Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[6:08pm, 6/14/2017] Bebe'arth(yar gatan hudah: 💦💧💦💧SILAR
SOYAYYA💦💧💦💧
(Labarine Wanda yakunshi SOYAYYA ,tausayi,fadakarwa ,nishadantarwa )

®Adabiancy
💬©O.H.W

Dedicated to RSN novels


Ina,mika godiyata ga ubangiji ,domin babu abin godiya saishi ,Shi yanufeni da fara littafinnan ,Allah kma yasa na kammalashi lafiya ,

Allah karabamu da sharrin masu sharri aduk inda suke,


Dimbin gaisuwa ga masoyana ,ina kaunarku aduk inda kuke,da masu karanta novels Dina dama wayanda basa karantawa Adabiancy na Kaunarku😘


1-2


*GIDAN FARARE*
shine asalin sunan da ake kiran wannan gida,
Kafatanin yan gidan ba baki ko daya,dukkaninsu fararene tas ,

Alhaji bukar shine asalin mai gidan ,bafulatinin mutum ,kyakkkyawan gaske ,Allah yaimai tarin dukiya mai yawa,matarshi daya hajiya bilkisu ,balarabiyace itakuma ,kyawunta ma baxai faduba ,
suna da Ya"Ya biyar duka maxa ,
Hassan Hussain. Nura ,shamsu Abdallah ,
sun taso kawunansu a hade ,suna matukar Kaunar juna ,dukkaninsu kyawawane babu baya cikinsu ,fararene kar ,
Yayin dasuka isa aure ,iyayansu suka turasu danginsu suxabo mataye acan,dama al'adarsu knn auren xumunci ,
Alhaji bukar yagina gida katoton gaske ,akashatarwa kowa akaimasa gini mai kyawun gaske ,
gidaje shida akayi acikin wannan gida ,gidan yatsaru matuka gaya,

duk Wanda yai aure cikin wannan gida yake tarewa ,tafi2 har dukkaninsu sukai aure , da binta
Hassan Aisha
Nura hafsa
Shamsu Hauwa
Abdallah Rabi'ah
Matayen dasuka aura kenan ,dukkaninsu yan dangine ba bare ,kma dukkaninsu fararene tas,
Alhaji bukar ma yatare acikin wannan gida ,gida ya hadu yaxama family guda


Tafi 2dukkaninsu suka tara iyali ,
Hussain yana da Ya"Ya 4
Hasanma 4
Nura 3
Shukurah,safiyya sai autanshi MIQDAD yaro mai farin jini takensa kenan, agida ko a makaranta ,
Tun yana yaro yake da farin jini har kawo samar takarsa
Kyakkyawane ajin karshe ,dan gayune ,yahadun mutuminnan ,hatta tafiyarshi abar kalloce ,
shamsu shikuma yayanshi uku duk Mata ,
nabila ,Fatima ,MUJIBAH,
kyakkyawace ta karshe ,kyawunta irin mai fisgar hankaline ,yarinyar tanaji da gayu ,

Abdallah ,yayanshi biyu shikuma ,
Ahamad Aysha ,

sai matar shamsu ta biyu da yayi mai suna khadija itama bafilatanace ,Amma ansha gwagwarmaya kan ya aureta ,sbda ksancewarta ba yar dangiba ,
Yayanta biyu
Mubina, MUWADDAH,

dukkanin wannan family fararene kar ,shiyasa akewa gidan take da
*gidan farare*
Amma MUWADDAH ta kasance .....





sakon gaisuwa ga kawata xaharatee luv u😘





Adabiancy😘
[6:08pm, 6/14/2017] Bebe'arth(yar gatan hudah: 💦💧💦💧SILAR💦💧💦💧SOYAYYA



(2017)

