You Cannot Download this book untill you login but you can read it .
Login Register
laifi ba'a gani sai a boye kinga zo mu wuce dan Allah karma su ganmu", ai kami ta rufe baki Goga da bud'ad'd'iyar muryarsa ya ce "ku dakata daga nan idan kuma kuka matsa na rantse da Allah sai na keta mutumcinku", jikin Teemah ne ya kama rawa gabanta yayi wata irin mummunar fad'uwa jin abinda Goga ya ce.
Goga na k'arasowa ya tsaya akan Khairat data rungume hannu duk da itama taji shakkarsa dakewa kawai tayi, kallonta yake har yana wani karkace baki yana fiddo harsha irin na y'an iska kawai basuyi tsammanin maganar da zata fito bakinsa kenan ba ya ce "ina sonki", ya fad'a yana kallon Khairat wani kallon banza tayi masa wani murmushi tayi ganin Anwar na nufo wajansu da sauri bawan Allah har yana had'awa da gudu yana isowa yaji Khairat ta ce "ni ga wadda nake so nan ya k'ara so", ta idasa maganar tana matsawa inda Anwar yake tsaye yayi mutuwar tsaye wata irin shegiyar dariya Goga ya saki ya ce "tabbas ina sonki kuma sha'awarki nake duk wadda ya ce zai shiga gonata to sai nayi SILAR MUTUWAR SA kima sa wannan a ranki shi kuma sakaran da keki so kece zaki ceceshi daga halaka", yana idasa maganar yaja y'an koransa suka bar wajan kuka Khairat ta saki ita da Teemah da sauri Anwar ya ce dan Allah ku daina kuka haka nan Insha Allah ba abinda zai iyayi inba abinda Allah ya rubuta a cikin littafin K'ADDARAR MU ba", share hawaye Teemah tayi ta ce "hakane amma har yanzu baku san waye Goga ba ina tsoron abinda zaije ya dawo wallahi", da sauri Anwar ya ce "babu abinda zamu gani sai alkhairi kunga kuzo mu wuce class kubar wannan maganar ma please", badan maganar zata iya fita a ransu ba suka shiga aji haka dai aka gama lecture's har uku ba abinda suka gane daga su har Anwar d'in dan kuwa damuwa ce dank'are akan fuskarsu dan yau Anwar ko tsayawa koyar da d'alibai bai ba suma kansu sunga yana cikin damuwa.
Har tsawon sati uku basu k'ara ganin Goga ba har hankalinsu ya d'an kwanta har soyayyar Anwar tayi tasiri a zuciyar Khairat soyayya suke mai cike da nutsuwa abinda basu sani ba shine Goga bawai kyale su yayi ba zuba musu ido yayi kuma yana sa y'an baradarsa suna sa mai ido akan Anwar da kuma Khairat zuciyar Goga a bushe take kamar tsohon arne kwata-kwata ba Allah a cikinta bare imani shed'an yana nan yana kitsamai mugun abun daya shirya musu dan har cewa yake "indai ba zai d'an d'ana zumar Khairat ba, to ya rantse da sarkin dake bosa mai lumfashi sai dai kowa ya rasa ta zai iya hallaka kowa akanta kai harma da ita, inta k'i basa had'in kai............✍️
*ZAHRA ROYAL STAR CE*
share fisabilillahi🥰🙏
*💔🧟♀️☠️SILAR MUTUWA🧟♀️☠️*💔
(Horror Story)
ZAHRA ROYAL STAR CE.......✍️
*ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION*
*DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN K'AI*
PAGE 1️⃣3️⃣➡️1️⃣4️⃣
Bak'ar rana ita ce ranar da Federal University Dutsanma da yawa wadda suke cikinta kai harma da cikin gari baza su manta da ita ba.
Washe gari cike da nutsuwa Khairat da Anwar suke tafiya dan Teemah bata samu shigowa school d'in ba dan kwata-kwata bata jin dad'i.
Kamar an jefoshi ya shiga gaban su yana zazzare idonsa irin na y'an shaye-shaye cike da muryarsa irin ta y'an iska ya ce "Khairat bazaki rabu da wannan malohon ba dai ko na rantse da wadda raina ke hannunsa idan baki rabu dashi ba nine zan zama SILAR MUTUWARSA indai a kanki ne kai kuma", ya idasa maganar yana kai dubansa kan Anwar yana tsaye ko gezar bai ba sai ma ya b'ude baki cike da rainin wayo ya ce "kai harka isa ka raba ni da RAYUWATA inba Allah ba koda yake kufa ba sanin Allan kukai ba ban tab'a ganin dabba...... Kamin ya idasa maganar Goga ya kai mai wani shegin naushi yana cikumo wuyan rigar sa, cike da tsananin tashin hankali da tsananin tsoro Khairat ta rushe da kuka tabbas babu abinda Goga bazai iyayi ba a kanta da sauri ta nufi inda suke da sauri Goga ya waiga yana ware mata jajayen idonsa ya ce "tabbas kin jamai mutuwa dan ba abinda zai hana ban hallaka sa ba ke indai ban same ki ba sai dai kowa ya rasa harke zan iya d'aukar RAYUWARKI", wani irin ras taji gabanta yayi wata mummunar fad'uwa har tana yin baya ta fad'i k'asa hawaye na k'ara b'alle mata wannan wacce irin k'addara ce haka take shirin faruwa da ita.
Da kyar mutane suka b'anb'are Anwar jikin Goga da kyar ya samu wunyansa ya dawo dai-dai dan ba k'aramar shak'a yayi mai ba, da sauri Khairat ta ce "dan darajar Allah Anwar kabar makarantar nan yau-yau d'in nan ina gudun abinda zaije ya dawo bazan tab'a yafe ma kaina ba idan wani abu ya same ka", "karma kice haka babu inda zani", yana idasa maganar ya tashi ya fice daga school dan kwata-kwata baya ma jin dad'in abinda ke faru dan dai ba yadda zaiyi ne har k'arar Goga yasha kaiwa amma babu abinda akeyi sai kaga kamar da gaske za'a d'au mataki amma sai dai kaji shuru.
Khairat kuwa ganin dare ya fara yi dan da k'arfe shadda tayi rana ke fad'uwa duhun dare ke mamaye ilahirin garin cike da tsananin tsoro take tafiya har tana hard'ewa dai-dai zata sha wata kwana wata bak'ar mota ta zo da gudu kamin tayi wani yink'uri suka jata da tsiya suka tusata cikin motar tana niyar ihu duk da school d'in sai mutune dai-dai ku kuma dai-dai kwanar ba'a cika binta ba saboda school akwai girma, suka sa tsunma suka d'aure mata baki hawaye ne kawai ke zuba ta idon Khairat kamar fanfo.
A wajan Anwar yana zaune a shi kad'ai domin d'ebe kad'ai ci ga gabansa dake fad'uwa kawai yaga dan-dazon maza a kansa rik'e da wuk'ak'e da sandina kamin ya ce tak suka rufesa da Uban duka kota ina baji ba gani baka jin k'arar komai sai na dukan da suke mai sai na ihunsa tun yana motsi har ya daina sai da suka duba ganin baya motsi da sauri wani cikin su ya ce "kai gayis kamar fa ya mutu muyi maza mubar gun nan ku tabbatar baku bar wata shaidar da za'a gane mune ba", sai da suka tabbatar sun kwashe duk wani k'arfe nashi sana suka ajiye shi tsakiyar titi dan ayi zargin mota ce ta bank'e sa dan irin bugun da zuka mai yadda kasan tirera ce tabi ta kansa Anwar kuwa dama rai tuni yayi halinsa tun farkon bugun da suka kaima dama ransa na gaf da fita sai ya zama sune sanadi.
A wajan Khairat kuwa bata tsinci kanta a ko ina ba sai a gaban Goga, zaune yake kan kuje wata irin dariya yayi yana cewa "yanzu akwai wadda zai iya cecanki wadda kike tak'ama kina so tuni yanzu na sani yayi bankwana da duniya kuma yaune zan cika buri na a kanki", wata irin zabura Khairat tayi tana zubewa k'asa wani irin kuka ta saki tana cewa "Wai kai wani irin bawa ne marar imani badai sawa kayi a kashe Anwar ba to wallahi dana bari ka keta mutumci na gara na mutu nima nabi masoyina na rantse bazaka tab'a cika burinka a kaina ba", Goga tashi yayi a zuciye yana kai mata wani bahagon mari ji kake tassss har saida Khairat ta kifa a k'asa tashi tayi tana dafe kumatunta iyanzu zuciyarta ta bushe bata ma tsoronsa k'ugunta ya kamo da sauri tasa hannunta domin hankad'e sa sai dai ina yayi mata mugun ruk'o, miyau ta tattaro ta tofa mai a fuska, runtse idonsa yayi cike jin haushinta ya k'ara kai mata wani marin har guda biyu tassss tassss tassss kake ji kamo gashin kanta yayi dake cikin hijab da k'arfi wata y'ar k'ara ta saki tana kallonsa da idonta da sukai jawur sai da ta dai-dai ci wajan mafitsarar sa tasa k'afarta da k'arfi ta daddage tana kaima wajan wani shegen naushi ba shiri Goga ya saketa yana sakin k'ara ai kamin kace mi ta d'auki wani k'aton k'arfe ta bibbigi duk wadda yasha gabanta da sauri ta b'alle K'ofar gidan tana fice da gudu hawaye take tana wani abun gudu gasu Goga dake binta a baya yana cewa "ku tabbatar bata shaba inba haka ba wallahi dukanku saina yanke muku mummunan hukunci", jin abinda ya ce suka k'ara k'aimi dan sunsan Goga kamar mai zuciyar fir'auna bashi da imani ko kad'an, gudu take tana waige harta hau babban titi bata sani ba wata babbar mota ce ta taho gadan-gadan kanta ga mai motar nata so ya kawuce mata amma ina sunzo gaf da juna Goga ne ya fasa wata irin k'ara yana faman cewa "keee Khairat baki da hankali mota ce fa gabanki", wata irin dariya ta saki tana cewa "ai dana bari ka kassara rayuwata gara mutuwa ta cinmini a yanzu kayi SILAR MUTUWAR masoyi na ka rubuta ka aje zaka girbi abinda ka shuka nan bada dad'ewa ba in...... Kamin ta idasa maganar ma motar tayi gaba da ita ba k'aramar banka ce akai ma Khairat ba dan sadda zata dawo k'asan titin kanta ne ya fashe dan har kana iya hangen tsakiyar kanta, shi kansa Goga ya girgiza da sauri suka bar wajan mai motar shima bai tsaya ba guduwa yayi (kai Allah ka kasa mufi k'arfin zuciyarmu Najeria kenan).
Wayewar gari ba k'ara min tashin hankali garin Dutsanma da kewaye aka tashi dashi ba Teemah kuwa kasa d'aukar maganar kanta da tunaninta yayi suma ta rink'a yi har saida akayi asibiti da ita sadda dangin Khairat zasu k'araso nanma sabon tashin hankali ya k'ara b'arkewa kuka kam ba'a magana duk wadda ke cikin school d'in nan indai mai tausayi ne sai da yayi kuka imani ya k'ara shigarsa har mutuwar Anwar an danganta tane da had'ari yayi makarantar kanta ta girgiza har saida aka daka ta da komai na kwana biyu.
A sadda Teemah zata farka kuka take tana cewa "wallahi Allah ba mutuwar Allah da Annabi ce sukayi ba kashe su akai" ba wadda ya d'au maganar da mahimmaci saima aka dankanta da hakan da cewa mutuwar ce ta zautata ba k'aramar jinya Teemah tayi ba k'arshe ma karatun katseshi tayi ta ce ta hakura da karatun, sai dai abinda ya dakatar da Teemah daga barin school d'in duk sadda nayi niyar barin school d'in nan ina yawan wasu irin mafarkai masu rikita min tunaninta a cikin mafarkin ina yawan ganin Khairat tana cewa "in daina sa damuwa a raina kuma kar nabar karatu na akan wannan abun k'arshen Goga bazai kyau ba in zauna a cikin makarantar nan zanga yadda Allah zaiyi ikonsa akan Goga".
Teemah ta idasa maganar tana kallon su Surayya yadda kowa daga cikinsu tunkan aje k'arshen labarin suke kuka harda shashsheka ita kanta kuka take Surayya ta share hawayen tana tashi tsaye kamar wani abu ya shiga jikinta muryarta ta koma wata iri ta ce "tabbas saina sa su Goga cikin uk'uba da kansu zasu kai kansu koto kuma dole a yanke musu hukunci dai-dai da laifinsu", cike da mamaki suke kallonta har Teemah kamin suyi magana suka nemi Surayya suka rasa sama ko k'asa babu ita kamar ba'ayi wanzuwarta a wajanba sosai suka shiga tashin hankali anya Surayya ita d'aya ce kuwa.......✍️
*ZAHRA ROYAL STAR CE*
Share fisabilillahi🥰🙏
*💔🧟♀️☠️SILAR MUTUWA🧟♀️☠️*💔
(Horror Story)
ZAHRA ROYAL STAR CE.......✍️
*ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION*
*DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN K'AI*
PAGE 1️⃣5️⃣➡️1️⃣6️⃣
Wani irin daji ne mai duhun gaske su Goga suna tashi suka tsinci kansu a ciki ga wasu irin koke-koke ba dad'in ji, wata irin dariya suka ji daga bayansu dariyar na wata irin tashi gaba d'aya kogunan dake dajin da bishiyoyi har wani amsawa suke suna wata irin girgiza waigawar da zasuyi suka ga wata mace sanye da take da wasu bak'ak'en kaya fuskarta rabi a k'one idonta ko d'igon baki babu gashin kanta na tashi sama kamar iska na hurasa sosai suka tsoron ta suka fara ja baya Goga ne mai k'arfin halin bud'e baki ya ce "bawar Allah shin wai ke wacece da kiketa azaftar damu haka?", wata dariyar ta sake yi wata irin murya bud'ad'd'iyar muryar ba dad'in sauraro ta cika musu kunne har saida suka runtse ido muryar na fitowa a rarrabe ta ce "harka manta da abinda kayi duniya to shine yanzu kuke girbar abinda ka shuka kaida mutanan ka wallahi Goga kamin in bari kaje wajan shari'a su yanke ma hukunci saika d'and'ana kud'arka", zubewa Goga yayi a k'asa ya fashe da kuka kamar yaron goye yana cewa "kayiwa Allah kabar mu haka wallahi munyi laushi kuma nida kaina zanje kotu domin yanke min hukuncin abinda nayiwa Khairat ne nasan cewa shine yake biya-biyata", wata dariyar ta sake kecewa da ita mai ban tsoro ta buga mai wata irin tsawa ta ce "kai har kasan Allah sadda zaka cuci mutane ai sun had'a ka da Allan ka kyale su ne dan haka yanzu ma sai kunyi muguwar nadamar da har abada bazakuyi marmarin cutar wani ba har abadan kuwaaaaa", ta idasa maganar tana buga wata sadda dan danan wasu irin namun daji masu had'arin gaske suka wanzu a wajan.
Kamin kace mi su Goga sun arce da mugun gudu cikin jejin umarni taba namun daji ai kuwa kamin ta rufe baki sun bisu da mugun gudu su Goga ganin yadda suke gudu namun dajin gudun nasu kamar walk'iya haka suke gudun.
