Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[1/13, 9:47 PM] 💜: *'KWARYA TABI 'KWARYA*
*NA*
_BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com*


*MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊️*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
_________________________
*Littafin na kudi ne....!*
_#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_
_Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_



*SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊🏻)
1&2
Lokacin dana shiga masarautar sai da nasha jinin jikina dan ganin yanda tarin bayin dake karkashin masarautar suka nutsu gabas yamma kudu Arewa dukkaninsu suna tsaye sunja layi mazansu da matansu da 'ya'yansu suna sanye da uniform wanda ke dauke da tambarin masarautar gaba da baya, kowanne kansa a sunkuye 'kwakkwaran motsi babu wanda yake iya yi.......Can wata rumfa na hango iyayen masarautar zaune kan kujeru na alfarma sun jeru su uku wanda yake tsakiyarsu shine nafi tunanin shine shugaban masarautar wato (Sarki Maimartaba) abinda yasa nake tunanin shine Sarkin sabida ganin yanda wasu mutane gudu biyu masu dauke da jajayen kaya suke tsaye a gefe da gefensa suna masa firfita da wani irin mafici mai baza gwanin birgewa........Shiru masarautar babu hayaniyar mutane busar algaita gami da sarewa ne kawai take tashi a gurin.
Cikin nutsuwa wasu lafiyayyun motaci guda guda su shigo cikin masarautar, Maimartaba ya fara yun'kurin miqewa tsaye fuskarsa dauke da wani qayattacan mirmushi, Ganin zai miqe yasa fadawan dake gurfane a gabansa suka miqe da sauri suna baza manya manyan rigunan jikinsu......Waziri Galadima Ciroma suma suka miqe tsaye sabida ganin maimartabar ya miqe, dan ganin iyayen masarautar sun miqe ya sanya dukkanin wa'inda suke zaune suma suka miqe tsaye domin girmamawa.......masu busar sarewar suka rud'e tare da sanja salo....gabadayansu suka nufi inda motocin nan sukayi parking suna ta aikin busa algaita gami da sarewa, Wani bafadane yayi saurin bude motar ya fito da sauri ya bud'e daya hannun ya matsa gefe guda tare da dun'kule hannunsa alamun jinjina ga wanda ke cikin motar "Barkan ka da dawowa masarautar gado Aliyu Haidar namijin zaki Sarki mai jiran gado fari kake mai farar aniya Ali baka fito ba sai da ka shirya hakika masarauta da duk wanda ke karkashinta yana murna da dawowarka lafiya." Wannan kirarin daga bakin bafadan yake fitowa....shuru gurin yayi na minti biyar kafin ya zuro qafarsa d'aya kafar dake dauke da takalmin sarautar na tsirawa ido cikin socond guda na gane cewar mamalakin kafar mugun d'an izzah! ne a qalla ya kai minti biyar da zuro kafa daya ya gagara fito da dayar ko me yake a cikin motar oho! gabadaya idanun kowa a gurin yake mutane da dama sun 'kagauta suyi tozali dashi mussaman na qasa wa'inda basu sanshi ba sai dai labarin sa, cikinsu har da Sumayya wacce ta kasance d'aya daga cikin 'ya'yan bayin masarautar itama idonta kur! a gurin tana jira ya fito daga motar ta ganshi tun kafin ya fito ta gazgata abinda jama'ar masarautar ke fada a kansa wato shi d'in mugun d'an izzah! ne mugun d'an d'agawa ne! mugun d'an gadara ne! Mugun muskili ne wanda babu wanda yake gane al'kibularsa sai mutum d'aya itace mamanshi amma hatta da mahaifinsa maimartaba baya gane inda ya dosa.

