Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

MALIKUSSAIFI DAN ZIYAZZANUN
littafi na daya 1
part 1
post by Shuraih 99%

Godiya ta tabbata ga Allah madaukakin Sarki da manzon sa Annabinmu Muhammad tsira da amincin Allah su kara tabbata a gareshi,

wanda ya bamu iko ga jama'a domin su samu abin debe kewa da nishadantarwa yayin
karantashi.

Shi wannan littafin, fassarace daga harshen larabci zuwa na hausa domin jama'a Su amfaneshi.

Shi wannan littafi mafi yawancin mutanen yanzu basu sanshi ba, domin Malamai ne ada suke karanta wa jama' a shi idan sunajin nishadi.

Zakuji cewa Wannan littafin ya kunshi labaran soyayyaya, nishadi da kuma abubuwa iri daban-daban, wadanda suka kunshi sha'anin
bokanci da tsafe-tsafe wanda mutanen wancann lokaci suka kware a kai.

Za kuma aji yadda rayuwa take kasancewa ga
wannan sarki, tun tasowar sa da kuma girmansa, kama izuwa lokacin daya zama kasaitaccen Sarki da kuma mutuwar sa.

Kuma za aji cewa wannan littafin ya shafi bangaren addini da kuma ma'amaloli na rayuwar alumma. halakata. MAALIKUS-SAIF
Bin ZIYAZINUN a karan kansa an taba samu rayuwa irin tasa.

ldan muka duba tarihin masarautar BORNO zamu samu cewa daya daga cikin wadanda suka taba yin sarauta a wannan masarauta wadanda akeyiwa lakabi da Saifawa Dinas (Wato
Daular Saifawa), tayi kimanin Shekara dubu kafin ta gushe,

wannan zuria ta saifawa sun samo sunansu ne daga wannan babban Sarki kuma kamar yadda tarihi ya nuna shine ya kafata.

Don haka labari da aka bayar akan wannan Sarki SAIF yana iya zama kirkirerren labari ko
kuma shi Sarkin ya zamto antaba samunsa A hakikama yankin da wannan sarkin ya zauna wato HAMRA'U YAMEN ko YAMEN wato kamar yadda

wannan littafin tarihin ya nuna. A wani zamani mai tsawo daya wuce, zamanin Annabi Nuhu {Alaihissasatu wassalam yayi
wa 'ya'yansa addu'ar Allah yasa daya daga cikin 'ya'yansa a samun wanda zai mallaki duniya ya kuma yada addinin Allah.

Cikin ikon Allah sai wannan addu'a ta sa ta fada akan babban dansa SAMU, wanda shi SAMU a wannan lokaci zuriyar sa farare
ne {larabawa), shikuma karamin dansa HAMU zuriyar sa bakake ne.

Bayan Sun bar wajen Mahaifinsu, sai SAMU ya doshi gabashin duniya,yayin dashi kuma HAMU doshi yammacin duniya.

Bayan wani lokaci mai tsawo, sai akayi wani Sarki mai suna ZIYAZINUN shi wannan Sarkiire-iren zuriar SAMU ne, kumaya samu tarihin adduar da Annabi Nuhu {Alaihissasatuwassalam} ya yi wa kakansu na cewa "Allah yasa a irin zuriyarsa a samu wanda zai mulkiduniya, kuma a samu wanda zai yada addinin ibrahimiyya, da yake a wannan lokaci zamanin Annabi Ibrahim ne{Alaihissasatu wassalam}. Sarki ZIYAZINUN ya lashi takobin InAllah ya yarda a kansa wannan addu'ar zata fada, saboda haka ya yi ta yake-yake a gabashin duniya kuma ya murkushe kasashe da dama da yaki, har ya fado yammacin duniya.

Sai da takai hardai tsufa ya riskeshi. Wata rana Sarki ZIYAZINUN ya sauka a wanı guri, sai yaga yanayin wannan waje yana da kyau kuma yana da dadin zama, saboda haka sai yasa aka gina masa birni aka sa masa suna HAMRA'U YAMEN.
Shi wannan birni daya ginaa yana karkashin
masarautar HABASHA ne, wanda a wannan
lokaci ita wannan kasa tana karkashin wani sarki mai suna SAIFURRA' ADU su kuma ire- iren HAMU ne wato su bakake ne.

