Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ce mata "bana son gaddama fa kin sani zan iya zuwa har class d'in naku na d'auke ki Allah kinsan zan iya ko in......kamin yama idasa maganar da yake son fad'a ta yanke wayar tana nufar office d'in nashi a zuciya kuwa cewa take kad'an daga aikin Sadeeg Garkuwa tsaf zai iya barinta da jin kunyar jama'a, sai da tayi tabbaya taje ga office d'in dan iyanzu ba wadda bai sheda wanzuwarshu a school d'in ba yadda aka basa babban matsayi shi kansa Office d'in nasa abin kallo ne dan sauran Malamai ba k'ara min ji suke dashi ba har cewa suke su ai gaba ta kai su ko banza makarantar su ta kafa tarihi na zuwan Garkuwa cikinta, ba yadda ba taiba su Nawwara su rakata sukak'iya suka ce "ina zamu shiga tsakanin mata da miji yana buk'atar ganinki ne shi yasa sai kin dawo", cike da jin haushi tabarsu kamar ta d'ora hannu akai ta zunduma ihu haka take ji.


Shigarta Office d'in abinda tagani ne yasa taja turus ta tsaya ganin wata mace tasha wasu shegun kaya daga gani ma wannan ba dai d'aliba ba sai dai ko Mlm ce wani irin kishi ne ya rufe Surayya duk da tasan halin mijinta kuma taga shi Sadeeg bata ita yake ba, nunawa ma yayi kamar ba kowa a gabansa, aikin gabansa kawai yake ganin shigowar ta yasa ya tashi kad'an ya saki fuskarsa cikin harshan turanci ya ce "Dr Zuby zaki d'an iya bamu waje nida iyali na", wani irin dammm dumm taji gabanta ya fad'i juyowa tayi tana kallon Surayya, mi yake nufi ne ba dai matarsa yake nufin wannan y'ar abar ita ce ba kenan duk burin data ci ya rushe kenan.


Tashi tayi jiki ba kwari ta fice daga Office d'in zuciyarta na zafi.

Tana fita Surayya ta juya cike da fushi zata fice tana turo baki da sauri ya sha gabanta yana turata jikin bango kallonta yake da rikitattun idonsa k'asa tayi da kanta dan kwata-kwata yau d'in wani irin kwarjini yayi mata zata bud'e baki tayi magana tana faman turo baki bata zata ko tsammani ba ya had'e bakinsu waje d'aya jikinta ne ya kama kyarma kamar wacce aka jonama lantarki kwata-kwata ta kasa d'aukar abun saboda bata tab'a yi ba ganin yadda jikinta ke kyarma yasa a hankali ya zare bakinsa cikin nata ya juyawa ya koma kan kujerar dake office d'in yana cewa "hukuncin ki kenan idan kika k'ara min gaddama ban sallame ki ba, zaki fita", ya idasa maganar yana shar mur, irin baya son raini yadda kasan bashi ya gama kiss d'in ta ba.


Cikin sanyin jiki take binsa da kallo ganin yana nuna mata kujera yasa dole ta zauna, a hankali kamar wadda aka cirema lakka k'asa tayi da kanta can ta tsinkaye muryarsa yana cewa "ki tabbatar gobe ki sanyo hijab inda hali ma kisa abun rufe fuska bana son kina sa gyalan nan kin sani, dan haka daga yau bana son in k'ara ganin wani wai shi gyale a jikinki kinji?", x
da sauri ta d'ago tana kallonsa cike da mamaki tasan za'a rina ita wallahi takura mata zaiyi zuwanshi school d'in nan haba ta idasa maganar a zuci can taji muryarsa ya ce "zan takura miki kike cewa ko?", Da sauri ta k'ara dubansa cike da mamakinsa wai shi kamar wani aljani.