Cikin nutsuwa ya rankwafo ya fito daga cikin motar tare da zura bak'in gilashin dake hannunsa dan saboda gujewa had'a ido da jama'ar da sukayi masa caaa! da idanunsu ya tsani kallo a rayuwarsa shiyasa sam baya sakarwa mutane fuska mussaman mata dan ya fahimci kamar kallo a jininsu yake be sai ba ko shi suka raina suke k'ure shi da kallon 'kurrula.
Wasu matasan samari ne wa'inda sukayi sa'anni dashi naga sun fito daga d'aya motar su biyu suna sanye da kayan sarauta a jikinsu amma shi uban gayyar suit ne a jikinsa Shatima da Moddibo sune suka tilasta masa d'aura alkyabba a jikinsa saboda da ita sukaje airport din suka kuma sheda masa cewar maimartaba ne yace lallai su bashi yasa ya shigo da ita cikin masarautar.
Da sauri naga wasu bayi su hudu sun shimfid'a wani farin abu mai tsayi a dadai kafafunsa sai da abin ya dangane har inda iyayen masarautar suke Cikin nutsuwa yasa kafarsa akan abin ya fara tafiya.
Tafiya yake abokansa kuma 'yan uwansa na gefe da gefensa, yayin da masu busa algaitu suka cigaba da aikinsu tare da rufa musu baya....Lokacin masu camera man vedio camera suka fara aikinsu suma 'yan Jarida ba'a barsu a baya ba aikin daukar hotonsa kawai sukeyi shi kuma yana d'agawa jama'ar dake gefe da gefan sa hannu ammafa babu walwala ko ta kwabo a fuskarsa wanda ya kamata ace ya saki fuskarsa ya tar'bi dubbanin mutanan dake murnar dawowarsa gida ko a jikinsa daga karshe ma daya ga yana damun kansa sauke hannunsa yayi sai kawai ya sunkuyar da kansa ya cigaba da tafiya babu um! babu umum!! Sukuwa jama'ar masarautar sai kirari suke masa gami dayi masa fatan alkairi a rayuwarsa amma gogan bai d'ago kansa ba ballantana yasan sunayi.........."Wani irin takaici ne ya rufe ni naja tsaki tare da kauda kaina daga kallonsa tabbas na gazagata maganganun da jama'a sukeyi a kansa na rashin kirkinsa yanzu ina laifi ga wanda ke murna da zuwanka gami dayi maka addua idan da mutunci yaci ace ya d'ago kansa ya nuna jin dadinsa amma saboda tsabar izzah! ya gagara kallon inuwar inda mutanan ke tsaitsaye.
Silalewa nayi daga cikin iyayena na kama hanya domin tafiya can shashenmu na bayi, zuwa zanyi na huta dan bazan iya jurar tsayuwa ba rana sai duka na take gashi wanda akeyi dominsa baya gani, mahaifina kawai nake tausayawa dan ba wata cikakkiyar lafiya gareshi ba amma saboda tsabar bin dokar masarauta yasa ya lalla'ba ya fito ya tsaya a matsayinsa..............
*BINTA UMAR ABBALE*

*Kuyi sharing👏🏻*
[1/13, 9:47 PM] 💜: *'KWARYA TABI 'KWARYA*
*NA*
_BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com*


*MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊️*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
_________________________
*Littafin na kudi ne....!*
_#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_
_Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_



*SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa Dashan Allah✊🏻)
5&6
Bayan mun koma gurin tsayuwar mu mun nutsu sai maimartaba ya umarci yaron nasa daya fito ya nunawa jama'a farin cikinsa na dawowarsa masarauta lafiya....A lokacin idanun jamaa yayi caaa! a kansa kowa kokarinsa yayi tozali dashi, ni dai sunkuyar da kaina qasa nayi saboda jin yanda gabana yake faduwa haka kurrum naji bana bukatar kallonsa ba dan komai ba sai dan mugun halinsa na rashin ganin darajar mutane........Wani bafade ne yay gaggawar gyara masa abin magana ya saita masa daidai bakinsa, kamar wanda akayi wa dole yay gyara sai da yaja lokaci tukkuna cikin rashin walwala a fuskarsa da maganarsa yace."Alhamdullilah Allah kaine abin godiya. hakika nayi farin ciki mutuka daga dawo dani gida cikin koshin lafiya gami da tarin nasarori masu yawa." shiru yayi tare da sunkuyar da kansa qasa. Jin yayi shiru yasa nayi saurin dago kaina ina kallon gurin da yake, gani nayi kansa a sunkuye yana kallon 'kasan gurun tamkar me neman wani abu......Tsaki naja a cikin zuciyata nace"Wannan anyi d'an wulaqanci ya sani sarai jama'a shi suke sauraro amma ya fara magana yayi shiru, kaina na d'auke ina jin takaicin abinda yake......Gyaran murya ya kuma yi kafin ya cigaba da magana..."Sannan kuma nayi farin cikin samun iyayena da 'yan uwana da dukkanin wanda ke k'ark'ashin masarautar nan lafiya hakika naji dadi sosai da ganin yanda kuka fito 'ya'yanku da jikokin ku kuka nuna farin cikin ku dangane da dawowa ta gida Nagode sosai inayi muku fatan alkairi." yana k'are maganarsa ya janye bakinsa daga gurin abin maganar can kusa da Waziri ya koma ya tsaya har yanzu babu fara'a a fuskarsa.
Hayaniya da kace kace ne ya cika gurin, Wani bafade yayi tsawa tare da umartar kowa yay shuru kafin minti biyu gurin yayi tsit! Maimartaba ya miqe a nutse ya karasa gurin da abin magana yake, kafin ya fara magana sai da ya d'aga hannuwan sa sama alamar gaisuwa ga tarin jama'ar dake gurin.....Gurin ya sake rikicewa da hayaniya kowa sai fadin albarkacin bakinsa yake akan maimartaba. Da kyar aka samu sukayi shuru suka bar maimartabar yayi jawabi gami da miqa godiyarsa ga Allah ya kuma miqa godiyarsa ga tarin manyan mutanan da suka samu hallatar gurin suma bayin dake karkashin masarautarsa sai da ya miqa godiyarsa a gurinsu sannan ya koma ya zauna gurin zamansa, Baba Waziri yazo yay nasa jawabin Galadima da Ciroma suma sukayi nasu daidai gwargwado sannan maimartaba ya rufe taron da addua, ya miqe da niyyar shiga cikin gida fadawa ne suka kewaye shi suna ta gyara kintsi dai."!! Gurin ya karad'e da bushebushe gami da tashin muryoyin maro'ka da hayaniyar jama'a, sai da Sarki da muqarrabansa suka shiga gida tukkuna aka samu lafiya, jama'ar gurin suka watse kowa ya nufi 'bangaran da yake a cikin gidan.........Nida iyayena Cikin yanayi na ciwo muka shiga gurin mu, da sauri muka zaunar dashi, Tambaya ta ri'ke kafadarsa ni kuma hankali a tashe naje na d'ebo masa ruwa jiki na kyarma nazo na tallafo kansa ina kokarin bashi ruwan, bakinsa ya bud'e ina sa masa ruwan yana dawowa, lokaci guda zuciyoyinmu suka karye nida mahaifiyata hawaye muka fara, cikin karfin hali gami da kokarin janyo maganar yace."Ku daina kuka bashi ne abinda nake bukata ba."!
Zama nayi kusa dashi na rike hannunsa har yanzu hawaye bai da zubo min ba nace"Baba wai dan Allah me yake damunka kwana biyu ka'ki lafiya kullum cikin rashin kuzari da karfin jiki gashi kuma ka'ki ka bari a kira mai kula da lafiya yazo ya duba ka."
A hankali yace."Sumayya ba wani ciwo mai tsanani bane yake damuna zazza'bi ne mai zafi sai hajijiya gami da rashin kuzari to ni dik a tunani na ko shawara ce shiyasa na mayar da hankalina gurin shan maganinta amma yanzu ina ganin dole kije ki kira d'aya daga cikin masu kula da lafiya yazo ya dubani dan ni kadai nasan abinda nakeji a cikin jikina.
Tambaya hawaye ta share a sanyaye ta kalleni da fadin"Kiji can bangaran masu kula da lafiyar ki kirawo daya daga cikinsu yazo ya dubashi ni kaina jikina yay sanyi da wannan rashin lafiyar tasa a tsaitsaye fa ya kai sati hudu yanayi duk da yana shan maganin shawarar babu sauki kullum jikin rikicewa keyi."
Miqewa nayi da sauri nace "Bari naje can gurinsu na samesu." takalma na zura da saurin gaske na kama hanyar sashen masu kula da lafiyar gabad'aya bana cikin hayyacina ina tsananin kaunar mahaifina shiyasa rashin lafiyarsa ta d'aga min hankali mutuka.