Sarki SAIFURRA'ADU ya samu labari cewa ga wani farin Sarki can ya sauka a kasar sa harya kafa birni ba tare kuma da izininsa ba. Dan haka sai ya tura yan leken asiri domin su gano masa irin shirin da Sarki ZIYAZINUN yazo dashi.

Suka je suka sanar wa da Sarkin su cewa ai Sarki ZIYAZINUN yazo da runduna ta sadaukai masu tarin yawa, kuma suka fada masa cewa bazai iya yakarsa ba.

Nan da nan Sarki SAIF yasa a ka tara masa bokayen kasar HABASHA domin su ba musulmai bane, taurari suke bauta mawa. Ya Ya

umarci bokayen nan dasu duba masa su gani idan ya yaki wannan Sarki akwai nasara ko
babu. Bokayen nan suka dukufa suka fara bincike kowanne yayi- yayi amman babu nasara, karshe dai suka sanar wada Sarki SAIF ya hakura babu nasara. Sarki ya sallamesu suka watse daga nan kuma Sarki yasa a ka kira masa wasu manyan bokayensa masu Suna SAKARADISA da SAKARAJUNA da Wazirinsa mai suna Waziri BAHARU.

Nan da nan wannan mutane guda uku
suka zo gaban Sarki SAIFI suka zauna. Sarki ya ce **Yana so ne su bashi shawarar yadda zai bullo wa Sarki ZIYAZINUN?".


Da bokayen nan suka ji wannan bukata ta Sarki sai sukace "Tauraruwa ta baka nasara, ai abinda zaka yi shine ka dauki daya daga cikin yardaddun bayin
ka ka bata guba, ka ce kana so ta boyeta a jikinta yadda kowa bazai iya ganinta ba, idan ta boye sai ka turata izuwa Sarki ZIYAZINUN a matsayin kyauta ta karramawa, ita kuma ka umarceta da idan ta tashi bawa Sarki ZIYAZINUN ruwa ko abinci da ta saka masa wannan gubar daya ci ko ya sha, sai ya mutu kaga shiken ba sai mun yakesa ba.

Sarki SAIF yayi murna da wannan shawara daga bakin SAKARAJUNA. Nan da nan yasa a ka kirawo wata kyakykyawar kuyanga wadda
tana daya daga cikin yardaddunsa
KAMRIYYA.

Aka kawo guba mai Suna
ya bata ya ce "Ta boye inda ba wanda zai ganta koda cajeta aka yi". KAMRIYYA ta karbi gubar nan ta cusa a gashin kanta yadda
inba wanda ya sani ba ba yadda za' ayi mutum ya gane. Daganan ya yi mata bayannin ce wa zaiyi Sarki kyautar ZIYAZINUN, idan ya karbeta ta ga suna tare to tasan yadda za tayi domin ta bashi wannan gubar ko dai a abinci ko kuma ruwan sha
yaci ko ya sha.

Ya ce "Idan ta aikata hakan zai 'yantata kuma zai bata dukiya mai tarin yawa,idan kuma ta kasa yin hakan to muddin ta dawo HABASHA to

sai ya halakata". Da KAMRIYYA taji haka sai ta ce "Zata aikata duk abinda Sarki yake so.

Shi kuwa Waziri BAHARU da yake musulmi ne, ya musulunta ne ba tare da sanin Sarki SAIF ba domin da yasan da musuluncinsa daya sa hallakashi, saboda da gudun abinda zai sameshi sai ya boye an musuluncinsa.


Saboda kishin addini, kuma ZIYAZINUN musulmine sai yasan Sarki
hankalinsa ya tashi, kuma yasan

saboda da gudun abinda zai sameshi sai ya boye musuluncinsa. Saboda kishin addini, kuma yasan Sarki ZIYAZINUN musulmine sai hankalinsa ya tashi, kuma yasan lallai Sarki ZIYAZINUN bazai iya gane makircin da aka kulla masa da KAMRIYYA ba.

