Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

daman ban gama kashe wutar nan ba shi ne kuka ƙara wurata har ta kai ku da gwada yar ƙashi ..,


Cikin haƙi jalila tace '' wallahi momcy idan ban karya yarinyar nan ba wallahi Allah ba zata fahimci ni da ita da babbanci takwalas ne ya turo da kuɗi yace gashi nan mayi kunshin bikin ajo shine wai dubu daya zata bamu ta riƙe dubu shidda..,

taɓarya ta dauko a kusa da bayi tace

'' ku cika juna ki na sauke muku allon kafaɗa wannan wanne irin iskanci ne ku bani kuɗin kowa ya rasa da man ke jalila baki kawo min balance ba maza maza ke sumy zo ki ciro min kuɗin nan wallahi kun rasa saboda da tsabar mammaƙo wanda kika je gurin sa ko kobo bani da tabbacin ya baki...,

rabuwa sukai har rigar naja ta yage bako kunya ta bata rufe jikin ta ba duk kirjinta a buɗe

maza ku miƙo min tun kafin na ci mutuncin ku asabe ta faɗa tana kafe su da idanuwanta

miko ATM din tayi amsa tayi tana cewa mene pin din

Kau da kai naja tayi ita bawai faɗar ne ba za tayi ba yanzu momcy zata samu damar ɗaukar mata kuɗi tana yi mata bincike tace

'' kawo naje na curo har yanzu sumy bata cikin hayyacinta...,

miƙa mata tayi ta amsa shiga daki tayi ta canza kaya ta fita neman guri jalila tayi ta zauna akan tabarmar da mufeeda ta shinfiɗa

Lami yar gumama tace

'' sai yanzu kika dawo..,

wallahi baba sai yanzu dakyar ya bani shi kinsan fa yanzu komai ya tsaya asabe ta faɗa tana zama ɗaukan kayan da ke gaban baba tayi tana cewa kai wannan riga tayi kyau


Ajiye ninƙin da take tayi tace

'' nima wallahi naga kyawunta yan zun nan challi ta kawo min su gobe insha Allahu yarinyar nan zata dauka mi tafi kasuwa..,

ni wallahi Allah bana son zuwa gurin yan gumamar nan yan iska ne wallahi mufeeda ta faɗa tana turo baki

wani kallo baba lami tayi mata sannan tace

'' dan kan uwar ki sai kin je su wa'yannan manyan mata ne ke ce ƙarama duk da dai kina nema ki kere'su ga kirga dangi nan duk ya cika miki kirji yawa za su faso kirjin ki su fito amma ba fuss tsuliyar me duki...,

turo baki tayi tana kunƙini ta tashi jin an kira sallar magariba tashi tayi ta dauro alwala bayan ta idar ta kalle su tace

'' baba an kira sallar magariba fa..,

ba wanda ya tanka ta balle baba da ta cika tayi fam ninke kayanta ta ci gaba dayi tana rera wakarta da tashi tayi ta shiga daki ta tada salla

zama tayi har aka kira sallar isha'i lokacin kuma har gidan su ya fara dinkewa da jama'a na kallon gurmi bata fita ba ta kwanta a ɗaya tana jan carbi domin hana zuciyar ta tunanin komai

ke miko min mayafina kinga naja shiru yawa an aiki bawa garin su kar dai yau ba a nan zata kwana ba

tashi nayi zuciyata na ƙuna na miko mata mayafin ta sannan na koma na zauna fita tayi tana sababi


TUDUN YOLA

ƘARFE 8:45

baka jin karar komai sai ta chokali da AC kowa ya mai da hankali kan abincin da suke ci ido Hajiya ta karawa Ashraf tace

'' Ash kamar akwai abin da ke damunka tun dazu sai juya chocali kake ka kasa ci idan har ba zaka hana kanka tunani ba wallahi zakai mutuwar tsaye ka takurawa zuciyar ka sai tunani kake mara makama da abin yi to wallahi ka rufawa kanka asiri ni wallahi abin ka har tsoro yake bani ai wannan rashin tawakkali ne yanzu ina iyayena ba hakura nayi ba na ci gaba da rayuwa bawai tana yi min dadi ba a'a kawai dai na ɗauki hakuri amma kai ke nan ai ta abu ɗaya..,


