Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ya na
alhinin aurar da d’iyar bayin da yayi maimakon d’iyar sa,
maimakon ya kawo k’arshen gaba, gudunmawar dad’a k’arfafa
gaba yayi muddin sarkin Fabarusa ya fahimci yanda ya haince
shi saboda san zuciya.
Daga tawagar shugaban k’asa Kwaminishinan da yayi jawabi
ne ya mik’a gaisuwar shugaban k’asa tare da gudunmawar sa
na buhuhunan hatsi, shinkafa da dabino ga masarautar ta
Sa’ayrsa, wanda sam kyautar ta shi ba burge su ta yi ba, a
fad’ar su sai da yunwa ta ci ta cinye su har su ka kai ga neman
taimako gun abokan gaba sannan zai wani kawo musu
gudunmawar sa na bogi. Kafin kwaminishna ya k’are jawabin
sa, wayar Junaidu ta d’au k’ara, ko da ya amsa kiran tuni
fuskar sa ta canza, cikin dabara ba tare da ya bari an san halin
da ake ciki ba ya ja Aisar su ka yi waje.
A cikin mota ya ke sheda masa ai jikin Shugaban kasa ya
dad’a tashi kiran da aka masa kenan, su za su fara yin gaba in
ya so sauran tawagar za biyo su a baya gudun kada a d’aga
hankalin jama’a. Aisar ya na ji ya na gani haka su ka bar
yankin Sa’ayrasa, ya na mai kudirin dawowa da sun sami kan
Shugaban k’asa.
Daga d’akin taro kuwa tawagar shugaban k’asa sai neman su
Aisar su ka yi su ka rasa, bayan sun kira su ne su ke sheda mu
su ai sun yi gaba saboda wani uziri da ya taso, duk da dai ba
du sheda mu su ainihin abun da ke faruwa ba, sai da jikin su
yayi sanyi matuk’a.
An kamala taro yayinda aka ci aka sha, dan kuwa yau take
salla a masarautar Sa’ayrasa. Yarima Jafar ne ya nemi a kai
su ga masaukin su da ke su dama nan Sa’ayrasa za su kwana
su da tawagar Yarima Sadauki. Amma bakin ciki da kuma
Allah Allah da ya ke ya bud'e ido ya gan sa a Fabarusa domin
shedawa Mahaifiyar sa cin fuskar da aka masa ya sa Yarima
Sadauki fasa kwana, nan ta ke ya juya shi da tawagar sa ba
tare da sun jira Sarki ba. Su Yarima Barde kuwa da wasu
dogarawa aka had’a su domin kai su masaukin su.

Bintu ɗiyar bayi ce (book 2) Chapter 4&5
Admin 001 SAYYADI SADIQ
@Whatsapp 08146934644

4⃣
Bayan sarkin Fabarusa ya yiwa Sarkin S’ayrasa bankwana, ya
d’au hanya tare da tawagar sa. Haka d’aya bayan d’aya taro ya
shiga watsewa. Tawagar shugaban k’asa ma tuni su ka d’auki
hanya dan tadda su Aisar.
Sarkin Sa’ayrasa na komawa turakar sa Jakadiya ta zo ma sa
da buk’atar iyalan sa na ganawa da shi. Ganin magariba ta
gabato ya ce su maza su iso gare shi kada ya rasa sallah.
Hajja Kilishi, Inna Salti, Gimbiya Binta da kuma Gimbiya
K’amariyya ne zaune gaban sarki, sai kuma Jakadiya da Bintu
can gefe nesa da su. Jikin Bintu har karkarwa yake, fatan ta
Allah ya sa Sarki ya duba lamarin ta hanya warware auren
masifar da aka d’aura mata.
Ya na mai kallan Gimbiya K’amariyya ya ce
‘’ke mu ke sauraro’’
Maimakon ta bashi amsa sai ta kai kallan ta ga Inna Salti, cikin
idanun ta ta na mata magiyar ta taimaka ta shedawa sarki.
Inna Salti da ta gane halin da K’amariyyar ke ciki ta ce
‘’Allah shi ja da ran Takawa, batun amren da aka d’aura ne,
wanda aka d’aura amren da shi, shi ke neman amren
Kamariyya’’
‘’dama akwai wanda ya zo ya same mu da batun amren d’iyar
mu? Ba mu san da wanga Magana ba’’
Fad’in Sarki Sule. Inna Salti na mai kame kame ta ce
‘’eh dama ba su zo din ba, kasancewar da akwai rashin jituwa
tsakanin Masarautar ta Fabarusa da ta mu, hakan shi ya kawo
jinkiri Allah ya taimaki Takawa’’
Sarki Sule na mai gyad’a kai cikin nuna 6acin rai ya ce
‘’ki nufin d’iyar mu ta na sauraran wani ba tare da sanin mu
ba?’’
‘’ta yi kuskure, ayi mata afuwa’’
Cewar Hajja Kilishi, da ita kad'ai ke iya bawa Sarki hakuri idan
ya na cikin yanayin 6acin rai. Shiru ne ya biyo baya, kafin daga
bisani Sarki Sule ya ce
‘’a shedawa wanda d’iyar mu ta ke saurara a bayan idon mu,
ya zo nan da kwana biyu dal mu na so mu gana da shi’’
‘’shi ne Yarimar da aka d’aurawa amre da d’iyar bayi Allah ya
huci zuciyar babban bijimi’’
Cewar Inna Salti a hankali kamar wacce ke tsoran maganar.
Sarki na duban Gimbiya K’amariyya ya dad’a tambayar
‘’ku na nufin Badde na Fabarusa?’’
‘’Badde kuwa Allah ya k’ara ma ka lafiya’’
Ga mamakin su sai gani su ka yi Sarki ya murmusa, kafin ya
k’ara da
"shin kin san ita d’iyar bayi a matsayinwa aka d’aura mata
Badde?’’
Inna Salti wacce ta fara dana sanin furta maganar ta ce
" a matsayin Binta, Allah ja da ran ka’’
‘’wacece Binta?’’
Tambayar Sarkin Sule da ya sa kowani mahalukin da ke wajan
sai da ya sha jinin jikin shi. Da kyar Inna Salti ta yi k’arfin halin
furta
‘’d'iyar babban bijimi ce’’
Cike da 6acin rai ya ce
‘’ita Kamariyya da aka amrer da d’iyar bayi a matsayin kaunar
ta, kuma ta zo mana da zancen alakarta da wanda aka d'aura
din, ya ta ke so mu yi ma ta?’’
Shiru babu wanda ya iya furta komai. Idanun sa bisa silin yace
‘’an bar mu muna jira, ke mu ke sauraro K’amariyya!’’
Murya na rawa ta ce
‘’dama tin da haka abin ya kasance, na ke so a warware
matsalar ta hanyar raba amren …….’’
‘’yashasheshshen zance!’’
Sarki Sule ya katse ta ta hanyar daka mata tsawa, tuni jikin
K’amariyya da Binta ya hau k’yarma tsabagen firgici, kowa sai
da ya sha jinin jikin sa, Jakadiya ta durkusa ta na fad’in
‘’tuba mu ke ran Babban biji ya dad’a, Allah huci zuciyar
Babban Biji, lafiya salamun’’
Sarki kuwa be gushe b ya cigaba
‘’mun biye mu ku mun bi san zuciya mun aikata ha’inci,
hakik’a Sarki Abdulrahman ya kasanse mai zurfin tunani, mu
kuma mun kasance daga cikin ma’abota san zuciya, fatan mu
shi ne gyara wanga kuskure da mu ka aikata bisa san zuciya
ba tare da 6ata dangantakar arziki da mu ka kulla a wanga
rana ta yau ba’’
Kallan sa ya mayar ga Bintu, kana ya ce
‘’ina Kilishi?’’
‘’ran Takawa ya jima, gani kusa gaban ka’’
Cewar Hajja Kilishi.
‘’wagga d’iya ta arziki (yayi nuni ga Bintu) ta ma na abun da
jinin mu basu ma na ba, sanadiyar ta yunwa ta kau a
masarautar mu, idan ba mu maishe ta d’iya ba, ko shakka
babu mu na daga cikin wanada ake kira butulu, wagga d’iya
d’iyar mu ce, ni Sule na kira wagga d’iya da d’iya a gare mu,
maza a shirya d’iyar arziki, idan an wayi gari ta bi tawagar
masarautar Fabarusa dan kuwa jinkirin makwannin biyun ka
iya zama barazana a gare mu, da zafi zafi akan bugi karfe…
mun gama Magana’’
Ya na dasa aya ya tashi cike da Sarauta yayi shigewar shi daga
ciki, ya na jiyo koken Gimbiya K’amariyya da Gimbiya Binta
amma ya mu su kunne uwar shegu duk da kuwa har ran sa ya
ke jin abun.
Ita kan ta Bintu jin gobe gobe za a wuce da ita hankalin ta ya
dad'a tashi, ta ma kasa motsawa daga in da ta ke, ta nemi
kuka ta rasa.
Gimbiya K’amariyya kuwa wacce har shid’ewa ta ke tsabagen
kuka da ya ci karfin ta, tuni ta sake fad’uwa sumammiya a
karo na biyu. Nan waje ya sake kaurewa da salatin su Hajja
Kilishi da Jakadiya. Dan kok’ari har da Bintu cikin kawo d’oki
ta hanyar ciro mayafin ta, ta shiga yiwa Gimbiya K’amariyya
fifita, yayin da Inna Salti ke yayyafa mata ruwa.
