'in mayafi banda edon su baka isa katsin kayi wata halitta ajikinsu ba, d'ai daga cikinsu ne wanda ga alama shine babba yaciko aguje yanufo *Ramlat* ganin tanufo inda wutar kecin iyayen ta, da zuwansa ya d'auketa da lafiyayyen mari saida ta had'iye kukan da takeyi tafad'a kasa tamkar anyi jifa da pure water ya d'auko bindigarsa yayi kicking yasaita bindigar dai_dai kanta sukayi edo 4 shida ita hannunsa yad'au rawa nan take yaji zufa takaryo masa duk jikinsa ya d'au rawa ajikinsa yaji wann yarinya Akwai wata baiwa a tattare da ita girgixa kansa yayi yamayar da bundigar aljihu yace "ku k'wamuso ta muje k'araminne daga cikinsu yace
"haba master miyassa zamu barta wannan fa mai wayoce ...duk saida tagama yiwa fuskokin mu kallo d'ai bayan daya, akanme zamubar ta,
Murmushi yayi kafin yace "Aa dan uwa mubar wannan yarinya atare damu domin nan zuwa gaba zatayi muna amfani musamman kaida kake gwauro suka kwashi dariya tare suna nunashi da yatsa.
_Suka fixgota tana kuka tana kiran Ummanta tana kallon motar naci da wuta daga nesa kana tsinkar gawar mahaifinta tana dukan bayansa akan yasauketa Amma kamr ba yajinta sai tafiyar mulki suke suna nuna isa, suna kai bakin gate alokacin taga gawar mai gadin gdn su wadda take kira da baban k'ofa, kwance acikin jini kallo d'ai zakayi masa kagane cewa bullet nea ya ratsa ta kansa, wata JIB cea baka naga sunsaka ramlat suma sun tsunduma aciki duk tsegumina saida nayita lek'e2 Amma ban iya ganin mutumen da keciki zaune ba,_
_bayan sun tayarda motar naga ya saukar da gilashin motar yazubar da yawu anan edona suka ganemun abin mamaki wazangani Honarable mukhtar wanda sukayi sa'insa da Alh hisham mahaifin ramlat acikin Ofishin sa,_
Gudu sukeyi cikin dajin Allah suka nufi wani mummunan daji dake cikin k'auyen Gurmu domin duk wata tsiya da'akeyi acikin YOBe a gurma ake tsulata,
Misalin karfe 10 na dare sukayi parking acikin dokar daji sukafito su duka sukabaro ramlat acikin motar kasan cewar barci yayi awon gaba da ita kud'i naga honarable yaciro ya damka'a musu haka dai suka jima suna shawarwarin su
_A mota kuwa Ashe ramlat ta farka tana kokarin bud'e kofar motar amma takasa abinka da k'aramar yarinya saifaman dukan glass takeyi azatonta murfin zaibude jikake gam gam da sauri sukanufo motar kasan cewar akwai tazara tsakanin su da motar cikin sa'a kafin suk'araso gambun motar ya bud'e tafado ak'asa tatashi takama tata hanya suka mara mata baya.....!!_
Gudu takeyi babu waige2 tanufi dajin Allah ita kanta batasan a ina take ba' gashi dajine mai hatsari cikin ikon Allah gudun da ramlat tayi koda babbr macece kokarin ta bazai wuce nan ba,
Koda ta isu bakin wani k'aton kogi taduba ko ina babu alamar hanya babu dama ta tsallaka wurin domin wurine mai ruwa da kuma manya duwatsa gashi da zurfin tsiya anan taja burki gashi ta galabaita, juyowar da tayi ta hangesu da fitillu sunnufo inda take
wasu kuyangar kara tagani dunk'ule kamar gije haka yarinyar nan ta kutsa aciki tasa hannu tatoshe bakinta tana k'watar numfashi tazare fararen edon nan nata tana kallon su kamar tasake da kuka koda suka k'araso wurin suka nemeta suka rasa, amma ita tana ganin su
Sunjima a wurin suna neman ta, amma wayam babban ne daga cikinsu ya taka hannunta da manya takalminsa batare da yasani ba amma haka ramlat tajure kuma tanajin zafi jikinta ya kwashi rawa harta sake da fitsari da xafin yayi mata yawa takasa hak'uri saita kaimasa zazzafan cizo asaman kafar sa yayi ihu yaciro k'afar yana fad'in kunama tacijesa
*Ganin hakan tafito tanufi kogin da nufin fad'awa da sauri domin babu wata hanya mafi sauk'i a wurinta inba nan ta nuyo ta kalle su saida tak'are musu lallo kana tajuya tanufi kogin da nufin fad'awa ganin hakan honarable ya kar6i bundiga yayi saitin ramlat* _"kitsaya nacee yafad'a cikin tsawa_
*Amma ina yaro baisan mutuwa ba hakan baisa *ramlat* *tatsaya ba kukan harbi kakeji damm bullet yasauka ajikin ramlat tafad'a cikin katon kogi mai cike da manyan duwatsu...!!*
Via OHWπŸ“š
πŸ€πŸ’πŸ€
*RAMLAT"*
_Yar Tsintuwa_
πŸ€πŸ’πŸ€
*_Written BY raheem jEga_*
πŸ’ _RaMlaT_ πŸ’
*11_15*
*_ A K'AUYEN GURMA_*
_Washe gari misalin k'arfe 7:00am Al'adar garin ce sukan fito maza da mata domin zuwa d'ibar ruwa a babban KOGIN da ya ratso tacikin wanan k'auyen nasu mutanen k'auyen sun kasance suna bautar wani abu wanda ba Allah ba Sun kasance tamkar bayi haka ake mulkinsu cikin k'azamtacciyar rayuwa musamman ma 'yaya mata da aka mayar tamkar dabbo acikin garin_
*Al'adunsu kaff irin na musulmi ne Amma idan kazauna acikin su baxaka kirasu da musulmai ba,*
Matashin saurayi ne kyakkyawa dashi durk'ushi abakin kogin ya tara tulunsa da nufin d'ibar ruwa sai alamar jini yagani biye da ruwan hakan yasa ya d'auke tulunsa da sauri yakai duban sa a inda ruwan suke fitowa caraf edonsa yafad'a akan wani abu dake zuwa cikin jajayen kaya haka ya d'ora edon sa akan abinda ke zuwa ko k'iftawa babu kyakkyawar yarinya yagani fara fess da ita cikin rauni wasu sassa najikinta na fitarda jini bak'aramar razana yayi ba alokacin da edonsa yayi tozali da fuskar wannan kyakkyawr yarinya Amma yayi jarumta ya tsamota acikin ruwa ya rungumeta zuwa jikinsa Alokacin tayi ajiyar zuciya batara data k'arayin wani numfashi ba,
_Ganin haka yaciro mayafinda yake kansa ya rufe mata fuska dashi domin yasan irin hatsarinda zaishiga idan Aka kamasa da irin wann kyakkyawar yarinya a hannun sa, baijira komaiba darect gida ya nufa cikin ikon Allah harya isa gida batare da wani yasan abinda yake faruwa ba,_
Gida ne k'arami na itace tamkar na 'yan china wanda dagashi sai ummar sa da kuma qanwarsa humrat suke zaune aciki da shigarsa yajiyeta akan wani gadon kara wanda ko mashinfid'in kirki bashida kana yad'auko ruwa tare da wani farin kyalle ya goge duk jininda yake jikinta yacire kayan da ke jikinta da suka 6ace da jini ananne yaga Alamun harbi ajikinta da sauri ya d'auko Allura tare da wani k'arfe guda 2 masu tsinin gaske yaciro bullet d'inda yake jikinta hka dai yacigaba da bata taimako daga k'arshe ya shafe mata jikinta da magani a inda takeda raunuka harya k'arasa shiryata batare data farka ba, tsaye yayi akanta ya game hannayen sa yana rok'ammata sauk'i a wurin uban gijinsa, Ashe duk wann abin dayake qanwar sa humrat na tsaye tana kallon sa,...!!
*Hawaye sukayo chaaa a edon ta ta fad'a jikinsa tana kuka cike da tausayin wann k'aramar yarinya dake cikin wann yanayi sunjima a haka yana bubbuga bayan ta sannan ya d'ago ta yaja hannuta suka nufi inda ummar su.............))*
_Ya kwashe lbrn duk abinda ya faru yabasu tundaga lokacin da ya tsinto ta har izuwa yanxu, suka tashi suka nufi d'akinda take kwance har Alokacin bata farka ba, tun alokcin da edon umma yayi tozali akan wannan yarinya taji ajikinta cewa zaman wann yarinya atare dasu babbar matsala ce agarsu girgixa kai tayi ta kalle sa canxa fuska tace tace_
*"Ashraf* Ni mahaifiyar kace na umurce ka dakayi gaggawar fitarda wann yarinya acikin gidannan "yakake tunanin rayuwar mu zata kasance idan shugaba murtu yasan da zaman wann yarinya a gidannan? Wane irin hukunci kake zaton abin bauta zayyan ke muna idan yagane cewa muna 6uyar wani mutum batare da mun bayyanar dashi ba,
*wannan yarinya ba jininmu bace abin bauta yatsaneta* kayi gaggawar mayarda ita a inda kad'auko ta abin bauta yatsane ta, Afusace tabaro d'akin yayin da Ashraf ya fashe da kuka idan ya kalli yarinyar sai yaji tausayinta ya ratsashi yaji baya iya rabuwa da ita,
_Yaje ya samu mahaifiyar sa, ya durk'usa ya kama k'afarta "ummata ina rok'onki daki bari muzauna da wann yarinya atare damu kidubi irin raunukan da suke jikinta, a wane irin hali tafito bakisani ba, yazakiji idan daya daga cikin 'yayanki suka tsinci kansa acikin irin wannan hali, abin bauta zayyi alfahari damu idan muka ceto rayuwar wannan yarinya....!!_
*Ninajiya ajikina wann yarinya Akwai baiwarda ketare da ita, yak'arasa maganr cikin kuka wani irin tausayinsa yakamata ta dafa kansa tace "Shikenan d'ana na aminta kaci gaba da kulata Abin bauta ya albarka ceka wani irin dad'i ya ziyarci zuciyarsa murmushi yayi ya rungumeta yace "Jinjina ga abin bauta.....))*
*BAYAN KWANA BIYU*
Zaune suke a cikin wani Lambu mai sanyi da kuma k'amshin gaske ga wasu manya jarumai a zagaye dasu dagani kasan su 'yayan gidan sarauta ne shiru kakeji na tsawon Lokaci batare da kowa yayi magana acikinsu ba, Alamun suna cikin zafin zuciya bud'e bakinta tace
_"Ashraf a yanxu kacanxa narasa mei yake damunka nea hatta da wurin bauta kadaina zuwa kuma a haka kake zaton Zamu samu Albarkar aure a wurinsa, "waime yake damunka nea Ashraf? tak'arasa maganr cikin b'acin rai,_
Ya d'ago kai ya kalleta yace "bahaka bane *HAYBA* na rantse da abin bauta ina sonki kuma zan aure ki Amma a yanxu Akwai abinda yake gabana wanda nikaina banada Lokacin kaina balle nawasu "Amma....^ kafin yak'arasa yaji muryar qanwarsa Humrat..!!
"Ya Ashraf kazo da sauri *'Yar Tsintuwa* ta farka wani zare edo yayi ta farka ya maimaita abakinsa cike da farin ciki ya mik'e da sauri yace
"I'm sorry *HAYBA* pls zanje gida saimun sake had'uwa baijira tayi magana ba, ya zarce da guda yanufi gida cike da mamaki tace "Yar tsintuwa Waye ita wlh Ashraf baka isaba ta fixgi takobin da ke hannun dai daga cikin Fadawanta ta tabi bayan *Ashraf* A fusace....!!
Via OHWπŸ“±πŸ“š
πŸ€πŸ’πŸ€
*RAMLAT"*
_Yar Tsintuwa_
πŸ€πŸ’πŸ€
*_Written BY raheem jEgaπŸ“š_*
πŸ’ _RaMlaT_ πŸ’
*21_26*
_Tsaye take tana kallon k'ofar gidan cike da tausayi a lokacin tunanin iyayenta ya fad'o mata arai tatuna irin yanda take samun gata da cikakkakiyar kulawa a wurin Abban ta fashewa da kuka saida tayi mai isarta edo sun mata jajir gatq a tsaye tana kallon gdn Amma mahaifiyar Ashraf tayimata iyaka dashi, tajima a tsaye canta canxa fuska kawai ta kutsa kai takoma Acikin gidan taje inda umma taja birki tagame hannayen ta 2 tanaba ta hkr kamar yanda taga sunayi idan suna bautar su,_
A fusace umma tad'aga hannu sama danufin wanketa da mari caraf humrat ta rik'e mata hannu tace
"haba umma idan kikayi haka kinzubar da darajar ki awurin abin bauta, yau kusan kwana 10 da zuwan 'yar tsintuwa a gidannan amma batataba cutar muba hasalima sai soyayya ke k'ara shiga tsakanin mu da ita meyasa zaki koreta umma? Mei tayi mikine kike mata wann tsana to wlh idan harkikace dole saita bar gidan nan tonima zanbita domin nasan nata iyayen baza su hanani zama atare da suba,
_umma ta fixgi hannun ta daga hannun 'yarta humrat tayi kyaci tawuce abinta, wani dad'i Ashraf yaji rungume 'yar tsintuwa yayi yana ta shafar kanta itama tasa hannu tana share hawayen da ke zuba a edonsa kasan cewar lokacin darene ya d'auketa zuwa d'akinta ya shimfid'eta kafin yatafi yajima yana mata tambayoyi Amma har a lokacin bata bud"e baki tayimai magaba ba, saidai ta girgixa kai Alamar eh ko aa, tashi yayi danufin tafiyar sa tabata rai kamar zatayi kuka hakan yasa yaje yad'auko kayan barcinsa, yaxo suka kwanta tare,_
Misalin karfe 2:30pm na dare 'Yar tsintuwa ta farka a hankali ta zame jiki taje ta bud'e kofar d'akin tafita batare da Ashraf ya farka ba, sannan ta rufe k'ofar a hankali take tako d'ai bayan daya harta sace jiki tafita daga gidan batare da daya daga cikin su ya farka ba, cikin tsalelen dare gashi ba wuta banda kukan karnu ka ba abinda kakeji haka takama hanya saikace Aljana tanufi gidan shugaba, murtu Acikin tsalelen dare Abin mamaki mei ya fidda ta Acikin wannan dare kuma mei zatajeyi a gidan shugaba, murtu a wannan lokaci sarkin da kowa yake matuk'ar tsoron sa,
Harta isa gidan sarautar bataci karo da kowa akan hanya ba, Amma zuwanta kofar gidan ta taradda k'attinan jarumai sai zagayen gidan suke wasu da takubba wad'ansu da bindigogi a hannayen su wasu kuma a saman gidan sunyi tsaye kamar guma ka,
Babu tsoro kokad'an ajikinta tawuce kai tsaye bata tsaya ko inaba sai bakin gate d'inshiga Acikin wann babban gida na sarauta wani sai a lokacin wani k'aton mutun bak'i kakkaura a k'alla zaikai girman mutum 3 tundaga nesa ya hango ta cikin jajayen kaya bak'aramar razana yayiba, da sauri ya zaro takobinsa ya haskota da wata irin touch light mai haske yace.....
"Tsaya daga nan ke wacece mutum ko Aljan? tayi kamar batajishi ba, sai k'ara yowa cikinsa take jikinsa ya da'au rawa ya kamaja da baya abin dariya yabata ganin haka hankalin sa yak'ara tashi yayi ihu ya bud'e gate d'in da sauri nan take kaga fadawa sunfito d'auke da makamai azaton su farmaki nea aka kawo musu
Ganin fitowar su A saman dawakai tad'anji tsoro tabuya a k'arkashin wani tebur harsuka gama fitowa fitowa tayi da gudu tanufi cikin gidan batare da wani yaga wuce warta ba, tafad'a cikin wann gida na sarauta duk wann abin da'akeyi haryan xu kowa yakasa fahimtar abinda ke faruwa,
Wani d'aki tanufa wanda aka k'awatashi da kayan ado irin na sarauta ta kutsa kai aciki caraf edon ta suka fad'a kansa tayi ajiyar zuciya tabbas shine wadda tagani a gidan su Ashraf kuma shine jagaron wad'anda suka kashe mata iyaye,
kwance yake saman wani Lafiyayyen gado sai kwasar barcinsa, yakeyi tayi murmushi ta mayarda k'ofar d'akin tarufe ta janyo wata igiya dake kasan gadon tad'aure masa kafafu kana ta kama hannayen sa, ta d'aure batare da ya farka ba tacire k'yallen da ke rataye a kafad'ar ta ta rufe masa baki ananne ya farka Azuci take fad'an "yau kwanan ka yak'are kaima zaka d'andani Azabar mutuwa kamar yanda kuka rabani da iyayena, firgigit yatashi kamar wanda aka cema tashi za'akashe ka ya k'ureta da kallo tabbas yatuna wann fuskar da karfi yayi yunk'urin tashi yaji jikinsa a d'aure dariya tayi tafidda wata sharb'ebiyar wuk'a ajikinta duk inda tasamu soka masa takeyi fuskarta duk jinine hakama hannayen ta bata bariba saida taga yadaina numfashi,
_A wurin Ashraf kuwa mummunan mafarkine yayi ankashe 'yar tsintuwa firgigit ya farka ya lalubo ta, ko sama ko k'asa babu yar tsintuwa yashiga kiran sunanta yana dube dube hankalin sa, yatashi yatada humrat ya tambaye ta "ina 'Yar tsintuwa ? Tace niban ganta ba, "ina tashigane. suka fito waje suna kiran sunanta Amma shiru kakeji nan hankalin su yayi matuk'ar tashi yakama hanya baimasan inda zashiba, sai faman kiran sunanta yake shikad'ai Acikin dare.......))_
Nan humrat ta fashe da kuka tace "ya Ashraf dan Allah kadawo kada Azzalumannan sukama ka, nasan bazasu barka da raiba, Ashraf baima san tanayi ba saik'ara kutsawa yakeyi cikin duhu
*Sunci bid'a harsun gaji suka dawo gida suka jawo kofa suka rufe suna juyowa kwatsam suka ganta a tsaye jikinta duk jinine sai murmushi tana d'aga musu hannu. tana kallon su gabaki d'aya tsoro ya kamasu cikin rawar murya Ashraf yace 'Yar tsintuwa Nine Ashraf kece kuwa....??*
Via OHWπŸ“±πŸ“š
πŸ€πŸ’πŸ€
*RAMLAT*
_Yar Tsintuwa_
πŸ€πŸ’πŸ€
*_Written BY raheem jEgaπŸ“š_*
_πŸ’RaMlaTπŸ’_
*26_30*
_Ta girgixa masa kai k'arasawa yayi kusa da ita cikin tsoro ya d'ora hannun sa, a kafad'arta ya zame rigarda ke jikinta nan yaga tambo ajikinta hakan ya tabbatar mai dacewa itace Amma mei ya fidda ita acikin wannan dare kuma a ina tagamu da wannan jinin dake jikinta, wann itace tambayrda yakema kansa. Humrat tadafa ta tace "k'anwata daga ina kike ? Kuma waye yabata miki jiki da jini haka? tasoke kai k'asa batace da ita k'alaba, durk'usawa humrat tayi ta rik'e hannuwanta 2 tace "Nasan keba kurma bace SBD kinajin abinda muke fad'a dan Allah kigaya muna wacece ke.....?_
Nan tasake da hawaye ta fara kuka ta kw'ace hannunta taje inda Ashraf ta rungume sa, tana kuka zame jikinsa yayi ya zaunar da ita, ya dubeta yace "Yar tsintuwa ta Nasan bazaki b'oyemin komaiba kifad'amin kinkashe wanine a cikin darennan ? Ta girgixa masa Alamar Aa....yayi ajiyar zuciya yace to "A ina kika samu wann jinin tanuna masa k'ofar fita da yatsa Amma shi haryanxu baigane abinda take nufiba, yace Ni banga kowa ba, k'anwata "kinyi Alqawarin da safe zaki kaini inda kikaje a cikin wann dare ta d'aga kai Alamar ehh....!!
*Baik'ara tambyr ta komaiba humrat tajata taje da ita tayi mata wanka ta canxa mata kaya tajata zuwa dakinta suka kwana tare har garin Allah yawaye*
Yau takama Ranar Laraba, ranace babba agaresu maza da mata kowa yana fitowa zuwa wurin bauta kamar yanda suka saba kuma ranace da kowa yakeyin abinda yakeso batare da takuraba, wad'ansu susha kayan maye kuma suna zuwa wurin wasanni a gidan SARKI MURTu a ranar cea duk wani Namije yanada damar yayi Amfani da duk wata mace da yakeso dake cikin gariN GURMA,
_A wurin su Ashraf kuwa suma sunyi Nasu shiri cikin fararen kaya Massamn Ashraf yaci kwalliya irin yanda yasaba, doguwar riga da wando white yad'auko rufaffen takalminsa suma farare yasaka kana yad'auko wani farin mayafi yarataya a kafad'arsa ga sumar kansa ta kwanta luf_luf _haka ma a wurin umma da humrat nd 'Yar tsintuwa duk cikin fararen kaya suke k'amshin turare kawai kakeji suka fito suka
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4

Please Login or Register in order to submit comment