ƙasa yayi da kansa kallon sa mahaifinsa yayi yana cewa haba Ashraf yan zu kai takure kanka da kayi shine jin dadin ka kome Ubangiji yana jaraba mune yaga iya kacin imanin mu mutane nawa suke naman damar da Allah ya baka mutane nawa suke cikin wani mawuyacin hali amma sun saka hakuri da dangana Ubangiji fa yana jarabtar bayin sa na kware ne

Ashraf sunkuyar da kai yayi yace

'' insha Allah zan ɗauki nasihar ku bawai na kasa cire nusaiba a raina bane yanzu wannan lalurar da inteesar take ciki ita take ƙara jefa ni cikin rudani...,

damuwar ka ba zata saka ta samu lafiya ba sai ma ayi biyu da kwance uwa kwance kaga ba amfani ke na ko Hajiya ta fada tana goge bakinta da tissue

Kai ya jinjina sannan ya ci gaba da cin abincin sa dan ƙadan ya ci daman shi dabi'arsa ce baya cin abinci da yawa tashi yayi yana cewa Hajiya Alhaji sai da safe insha Allahu nan da wani satin zan kaiwa junaid ziyara Cyprus daga nan zan biya nayi umara

to masha Allah Allah Ya kai mu lokacin

Alhaji ya faɗa cikin kulawa

Hajiya tace

'' insha Allahu lokacin da matar ka zaka tafi..,

ajiyar zuciya ya sauke ya juya ya fara tafiya hajiya ta kasa fahimtar sa shi ba wai zama da macen ne bazai iya ba a'a gani yake ba matar da zata iya kula da inteesar gwara su zauna su biyu har ta girma yayi mata aure ba zai juri ganin ana wulakanta mai yarinya ba

musamman ma , matan yanzu da kansu kaɗai suka sani babban burin su idan sun shigo ba wanda zai raɓi mijin su sai su kaɗai da yan uwansu wata ma kuwa duk wani naka saita rabaka dashi sun matana da ita rayuwa shiga da fice ce wanda beba ma akai mai balle kinyi wata da addabawa uwar miji ta manta da wannan karatun cewa

itama uwar miji ce wata rana yana wannan tunani har ya kasara shashinsa chak ya tsaya ganin kamar tana yi mai murmushi ta wara hannu wanta biyu da sauri zai kamota sai ta ɓace runtsai ido yayi jijiyoyin kansa sun fito rada rada tabbas shi da kansa yasan ba lafiya yake ba anya kuwa be zama dis order ba ta ko ina ya kasa haɗa son da yake wa nusaiba ta ko ina tayiwa mata fintinkau adai zamanin nan ba lallai a samu kamar ta ba
🤔
dakyar ya ja ƙafafuwansa ya dauko mukulli ya buɗe shiga yayi tsayawa yayi yana kallon ko ina na gurin kamar yau fa aka kawo masa ita a matsayin mata duniyar tunani ya lula

wai waye adon tafiya

wallahi nusaiba ji nake kamar na janyo ranar nan ta dawo yau

Ashraf ya faɗa yana kafeta da idanuwansa

kau da kai nusaiba tayi tana wasa da hijabinta tace

'' da yau da ranar juma'a duk ɗaya ce a gurin Allah, Allah dai ya kai mu da rai da lafiya...,


Anya kuwa ban fiki son mu kasance tare ba

rufe fuskarta tayi da tafukan hannayen ta tace

'' bansan da wanne baki zan kwatanta maka irin adadin son da nake maka ba..,

ni wallahi sweet anya kuwa wannan kunyar take zata bari ki nunamin son da kike min

jin gina tayi a jikin kujera tace

'' kaidai Allah ya nuna mana lokacin lafiya..,

sarkin wayo maganar ce bakya so ko

har abada bazan gaji da sauraron daddaɗar muryar ka ba ina rokar Ubangiji idan zaka mutu mu mutu tare bazan iya rayuwa idan bakai son ka shine jini na jikina kaga kuwa mutum zai iya rayuwa ba idan babu jini

lumshe idanuwa yayi sai kuma ya buɗe su yawa me jin bacci yace

'' nima bazan iya rayuwa babu ke ba Allah ya raya mu tare ya kashe mu tare..,

amin ya Allah

tashi yayi yace

'' zan shiga daga ciki lokacin da Hajiya ta diba mana ya cika tsoro take kar nayi aika aika..,