"Sumayya." Sunana naji an kira da sauri na tsaya ina waigen bayana.

babu walwala a fuskarsa ya karaso inda nake tsaye kai tsaye yace."Ina Lawi yake ya bar aikinsa kamata yayi ace kafin mu fita gurin taro ya zubawa dokuna abinci yanda zai ishesu yanzu yanzu na shiga gurin na tarar da gabad'aya babu abinci a gabansu idan fa maimartaba ya samu labarin abinda yake zai fuskanci hukunci."

A marairace nace"Buba dan Allah kayi hakuri kada ka kai 'korafi wallahi babana bashi da lafiya tsayin sati hudu yake ciwo a tsaitsaye dukkanin abinda yake dauriya kawai yake dan Allah ka taimaka masa kana bawa dawakan abincin kafin yaji sauqi.

"Ke! saurara da wannan maganar.'' Nayi saurin kallonsa kwalla na kokarin zobomin, Ya cigaba da cewa''Kowa da kika gani akawai aikinsa a masarautar nan nawa aikin ma yafi nasa wahala tinda ni kwana nake a tsaye ina zirga zirga banga dalilin da zai sanya na d'auki nauyin wani na d'orawa kaina ba, ke aikin me kike da ba zaki d'auki nauyin mahaifinki ba kafin ya samu lafiya.

Hannu nasa na goge hawayen da suka zubo min nace" Shikkenan zanyi kokari ganin na dauki ragamar kula da dawakan kamar yanda babana yake yi amma ka san dai muna zaman karatu ranaku uku a sati ko kuma idan mun zauna tin safe sai yamma muke tashi.
D'aga kafad'a yay yace."Ke zaki tsarawa kanki yanda al'amura zasu tafi ni dai na fad'a miki ku kula da aikin ku kada maimartaba yaji wata magana.

Ajiyar zuciya na sauke mai zafi! nace"Shikkenan Buba nagode sosai insha Allahu zan iyakacin bakin kokarina." Gyda kansa yayi ya bar gurin, nima da sauri na wuce domin nufar inda nayi niyya.

Na jima a tsaye a bakin kofar d'akin nasu ina sallama kafin naji an amsa da fadin"Ko wacece ta shigo.'' Jim nayi ina tunanin shiga dan gabad'ayansu maza ne a ciki ina ganin kamar hakan bai dace ba.

Sallama na sakeyi, naji anyi min tsawa! da fad'in "Wai wacece take sallama ne ki shigo ki fadi uzirinki." Shahada nayi na tura kaina dakin....wasu na kwance kan katifunsu wasu kuma na zazzaune daga su sai gajerun wanduna.
Daga bakin kofa na tsaya nace"Dan Allah d'aya yazo ya duba babana Lawi bashi da lafiya."

Shuru sukayi min kowa ya cigaba da sabgarsa, raina ya 'baci! nace"Magana fa nakeyi muku kuna jina." 'Dantala ya zaburo min da hayaniya yace."Ke! babu wanda zai katse abinda yake a cikinmu yaje ya duba babanki idan kina so ayi miki abinda kike so ki shigo ciki muna bukatarki."

Cike da mamaki nake kallonsu nace"aikin ku ne fa mai zai sanya kuce sai nayi muku wani abu sannan zakuyi to ni ba 'yar iska bace idan kun saba latsa 'yan matan dake masarautar to ni ba' irinsu bace kuma wallahi idan bakuyi wasa ba yanzu zanje fadar sarki na sheda masa abinda kuke aikatawa..........A fusace! naga ya miqe yayo kaina zai mareni na kauce da sauri ina kare fuskata....wanda yake da sauqin halin cikinsu ne ya miqe tare da zira rigarsa ya kalleni da fadin" Shige muje na duba jikin mahaifin naki." Da sauri na fita daga dakin gabana sai faduwa yake......Tafiya nake zugwi zugwi ina mamakin al'amarin, kawai naji ana ta'ba min mazaunai! Da sauri na juyo ina kallonsa, murmushi yayi ya sosa kansa ido jawur yace."A gaskiya Sumayya Allah yayi miki baiwa mai mutukar daukar hankali, kina da duk abinda d'a namiji ke bukata a jikin mace kirjinki a cike yake dam-dam uwa uba mazaunai masu masifar rikimin lissafi wallahi tunda kika shiga dakinmu sha'awata ta tashi dan Allah ki bani damar mallakar wannan jikin naki wanda yake kokarin fitar dani hayyacina.