Ganin kallon da take mai yasa yashi yin wani shegen murmushi na gefen baki wadda ya k'ara ma fuskarsa tsananin kyau ya ce "zaki iya tafiya ba abinda kuke buk'ata na anfani keda k'awayan naki?", tashi tayi dan dama a k'agare take tana cewa "a'a babu abinda muke buk'ata akwai komai idan ma akwai wani abun zan sanar da kai", tana maganar tana niyar barin Office d'in tana gaf da ficewa ya ce "daka ta", tsayawa tayi bata waiga ba, jinsa tayi a bayanta, ya rungumeta ta baya, yana fesa mata hucin numfashinsa wata irin zubura tayi da sauri ya k'ara rik'e ta yana k'ara mannata a jikinsa, jikinta dan da nan jikinta ya fara rawa kai daka kalla kasan bata saba kasancewa da wani d'a namiji a irin wannan yana yin ba.


Sakinta yayi yana nuna mata hanya kan zata iya fita ai da sauri harda had'awa da d'an gudu ta fice shi kuwa dariya ma ta bashi, murmushi yayi yana shafa lallausan sajansa wadda yake zagaye da kyakkyawar fuskarsa, gashi ya k'ara mai wani sahihin kyau mai fisgar mutum, wani irin nishad'i yake ji idan yana tare da Surayya yasan Surayya ta daban ce.



Sadda zata fito yamma tayi sosai sai ya kasance d'ai-d'aiku ne a school d'in can kamar ance ta waiga taga su Goga sunyi ma wata yarinya caaa sai mutumcinta suke ci wani irin abu ne taji ya shegeta idonta yayi jajawur hankalinta ya gushe jikinta har wani kyarma yake na tsananin b'acin rai.


Su Goga basuyi tsammani ba kawai sukaga mutum a gabansu a yanzu sanye take da fararan kaya kanta a k'asa cike da wata irin murya ta ce "wato kudai bazaku tab'a dai na cin zarafin mace ba ko ni kuma bazan gaji da gana muku azaba ba ina mantar daku gobe ku k'ara na sake k'ara muku wata azabar, har sai Goga ka kai kanka koto ta bimini hakki na, na kashe min abin k'aunata da kayi can baya an danne min hakki ba'a yi muku komai ba to wannan na rantse da sarkin da ya halicci ni sai kakai kanka da kanka koto an yanke maka hukuncin dai-dai da abinda ka shuka lokaci na nan tafe da zansa a wannan baiwar Allah da nake jikinta zansa ta bin ciko abinda kayi min a rayuwa Goga bazan tab'a yafe ma ba, bazan tab'a bari ka zauna lafiya baaaaa", ta idasa maganar cike da wata irin murya mai amsa kuwwa muryar har wani rarrabuwa take kashi kashi.


Wata irin zubura su Goga su kai suna shirin arcewa da mugun gudu, wadda suke ma cin mutumci kuwa tuni an gusar mata da hankali an kauda ita daga wajan su kuwa suna k'ok'arin guduwa ta nuna bayansu da zungureran hannunta da yayi tsawo kamar shantu dan-danan wasu irin karnuka suka wanzu a wajan karnukan ba kyan gani bakinsu zak'o-zak'o da wasu irin hakura bakinsu na zubar da wani jini mai shegen kauri kallon fuskasu kuwa saita sa mutum zaucewa, umarni ta basu kamin kace kwabo sun bisu a goje gudu suke suna neman ceto babu ma mai jinsu bare ya gansu kwata-kwata an kauda hankalin mutane daga gare su sai da karnukan nan sukayi masu kaca-kaca da jiki duk sun raunata su sana suka b'ace b'at kamar ba'a yi wanzuwarsu a duran duniya ba.