Dan haka sai ya rubuta wasika zuwa ga Sarki ZIYAZINUN yayi bayanin ce wa "Shine Wazirin
Sarki SAIF, kuma shi Musulmi ne, ya kuma yi masa bayanin duk irin makircin da
aka kulla masa da KAMRIYYA duk ya rubuta a takardar, daya gama shine yayi kiran
wani yardajjen bawansa ya bashi wannan takardar, ya ce "Yayi sauri ya riga yan
aiken Sarki SAIF zuwa wannan birni na HAMRA'U YAMEN ya kai wa Sarki SAIF
wannan takarda ba tare da wani mutumin ya ganshi ba, sannan ya fada masa ce wa
"Idan har ya aikata hakan kuma ya dawo to zai 'yantashi, kuma zai bashi dukiya mai
tarin yawa'".

Waziri ya bashi takarda wannan bawa nasa ya daura sirdi ya sukani doki yabi ta wata barauniyar hanya ya nufi HAMRA'U YAMEN. Cikin dare ba tare da kowa ya ganshi ba...

Bayan kwana uku sai akayi sa'a wannan bawa na Waziri ya riga yan aiken sarki SAIF zuwa Hamrau Yameen.

Da zuwansa ya isa fada gurin Sarki ZIYAZINUN a kai masa iso gurin Sarki, ya fadi yayi gaisuwa yakuma isar da sakon Waziri BAHARU gurin Sarki ZIYAZINUN, yakuma ce wa Sarki ya sallameshi da wuri domin.

kada yan aiken Sarki SAIF suzo su taraddashi anan suyi tunanin wani abu. Nan da nan Sarki
yayi masa kyauta ya sallameshi ya juyo izuwa kasar Habasha.


Bayan kamar sa'a uku saiga yan aiken Sarki SAIF sun iso kasar HAMRA'UU YAMEN. Da zuwansu suma sai suka wuce fada, akayi masu iso gurin Sarki ZIYAZINUN, da isarsu suka fadi gaban Sarki suka gaidashi kuma suka bashi kyautar KAMRIYYA da Sarkisu Sarki SAIF yaba Sarki ZiYAZINUN.

Koda Sarki ZIYAZINUN yaga wannan sako sai ya sake gaskata bayanin da Waziri BAHARU ya fada masa, amman dukda haka sai Sarki ZIYAZINUN ya karbi KAMRIYYA ya nuna kamar baisan makircin da ake shirin kulla masa ba.

Yasa aka bawa yan aikennan masauki suka kwana kashe gari suka kama hanya izuwa kasar HABASHA.


Bayan ansamu kamar wata daya. Wata rana sai Sarki ZIYAZINUN ya kadaita da
kuyangar da aka kawo masa wato KAMRIYYA, a wannan lokaci ya zare takobinsa ya umarceta da ta fito da gubar da aka bata ta bashi in kuma taki to zai halakata, da KAMRIYYA taga zai halakata sai ta ciro gubar daga kanta ya karba, sannan suka kwanta tare a wannan dare dai Sarki ZIYAZINUN bai gushe ba saida kuyanga KAMRIYYA ta samu ciki dashi.

Da Sarki yaga ta samu ciki sai ya kira wani
malamin sa yace ya buga masa kasa yagani, sai wannan Malamin yaga ai wannan ciki
na KAMRIYYA namiji zata haifa kuma shine wanda zai mulki duniya.

Sai ya fada wa Sarki wannan labarin, Sarki yayi murna kwarai. Daga nan sai Sarki ZIYAZINUN ya rinka nunawa KAMRIYYA kauna yana tattalinta.

Lokacin da cikin KAMRIYYA ya cika wata na hudu sai Sarki ZIYAZINUN ya kwanta ciwon ajali, inda yayi wasiyya cewa idan ya nmutu KAMRIYYA ta hau karagar mulkinsa har ta haihu, idan Dan ya girma ta sauka tabashi mulkinsa.

Bayan yan Kwanaki ya cika inda KAMRIYYA taci gaba da mulki kasar HAMRA'U YAMEN. Da aka samu yan kwanaki KAMRIYYA tana kan gadon sarauta sai ta rika dauko mutanen HABASHA dai-dai da dai-dai tana kawosu majalisar kasar HAMRA'U YAMEN tana kuma korar mutanen Sarki ZIYAZINUN suna mutuwa.


Cikin dan kankanin lokaci duk ta kori mutanen Sarki ZIYAZINUN daga majalisa ta
mayesu da sababbi.

Ba dadewa cikin KAMRIYYA yakai wata tara, ta haifi yaro namiji kyakykyawa fari tamkar mahaifinsa.

Tun lokacin da KAMRIYYA ta haihu,
kuma taga ta haifi na miji sai wani abu ya dinga darsuwa a zuciyarta.


Bayan gari ya waye sai KAMRIYYA ta shirya jaririn ta fito dashi fada domin jama'a su ganshi, bayan ta zaunane a bisa karagar mulkinta sai ta ajiye jaririn daga
gefe bisa wata shimfida wadda ba kowanne jariri ake kwantarwa akai ba sai 'ya'yan
manyan Sarakuna.

A wannan lokaci sai jamaar wannan gari suka fara zuwa wajen wannan jariri suna kwasar gaisuwa suna cewa "Yaron kuwa kamarsu daya sak da
ubansa suna cewa munyi mubayi'a."

Bayan sun gama kwasar gaisuwa gaban jaririn
tare da masa adduar Allah ya raya sai kuma su juya kan KAMRIYYA suyi gaisuwa.


Gani cewa tun yanzu, tun ba'aje ko inaba gashi anfara mancewa da ita ta wannan
jaririn akeyi sai kishi ya kamata, anan sai tasan gaba tubeta zasuyi su nada yaron.

MALIKUSSAIFI DAN ZIYAZZANUN
littafi na daya 1
Part 2
post by Shuraih 99%
.
KAMRIYYA ta boye abinda ke damunta a zuci da dauki yaron ta koma cikin gida
jama'a kowa ya watse.

Da isarta gida ta zauna tayi shiru tana tunani, hankalinta yayi
kokoluwar tashi domin tasan lallai idan wannan yaron ya taso ya girma ya samu
wasiyyar uban sa to lallai sai ya tureta daga gadon sarauta ya hau, kuma gashi ita ta
dandana giyar mulki taji da dadi.

Saboda haka ta yanke shawarar kawai ta kasheshi
shiya fi. Ta dauko wuka zata yankashi amman saita fasa, ta sake yunkurawa zata
yankashi sai ta fasa, ana uku data yunkura zata yanakashi sai wata tsohuwar kuyanga
ta shigo dakin koda ganin abinda ke shirin faruwa sai tace kai! Keko mai wannan
jariri yayi maki da har kike yunkurin hallakashi?

Nan KAMRIYYA ta fada wa
wannan tsohuwar dalilinta da tsohuwa taji haka sai ta bata shawarar kada ta yankashi
ta bari sai dare ya tsala su hau dawakai su biyu su sulale ba tare da kowa ya gansu ba
suje can daji su yadashi, kana su ajiye dukiya tare dashi domin duk wanda ya tsincesa
yayi amfani da wannan dukiya wajen rainonsa, domin idan ya taso hannun wani bazai
taba tunanin shi dan Sarki bane balle ma har yayi wani tashin hankalı.


Sarauniya KAMRIYYA ta yarda da wannan shawara ta tsohuwa ta fasa yankashi
ta bari har dare ya raba sannan suka sulale kamar yadda tsohuwa ta fada, sukayita
tafiya, har saida suka fita daga cikin kasar kana suka ajiye jaririn a gindin wata
bishiya, kuma suka ajiye akwatun cike da kudi sannan sukayi komawarsu.


Can cikin dare jariri ya farka ya fara kuka shi kadai a cikin daji, can yanata kuka
sai matar Sarkin fararen aljanu tazo giftawa tana dauke da yarta mai suna AKISA,
wadda a wannan lokacin tana shayar da ita.


Da aljanan nan taga jinjirin nan sai
tausayinsa ya kamata, sai ta tsaya ta daukesa ta bashi nononta yasha ya koshi, daya
koshi sai ya koma bacci, ita kuma ta ajiyeshi ta dauki yarta tayi gaba.


Can da asuba tayi jaririn nan ya sake farkawa ya kama kuka yana cikin kukanne sai
ga wata barewa mai shayarwa tazo wajen, taga jaririn nan sai ta tsugunna ta kara
masa nononta yasha.

Yana cikin Shane kawai sai wani maharbi ya hango barewar
nan. Aiko ya lallabo ya na sanda saboda barewar bata ganshiba, koda ya matso kusa
sai yaga ai barewar nan jariri Dan mutum take bawa nono, sai ya tsaya ya na mamaki
hardai barewar nan ta ganshi ta gudu.


Maharbin nan ya matso kusa da yaron nan ya
tabbatar dan mutum ne, kuma ga wata akwatu kusa da shi, daya bude akwatun yaga
dukiya sai ya maida yarufe, ya dora akwatin a bisa Kai, yakuma dauki jaririn ya
rungumeshi ya na murna ga dukiya ga kuma Yaro sun samu.

Saboda haka ya juya
akalarsa zuwa gida.

Shi wannan mutumin mutumin kasar DUWAR ne, kuma ita wannan masarsuta ta
na karkashin Kasar HABASHA ne.

Da Isar wannan Maharbi gida tundaga waje ya
Fara kwala wa matarshi Kira harya shiga cikin gidan.

Da isarshi ya mika mata yaron,
kana ya sakko da akwatun da yake a kansa, sannan ya kwashe labari kaf! Ya bata.


Yace kinga shikenan daman bamu taba haihuwaba gashi Allah ya bamu d'a, sannan
kuma ga dukiya Allah ya bamu.


Da matar tajihaka sai tace "Haba! Mai gida kaika dubi irin.wannan kyakykyawan
yaron da ganinsa kasan dan sarakuna ne, KO kuma manyan attajirai ta yaya zamu I
ya rikeshi? Kuma kaga shi farine muko duk bakakene ai. Ana gani za ace satoshi
mukayi aje a samu a cikinwani hali, kawai yanzu ka daukeshi kaje ka Kai wa Sarki shi
domin wannan yaro yafi karfin mu.

Da mijin yaji haka sai ya zauna yayi tunani kuma

saiya aminta da shawarar matar tashi. Saboda haka saiya kinkimi akwatunan sannan
ya dauki jaririn ya nufi gidan Sarki. Yana isa bayan yayi gaisuwa ga Sarki ya kwashe
labari Kaf ya labarta wa Sarki.

Sarki ya karbi wannan jaririn daga hannun maharbin nan.
Shidai wannan Sarki sunan sa AFARA'U, kuma ya kasance karamin Sarki ne dake
karkashin babban Sarki SAIF na HABASHA. Sarki AFARA'U daman bai taba
haihuwa ba, sai yayi murna da samun wannan jaririn ya baiwa matarsa mai suna
DAHASHANATU yace ta rikeshi dukda su bakakene shikuma wannan yaron farine
{Balarabe) ne.



Ita kuma can wannan Aljanar da taba jaririn nan nono ya sha, data koma gida, sai
take bawa mijinta labarin cewa "Tagawani jaririn mutum kwance a daji shi kadai, ta
daukeshi ta bashi nononta yasha."

Da mijin yaji wannan labari sai yace "Ai tunda
kika bashi nononki ai ya zama danki sbd haka yi maza kikoma kidaukoshi."

Nan da nan Aljana ta bazama nema. Ta koma kasar DUWAR. Ta duba inda ta bar
jaririn nan amman sam bata ganshi ba, sbd haka saita je wurin Sarki Aljanu na
wannan gari domin shima a karkashi mulkin mijinta yake.

Ta nemi dayabaza dakarun
Aljanu su nemo mata wannan jariri duk inda yake. Nan da nan Aljanu suka bazama
cikin kasar domin gano inda jaririn nan ya shige.

Jim kadan sukazo da labarin cewa ai
yaron yana gidan Sarki AFARA'U. Nan da nan aljanar nan ta juye ta koma izuwa
sutfar mutane, ta iske matar Sarki tana rungume da jariri, tana shiga sai tace nazone
na karbi dana.

Koda DAHANASHATU taji wannan batu sai ta fusata, jin cewa wata
tazo zata rabata da wannan yaro. Na da nan sai tayi kiran wasu bayi ta fada masu
suyita dukan Aljanar nan Harsu fitar da ita.

Da Aljana taji haka sai tayi wani ruri
wannada ya firgita duk wanda yake gidan, takuma fada masu ita ba mutum bace,
saboda haka su bata jaririn nan ko kuma ta halakasu gaba dayansu.


DAHASHANATU taji tsoro sai ta kama kukan bakincikin rabuwa da zatayi dashi.
Nan ta tura aka kira sarki ta bashi labarin abinda yake faru, nan take shima Sarki
ranshi ya baci ya umatci matarsa data mika wa wannan aljanar yaro.


DAHASHANATU ta mika mata yaron cikin bakin ciki. Koda aljana taga irin halin da
suka shiga sai tausayinsu y kamata, tace masu yanzu zan tafi dashi naci gaba da
shayar dashi amman idan ya cika shekara biyu zan dawo maku dashi.

Da gama daukar wannan alkawari, sai wannan aljanar tayi sama da yaron bata zame ko ina ba
sai a fadar mijinta, wato Sarkin fararen Aljanu.


Can kuma a HAMRA'U YAMEN, Sarauniya KAMRIYYA sai ta fada wa jama' arta ai wannan yaro ya mutu. Koda jama' a sukaji haka mafiyawancinsu basu
yarda ba, amman saboda zafin mulkinta sai sukayi shiru domin sun san lallai idan
suka karyata zancenta, to lallai zasu dandana kuransu. Kuma gashi duk mutanentane
a majalisar, wann dalilin ne yasa suka bita a yanda tace.


Shi kuwa jinjirin da aljana ta dauka yayin daya cika shekara biyu a fadar Sarki

AFAYARU, sai aljana ta yayeshi tare da yarta, kuma tanemi izini a gurin mijinta kan
cewa tanason maidashi gun Sarki AFARA"'U. Da Sarki AFAYARU yaji haka sai
yace da ita tabar yaron nan a wajensu, ya cigaba da cewa yaron yana da alamura masu
girma, domin kuwa dan Sarki ne, kuma shi zai kubutar da yarki daga wata masifa a
nan gaba, kuma wannan yaro shine zaiyi yaki duniya baki daya kuma yayi nasara,
saboda wannan girman lamari nasa nake ganin bai kamata mukaishi wajen mutane
yan uwansa ba domin zasu iya cutar dashi.

Koda DASUKATU matar Sarkin aljanu
AFAYARU taji haka sai tayi na' am da wannan magana amman kuma sai ta tuna ai ta
daukarwa Sarki AFARA'U da matarsa alkawari kan cewa zata maido dashi.

Anan sai tace da mijinta eh ta yarda da maganarsa amman itama tana da shawara. Ya
tambayeta yace to fadi shawararki muji.

DASUKATU tace Kaga mu ba mutane bane,
saboda haka halayyarmu data mutane ba iri daya bace zaifi kyau mu mayar dashi
gurin mutane yan uwansa domin ya samu taebiyya irin tasu.

Sarki AFAYARU ya
yarda da wannan shawara ta matarsa, yakuma yi mata izini data mayar da yaro gurin
Sarki AFARA'U da matarsa, amman ta ja masa kunne kada ya yarda wani abu ya
tabasa.

DASUKATU ta dauki yaro ta mayar dashi ga Sarki AFARA'U da matarsa
kamar yadda tayi alkawari kuma ta gargadeshi Kamar yadda mijinta ya fada mata.


Sarki AFARA"U ya karbi yaro ya shiga dashi cikin gida cike da farinciki ya kira
matarsa DAHASHANATU ya mika mata yaron koda ta ganshi sai tayi wuf! ta
karbeshi, ta rungumeahi tana kuka domin farinciki da murna da suka kamata.

Sannan
ya fada mata duk sharuddan da aljana ta fada masa. Anan Sarki da matarsa suka sama
wannan yaro suna WAHASHINFALA.


Bayan an samu kwananki Kamar kwana Arbain da dawo da WAHASHINFALA
wurin Sarki AFARA'U sai matar Sarki ta sami ciki, murna kan murna wurin Sarki
AFARA'U da matarsa DAHASHANATU basai an fada ba, gashi suna murna aljana
ta dawo masu da WAHASHINFALA gakuma DAHASHANATU tana da ciki.

Duk
gari akayita taya Sarki murna. Hakadai lokaci yayita tafiya har lokcin haihuwar
DAHASHANATU yyi tahaifo ya mace aka saka wa yarinyar suna SHAMATU.

Ita
wannan yarinyar farace kuma sai ya zamto Kamarsu daya da WAHASHINFALA.
Wannan lamari ya baiwa Sarki AFARA"U tare da duk sauran mutane mamaki saboda
sudai gasu bakake amman gashi sun haifi farar mace, balarabiya, kuma gashi tayi
kama da wannan yaro WAHASHINFALA, haka dai sukayita manaki.



A lokacin da WAHASHINFALA yakai shekara bakwai, sai ya bukaci yanason ya
fara hawa doki, sarki yasa aka dauko masa wani dan karamin doki, da
WAHASHLFALA yaga wannan dokin sai ya rainashi yace shi bazai hau wannan
karamin dokin ba, shi babba yake so. Sarki yasa aka mayar da wannan dokin aka
kawo masa wani baki ingarman doki mai digo-digon fari a wuyansa da kirjinsa.


WAHASHINFALA yace wannan doki yayi masa, yayi tsalle ya dare kansa yayi
sukuwa a gaban jama'a yana dawowa gabanSarki yana tirjiya.

Daga nan
WAHASHINFALA ya fara koyon yaki da takobi kuma cikin kankanin lokaci ya
kware a harkar fada da takobi yazama kaf yaran dake sa' anninsa bawanda zai iya ja
dashi har manyan ma.

Ganin haka yasa Sarki AFARA'U ya dinga alfahari dashi
kuma ya ware masa masu yimasa hidima.
Wata rana Sarki yana zaune a fadarsa da yan majalisarsa ana fadanci can saiga

bokan Babban Sarki mai suna SAKARAJUNA ya shigo fadar sarki da yan majalisa
suka mike domin girmamawa ga wannan boka saboda sanin matsayinsa a gurin
Babban Sarki wato SAIFURRA'ADU wato shugaban Sarki AFARA'U.

Boka
SAKARAJUNA ya zauna, bayan sun gaisa da sarki ne sai boka SAKARAJUNA
yace masa yazo kasarsa ne ziyara, daga haka akaci gaba da fadanci daga can sai Boka
SAKARAJUNA yaga WAHASHINFALA zaune kusa da Sarki.

Sai Bokan nan ya
tambayi Sarki cikin rada mai ya kawo wannan farin yaron nan, kuma mai yake yi a
cikin kasarka? shin baka da labari cewa irinsu ne zasu mulki duniya kuma su
maidamu bayinasu bayan sun karkashemu.

Nan take Sarki AFARA'U ya fadawa
bokan nan maganganu masu sanyaya zuciyar Boka SAKARAJUNA ya yarda, da
suka nitsa ne cikin hira sai Sarki AFARA'U yake bawa boka labarin cewa ai matarshi
ta haihu shekaru biyar da suka wuce ta haifa masa "ya mace.

Nan da nan boka ya
bukaci da akawo masa yarinyar ya ganta, Sarki yasa aka kawo masa SHAMATU dan
boka ya samata albarka.

Da boka ya daga ido ya kalleta sai yaga ai fara ce balarabiya,
kuma gashi tayi kama da wannan yaro WAHASHINFALA wanda Sarki yace ba
dansa bane.

Nan da nan boka yayi tsafinsa ya gani cewa lallai wannan yarin ya
SHAMATU yar Sarki AFARA'U ce kuma wannan yaro ba dansa bane. Sai ya umarci
daya mayar da wannan yaran cikin gida.


Sarki ya tura SHAMATU da WAHASHINFALA suka koma cikin gida. Nan dai
Boka ya sake buka rairayi
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4

2 Comments On MALIKUSSAIFI IBNI ZIYAZZINUN Book 1
avatar
haruna-dau

5 months ago

Reply

I really love to read this novel

avatar
abdullahi-isah-mika39i

5 months ago

Reply

Yeah

Please Login or Register in order to submit comment