Kallonsa kawai nake wani 'katoton abu ya tokare min a ma'koshi nace"Yanzu Usman ashe kaima halinku d'aya dasu Dantala a zahiri inayi maka kallon salihi ashe kaima baka da d'abi'a mai kyau Usuman dan Allah meye amfanin lalata da kukeyi da 'ya'yan mutane idan fa masarauta ta samu labarin abinda kukeyi ba zakuji dad'i ba.

A sanyaye ya sosa kansa cikin jin kunya yace."Sumayya dan Allah kiyi hakuri wallahi ni ban fiya haikewa 'yan matan masarautar nan ba su Dantala ne masuyi kema yanzu hankalina ne ya tashi sosai shiyasa na gaza hakuri na kai hannuna mazaunanki amma kiyi hakuri dan Allah kada naji maganar a bakin kowa.
Cikin takaici na girgiza kaina tare da juyawa na cigaba da tafiya raina a masifar 'kuntacce.

To koda Usuman ya duba babana nan ya gano cewa hawan jini ne ke damunsa hankalinmu ya tashi nida tambaya muka dinga kuka dan mun riga mun san ciwon hawan jini babban ciwo ne gani muke kamar mun kusa muyi bankwana dashi shiyasa gabadaya hankalinmu ya tashi....Usuman ganin duk muna hawaye yasa ya rarrashe mu tare da bamu shawarwarin yanda zamu kula dashi da lafiyarsa yace "Insha Allahu mutukar aka bi dokar da ake bukata masu dauke lalurar suka bi to zai samu lafiya, Ya miqe tare da fad'in " Zaije yanzu ya kawo masa magungunan da zasu taimaka masa...godiya mukayi masa muna zubar da hawayen tausayi......
*BINTA UMAR ABBALE*
[1/13, 9:47 PM] 💜: *'KWARYA TABI 'KWARYA*
*NA*
_BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com*


*MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊️*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
_________________________
*Littafin na kudi ne....!*
_#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_
_Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_



*SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊🏻)
3&4
Yarima Aliyu a nutse ya 'karasa rumfar da iyayen nasa suke zazzaune ya cire rufaffun takalmansa a nutse yaje ya gurfana a gabansu tare da 'kaskantar da kansa sosai yace"Allah shi taimake ka ina fatan na same ku lafiya."? Maimartaba ya d'ora hannunsa a saman kansa cikin farin ciki yace."Lafiya lau alhamdullilahi Aliyu ina fatan ka dawo gida cike da samun nasarorin da muke bukata." Ali! Yayi murmushi tare da sake sunkuyar da kanshi qasa, Waziri ne ya karaso gurin a nutse yasa hannunsa ya d'agoshi ya miqe tsaye! wani qayataccen murmushi yayi wanda yay masifar yi masa kyau tabbas da yasan dariya nayi masa kyau to da ya mayar da hankali gurin yi.......Rungume 'Kanin mahaifin nasa yay a daidai kunnansa ya furta "Baba Waziri ina fatan duk na same ku lafiya." Waziri cike da walwala da farin ciki yace."Lafiya lau ka same mu Aliyu haki'ka muna farin cikin dawowarka masarauta lafiya." Idanunsa dake lumshe ya bud'e! still da ragowar murmushin a fuskarsa yana kokarin yin magana suka hada ido da Galadima shida Ciroma suna tsaitsaye a inda suke fuskarsu babu wata cikakkiyar walwala.

Gyara fuskarsa yayi dan saboda yasan halinsu da rainin hankali suna iya tsinkashi a gaban mutane a kullum burinsu suga sun 'bata masa rai tun yana yaro suke nuna masa qiyayya tamkar wani abokin gabarsu.