®Adabiancy
©O.H.W


Dedicated to Rsn novels


3-4

MUWADDAH takasance bakace ita ,Amma bakinta mai kyaune ,
irinsu ake kira chaculate colour ,kyakkyawace dai2 gwargwado ,

duk cikin jikokin alhaji bukar ,yafi qaunar MUWADDAH ,akodayaushe tana gurinsa ,musamman in amminsu nagun Aiki ,dayake barrister ce ,
Wannan Kauna da alhaji bukar ke nunawa MUWADDAH Shi yakara janyo tsanarta a family ,

suna ganin duk cikinsu itace bakar fata ,Amma duk dahaka alhj bukar yafi nuna Mata so ,
Yadda yake nuna Mata so ,kamar Shi yahaifeta ,
Makaranta dakanshi yakaita ,komai nata alhj bukarne ke biyanshi ,dahaka har saida MUWADDAH tadawo gurinshi da xama ,
Ada ahalin gidan farare naxiga hjy bilkisu ,har tafara tsangwamar MUWADDAH bashiri alhj bukar yaimata Jan Ido ,nan da nan taxub da mukaman yakinta tarungumi MUWADDAH ,ta taya alhj bukar kaunarta ,

MUWADDAH tunda ta taso akwaita da san shigar yan filani ,
Kuma intai shigar ba karamin kyau take mataba ,sai tafito a bakar bafilatanarta sak ,

Tare suka taso da MUJIBAH kansu daya ,dama sa'annine,
MUJIBAH na kaunar MUWADDAH ,Yayin da mahaifiyar MUJIBAH bata kaunar MUWADDAH da mahaifiyarta ,tana matukar kishi da ita ,itakwa ammin su mu MUWADDAH xuciya daya take xaune daita ,ita bata ma gabanta aikinta kawai tasa gaba ,duk da tasan irin kisan mimmiken datake Mata gurin abbansu MUWADDAH ,duk sai tahadasu ta watsar tamai da hankalinta kan aikinta ,


Takwana da sanin duk matan gidan haushinta sukeji ,saboda anfi kaunar yarta ,sunbi duk sun hade Mata kai ,barema kishiyarta mamin su MUJIBAH da momyn su MIQDAD,suna matukar yimata hassada ,Amma gabadaya sai taja lamarinsu ta ajiye gefe ,


Wannan Abu da ake baishawa MUJIBAH da MUWADDAH kaiba ,
suna matukar kaunar junansu kai kace ciki daya suka fito ,ganin haka yasa alhj bukar Maida MUJIBAH makarantar da MUWADDAH takeyi ,duk makarantunsu daya kuma ajujuwansu daya ,ahaka suka tashi har sukai candy ,
sukai sauka duk tare ,yanxu suna xaune agida sai islamiya dasuke xuwa ,alhj bukar yace duk mesan cigaba tabari sai tai aure in mijinta naso tayi ,haka yaiwa yayyansuma kafin su ,
Mubina ma yayar MUWADDAH nanan ya hanata cigaba ,
Anwar ne dan gidan auncl Hussain kesanta ,yace
"yabarta tafara Amma fur yaki yace in anyi auran tayi karatun ,

Wannan kenan
Kudai kuci gaba da bina cikin nishadi



*****

MIQDAD yana matukar shiri da MUJIBAH Amma basa shiri da MUWADDAH ko kadan ,yarasa sbda me Shi kawai haushin yarinyar yakeji ,
itakuma MUWADDAH tana so suyi shiri dashi kmar Yadda suke da MUJIBAH ,Amma baya sakar Mata fuska ko kadan ,asalima inyagansu tare baiwa MUJIBAH magana ,

gashi ita akodayaushe tanaso sukasance tare ,xuciyarta na kwadaita Mata kyawunshi ,
Kyawunshi yana fusgarta ,burinta akodayaushe tadinga ganin kyakkyawar fuskarshi ,
in suna tare da MUJIBAH saidai ta buya tadinga lekenshi
Tun batasan me hakan ke nufiba ,har tagano takamu da masifar son MIQDAD ,Wanda ko muryarshi taji ,sai taji kirjinta yabuga ,
ba karamin tsurewa taiba ,data gano ,inda xuciyarta kesan kaita ,tafara lallashin kanta ,domin tasan ko da kudi MIQDAD baxai auretaba , yake da hadaddun yan mata ,domin har gida suke biyoshi ,dan haka mai xaici daita yana ganin jajayan fata kalarsa ,
ga MUJIBAH ma hakan take ,domin tajita tsundum cikin kaunar MIQDAD ,Wanda hartakasa barinshi cikin xuciyarta tagayawa MUWADDAH ,
Aranar MUWADDAH tashiga tashin hankali sosai ,kuka tadinga yi wiwi ,tasan tarasa MIQDAD har abada ,yana ganin MUJIBAH mai xaiyi daita ,

To ga MIQDAD ma hakanne ,xuciyarshi tayi male2 cikin kaunar MUJIBAH ,
Kyahunta na rudarshi ,domin kyawunta yana fisgar Shi ,duk da yana da yan matan dasuka takata akyawu ,Amma baiji san ko daya cikinsuba sai MUJIBAH ,itakadai yakeso ,
Amma har yanxu bai sanar mataba ,

Akwai wata MUBARAKA cikin yan matanshi da ta nace masa ,
Tana matukar kaunarshi ,Amma Shi burinshi ya yakiceta ,Amma taki yakicuwa ,ta like mai kamar cingum,





*****

Wannan satin aka Shiga hada hadar bikin Mubina da Anwar ,
MUJIBAH da MUWADDAH ba xama ,kullum yinan yican suke ,
Suna ta shiri ,sosai ,
hakama Ammi shiri take ba na wasaba ,domin wannan karan ne farko fara aurar da yarta da xatai ,

Gidan farare yacika taf da yan uwa ,aka fara bidirin biki.





Adabiancy😘
[6:08pm, 6/14/2017] Bebe'arth(yar gatan hudah: 💦💧💦💧SILAR 💦💧💦💧SOYAYYA


(2017)


®O.H.W
©R.S.N


5-6

*fulani day*

yau ranar ta yan filloce ,
ka'fatanin Wanda ke gurin duk yan fillone ,kma dukkaninsu sunyi shigar filani ,

Amarya da ango ma shigar filani sukai ,sunyi matukar kyahu ,

can nahango MUJIBAH da MUWADDAH sunyi kyau suma sosai ,
suna ta xuba hotuna ,
MUWADDAH ta tatsaya jikin mota ,da korya a hannunta ,aka kyasa Mata ,
ba karamin kyau taiba ,haka dai sukaita daukar juna ,
Kamshin turaransane yafa'ra xiyartar hancinta ,
ta'riga da ta haddace kamshinsa ,domin tana matukar san ta shaki kamshinshi ,akodayushe burin hancinta yashaki kamshin MIQDAD ,

Kanta tadaga tana bin gun dayake tahowa da kallo ,
ba dan karamin kyau MIQDAD yaxubaba,
Sakin ba'ki kawai tai tana binshi da kallo ,

Murmushi yake saki mai tsima xuciya ,
A tunaninta ita yakewa ,
itama sai tasakar mai murmushi tana kallanshi ,har yakaraso daf daita ,kawai sai taga yashigeta ,baki bude tabishi da kallo ,

Ya'isa ga MUJIBAH da ke tsaye tana sakar mai murmushi ,
Ya danyi murmushi mai sauti ya ka'ma Han.unta yadan murxa ka'na yafurta I love u

. Kalmar da tadade tana jira yafurta Mata ,sai gashi ba xato ba tsammani yau yafirta Mata ita ,
Aikwa batai wata2 ba tace masa me too ,
yasa hannu ya la'kace Mata hanci ,suka saki dariya atare ,


MUWADDAH datai suman tsaye a gurin ,ji take kafafuwanta sunyi nauyi ,sun kasa daukarta ,
ga wani Abu da yataho ya tokare Mata kirji ,
gashi kanta sai juwa yake ,
Idanuwanta yacika taf da hawaye yana kokarin xubowa ,


MIQDAD yacewa MUJIBAH mukarasa ciki mana ,tajuya gurin da MUWADDAH take ,tace :
" MUWADDAH Kixo mushiga ciki" ,

Murmushin yake tai ,tadaga Mata kai ,
tana daga kafarta xa'ta motsa ta fa'Di sai ji kake tim ,

A hargitse MUJIBAH tayo gurin da take tana jijjiga'ta , Amma ina ta sume
Kuka MUJIBAH take tana girgixa'ta

Shi kwa MIQDAD ya rasa ma me xaiyi
dai2 nan Amminsu ta fito kenan ,da hanxari taka'rasa gun dasuke ,
ganin MUWADDAH a kwance , nan ta'ke hankalinta yatashi ,
tana tambayar me ya sameta ,
nima wlh Ammi ban saniba kawai ganinai ta fa'di ,MUJIBAH ta ba'ta Amsa ,

Ammi tace tashiga ciki ta daukko Mata ruwa,
da gudu taje tadaukko ta ka'wo aka yayyafa mata ,

Tana far fadowa ta fashe da kuka ,
Ammi ta rungumo ta jikinta tana tambayarta mai ya'faru ,
bata ba'ta amsa'ba taci gaba da kukanta ,har sai da taga ran Ammi ya fa'ra ba'ci sannnan ta tsaigaita kukanta ,
tace :
"Ammi kawai jinai kaina yana juya'wa ,jiri na diba'na ,shine nafadi ,

sannu Ammi taimata ,sannan ta ka'Mata ta mike ,
MUJIBAH nai Mata sannu Amma ko tajuya ta kalleta ,saima ciki2. da ta amsa ,jitai kwata2 ba'ta'san kallanta wani irin haushinta takeji ,



Ammi ni gida xan koma kaina ciwo yake ,
to xa'ki iya karasa'wa ke kadai ko MUJIBAH ta rakaki?
Ammi ta tambayeta ,

ta turo ba'ki a'a xan iya ka'tasawa Ammi ,kuje kawai ,Ammi tace to shikenan ,in Kunje kisha magani kan nada'wo Allah ya sawake ,
tace Ameen ,tajuya ta tafi ,


tana xuwa daki gado ta fa'da taci gaba da risgar kuka kan kice meye wannan xaxxabi ya rufeta ruf ,
tana ta karkarwa hakoranta suna haduwa da juna ,
Ahaka suka dawo suka tadda ita ,

MIQDAD ne ya duba'ta ,(likitane a shekar karshe yake da xai xama cikakken doctor)

ya kalleta ,yace : ke me ke da'mun ki ?
can kasan makoshi ta furta *SOYAYYA*
Yace :
"me kikace?" tace "ba komai nace "

karya kike bayan binciken danai ya nunan harda damuwa ke damunki ,me ya jaho hakan ,?
cikin ranta ta furta *SILAR SOYAYYA*
Kmar tai kuka tace:" ba komai ni ba abinda ke damuna "ta turo baki ,
tsaki yai
Ya rubuta Mata ma'gun guna ,


A haka aka karashe wannan biki MUWADDAH ba lafiya cikakkiya ,sai da tai sati ,sannan tai garau daita kamar bataiba
Soyayyar MUJIBAH da MIQDAD sai bunkasa take ,tun a family ba'a saniba har taxo da kowa ya sani ,an tsai da ranar bikima ,yana kammala karatunshi ,kannan MUWADDAH ma ta tsayar ,



MUWADDAH kwa kullum tamkar ka'ra Mata kaunar MIQDAD ake
Xaxxafar kauna take masa ,
soyyyyace xallah wacce babu digon algus aciki ko kadan ,
Idanuwanta sun Riga da sun Saba da kuka *SILAR SOYAYYAR* MIQDAD ,

ga wani xa'fi da kirjinta ke Mata ,
samun saidarta tai idanuwa hudu da MIQDAD shine kwanciyar hankalinta ,

duk ranar da kaga MUWADDAH cikin farin ciki da nishadi ,to sunyi Ido hudu da MIQDAD,
Abinci MUWADDAH bata iya xama taci miki sai ta'ga MIQDAD,
soyayyar MIQDAD na neman xautar da MUWADDAH ,

duk bidirin da take ,ba Wanda ya rafko jirginta ,sbda ta iya takunta ,
bata fatan kowa yasani ,domin idan xancan yaje kunnan alhj bukar ,MIQDAD ko yana so ko ba'ya so dole ya aureta ,

itakuma bata fatan haka yakasance ,shiyasa tabarwa kanta sirri ,daga ita sai xuciyarta ,

Lokacin da aka sanya lokacin bikin MUJIBAH da MIQDAD kwanciyarta asibiti biyu ,dakyar aka shawo kanta ,tun lokacin take fa'ma da matsanancin ciwon kirji ,duk dan *SILAR SOYAYYA*




Ko da la'bari yajewa muba'raka nasa ranar MIQDAD hankalinta inyai dubu ya tashi matuka ,

da tasamu MIQDAD da xancan sai cewa yai aishi da'ma bai amsa mata soyaytarta ba ,itace dai take haukanta ,








Adabiancy😘
[6:08pm, 6/14/2017] Bebe'arth(yar gatan hudah: 💦💧💦💧SILAR💦💧💦💧SOYAYYA


(2017)

®Adabiancy
©O.H.W


Dedicated to R.S.N. novels😘


7 -10

_À kace Ra'n'a ba'ta karya saidai uwar diya taji kunya ,_

_to dai a wannan satin aka shiga hidimar bikin MUJIBAH da MIQDAD , har lokacin soyayyar MIQDAD n'a nan cikin xuciyar MUWADDAH ,duk da ta'riga da ta fudda ran sa'mun MIQDAD ,Amma kullum ka'mar ka'ra Mata kaunarshi ake ,_

dauriya take kawai ,ake hidimar daita ,sbda itace aminiyar MUJIBAH kuma yar uwarta ,MUJIBAH ta wuce komai à gurinta ,sbda tana kaunarta ,ba'ta daka ta maminsu da sauran yan uwanta ,ba'ta yan ubanci dasu ,shiyasa itama take kaunar MUJIBAH ,

À Ranar da akai dinner ,byan Sun da'wo gida xaxxabi mai xa'fi ya rufe MUWADDAH ,MUJIBAH n'a gefenta tana tai mata sannu ,
çan dai kirjinta ya faraimata ciwo ,kamar ansa blo an tokare mata shi ,numfashi take sama2
MUJIBAH da ta Ankara da ita ,hankalinta ya tashi ,ta danna numb MIQDAD tana kuka ta sanar dashi ,

yana xuwa daukarta yai kawai ya nufi asibiti da ita ,
À gidan ba wanda ya sani ,har saida aka gama du'bata ,aka ba'ta kwanciya ,sbda tunda ta sume har lokacin bata farfadoba ,

Wa'ya yai gida ya sanar dasu ,
Aikwa à daren Ammi da hajiya bilkisu suka taho ,
Alhj bukarma ya biyo ba'yansu hankali ta'she ,
haka sukai jigum 2 har misalin 12:00pm MUWADDAH bata far fado ba ,MIQDAD ne ya lallami alhj bukar da kyar ya tafi gida ,Amma yace hajiya bilkisu ta xauna ,

sai misalin 01:00pm MUWADDAH ta farka lokacin MIQDAD ya shigo dubata ,
ido hudu sukai dashi ,take xuciyarta ta fa'ra sanyi ,
ta kura mai ido tana kallanshi ,
yace :
"Yanxu me ke da'mun ki ?"

tace :
"ba komai "

Yace
"MUWADDAH tunkan n'a sanar da kowa ,ki gayan me ke da'munki ,
kinga da'muwa tayi miki yawa ,har jininki ya fara hawa ,kin riga kin sanya abu à ranki ,ga xuciyarki n'a neman ka'muwa da ciwo "

hawaye ne ya sirarowa fuskarta ,cikin xuyarta ta furta duk SILAR soyayyar ka nake cikin wannan ha'lin ,Amma baxan taba furta'wa ba ,sbda ka riga ka haramta agareni ,sbda à gobene in Allah ya kaimu xa'à daura auranka da yar uwata ,hawaye masu dumi suka buyo fuskarta ,

ya kalleta ,tausayinta ya ka'mashi ,yarinya da ita ta ka'mu da ciwunkannan ,xaiso yaji me ke da'munta ,ko xai iyai mata wani abin ,
Yace
" tambayarki nake kinmun shiru ,ko n'a gayawa su Ammin kya gaya musu abinda ke da'munki ?""

ni ba abinda ke da'muna kawai ciwone daga Allah ,n'a rokeka kar ka gayawa su Àmmi ina da da'muwa ,nasan xasu tilasta'ni fadar abinda ba shineba ,dan ni banda wata da'muwa ,

ya girgixa kai yace MUWADDAH kina da taurin kai ,Amma tunda baxa ki gayan ba shi kenan. ,
ya dannan numb MUJIBAH ,yasanar dasu su shigo ta farka ,
da murna suka shigo suka nufi gun da take ,
Ammi ta xauna bakin gado ,ta dora kanta kan cinyarta ,tana sha'fa kanta ,sannu MUWADDAH kinji ,ya jikin n'a'ki ? tace Ammi da sauki ,su hjy bilkisu da MUJIBAH suma sukai mata sannu ,

Ammi ta kalli MIQDAD da yake à tsaye ,tace me ke da'munta ,
Xai magana suka hada ido da MUWADDAH ta marai raice mai ,tausayinta ya ka'mata ,
Yace ,
"Ammi xaxxabine ,da kuma ciwon kirjinta ya tashi ,da'ma in ya tashi tana shan wahala sosai ,dakyar n'a iya controle din matsalar ,"

Ammi ta kalleta cikin tausayawa ,tace sannu kinji MUWADDAH ta ,Allah ya ya'ye miki wannan ciwon ,suka amsa da Ameen dukkaninsu ,
MIQDAD yace
"toni Àmmi xan tafi ,sai xuwa sa'fiya xa'à sallameku "

Àmmi tace
"Allah ya kaimu safiyar ,Allah ya sakama da Alkairi "

yace Ameen ,ya kalli gurin da MUJIBAH take ya kifta Mata ,ido
ta ga'ne me yake nufi ,sai ta make ka'fada ,
.Ammi da ta lura dasu ,tacewa MUJIBAH ki ta'shi ki bishi Ku tafi kinga gobene daurin aurannaku ,gwara ki Kwana à gida ,

tace
".nidai Ammi baxan tafiba sai da MUWADDAH ,in naje bansan me xanyiba ,baxanji dadiba indai babu MUWADDAH a kusa dani ,kawai yai tafiyarshi nidai ,"

Kanma takai karshan maganarta ,ya riga da yai tafiyarshi ,Àmmi tace to shikenan ,Allah ya kaimu goben ,
suka Amsa da Ameen ,




MUWADDAH tacewa Ammi :
"Abbanmu baisan banda lafiyaba Ammi?"
"
Ammi tace:
" inajin dai bai saniba "

Hmmmm
Ammi n'a rasa me naiwa mahaifina bai da'mu da lamurana ba ,duk cikin yayanshi ni kadai yafi tsana ,

Kul MUWADDAH n'a hana ki irin maganganun nan ,dukkanku yana kaunarku ,

Hmmm shikenan Ammi n'a daina ,
Yawwa ko kefa ,keda ma kike yar ga'tar Alhj ,tun da aka kawoki yake asibitinnan ,da kyar aka lallameshi ya tafi gida ,


😀 Allah sarki ,mai gida'n'a Ai n'a xata baixoba ,nace n'a fa'sa auran ,

Hjy tace
"Kinga kwa da naji da'di an fa'sai mun kishiya😀 "

😀 kidaina ma murna ,dan nida alhj mutu ka raba ,
hakadai sukadinga hira cikin raha ,kmr ba mara lafiya ba ,har bacci ya fara daukesu daya byan daya ,






****
Wa'she gari da sasssafe mami tayiwa MUJIBAH Waya maxa2 ta baro asibitinnann kafin ta batar mata ,masifa ta xaxxaga mata cikin wayar ,
bata sanar da su Àmmi abinda mamin tace mata ba ,kawaidai tace musu xa ta tafi mami ce ke kiranta ,
Ammi ta ba'ta kudin mota ,tace taje suma suna nan tahowa ,
har taje ba'kin kofa ta dawo ,ta kalli gadon da MUWADDAH ke kwance tana bacci ,ta dawo gaban gadon ta shafi gefen fuskarta ,Allah ya baki lafiya ,ta furta sannan ta juya ta fita ,



tana tsaye à gefen titi tana jiran mota ,
Wata blue black din mota tai parking gabanta ,
aka saukar da glass din motar ,MUBA'RAKA ta gani budurwar MIQDAD ,Amma ita batasan budurwarsa bace ,kawaidai tasan makarantarsu daya ,
Murmushi tai mata ,tace ina xa'ki haka da safiyarnan ?

Wlh gida xani ,kma kinga duk motocin Sun dauke ,

To in ba da'muwa Kixo n'a ajiyeki mana ?

baxan tsaida keba?

Kar ki da'mu Kixo kawai n'a saukeki ,

tace ,Tam ,godiya nake ,tashiga motar taja suka tafi ,

Yaushe ne ran daurin aurannaku ?

Yaune ,ta bata amsa ,
tai murmushi ,ta fito da wani kyalle ta sha'ka mata ,ta fashe da dariya ,ko kunya baki jiba ,hadda cewa Yaune ,to saidai kuyishi à la'hira in ana yi ,
dan matukar ina ra'ye à duniya babu macen da xata auri MIQDAD saidai ni ,

ta kara gudu da motar ta ,

Wani wa'wakeken ruwa ,taje ta jefata à ciki ,tayo kwana da motarta xuciyarta fal farin ciki ,





10:00am
sai lokacin aka sallami su MUWADDAH ,suka nufi gida ,

suna xuwa mami ta dirarwa da Àmmi da masifar ta janye mata ya ,sai kace itace ta haifa mata ,
Ammi tace ai tun da'Xu MUJIBAH ta baro asibiti tace ke kike kiranta ,

hankali tashe mami tace ita bataga MUJIBAH ba ,nan gida ya harxike ,ana ta kiran wayarta à kashe ,
hankalin kowa ya tashi ,musamman ma MIQDAD hnkalinshi yafi n'a kowa tashi,

nemanta ake gida2na yan uwa ,Amma duk maganar dayace bata xoba





*****
MUBA'RAKA byan ta da'wo gida cikin farin ciki ,ta tadda kawarta easy tana jiranta ,
tace
"Kawa'ta ya naganki cikin farin cikine ,kaddai kin aikata mugun nufin da n'a haneki kar kiyi,"?

Kema dai me xa'.à fa'sa?
Ai in kinga MIQDAD yai aure ,saidai in ba'n'a ra'ye ,
*SILAR SOYAYYA*babu abinda baxan iya ba ,akan MIQDAD xan iya raba kowa da ranta ko wa'ce ita ,

Ko nice?easy ta tambayeta
Wlh Ko kece din ,

cabf ,Amma Allah ,ya shiryeki ,kawance n'a dake kwa ba alkairi bane ,tunda har xa'ki iya kasheni ,kinga tafiyata ,

Allah ya raka ta'ki gona ,kma wlh naji bullar maganar nan ,kema kwananki ya kusa karewa ,






******
Mutane
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4

Please Login or Register in order to submit comment