Basu daina gudu ba har sai da suka isa gidan da suke inda suke kwana suna shiga wani babban parlo nasu duk tarkacan shaye-shaye ne cike da parlon suna faman ihu da kuka kamar k'ananan yara dan kuwa wani irin rad'ad'i suke ji a jikinsu inda karnukan suka yayyage su, ji suke yadda kasan ana zuba masu gishiri akan ciwon sai birgima suke a k'asa bare Goga kamar da gayya Karan da aka turo mai yafi mai lahani.......✍️





*ZAHRA ROYAL STAR CE*




Share fisabilillahi🥰🙏

*💔🧟‍♀️☠️SILAR MUTUWA🧟‍♀️☠️*💔
(Horror Story)





ZAHRA ROYAL STAR CE.......✍️






*ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION*






*DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN K'AI*



PAGE 7️⃣➡️8️⃣



Suna cikin shan wannan azaba suka tsinkayi wata murya mai amsa kuwwa harda wata irin dariya aka ce "wai ku nufin kun tsere kenan ai yau azabar ku ta daban ce hahahaha", aka idasa maganar da wata irin dariya dariyar na rarrabuwa kashi-kashi.


Wata irin zabura sukai suna shirin arcewa a guje tana daga zaune akanta a k'asa wani irin gashi ne a tsakiyar kanta wuta na faman cinsa yana k'unewa wani na tsirowa hatta jikinta gashi ne kamar biranya wani irin shegen kallo take musu ganin suna kaiwa k'ofar ta datse gam.


Tsayawa sukai sai rawar d'ari suke suna hawaye mutunan naku Goga harda sakin fitsari wata dariyar tayi tana kallon wani faranti shak'e da wiwi kallonsa tayi tana lauyar da kai nunasa tayi da yatsa nan take cikin farantin ya koma cike da wasu irin tsutsotsi marassa kyan gani juyowa tayi ta ce "bismillah ku fara ci yanzu na ceeee", ta idasa maganar cike da bada umarni, ai dan da nan jikinsu ya kama wata irin kyarma suna zubewa k'asa har suna had'a baki wajan cewa "dan girman Allah kuke ganinmu bamu muke ganin ku ba kiwa Allah ki yafe mana ai in muka ci wannan irin abincin naku ai sai dai wasunmu badai mu ba", dariya ta kece da ita tana d'aga kanta sama tsananin dariyar da take ce d'akin ya fara wata irin girgiza kamar zai tashi daga inda aka gina sa.


Had'ewa sukai suka cure waje d'aya dariyar ba k'aramar firgita su tayi ba d'agowa tayi tana bin su da kallo cikin tulun gashin dayayi ma fuskarta kawanya ta ce "ashe har kunsan Allah dan ubanku zaka fara ci ko kowa sai na fara d'aukar ranku d'ai-d'ai da d'ai-d'ai", ai har suna rige-rigen jawo filat d'in kuka suke kamar mi ai suna had'a ido na tsutsotsin nan yadda suka ga kamar hararara suke aika musu yasa wasunsu fara sumewa a nan take wani irin kuka ne suka fara ji kamar na jarirrai ga wata irin iska data mamaye ilahirin parlon ji sukai kamar ana zagaye su ana wata irin magana cikin wani irin yare maganar na fitowa kamar ana rad'a ga wata irin dariya kamar ta jinjirin jaki ga parlon duhu ya mamaye shi sauran daba su sume ba tuni suma sun riga da sun sume hankalinsu yabar jikinsu.




Surayya kuwa bata tashi tsintar kanta ba sai a d'akinsu sallar asubahi su Nawwara suka tashi suka ga ita ce ta tada su sunyi mamaki suna son tabbayar ta amma sun kasa idan ita kanta tashi tayi sallar ta ganta kwance a kan gadonta.



Gari na idasa wayewa suka shirya suka nufi cikin school suna tafiya sanye take da hijab har k'asa dan taji gargad'in Sadeeg inya fad'i abu yafi so ayi nan take tafiya take waya manne a kunanta tana waya da Ammee tana sanar da ita semester ta kusa k'arewa suna shirin fara exams dan kuwa school d'insu karantunsu gudu yake amma suna mugun kada d'alibai tana sauke wayar taga wasu y'an mata sunsha gaban su daka kalle su kasan y'an tasha ne dan kuwa sai wani kallo suke aika musu suna faman taunar chingum, Bilki ce ta ce "bayin Allah lafiya dai?", da sauri wata tasha gaban Surayya ganin zata rab'a su ta wuce dan ita bata ga anfanin tsayawa da wa'innan matan ba marassa kamun kai zaro ido Surayya tayi tana bin wadda tasha gabanta ta ce "ina kuma zaki baki ji miya kawo mu ba", Surayya kuwa wani murmushi tayi maisa ma wadda akai danshi jin haushi dan kuwa na rainin wayo ne ta ce "to mi zan tsaya naji inba shirman Dr Zuby data baku labari na shine kuka kwaso k'afa domin wai ku jamin kunne akan saita auri Sadeeg Garkuwa hmm to tun wuri ku fad'a mata cewar Ahmad Sadeeg Garkuwa na Surayya ne ita kad'ai taje ta binciki waye shi in banda ni ita bata isa ta ganshi ba bare harta yi tink'aho wai saita shigo rayuwarmu da alama har yanzu bata san waye Garkuwa ba", kallonta suke cike da tsananin mamaki kamar wata aljana ya akai tasan komai da suka zo sanar da ita, wata daga cikin ta ce "koma dai miye ki shirya amsarta, ai ba dan ke kad'ai aka haifi shi Sadeeg Garkuwan ba yana da ikon yayi mata har hud'u sabo...... Kamin ta idasa maganar Surayya ta daka mata tsawa da yasa su firgita ta ce "ke ba sa'ar yina bace idan ta isa tazo da kanta kuma kuce mata duk inda zata taje domin mallakar Garkuwa na bata dama inta isa duk wajan bokayan da zata ko malamai taje bana shakka ko tsoro da alama bata san wacece Mrs Ahmad Sadeeg Garkuwa ba", ta idasa maganar tana masu kallon banza rab'a su tayi zata wuce wadda tafi su rashin kunya da alama yadda suke kama da Dr Zuby ba tantama k'anwarta ce ta jawo hijabin Surayya cike da isgilanci.


Batai aune ba taji saukar mari tassss tassss duka kumatunta Surayya ta sharara mata mari mai zafin gaske tana fisge hijab d'inta, ta ce "ke da alama wata ce wajan Zuby ko?, ke nifa akan mijina wallahi zan iya komai dan haka ku kama kanku kusan dawa kuke magana", tana nuna su da yatsa su Nawwara kuwa murna suke suna cewa "maganinku kenan indai Surayya ce ba kanwar lasa bace", suna maganar suna bin bayan ta suka barsu sake da baki......✍️



*ZAHRA ROYAL STAR CE*



Share fisabilillahi🥰🙏

O
*💔🧟‍♀️☠️SILAR MUTUWA🧟‍♀️☠️*💔
(Horror Story)





ZAHRA ROYAL STAR CE.......✍️







*ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION*







*DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN K'AI*



PAGE 9️⃣➡️1️⃣0️⃣


Su Goga sanyin asuba ne ya tada su jikinsu yayi tsami da kyar Goga ya d'auki waya ya kira likita koshi doctor d'in ya girgiza da ganin irin ciwokan dake jikinsu da kyar yasa mu ya gyara musu ciwon ya basu magani ya tafi ya barsu da tsananin jinya.


Kusan satinsu d'aya y'an school basu ji d'iroyar su Goga ba y'an makaranta sai murna suke kwana biyu sun d'an sarara duk inda ka zaga maganar su Goga ce kwana biyu an huta.



Su Surayya bayan sun gama lecture fitowa su kai duk ranta a b'ace ba taima su Nawwara magana ba ta nufi office d'in Sadeeg girgiza kai Bilki tayi ta ce "kai yaufa akwai rigima ni nasan dama sai anyi haka d'an gayu ga kyau ga kud'i, ai dole a samu y'an matan da basu da class su kai kansu gare shi", sauk'e ajiyar zuciya Nawwara tayi tana juyawa ga Bilki ta ce "ai wallahi banga laifin su ba tsananin kyau irin na Ahmed Sadeeg Garkuwa wai a haka ma dan bai taho da masu bashi tsaro ba a hakan ma again a nan ba wani nuna kud'i yake ba har yanzu basu san shi d'in wanene ba kinsan Allah Bilki da zai nuna ainahin kalarsa wata mace bata isa kawo mai raini ba koda yake ma ko yanzu sai dai suzo wajan Surayyar ba dai wajan sa ba ina ji fa jiya wata wadda ba y'ar department d'in mu ba suna maganar sa amma kwarjinin sa da haibarsa sun kasa tun kararsa kinsan Allah wasu matan banzaye ne da sun kalli Ahmed Sadeeg Garkuwa ai sunsan na gaba yayi gaba na baya sai labari", Bilki ta ce "wannan maganar taki gaskiya ce zaka iyayin komai indai akan irin su Garkuwa ne Allah dai ya raba Surayya da shirrin mutane muje kawai mu jirata wajan cin abinci dan yinwa nake ji", Bilki na idasa maganar suka bar wajan.



A wajan Surayya kuwa tana shiga Office d'in wani irin matsifaffen k'amshi ne yayi mata ziyara da wani sanyi maisa natsuwa lumshe idonta tayi duk matsifar data zo da ita tana had'a ido dashi ta nemeta ta rasa, yadda yake kallonta yayi bala'in kyau sanye yake da wani irin arnan yadi kalar fari tas, ba k'aramin kyau yayi mata ba kullum indai zata sa Sadeeg a idonta to sonshi da kishin shi ne ke k'arowa a zuciyarta.


A hankali take nufar wajansa tasowa yayi ya jawota jikinsa da sauri zata zame ya ce "Ohh shat wai ke sai kace y'ar k'auye, sai kace baki waye ba wai kefa halali na ce bana son irin haka fa", turo baki Surayya tayi, sa hannunsa yayi ya d'alle mata baki da sauri tasa hannunta hawaye na b'alle mata cikin y'ar rud'ewa ya ce "minene nasan dai wannan a hankali nayi miki akwai wani abu please mike faruwa?", fad'awa tayi jikinsa tana k'ara fashewa da kuka da sauri ya k'ara rungumeta yana shafa bayanta alamar lallashi sai da ya bari ta gama kukan ya d'agota batayi aune ba yasa harshan sa yana lashe hawayen kallonta yake da idonsa masu kaifi, k'asa tayi da kanta cikin zazzak'ar muryarsa ya ce "kinsan yadda nake jin kukan ki kuwa a zuciyata zuciyata zafi take, minene ke faruwa", da kyar ta bud'e baki ta fara bashi labarin abinda ya faru kamin ta kai maganar ma ya jawota ya had'e bakinsu waje d'aya dole tasa tayi shuru tana zaune kamar gunki sai da ya gaji dan kansa sana ya zare bakinsa cikin nata idonsa harya canza kala cikin sanyin murya ya ce "ki daina sama kanki damuwa kinsan waye mijinki so please kima daina biye masu kinji", da kyar ta d'aga mai kai sun dad'e sosai a haka har sai da yaga hankalinta ya kwanta inka gansu a yanzu yadda suke wasa da dari saika rantse kamar ba masoya ba, sai kace abokan wasa ne ita kad'ai yake ma wannan abun dan Sadeeg Garkuwa baya da wasa ita kanta wani lokacin inya birki ce mata bata iya gane kansa, danma ita ke iya sakko dashi ko in yayi fushi ko wani abu ya shige mai duhu cike da farin ciki ta bar office d'in nashi.



Sadda zata fito ganin yawan d'alibai sun ragu yasa ta wuce inda gidan da suke kwana dan kuwa jibi zasu fara exams yauma sai da sukai text abubuwa sun fara yawa danma a CBT zasuyi wata.



A sadda ta isa d'akinsu harsu Nawwara sun gama abinci suna karatu ko wacce da littafi a hannunta da handing out suna ganinta yadda ta saki ranta suka fara tsokanar ta sharesu tayi ta cire kayanta tabar y'ar wata riga, yadda surar jikinta ta fito kai gaskiya Surayya kyakkyawa ce ta k'arshe gata da k'ugu da manyan cinyoyi da Hips kamar su fad'u in tana tafiya kamar su fad'o, gata da nonuwa y'an dai-dai ba irin masu mugun girman nan ba amma a tsaitsaye suke ko a cikin riga zaka iya lura da hakan gasu tabarkalla cike suke kamar balan-balan, tana da tsawo amma ba can ba fara ce tas hancinta ba irin dogon nan bane matsakai ci ne fuskarta dogowa ce sai bakinta d'an mitsitsi kamar na tsuntsu jawur dashi kamar na jariri, dan ba laifi ana zafi saida taci abinci itama sana ta d'akko handing out domin yin karatu kwanciya tayi rufda ciki tana cikin karatu sai kuma ta d'ago ta ce "wai ni kuwa Nawwara da Bilki a cikin school baku ji anata maganar wani waishi Goga ba kamar fa nasan shi ina tunanin kamar wata y'ar tsama ta tab'a had'a ni dashi ina so nasan miye ya aikata da yasa school d'in ake zancan sa naji kwanansa biyu bai shigo ba mutune sai murna suke da alama ba k'aramin tantiri bane", da sauri su Nawwara har suna had'a baki wajan cewa "kai Surayya ke kuwa mi zai had'a ki da Goga shu'umi abokin shaid'an, muma kanmu muna son sanin miye ya aikata da ake ta zan cansa kuma in ka tabbayi wasu kamar basu son baka labarin sai kiga zuciyarsu ta sosu, da alama labarin akwai sosa zuciya ya kamata gobe ko jibi in mun fito exams mu fara binciken tarihin su k'ila mu d'au darasi cikin labarin", "tabbas kuwa haka za'ai ai ko indai su Goga ya kasance laifin da suka aikita babba ne wallahi ko wanene ko na ce wacece suka aikita ma laifin zan tsaya tsayin daka zan sanar da Sadeeg domin a makasu a koto dan banga ma anfanin barin irin su Goga cikin jama'a ba har abarsu suyi karatu ai hakan babbar barazana ce ga al'ummah"..........✍️





*ZAHRA ROYAL STAR CE*




Share fisabilillahi🥰🙏

*💔🧟‍♀️☠️SILAR MUTUWA🧟‍♀️☠️*💔
(Horror Story)





ZAHRA ROYAL STAR CE.......✍️








*ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION*






*DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN K'AI*



PAGE 1️⃣1️⃣➡️1️⃣2️⃣


Bayan kwana biyu izuwa yanzu exams d'in su Nawwara tayi nisa sosai sun tari mutane da dama domin jin labarin su Goga wasu ana tabbayar su kuka suke saki wasu kuwa fuskarsu ce zata canza daga farin cikin da suke ciki zuwa damuwa yau saura kwana d'aya su idasa exams d'insu suna shirin komawa gida duk da hutun semester ba wani mai yawa bane sati d'aya ne da y'an kwanaki sun samu wata mai suna Teemah ta ce zata sanar dasu ainahin abinda ya faru a yau shi yasa su dukansu da zumud'i suka fito suka nufi Teemah dake k'ark'ashin bishiya itama fitowarta kenan daga jarabawar dama su take jira suna zuwa suka zagaye ta ta ce "kun shirya jin labarin dake sa kuka domin kuwa labarin nan ba wani yawa ne dashi ba amma kawai ban tausayi", ta idasa maganar hawaye na wanke mata fuska su duka jikinsu harya fara sanyi da sauri Surayya ta ce "please Teemah karki karyar mana da zuciya tun yanzu mana muna sauraranki", gyara zama Teemah tayi ta ce "Shekara hud'u da suka wuce ko na ce biyar, ni na kasance k'awa ga Khairat, mutuniyar kirki ce sadda ta fara shigowa school d'in nan, tafiya take tana ta waige-waige domin kuwa zuwanta ne na fari, tuntub'e tayi littatafan dake hannunta suka watse a k'asa tana niyar kai hannu domin kwashe su idonta yayi mata tozali da hannun na miji a hankali ta d'aga kanta harta sauke idonta akan kyakkyawar fuskarsa kallonsa take cike da mamaki da kuma kallon rashin sani da sauri ya idasa kwashe book's d'in ya mik'a mata ya ce "sorry fa ni sunana Anwar tunda kika shigo school d'in nan naji ina son abota dake zamu iya zama abokai", idasa maganar yana aika mata da murmushin nasa wadda baya barin fuskarsa ita dai Khairat murmushi ta d'anyi mai ganin Teemah na tahowa yasa ta wuce sa bata ce komai ba shi kuwa girgiza kansa ya d'an yi yana cewa "kai mata komai sai anja aji", jin sunanta Teemah na cewa "lah Khairat kece haka da ranar nan Ohh keda Anwar ne can, ai Anwar ba ruwansa wallahi, yana da kirki ga son jama'a gashi da k'ok'ari yana k'ara koyar damu idan Malamai sun fita yana k'ara ganar damu bashi da matsala wallahi", da sauri Khairat ta ce "to fad'i ba'a tabbaye ki ba, na ce ki fad'a min ya halinsa yake ne daga ganin mutum kawai saina saki jiki dashi nidai wuce muje", dariya Teemah tayi ta ce "hmm kinfa sakko da kanki dan kuwa Anwar na fad'a na k'ara fad'a bashi da matsala Allah sarki bawan Allah bashi da kowa d'an talakawa ne a cikin garin katsina yake kinsan zakiyi mamakin idan ya koma katsina adai-daita saho yake ja domin rufawa kai asiri duk iyayansa sun raso shi ke d'au nauyin karantunsa da kansa wallahi mugun tausayi yake bani, dan Allah Khairat idan ma cewa yayi yana sonki karkiyi mai wulak'anci baki san nan gaba mi zai zama ba please na rok'eki", ta idasa maganar tana had'a hannuwanta waje d'aya alamar rok'o Khairat kuwa tuni hawaye sun wanke mata fuska da sauri ta juya inda ta barshi bata gansa ba sai dai bayansa data hanga yayi nisa dasu kamar ya sani ya waigo daga inda yake hana faman mata murmushi, itama murmushin ta mayar mai lokaci guda taji bala'in tausayin Anwar ya shiga zuciyarta.



Fita sukai wajan school d'in kad'an da yake nan aka kama masu gida da yake Federal University Dutsanma bata da hostel a cikinta.


Washe gari ita da Teemah suka shigo school d'in suna cikin tafiya suka hango su Goga suna nufo inda suke tafiya da sauri Teemah ta ce "kinga Khairat zomu koma in suka wuce sai mu wuce dan wannan mutanan suna da had'ari", "had'ari kuma?, Teemah to mi yasa aka barso suna shigowa school d'in?", cewar Khairat girgiza kai Teemah tayi ta ce "kamar baki san a cikin Najeria kike ba, to shima mai kud'i ne yana da kud'i sosai kud'in sa basu anfane sa da komai ba sai shaye-shaye da tara y'an iska yana k'ara lalatasu, ubansa ya mutu yabar mai mak'udan kud'ad'e sana d'an siyasa ne yasan mutune da yawa koda yayi

Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3Chapter 4

Please Login or Register in order to submit comment