murmushi tayi batare da tace mai komai ba wallahi maganganun sa kunya suke bata ashe shima ba kanwar lasa bane a satin nan fa lamarinsa har mamaki yake bata kamar ba yayan da tasani bane me muzurai da tsare gida amma a yanzu kam ita sheda ce ko kallon da yake mata na zallar so ne magana fanake miki kinyi shiru ko na zo na raka ki dakin ki
Ashraf ya faɗa yana ƙara kafeta da idanuwansa

rufe baki tayi tana zaro Ido

UWAR GAFALALLU

EPISODE 8-9

PERFECTLY PEN'S

rufe bakin ta tayi tana zaro Ido tace
Please yaya ka rufan asiri ka tafi kar Hajiya ta biyo sahun mu wallahi Allah jiya faɗa tayo min sosai tace sai ta hana ni fita idan an kai ni gidan mayi kome za mu yi

dariya yayi ya nuna mata hanya yace

'' Hajiya kenan ta gama isarta ƙarshe dai dole ta kawo miki bissalam Allah ya tashe mu lafiya..,

nusaiba tace '' amin ya Allah tana fara tafiya sai da yaga tayi nisa sannan ya juya ya tafi part dinsa yana shiga junaid ya shigo da yake dakin su yana kallon na juna kallon a gogon parlour ASHRAF yayi yace

''9:30 kai kuwa ina kaje haka kasan fa Alhaji baya son yawa Junaid a dinga kiyaye wa kar kuma ya saka maka dokar fita..,

kallon a gogon dake manne a bango Junaid yayi yace

'' wallahi naje gidan su Abubakar ban san lokaci ya ja haka ba amma insha Allahu zan dinga kiyaye wa hakan ba zata sake faruwa ba ...,

Kai ASHRAF ya jinjina yace

'' Allah ya saka yana shiga dakinsa shirin bacci yayi sannan ya kwanta..,

Washegari

cikin sauri take haɗa musu breakfast Hajiya ce ta fito tace

'' a'a nusaiba har kin tashi kin fara aiki...?,

Eh wallahi Hajiya bana so na ɓatawa yaya lokaci ransa ya ɓaci yayta jira shi ya saka na ɗora da wuri cewar nusaiba kanta tsaye domin ta manta da halin hajiya na zolaya yanzu zata tusata a gaba

dafa table din kitchen Hajiya tayi tace

'' kaga me miji wato kar ki ɓara mai rai daman haka ake so matar kware ta dinga yi..,

murmushi tayi batar da tace komai ba

fita Hajiya tayi bayan ta gama ta kwashi komai ta kai dining jin sallamar su ta ɗago amsa wa tayi tana gaishe da Alhaji har ƙasa

Cikin kulawa ya amsa jawa kowa kujera tayi sannan ta zauna zuwa kowa tayi junaid na tsokanarta Alhaji na tare mata shi kuwa ASHRAF kamar baya gurin cin abincin sa yake cikin kwanciyar hankali bayan ya gama ya saka tissue ya goge bakinsa ta tashi zai bar gurin yana cewa

Zan tafi gun aiki

kallon sa alhaji yayi yana cewa gaskiya bana son zuwan ka wajen wutar nan ga kasuwanci nan idan ma baka san zama a ƙasar nan ga shaguna na Dubai kaje kayi kasuwancin sai da gold ana samu sosai

ƙasa yayi da kansa baya so ya tashi a jingina da ƙarfin mahaifin sa yafi so ya nemi nasa yasan zafin nema dariya Hajiya tayi tana cewa ASH ba magana naga kayi shiru

sosa ƙeyarsa yayi yana cewa sai na dawo na tafi

Alhaji ne yace

'' Allah ya kiyaye hanya ya bada nasara da sa'a tun da kafi son nan sai mu bika da addu'a...,

wallahi kuwa Hajiya ta faɗa tana kallon nusaiba ta ci gaba da cewa nucy ba rakiya...?,

kai ta gyaɗa mata a hankali tace

'' Hajiya ba sai na raka shi ba..,

kwaji da shi zama ku dawo dai-dai ne ta faɗa tana tashi daga gurin shiga bedroom dinta tayi bayan kowa ya gama ta kwashe kayan ta kai su kitchen

akwana a tashi ba wuya yau ta kama juma'a za ayi daurin aure sosai manyan ƙasar nan suka halarci daurin auren NUSAIBA ABDUL HADE da ASHRAF MANSUR GWARZO amma ban da dangin mahaifin nusaiba kalilan ne suka zo domin ba son auren suke ba akan wani ban zan dalilinsu mara makama da abin yi gani suke Hajiya ta nuna musu kuɗi taya yaya yarinya ta taso a gunta kumu ta aurer da ita ba tare da ta Da musu da ita ba dan tana taƙama da kuɗi...