Inda suke ya nufa ya d'an risina cikin nutsuwa yace."Ina fatan na same ku lafiya."? Galadima ya gyara yanayin sa yana kokarin danne 'bacin ran dake ransa yace."Lafiya lau Alhamdullilahi ina fatan ka dawo gida tare da nasara."
"Alhamdulillahi." Shine a binda ya fada tare da yin kasa da kansa gami da goya hannuwansa a baya................Daf da zan shiga kofar mu d'aya daga cikin matsu tsaron 'kofa ya dakatar dani, tsayuwa nayi ina kallonsa har ya qaraso inda nake, Yace."Waye ya baki ikon barin gurin taro bayan ba'a tashi ba." Kai tsaye nace"Kaina ne yake ciwo sannan rana na takura min shiyasa na dawo gida.
Shar'be'biyar bulalar hannunsa ya labta min a qafafuna yace."Kina a matsayin baiwa maqasqanciya kike wannan maganar, baki san abinda kikayi ya sa'bawa dokokin masarauta ba to bari kiji har iyayenki sai an hukunta sabida abinda kika janyo musu." Wani irin gumi! nake ina kallonsa bakina sai rawa yake yi ga wani irin zafi da kafafuna sukeyi min.
Bulalar ya sake d'agawa zai shaud'a min nayi saurin riqe hannunsa hawaye suka 'kwace min nace"Bafa ni da lafiya na fad'a maka kaina ke ciwo sannan ga rana a gurin laifi ne dan na dawo gida na huta."!

Finkice bulalar yayi daga hannuna ya daga da karfin gaske ya shaud'a min a bayana ban san sanda na k'wallara k'ara ba, wannan 'karar da Sumayya tayi har can gurin taron babu wanda beji ba.
Maimartaba ya tashi fadawa da sauri yace suje su duba cikin gidan..........."Wuce mu koma gurin taro ki fuskanci hukunci ko su waye iyayenki a cikin gidan nan kin janyo musu fushin masarauta.'' Abinda yake fada min kenan tare da inginza ni wai lallai sai mun koma gurin taron, ni kuma tsabar taurin kaina sai turjiyewa na keyi hawaye na zuraro min.
Fadawan da Sarki ya turo suka karaso gurin suna tambayar abinda ke faruwa, a take Sarkin kofa yayi musu bayani, Naga babban cikinsu ya zare min ido hade da buga min razananniyar tsawa! ya bani umarnin shigewa mu tafi. Turjewa nayi ina kallonsa da busassun idanuna a fusace! ya tattare babbar rigarsa ya d'auki ni ya sa'ba a kafad'arsa kai tsaye gurin taron ya nufa dani ina kuka da dukansa da zille zille haka ya dinga ratsa mutane dani bai dure ni a 'ko'ina ba sai gaban maimartaba. gurfana nayi nayi qasa da kaina hawaye na karakaina a fuskata.......Lawi da matarsa hankalinsu ya tashi dan ganin 'yarsu a gaban maimartaba da alama ta janyo musu fushin masarauta sai duk jikinsu yay sanyi cikin kaskantar da kai suka sunkuyar da kansu gabansu na faduwa, Gabad'aya gurin shuru yay kowa na jiran sarki yayi magana.....wanda har lokacin Yarima Ali! na tsaye goye da hannu kamar wani soja! Maimartaba ya kalli bafaden yana bukatar karin bayani.
Da sauri ya sunkuyar da kansa kasa yace."Ranka ya dade wannan yarinyar can cikin gida muka sameta tare da d'aya daga cikin masu tsaron kofar bangaran bayi suna jayayya da juna kan umarnin daka bayar." Mai tsaron kofa yace."Allah ya taimake ka na ganta zata shiga gida sai na dakatar da ita tare da tambayarta wanda ya bata izinin baro gurin taro bayan ba'a tashi ba shine take fadin maganar da bata cancanta ta fito daga bakinta ba a matsayinta na makaskanciya bai kamata ta nuna gazarwata gurin jimirin tsayuwa a cikin rana domin tar'bar Yarima Ali ba, yarinyar tayi min bayani cewar ita ba zata iya tsayuwa a cikin rana ba."
Gurin yay tsit kowa na mamakin furucin da 'yar gidan Lawi bawa! tayi shin da me take taqama dashi ko kuma dame tafi sauran
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment