Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

*👩‍❤️‍👨💞 WAYAFI K'AUNATA 👩‍❤️‍👨💞*
(Love Story)




PAID BOOK #500






MALLAKIN
*©ZAHRA ROYAL STAR*





*Littafin kud'i ne wadda ya shirya yin tafiyar dashi zai iya turo kud'insa, ko katin MTN ko hoton katin saika turo shaidar biya #500 ne kacal*




8130479973
*FATIMA RABI'U OPAY BANKA*




Zaka turo shaidar biyanka ko hoton katin ta wannan number d'in,
(08130479973.08035023054)





Free Page 1-2



بسم الله الرحمن الرحيم العالم




Gombe state Kauyen AKKO, Babban kauye ne kusan ma kamar Local Government ne Amma ba a bashi LGA ba, garine na fulanin asali kana Shiga ba sai an fada maka ba,




Maryam Muhammad Amadu mai Shano shine cikakken sunana na tasu cikin Babban gida mai d'auke da sassa daban-daban Amadu mai Shano shine asalin mai gidan yana da matarsa guda d'aya mai suna Kubura wacce muke kira da Iya, da y'ay'a biyar Baffah na Muhammad, sai Kawu Sule shine mai bima Baffa na sai Kawu Iro sanan sai Kawu Mamman sai autar su Gwaggo Fati, dukan su mazan a cikin gidan suka yanki fili ko wanne da shashinsa dukan su suna da aure Kawu Sule yana da mata Rabi da y'ay'a biyar Abbas shine Babba sai Mansur Hafiz sai Gaje da Hajara itace auta , sai Kawu Iro yana da mata mai suna Hindatu da yara uku Naja'atu Sa'ida sai dan auta Ismail, Kawu Mamman shima yana da mata da yara guda biyu, Khamis, sai Zeena, takan bar y'arta Zeena ta kula dani, tun sadda na taso na taso na tarar da kaina a cikin gidan Baffah na ya rasu tun ina k'arama, Umma na kuma ta fita daga cikin gidan Amadu mai Shano tayi wani auran, ta barni wajan dangin Baffa na tun tasowata gidan mu hud'u ne sa'anin juna ni sai Naja'atu sai Hajara da Sa'ida sannan Zeena tun farko na kasance rikon kaka dan haka na taso ba kyara ko tsangwama a gidan bani da matsala da kowa sai Inna Rabi wato matar Kawu Sule ta tsaneni a gidan a cewarta wai na tare wa y'an uwana jin d'umin Kakarsu Iya dan haka nakan d'an jima ban lek'a sashin Kawu Sule ba, duk da kasancewar shid'in da yaransa suna matuk'a sona idan aka cire mutum d'aya Ya Abbas ya tsane ni kamar mi baya ma son gani na nima na taso da tsananin tsoronsa mugune nak'in k'ari a cewarsa na fiye shagwab'a da son jiki dan haka sam tamu batazo d'aya dashi ba, a duk sanda yazo garin hutu da yake yana karatu ne can cikin birni, nakan sha jinin jikina har sai ya koma nake samu na sake bani kad'ai bama duk yaran gidan tsoronsa suke, sai Ya Hafiz shi yana matuk'ar kulawa dani sosai duk sadda zai fita ya dawo da kalar tsaraba da zaiyi min duk sadda zai shigo sashin Iya da murna nake tarbarshi, tunda Inna Rabi ta nuna bata son duk wani d'anta ya nuna min kulawa, sai ya rink'a cewa Iya yayiwa tsaraba, amma duk haka tana ankare da yadda Ya Hafiz yake nuna tsananin kulawa a kaina tayi fad'an harta gaji kullum idan tana mai fad'a ta rink'a cewa Ya Abbas ne kawai shine ya d'akko halinta dan gani take yasan abinda take so yasan abinda bata so, shi ko a duk sanda tace haka basarwa yake abunda ta kasa ganewa ga yaron nata shid'in sawun keke ne, baka gane gabansa bare bayansa, sanan ya kasance miskili ne ba kowa yake ganin dariyarsa ba a duk yaran gidan amma kuma ni a yadda nake gani duk yafi tsana ta akan kowa, Gwaggo Fati dake aure a can cikin birni a wajanta yake zaune yana karatunsa,sauran mazan gidan duk anan sukai karatun nasu, shi yasa nafi zuwa sashin Kawu Mamman a kullum can nake yini matarsa bata da matsala ta d'auke ni kamar ita ce ta haife ni, dan haka shi yasa nafi sakewa da ita, Kakata Iya Mai dogon zango tana k'ara sona ita ko Inna Rabi tana k'ara tsanata da d'anta Abbas yayin da Ya Hafiz ke nuna min tsantsar kulawa a gefe guda wasu har sun fara zargin ko sona yake, ga K'awaye na kuma y'an uwana abokan wasana suna d'ebe min kewa,



Irin wannan rayuwar ke gudana a ahalin Amadu mai Shano wannan kenan mu shiga cikin labarin kai tsaye.



Tafiya muke gaba d'aya y'an matan gidanmu tasowar kenan daga islamiya, cike da farin ciki muka shiga cikin gidan namu sai dai, fara'ar tamu ce ta rage shigarmu gidan jin yaran gidan na cewa wai Ya Abbas ya zo yau, wani irin miyau na had'iye dan nasan had'uwar bata dad'i, ko wanne b'angaransu ya nufa daka kallemu kowa ya k'ara shiga taitayinsa jin Boss ya iso gari Allah ya gani har bamu so yazo garin saboda bak'in halinsa.


Kai tsaye sashin Kakata na, nufa tun waje nake faman kiranta ina faman cewa "Iya ta na dawo kina ina ne", wani tsaki naji anja daga baya na da sauri na waiga ido na ne yayi min tozali dashi, dake zaune kan tabarma, alama gaida Iya yazo yi, bud'e baki yayi cike da miskilancinsa ya ce "wai ke yaushe zakiyi hankali ne kullum kina girma amma ba hankali, yanzu da kike kwala mata kira muryarki na tashi kamar ba mace ba, baki iya bari ki k'ara so gaki ga ita kina abu sai kace mahaukaciya" zunb'uro baki nayi ina k'unk'uni Allah ya gani da nasan yana wajan Iya da bazanyi ganganci shigowa ina kwala mata kira ba,



Iya dake fitowa duk taji mi yake cewa tana sababi tana cewa "wai ni kam Abbas miye wannan yarinyar ta tare maka ne kasa yarinya a gaba ka hanata rawar gaban hantsi, bana son irin haka fa, idan takurata kazo kayi tashi-tashi bana son gaisuwar, haka kawai abi a takurama marainiyar Allah", tashi yayi ya fice yana murmushi dan ya saba da matsifar Iya indai aka tab'a wannan yarinyar Maryam,



Niko cike da farin ciki Iya ta shigar min na rungume ta cike da shagwab'a na ce "Iya tun d'azo nake d'okin ganinki shine fa dama na sanar dake ashe wannan Ya Abbas d'in yazo ni banso zuwansa ba wallahi", na idasa maganar ina kwab'e fuska, dariya tayi tana saki na ce "keni sake ni uwar son jiki kamar mage kuma ki rage shiga harkarsa kinsan abun kad'an yake jira dama ya had'a ku", zunb'uro baki nayi ina bubbuga k'afa na ce "amma Iya ai kinsan bana shiga harkarsa shine ma yake shiga tawa kifa duba tunda na shigo ko lura banyi dashi ba amma ya fara zazzaga min matsifa sai kace jirana yake", "jiran naki yake mana kinga ki wuce ki cire kayan islamiyar nan ga abinci can ki wuce kici ki manta da al'amarinsa fad'anku ai baya k'arewa na rasa mi yasa hakan", cewar Iya.






*KADUNA* POV


Zaune take akan cinyar mijinta sai zuba mai shagwab'a take k'ara rungumeta yayi, cike da tsananin sonta ya ce "Ohh my Noor kina ritani da shagwab'ar nan taki fa minene kake so", shafa d'an k'ara min sajenshi tayi tana kallon cikin idonsa cike da son mijin nata ta ce "to ai sonka ne yake azalzalar zuciya ta indai muna tare sai kayi hakuri da rigimar tawa", ta idasa maganar cike da wata shu'umar murya wacce ta kashe mai jiki da ruhi "Ohh my Noor wannan salon naki shi yasa kullum kike k'ara shiga raina", cewar Ramadan,


Tashi tayi tsaye daga ita sai wata y'ar ficiciyar riga iya gwaiwa, ta fara d'an tafiya cike da jan hankali, binta yayi da kallo kamar wani tsohon maye yana lumshe idanuwansa da suka fara canza launi.


Suna cikin wannan yanayi kamar daga sama suka tsinkayi muryar Ya Aysha cike da tsana Aysha ke bin Munnira da kallo, ganinta da wata y'ar ficiciyar riga yasa cike tsanarta ta ce "to makira ai da wa'innan y'an iskan kayan naki irin na karuwan farko kika gama da K'anina tashi ki bamu waje ina son magana dashi" ta idasa maganar tana warga ma Munnira dake tsaye hararara Munnira kuwa wani irin kuka ne take jin na shirin taso mata, da gudu tayi uwar d'aka Allah ya gani dangin mijinta basa sonta, hatta uwar mijinta, sun taso ta gaba, daga aure duka shekararsu biyun dayin auran har sun fara mata gorin haihuwa abun na mugun ci mata rai bata da matsala da mijinta amma danginsa sune babbar matsalar ga abunda ke k'ara mata fargaba suna son tusamai dole sai ya k'ara aure gani suke kamar ta asirance masu d'an uwa abunda basu sani ba tsantsar kulawa ce da take ba mijin nata, kuka ta fashe dashi tana fad'awa kan gado.


Ramadan dake zaune rantsa idan yayi dubu ya b'ace, wallahi baccin Ya Aysha Yayarsa ce da sai ya mata rashin mutum ci, kodan sunga kusan shine k'ara mi a cikin su shine zasu rink'a wulak'anta mai mata, d'aure fuska yayi tamau, zaunawa tayi kusa dashi tana tab'e baki tana cewa "ai dole ka d'aure min fuska mana an tab'a y'ar gwal to sak'on Hajiya ne ta ce a gaya maka ta baka nanda sati d'aya kaje tana son ganinka, kuma zata kawo ma matar da take so ka aura dan baza mu zuba ido mu barka da wannan shu'umar matar taka ba ehe" wani irin kallo yabi Aysha dashi cike da tsananin b'acin rai ya ce "ni gaskiya bana da niyar k'ara wani aure wai mi Munnira ta tsare muku ne ni banga wani abunda take muku na rashin dacewa ba sai ma k'ok'ari take taga ta kyautata muku, amma bakwa gani ya kuke so tayi ne wai?" ya idasa maganar cike da tausayin kansa da kuma matarsa yasan halin Hajiyarsu muddun ta tsani mutum to ya bani idan taso abu kuma sai anyi Aysha kuwa da ta tashi cike da matsifa ta ce "kaga dakata Ramadan bani ce zaka ba wannan amsar ba Hajiya zakaje ka bawa kuma da kake kare matarka uban mi take a cikin gidan nan idan ba taci ta kwanta ba Mtsww aikin banza kawai tama ji da kyau wallahi sai Halima ta shigo gidan nan" tana idasa maganar ta fice daga cikin gidan.


Ramadan kuwa zaro ido yayi yana mai-maita Halima badai Halima d'iyar Kharima ba k'awar Hajiya ba wadda bai san Kharima da bin bokaye da Malaman tsubbu ba, yanzu irin wannan matar take so ya aura idonsu ya rufe basa ganin gaskiya.


Cike da tashin hankali yake kallon Munnira dake tahowa tana zama kusa dashi taci kuka kamar ba gobe idonta sunyi matsifar ja, d'an kwantawa tayi jikinsa cike da tausayi ya k'ara rungumeta zai bud'e baki yayi magana ta tari lumfashinsa ta ce "mijina basai kace komai ba na sani ba laifinka bane sana kayi biyayya ga abunda Hajiya ke so shine zaka ga dai-dai bazan tab'a iya hanaka kabi umarnin iyayenka ba " ta idasa maganar hawaye na zuba a cikin idonta, shima kansa idonsa ya kad'a yayi jawur, cike da rauni ta fad'a jikin mijin tana, fashewa da kuka tayi, ta kasa rik'e kukan zuciyarta sai zugi take mata..............✍️








ZAHRA ROYAL STAR CE



SHARE FISABILILLAHI 🥰🙏


*👩‍❤️‍👨💞 WAYAFI K'AUNATA 👩‍❤️‍👨💞*
(Love Story)




PAID BOOK #500






MALLAKIN
*©ZAHRA ROYAL STAR*





*Littafin kud'i ne wadda ya shirya yin tafiyar dashi zai iya turo kud'insa, ko katin MTN ko hoton katin saika turo shaidar biya #500 ne kacal*




8130479973
*FATIMA RABI'U OPAY BANKA*




Zaka turo shaidar biyanka ko hoton katin ta wannan number d'in,
(08130479973.08035023054)





Free Page 3-4



بسم الله الرحمن الرحيم العالم



D'akina na shiga ina mita a zuciyata harna gama cin abincin ina k'unk'uni da takaicin Ya Abbas shi dai idan bai k'untata min ba, baya jin dad'i.


Iya ce ta shigo tana kallo na ta ce "nikam Maryam kin shiga wajan Kawunki Mamman Zeena ba lafiya ki gano ta?" d'an tashi nayi da sauri ina cewa "ayya Iya ai ban sani ba, da kamin ma na shigo nan saina lek'a na gano ta" Iya dake zaune kusa dani ta ce "eh ya kamata dai kije yanzu daga nan ki wuce shigon d'an lami mai kanwa ki sayo min, zanyi ma wancan mai bak'ar zuciyar d'an wake".


Tashi nayi ina b'ata rai tunda naji ta ce d'an wake nasan dama shi zatai mawa amsa nayi ina cewa "Allah danke zanje amma indan halinsa ne baza ka mai komai ba, nikam duk yau banga Ya Hafiz ba?" na idasa maganar ina kallon Iya, tafiya na farayi naji maganar Iya tana cewa "dan Allah karki dad'e Hafiz kuma zaki gansa k'ila dakin fita ai uwarsa ce mai bak'in hali itama inaga ita ta hanasa shigowa".


Nidai idasa ficewa nayi ina jin Iya ta fara masifa danmi zasubi su takura min, mina tare musu ne?, haka kawai sun taso ni gaba, ina tunani na idasa sashin Kawu Mamman, da fara'a matarsa ta tarbeni kamar yadda muka saba, sai da na duba Zeena da jiki har tana jana wai dodo na ya dawo, dariya nayi na ce "dodon kuwa dai, Allah bawan Allah nan ko a hanya banso mu had'u, kinga fa daga dawowarsa sai da yayi min masifar tasa" na idasa maganar ina jan tsaki har cikin raina nima nake jin na tsani Ya, Abbas kamar yadda ya tsaneni, dariya tayi min tana cewa "hmm bari Maryam nima nan tsoro yake bani jiki na har kyarma yake idan muka had'u ko a hanya, bare in ni kad'ai ce, wai amma a haka Sa'ida ke sonsa har wani yanga take idan ta gansa k'arfin halinta mamaki yake ban" tashi nayi ina cewa "uhm ita taji zata iya wahala, Zeena yoni ko mazan duniya sun k'are ai bazan tab'a zab'ar Ya Abbas ba, kinga bari na tashi na tafi aiki na fa Iya tayi".


Tashi tayi tana d'an b'ata fuska ta ce "kai Maryam daga zuwa sai tafiya kinga daga zuwanki har ji nayi na warke ma" dariya nayi mata na ce "kinsan halin Iya dama ta ce karna dad'e tasan idan na shigo sashin nan har mantawa nake lokaci ya ja", daga bayanmu mukaji muryar Aunty (mamar Zeena kenan haka muke ce mata), tana cewa "a'a duk zaman nan dama harda aike akai miki maza to tashi kije kar taga kin dad'e, idan kuna labarin nan naku ai bakwa ji baku gani".


Dariya mukai gaba d'ayanmu Zeena na niyar raka ni da sauri na ce "la kiyi zamanki kinji ki da k'arfin hali keda baki da lafiya, bari yanzu zan dawo wancan mugun wai Iya zatai ma d'an wake" na idasa maganar ina ficewa daga sashin.



Ina gaf ficewa daga zauran gidan namu kawai naji munyi karo da mutum kamin nayi wani yunk'uri naji an hankad'eni ana d'auke ni da mari tasssss dafe kumatu nayi hawaye na zubo min, nasan ba kowa bane sai Ya Abbas shi d'in ne kuwa jin saukar maganarsa a kaina kaina, na k'asa sai da na d'ako ba shiri jin wata uwar tsawa daya daka min yana cewa "wai ke dabbar ina ce kwata-kwata ba kiyin abu cikin hankali kina tafiya buguzun-buguzun sai kace ba mace ba gidan ubanwa ma zaki?, da yammar nan dare ya kusa" wasu irin hawaye ne naji sun k'ara zubo min zuciya na tuk'ukin bakin ciki naji zafin maganarsa ta farko daya kira ni da dabba, ko kallo bai ishe ni ba, na k'ara jin saukar maganarsa a kaina "ba magana nake miki ba ko sai na tattakaki a nan wajan shashasha kawai", bud'e baki zanyi domin yin magana kawai kuka ya k'ufce min.


Maganar Ya Hafiz ce ta katse mu gaba d'aya cike da kulawa ya matso kusa dani kama hannu na yayi yana bin Abbas da kallo tsaki Abbas yaja "Mtswww" yana barin wajan, kallo na Ya Hafiz yayi yana sa hannunsa ya sharemin hawayen dake sintiri akan kumatu na ya ce "shittt kayi shuru haka nan idan kina mai kuka a koda yaushe to kullum zai rink'a saki kukan ne, kiyi hakuri kinji inda sabo yaci ace kin saba da halinsa, muje na raka ki, mi zaki sayo ne?" murmushi na d'anyi ina jin zuciyata na yin sanyi dan ganin Ya Hafiz d'in na bud'e baki na ce "kanwa zan sayo kuma mugun fa shi Iya zatai ma abinci" da sauri yasa hannunsa mai taushi ya toshe min baki ya ce "Ohh my Maryam bana hana ki kiransa da mugu ba ki daina ba kyau kinji Yayanki ne shi", zunb'uro baki nayi cike da shagwab'ar da ta zame min jiki na ce "to amma Ya Hafiz ai mugunne shi" Ya Hafiz dake murmushi yana kallo na wannan shagwab'ar tawa tana matuk'ar birgesa ya ce "kashh bana hana ki fad'a ba?" dariya nayi yadda ya kwaikwayi muryata yayi maganar yasa na tushe baki na ina dariya na ce "na daina Ya Hafiz",


Haka muka idasa har shagon muka sayo muka dawo, muna wasa da dariya dashi, yana ta gaya min kalamai masu dad'i har yasa na manta da wani wai shi Ya Abbas, harda abunda ya had'ani dashi, sai dai muna shigowa harabar gidan muka iske Inna Rabi tsakar gida tunda muka shigo take binmu da hararara daga ni har Ya Hafiz, da sauri naja jiki na daga garesa ina matsawa gefe shima kansa yasan wallahi ku za'a yanka ta sai tayi maganar da ta saba yi, ai ko kamin ya gama tunani a zuciyarsa muka ji saukar maganarta akanmu cike da masifa tana cewa........





*KADUNA* POV



Washe gari haka Munnira ta tashi duk jikinta a sanyaye ganin mijin nata shima duk zuciyarsa ba dad'i yasa duk ta kori wata damuwa dake d'awainiya da ita ta fuskanci mijinta.


Tashinsa kenan daga bacci yana zaune yana kallon silin d'in d'akin yayi zurfi cikin tunani yasa da sauri Munnira ta zauna akan cinyarsa ta d'an kwantar da kanta a k'irjinsa tasa hannunta tana d'an shafa faffad'an k'irjin nasa mai cike da gargasa a hankali ta ce "mijina tunanin mi kake?, pls tunanin ya isa haka nan, na had'ama ruwan wanka", ta idasa maganar tana kamo hannunsa murmushi yayi shima lokaci guda ta mantar dashi wata damuwa da kanta ta taya shi yin wankan cike da jan hankalin mijin nata.


Sanye take da wata riga ta shan iska iya cibiya sai d'an k'aramin wando iya gwaiwa mijinta yafi son yaga mace kullum da k'ananun kaya, shi yasa kullum itama tana k'ok'arin ganin ta faranta masa rai, parlo suka fito sai da ta ciyar dashi abincin safe sana suka dawo parlo suka zauna suna fira jefi-jefi har lokaci ya d'anja, d'agowa tayi tana binsa da kallo cike da sonsa tasa hannu tana shafo fuskarsa ta ce "ya kamata my kaje yau wajan Hajiya tunda ta ce cikin satin nan take son ganinka ya kamata kaje yau kawai" kallon matar tasa yake cike da so, ya sakar mata murmushi ya ce "insha Allahu yanzo dana fita sallah zan wuce unguwar tamu" ya idasa maganar zuciyarsa na d'an bugawa, lumshe ido tayi cike da jan hankali ta ce "to yau mi kake so na dafa ma da rana uhum?" murmurshi yayi ya ce "komi kika dafa zanci ai bari na tashi naji an fara kiran sallah", tashi tayi daga jikinsa, yana gaf ficewa ta kira sunansa tsayawa yayi, k'arasowa tayi kusa dashi kamar yadda ta saba ta had'e bakinsu waje d'aya wani irin kiss ta aika mai dashi ai ko yaji sakon har tsakiyar kansa, ya lumshi idonsa yana k'ara rik'eta sun dad'e a haka sana ta sake shi tana cewa "mijina Allah ya kare min kai ya dawo min da kai lafiya ya kareka da dukkannin sharri ya dawo min da kai cikin aminci", sosai yaji addu'ar tata, duk da ta saba mai haka amma koda yaushe da kalar addu'ar da zata mai shi yasa kullum sonta k'aruwa yake bawai raguwa ba.


Haka suka rabo zuciyoyinsu cike da begin juna,


Yana fita ta d'an tsaya tana cewa "to mi zan dafa mai?," can kuma saita d'an girgiza kai tana murmushi.


Kitchen ta shiga ta d'akko b'arzazzar shinkafa ta d'akko roba ta juyeta a ciki ta wanke ta fas, sana ta d'akko tukunyar ta zamani sitima, tasa ruwa a k'asanta, tasa hawa na d'aya, ta d'akko mai da magi fari da d'an gishiri kad'an, duka tasa a cikin b'arzazzar shinkafar nan data wanketa, tasa mai fari mai d'an dama-dama, sana tasa farin magin nan da gishiri, sai tasa ludayi ta motsa ta had'esu, sai kuma ta d'an taro ruwa kad'an tasa a ciki, sai ta d'akko tukunyarta mai hawa-hawa ta fara zubawa gida uku ne ko ina tasa sai kuma ta d'akko gyad'a wadda ta daka ta sama-sama tasa a ciki, ko wanne gida sama-sama ta barbaza ta, ta had'a su waje d'aya ta rufe saman tukunyar da marfinta, ta d'ora akan gas.

Tana gama wannan ta d'ora wata tukunyar ta d'akko d'anyan naman kaza dake cikin firiza tasa a tukunya, ta yanka al'basa a kai ta d'ora a d'ayan gas d'in, sai kuma ta d'akko tafarnuwa ta dakata da kayan k'amshi tana gama dakawa ta juye a tukunyar data d'ora naman kazarta a ciki, sai da naman kazarta ya tafasa ya fara k'amshi ta d'akko markad'ad'd'und'on kayan miyarta ta juye a ciki ta rufe, sai da miyarta ta fara dafuwa, sana ta bud'e tasa kayan d'and'ano, danda nan gidan ya fara d'omewa da k'amshin girki, sai da miyar taja sosai sana ta d'akko manja tasa a miyar ta rufe, sai kuma ta rage gudun gas d'in, ta koma ga danbun shinkafarta ta bud'e sama tasa cukali ta d'ebo,
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3

Please Login or Register in order to submit comment