Gudu suke suna k'ara nausawa cikin jejin ko kallon gabansu basa yi ga namun dajin dake binsu masu had'arin gaske da yawa cikin mutanan Goga sun fara gajiya da gudun kuma ba damar tsayawa shi kansa Gogan numfashinsa har d'aukewa yake mak'oshin sa ya bushe k'amas wata irin k'ishir ruwa yake ji kamar zai mutu tuntub'e yayi da wani mugun icce ya buge kansa yana fad'uwa k'asa wata irin juyawa kansa yayi yana sarawa kamar zai rabe gida biyu zubewa yayi a wajan numfashinsa na barazanar d'aukewa su kansu mutanan Gogan zubewa sukai suna faman sauk'e numfashi sun riga sun sadak'ar namun dajin na k'arasowa zasu cinye su.
Sai dai namun dajin na k'arasowa suka b'ace b'at kamar babu kowa cikin jejin dajin ne yayi cit baka jin ko tari wata irin ajiyar zuciya suka sauke.
Wata irin k'ara daga cikinsu wani ya saki da sauri su Goga suka matsa kusa dashi hankalinsu yayi mugun tashi ganin wata shirgegiyar mage bak'a wulik girmanta ya wuce misali sai tayi girman wani jaririn ta kama k'afarsa da wasu irin farce zak'o-zak'o ta karceshi da k'arfin tsiya shi kuwa sai birgima yake dan wani irin azaba yake ji kamar ana yankan naman jikinsa, kallonsu take da jajayen idonta masu firgitarwa kamin suyi wani yink'uri ta b'ace b'at wani irin tsoro ne ya dirar masu ganin babu magen babu alamarta sukam sun shiga uku wannan waccce irin masifa ce haka.
Basu k'ara tsurewa ba sai da suka ga d'an uwansu wadda magen ta yakusa yana wata irin girgiza da wani irin gurnani kamar mage ta samu nama matsawa sukai kusa dashi domin basa taimako sai dai mi. Wata irin zabura sukai ganin idonsa ya koma fari fat tsakiyar bak'in ya koma wata irin kala hakuran bakinsa sun koma irin na masu shan jini masu tsinin gaske jikinsa na wata irin babbank'arewa kamar ana kakkarya k'asusuwan jikinsa wata irin mik'ewa yayi kamar an basa umarni yana wani irin gurnani.
A wajan su Zuby kuwa k'awayanta na komawa gida sukaita zuga Zuby akan cewa akwai wani boka mai aiki kamar yankan wuk'a, sha yanzu magani yanzu aikinsa ba k'arya yana yi k'anwarta ta ce "ai Aunty wallahi idan baki shiga gidan Ahmed Sadeeg Garkuwa ba sai na ce kinyi asara babba kuwa, koni na samu saina shiga wallahi had'uwa irinta Garkuwa ba abinda bazaka iyayi kan wannan bawan Allan ba kai ai Allah ya zuba halitta ga wanga mutune inji sakwatawa, wai ga kud'i ga kyau komai ya had'a ai dole ayi hauka a kansa ita kuma waccar banzar Surayyar harta isa ta ce ita d'aya keda shi ina tama shirya yanzu aka fara wasan muda ita", da sauri Zuby ta ce "kware kuwa hakane babu abinda bazaka iya ba akan irin su Garkuwa yanzu yaushe zaku raka ni wajan bokan a shirye nake nayi komai na kashe ko nawa ne", da sauri cikin k'awayan nata guda biyu wata ta ce "ai ko yanzu inkin shirya kina da uwar kud'in ki zamu iya zuwa", da sauri suka mik'e Zuby na cewa "ku tashi mu tafi da zafi-zafi ake bugun k'arfe ai ba zama inta kwana a zaune ni a tsaye na kwana tunda ta bari na kyalle ido naga Garkuwa hmm kota halin yaya saina same shi"...........✍️
*ZAHRA ROYAL STAR CE*
Share fisabilillahi🥰🙏
*💔🧟♀️☠️SILAR MUTUWA🧟♀️☠️*💔
(Horror Story)
ZAHRA ROYAL STAR CE.......✍️
*ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION*
*DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN K'AI*
PAGE 1️⃣7️⃣➡️1️⃣8️⃣
Kamin sunyi wani yink'uri ya kaima d'aya daga cikinsu cafka ya kada shi k'asa yana wani irin gurnani yana niyyar kai mai cizo kokowa suka farayi da sauri Goga ya d'auki wani itace ya kaimai duka a kai.
Sakinsa yayi da sauri yana fad'uwa k'asa ya rik'e kansa yana sakin wata irin k'ara da gurnani.
Da sauri Goga yaja d'ayan suka fara gudu ganin yadda ya tashi kamar ba'a kaimai duka ba ya fara binsu a bayansu yana shin-shine shin-shine gudu suke suna waigen bayansu ganinsa suke kamar walk'iya yana matsowa gare su.
Goga ne ya saki wata irin k'ara yana zubewa k'asa k'afarsa ya kama ganin wata irin k'aya mai tsinin gaske ta cakesa a tafin k'afarsa harta b'illo saman k'afar tasa da sauri sauran mutanan sa suka matso gare sa suna tabbayar lafiya yayi sauri su cigaba da gudu dan gaf yake da isowa gare su.
Da kyar Goga yasa hannunsa ya runtse idonsa yana cire k'ayar da sauri wata irin k'ara ya saki ta azaba wani irin zafi yake ji har tsakiyar kansa.
Ba yadda ya iya haka suka tashi yana d'angyashi suka cigaba da gudu.
Jan birki su kai su dukansu ganin gabansu wani irin ruwa mai shegen yawa ya tare musu hanya ruwan duk ya cinye hanyar ruwan sai yayi girman wani garin waigawa su kai ganin ba kowa dage binsu abin mamaki ma sai suka tsinci muryar wadda ya zama horror ya dawo dai-dai yana cikinsu cike da tsananin tsoro da mamaki suka bisa da kallo kauda mamakin su kai ai babu abinda ba zasu iya gani ba.
Da saui Goga ya ce "ga mai buk'atar shan ruwa yayi maza yasha kamin mubar wajan nan dan ruwan nan yadda yake da yawan nan zai iya anbaliya ya cinye mu gaba d'aya", ai da sauri suka duk'a domin shan ruwan sai dai mi ruwan ne ya zama wani irin jini mai kaurin gaske da kakai hannunka jini ne zaka d'ebo inka cika matsawa jikin ruwan kuwa ji zakayi kamar za'a kawoka ciki, da sauri suka tashi suna zare ido y'an hanjin cikinsu na hautsinawa iyanzu da yawa cikin su sai tsinewa Goga suke suna danasanin kasancewa tare dashi amma tsoro ya hana su nunawa a zahiri sai dai a zuci da yawa cikin sun fidda rai da fita wannan jeji anya ma za'a maida su cikin gari kuwa irin wannan jejin ko a film basu tab'a ganin irinsa ba wasu daga cikinsu zubewa sukai suka fara durzar kuka kamar wasu mata.
A wajan su Nawwara kuwa sun kasa zaune bare tsaye gashi sun kasa gayama Garkuwa dan mugun shakkar gaya mai suke to su cemai mi ma matarsa ta b'ace kai abinma ba tsari kamar an datse musu baki sai zarya suke cikin dare har gari ya waye da kyar suka shiga exam d'in k'arshe suna jimamin Surayya kar ta rasa wannan damar sai dai abinda ya basu mamaki suna shiga class d'in suka ganta zaune har Teemah ta girgiza da ganin ta a cikin class d'in a inda ta sab'a zama a nan suka hangeta suna fitowa exams d'in kuma kamar an yashe musu duk wata tabbaya duke dank'are cikin ransu murna ma suka kamayi da murnar zuwa gida.
Basu b'ata lokaci ba sukayi sallama da Teema inda Surayya ta ce "karki damu Teemah damun dawo hutu zakiji an yankewa su Goga hukunci Insha Allah", su duka mamaki sukai sun kuma kasa tabbayar tayaya hakan zai faru a cikin zuciyar Surayya kuwa cewa take a sadda zamu dawo su Goga sun d'and'ana kud'arsu sun kai k'arshen wahaluwa a dajin k'are kukanka, wata dariya ta saki a cikin zuciyarta dan yanzu ita kanta tasan akwai wani abu dake shiga jikinta kuma har magana sunyi kuma ta d'au mata alk'awarin ta cigaba da zama jikinta har sai an yanke ma su Goga hukunci.
Garkuwa ne ya aiko da mota y'ar ubansu wadda zata kai su Surayya Katsina dan duk a nan suke shi kuma ya riga su tafiya yahau jirgi zuwa Abuja a nan komai nasa yake kuma a nan yake zaune.
Surayya sai hushi take danmi zai tafi baisuyi sallama ba shima kansa yasan yayi laifi jira yake ta d'an huce tukun ya hau aikin lallashi, a sadda suka isa Kt sai da aka sauk'e su Nawwara sana aka wuce da Surayya unguwar sabon titin kwad'o unguwa ce sabuwar unguwa masu kud'i suka fara gini a cikinta ta zama unguwa ta masu dashi a nan aka sauk'e Surayya dai-dai wani gida mai shegen kyau da tsari da gudu ta shiga cikin gidan tana kiran Ammee ita kanta Ammee da sauri ta fito tana rungume d'iyar tata suna murnar ganin juna.
A wajan su Zuby kuwa wani irin dokar daji ne cikin wani mugun k'auye gidaje jefi-jefi har saida suka daina ganin tsilli-tsillin gidajen rugar sana suka aje motarsu gefan titin garin daba wani titi bane birji ne kawai, suka fara kutsa kansu cikin dokar dajin ko tsoro babu a ransu sai da sukayi tafiya mai nisa harsun jigata ba'a saba da wahala ba, sana suka hango wata bukka daga gefe wata wuta ce ke ci sai wata kwarya dake gefe tana fitar da hayaki.
Daga nesa aka buga musu wata irin tsawa aka ce "ku dakata daga nan la'anannun Allah nasan abinda yake tafe daku kina su ki mallaki Ahmed Sadeeg Garkuwa ko ba haka bane?", Da sauri bakinta har kyarma yake ta ce "hakane boka ina so a mantar dashi Surayya ya manta da ita kwata-kwata a rayuwarsa a tusa mai soyayyata cikin ransa sai abinda nake so zaiyi", boka ya fara dube-dube da sauri ya daka masu wata irin tsawa har suna zabura ya ce "dakata wannan abinda kike so ayi ba mai yiwuwa bane ban tab'a ganin aiki mai hatsari irin naki ba karki k'ara kiran sunan Surayya a nan shi kansa Garkuwar yana da kariya a jikinsa alwala bata sub'oce mai daga jikinsa kuma yana yawan azzakar dan haka ba abinda zamu iyayi a kansu", "amma boka itafa Surayyar" cewar Zuby zuciyarta cike da k'unci wata irin dariya ya saki har dajin na girgiza sun tsorota da dariyar har suna rungume juna sai zare ido suke tsawar da ya buga musu ce yasa suka k'ara had'ewa waje d'aya ya ce "ba na ce karki k'ara kiran sunanta a nan ba inba so kike dagani har ku mu shiga cikin wahala ba ku tashi ku fice min a nan kona sa aljanu su fitar min daku kuma ku sani duk inda zakuje duk wani boka wadda yake ji da tsafi magana d'aya ce zai sanar daku shi ne wannan amsar dana baku sai dai in kud'inku zaici ku tashi in daina ganinku daga nan", ya idasa maganar a tsawace.
Ai da gudu suka fito daga dokar dajin suna sauk'e numfashi da sauri k'anwar Zuby mai suna Shahida ta ce "amma wallahi wannan bokan baisan aikinsa ba haba ai wallahi sai mun k'ara zuwa wani