bayan an gama daurin aure da yamma akai lecture daga nan a ka wuce da ita dakin ta ba abin da Hajiya da Alhaji suka rage ta dashi komai sun mata haka kowa ya watsai ya bar ta ita kaɗai bata da tarin ƙawaye bayan isha na shigo gidan....

nima da yake bani da abokanai abokina ɗaya salim shima a waje muka rabu shiga nayi tare da addu'ar Allah ya kade mana fita Allah ya bamu zaman lafiya tura kofar nayi abin da na zata shi ya faru a buɗe take na shiga bakina dauke da sallama bakowa a parlour direct bedroom na nufa nayi sallama

ɗagowa tayi ta amsa min sallama ta tsayawa nayi ina kallon ko ina tare da da yiwa Allah godiya da ta cika mana burin mu mun mallaki juna

tun da mukai aure ba mu da taɓa samu. Saɓani ba nusaiba tana da haƙuri za kai mata ta dauke kai ni ko da tasan Kai mata din har Allah ya azurta mu da yarinya,

ranar da zata tafi ganin dangin ta lokacin inteesar tana da two year hatsari ya faru me kama da almara ajiyar zuciya ya sauke lokacin da ya gama tunaninsa tafiya ya fara har ya shiga palour sa zama yayi akan two seater ya zuba ta gumi kallon agogo yayi karfe 12:00 gaskiya ya dade a zaune a gurin nan haka ya kwashi lokaci..


Wannan kenan

baccin tane yayi nisa ta tamkar daga sama taji ana bugu tashi tayi tana kunna yar ƙaramar fitila tana jan tsaki ashe naja bata dawo ba tun daga zuwa ciro kudi tashi tayi jin zata karya musu kofar da suke ƙarawa da ita ta fita tayi ta isa soro ta buɗe kofa ta tsaya a baya tana liƙe bak'ar motar da aka kawo naja a cikin ta har da tinted to munafuka uban me kika tsaya yi sauran kuma kice mata na dawo

dan ubanki bani kuɗin da kika ciro da wanda kika samo ni wallahi bansan ke yar marasa bace sai yau

wallahi momcy be bani wani kuɗi ba yau muka haɗu dashi ta faɗa tana turɓune fuska

uban be baki wani kuɗi ba bani ko ya zu wallahi na caje ki asabe ta faɗa tana zaro ido


ba yadda ta iya haka ta miƙa mata kudin murmushi tayi tana kirga su dubu arba'in cis tace

'' ina dubu biyar din ta kwalas...?wallahi naja ki kiyaye ni kuɗin nan zu zasu wanke ki daga laifin da ki kaimin,

zun buro baki tayi ta miƙa mata amsa tayi tana washe baki Allah ya tsare ya kuma buɗa kofofin hanyar samu...

saboda takaici kasa barin gurin nayi ƙafafuwana sun kasa ɗauka ta yan zu rufa'i ko kirana ba yayi saboda taje har gidan su taja mai kunne tashi nayi na bar gurin ganin sun tafi sun barni kulle kofar nayi na koma ciki shiga daki nayi runtsai ido nayi ganin tashin hankalin da na gani jalila sumy suna ta aikata masha'a kamar ba yan uwa ba kamar addinin mu be yi hani da wannan dabi'ar ba kasa shiga nayi na dauro alwala na daman da hijabi a jikina shiga dakin baba lami nayi sai sharar bacci take har da mun shari shim fida daduma nayi na fara nafila

bayan na idar bacci ya ɗauke ni can kuwa ɗaki ai ko a jikin su ganin mufeeda ta gansu breast din sumy da shi jalila tayi bacci basa tunanin Ubangiji zai iya ɗaukan ransu a haka a kuma tashe su a haka me za su ce mai jin kiran sallar asuba suka tashi ko wacce taje tayi wanka ta dauro alwala kallon su mufeeda tayi tana cewa

kuji tsoron Allah abin da kuke aikatawa ba me kyau bane abu mafi muni

tun kafin ta ƙarasa sumy tace

'' kiyi mana shiru wallahi kema baki wuce na kwantar da ke ba na kwakuleki tas...,

kai ta girgiza ta bar gurin ƙasa sheƙewa sukai da dariya suka tafa

har sun tada kabbarar salla suka ji muryar takwalas da sauri suka sallame sallar suka fito yana sanye da jallabiya yaci dauri ture kaga tsiya wata uwar buɗa ya saki yace

'' kut gaskiya mutane na kun yi kyau kunyi acan acan dan tafiya lagos da nayi shine kuka tara wannan kayan aiki haka to gaskiya nima ba za a barni a baya ba ina momcy take ...?,

dariya sumy tayi tace

'' tana bacci kai ma wallahi Lagos ta amshe ka..,

kan bura ubancan kayyasa ai anan kano ba komai ake ba sai da naje Lagos sanna na ƙara fahimtar rayuwa wallahi idan har zata bar ku hmmm kudi ta riga da ta zama attajira sufa ba irin biyan nan suke ba musanman ma ki haɗu da direba ko yare ba abin da basa kashewa mace

ya faɗa yana buga cinya hadi da fari

naja ce tace '' dan Allah ta kwalas ...?,

murguɗa baki yayi yana fari da idanuwansa yace '' zauna wasa har lokacin ki yayi ya ƙare ba abin da kika tara can fa ba me damuwa da wani kowa harkar gaban sa yake...,


Ikon Allah yanzu kowa sai yayi sabgar gaban sa ba me damuwa da kowa anya kuwa jalila ba nan za mu tafi ba cewar naja

gyara daurin kirjin ta tayi tana cewa nima fa abin da nake tunani kenan wallahi gwara mu shiga sahun manyan mata

wata uwar shewa suka saki tare da cewa a hayye ras wannan shewa ita ta tasar da momcy ta fito dai-dai shigowar baba cikin daure fuska yace

'' kai bana ce maka kar ka ƙara shigo min gida ba ..?,

gaskiya ba ruwan ka malam ya kake yawa ne nan ina gidan yake kwango dai amma wannan ba gida bane ka bari sai arziki ya zo ya same ka kana kwanciyar asarar nan da kake kayi gida wallahi ba ruwan ka da kawayena da suke zuwa guna da kuma na ya'yana naga ma gado aka ci aka bar maka shine kake tun ƙawo da shi

Asabe ta faɗa tana yatsuna fuska da tabe baki

kasa magana yayi sai ma kasa da yayi da kansa ya wuce be ƙara ce mai komai ba bayan kaddarar da Allah ya yi mai to Ubangiji sai ya ƙara jarabar sa da asabe bayan ya shiryu shiga daki yayi yana jan carbi ko zai samu saukin zuciyar sa

kunga zo mu shiga daki takwalas sai ka sako da ga farko asabe ta faɗa tana nuna musu dakin ta shiga sukai ya dinga basu labari momcy tace


'' bara mu gama bakin ajo ko bayan ka tafi ne sa tawo har waccen yarinyar sai an tafi da ita naji dakai na wallahi...,

sai ma karshen watan nan zan tafi sai mu tafi tare

hakan ma yafi yi min gwara su sauka a hannun ki

ai momcy ina faɗa miki gida na gina kowa ya zo ya shiga ya bani yan kudina a agege

kai ka akai kace litkafa taci uwar ta da

Kware da gaske ai ina tare da addu'ar iyaye

ai kuwa Ubangiji bazai taɓar da ke fa ji sukai an ɗaga labulan dakin zaro ido sukai gaban su ya yanke ya waɗi ɓare baki takwalas yayi yana cewa

Kai lafiya ka zo ka tsaya mana a ka da zabgegiyar huƙa

yimin shiru ko yanzu naci kuttumar..ubanka ba wajen ka na zo ba ya faɗa yana kallon asabe

tashi yar kwalas yayi yana girgiza kugu yace

'' ke idan kana ta ƙama da kai dan dabane ni naje inda baka je ba naje inda aka fika dabanci da iskanci Dan haka maza wuce ka bani guri dan iskan ƙarya

ai be ƙarasa ba yaji saukar duba a bakin sa ihu ya saka yana cewa na shiga uku momcy ku duba min ya cire min hanci ko

momcy da cikin ta ya ɗuri uwa bama tasan me yake cewa ba kai a sabe da sauri ta ɗago jikin ta yana rawa yaci gaba da cewa

daman na faɗa miki inhar kere na yawo zabo ma yana yawo rana dubu ta ɓarawo rana ɗaya tak ta me kaya kin saka an kai ni gidan yari to yau zan aika ki lahira dan uwar....ki ke shegiyar ƙarya ce kuma wallahi sai nayi maganin wa'yannan ya'yan naki ba sune yan zuga ki ba to duk yanzu zan yanke musu hukunci kai kuma dan daud ko to yau zan dawo da kai kalar ka ta ainiyi a zaton ki zan dawwama a gidan yari ko

to yau zan ci ubanki ala'ada waje zan nuna miki jiya ba yau bace......



UWAR GAFALALLU


EPISODE 10-11

UWAR GAFALALLU


EPISODE 10-11


Gumi ne ya shiga wanke momcy tasan bata kyauta ba takurewa guri ɗaya su sumy sukai jikin su har rawa yake takwalas kuwa sai zare ido yake be taɓa ganin tashin hankali irin na yau ba wannan wacce irin rana ce

Wannan shi ake kira da ya taka sahun ɓarawo yace '' talge dan girman Allah kai min rai wallahi Allah ban shirya mutuwa ba...,

wata dariya ya saki irin ta arnan nan kamar anyi ruwa an ɗauke sai kuma ya murtuƙe fuska yace '' wallahi sai na ci uban ku..,
jin hayaniya baba lami da baba suka fito turus sukai baba lami ta dafe kirjinta tace '' innalillahi wa'inna'laihir raji'un idirisa kaga a kwashe kwashen asabe abin da ta kwaso mana insha Allahu sai dai abin ki ya ƙare miki a kai...,

kai lafiya ka shigo mana gida

wani kallo talge yayi mai sannan yace '' ba gurin ka nazo ba dan hakai ba idan kai wasa wallahi kai ma yanzu nan zan sala sala da naman ka..,

kama haɓa baba lami yar gumama tayi tace '' idirisa yi baya ita da tajawa kanta ya yanka ta ya soya ka na ganin huƙar nan sai kyalli take to wallahi maza zo mu bar gurin nan...,

Mufeeda ce taji abin yayi yawa ta fito tace '' baba me ke faruwa...,

zaro ido tayi ganin talge yana juya huƙarsa ja da baya tayi baba lami tace '' mufeeda kinga abin da uwar ki asabe reza ta jawo mana ko ai gata nan cikin ta ya ɗuri ruwa duk wannan masifar nan tata da daga murya kinji ta tayi muƙus a daki yawa anyi ruwa an ɗauke ko su futsararrun ya'yan nata kin ji su shiru...,

ke rufe min baki ko yanzu nayi miki ba dad'i wallahi

rufe bakin ta tayi tana zare ido ta ƙara ja baya a hankali har ta rufo kofar ta jikake garam ganin baba lami ta gudu mufeeda ma ta shige daki sai baba da yake kallon kudirar Allah yace '' bawan Allah zo ka faɗa min me tayi maka..,


cake huƙa yayi ya bushi sigari ya fesar yace '' wannan shegiyar matar nan da kake gani annamimiya ce ni ta saka a ka kai gidan dan kande dan tana da daurin gindi ta saka a ka daure ni wiwi na ta sara ta hanani kudi na shi ne nazo ta bani ta hanani tare da fadamin mugayen kalamai yau sai naci uwar ta wallahi..,

ƙasa yayi da kansa zuciyar sa ba dadi be san yaushe a sabe za tayi hankali ba yace '' kai hakuri yanzu ta dauki kuɗin ka ta baka shikkenan magana ta ƙare..,

kai saita baƙin ka ni kake faɗawa haka aini ban san hakuri ba ko baki ji sunan nawa ba talge sai da wuta

ya faɗa yana cije baki

bawan Allah ina haɗa ka da girman Allah da manzon sa kai hakuri ta fito maka da kuɗin ka

jikinsa ne yayi sanyi yace '' billahilla'zi da ace ba ka hadani da Allah ba bazan bar gurin nan ba sai na aikata abin da nayi niya yasin in badan rashin mutunci ya za ayi ta dauki kayana nayi magana ta saka a kulle ni..,

kai hakuri bata kyauta ba Allah ya wuci zuciyar ka

cikin sauri take fito da kuɗi bama ta san nawa ta miƙo mai ba amsa yayi yana zurawa a aljihu dubu goma yake bin ta da alama ma wannan kuɗin ya fi ƙarfin dubu goma ɗaukan huƙar yayi ya fita

da sauri ta fito tana zabga gumi yawa an tsumata a cikin ruwa gyara daurin daukwalinta

Book Chapters
Chapter 1Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4Chapter 5Chapter 6

Please Login or Register in order to submit comment