Wani k’akk’arfar ajiyar zuciya ta saki, alamar ta farfad’o,
amma idanun ta lumshe ta kasa bud’e su, hawaye ke gudana
bisa kuncin ta. Sai fa a sannan Gimbiya Binta ta ankare da
Bintu da ke sunkuye bisa kan Didin na ta, sai fifita ta ke ma ta,
ai kuwa ta daddage ji kake tas! Ta sauke yatsun ta biyar bisa
kuncin Bintu sai da ta ga wuta a idanun ta. Hannun ta biyu bisa
kuncin ta ta ke duban Gimbiya Binta, hakan ne ya dad’a k'ular
da ita, ta sake d’aga hannu da niyar kai mata wani marin caraf
Inna Salti ta ruke hannun ta, ta na mai fad’in
‘’kul kar ki kuskura ki sake! Kin san kuwa matar Yeriman
Fabarusa ki ka d’aga hannu ki mara? Ina hankalin ki ya tafi?’’
Jin haka Gimbiya Binta kamar ta yi hauka, fad’i ta ke
‘’d’iyar bayi na mara, d’iyar bayi wacce na saba takawa ita na
mara, babu wata matar Yariman Fabarusa da ta wuce Didi, duk
makirci da munahunci wanga wulak’antacciyar Baiwa arudu ya
k’are bisa kan ta! Ku ma mu zuba ni da ke ina mai tabbatar mi
ki alkiyamar ki ta zo dan kuwa da ki tafi zuwa Fabarusa a
gurbin Didi gwamma ki je ki kashe kan ki, dan kuwa masifa da
balak’I ya na nan an tanadar mi ki, kuma shi za ki riska, sai dai
uwar ki ta haifi wani…..’’
Ta juya fuuuu ta fice gudun kar Bintu ta ga hawayen ta, dan
kuwa su ke sauka d’aya bayan d’aya tsabagen bakin ciki da
takaici. Hajja Kilishi shi ce ta ja Bintu zuwa turakar ta dan
neman yanda za a yi idanun Bintu da ya kumbura da shatin
yatsun Gimbiya Binta ya baje, bayan Inna Salti ta bata baki bisa
ga lamarin Gimbiya Binta da kuma mata alk’awarin irin haka
ba mai sake faruwa ba ne. Nan su ka bar Inna Salti ta na
rarrashin Gimbiya K’amariyya, domin kuwa bakin alk’alami ya
bushe tuni.

5⃣
Da daddare bayan an idda sallar isha’i, Yarima Jafar da Yarima
Barde zaune a falo sun yi jigum kamar wanda aka yiwa
mutuwa, Khalil na daga d’aka ya na waya da matar sa.
Babban falo ne mai d'auke da k'ayataccun kujeru na sarauta,
masauki ne da dama a ka tanada na musammam domin
saukar bak'i na alfarma irin su Barde.
Tun da su ka isa ga masauki Barde ke zaune nan falon, sallah
kad'ai ke iya sawa ya motsa. Shigar sa na d'aurin aure ke jikin
sa, sai dai ya cire babbar riga da rawani, sumar kan sa kwance
lub lub bisa kan sa.
'Daya daga cikin dogarawa da ke ciran kofa ne ya shigo ya
zube gaban Yerima Barde, kana ya ce
‘’ran Yarima ya dad’e, Gimbiya K’amariyar d’iyar Mai martaba
Sarki Sule na S’ayrasa ce me neman iso gare ka’’
Jin sunan K’amariyya tuni kafad’a Barde ta tasa, yayinda
jijiyoyin wuyar sa su ka bayyana. Amma ya kasa furta komai.
Yarima Jafar ne ya ce
‘’ka iso da ita gare shi’’
Dogari na mai fad’in
‘’an gama ran Yarima Ja’afar ya dad’e’’
Ya tashi da sauri ya fice. Yarima Ja’afar ma tashi yayi, ya d’an
dafa kafad’ar Yarima Barde sa’annan ya shige ciki. Shigar sa
ke da wuya Dogari ya shigo biye da shi Gimbiya K’amariyya ce.
Sai da ya kawo ta gaban Yarima Barde sannan ya juya ya koma
waje in da bayan Gimbiya K’amariyya ke tsumayin ta.
Tin shigowar ta ya kafa mata ido, har ta iso gare shi sanye
cikin atamfa koriya wanda ta rufe da farar alkyabba ta alfarma.
Duk tashin hankalin da ta ke ciki da kuma wanda Yarima Barde
ke ciki be hana shi ganin kyauwun Gimbiya K’amariyya ba. Ga
wani k’amshi mai saka kwanciyar hankali da ya kasa gane kan
sa ke tashi daga jikin ta sa’in da ta zaune gaban shi. Yayi
kok’ak’arin sanya kwayan idanun sa cikin na ta, amma hakan
ya gagara kasancewar ta yi k’asa da na ta idanun.
‘’K’mariyya…..’’
Ta ji murya mai d’auke da tarin kwarjini ta daki kunnan ta,
wanda tun da aka d’aura masa aure da Bintu, kwakkwarar
kalma d’aya be fito daga bakin sa ba sai a yanzu da ya ga
K’amariyya zaune gaban sa.
‘’K’amariyya’’
Ya sake kiran sunan ta a karo na biyu, maimakon ta amsa,
kawai sai ta sa ma sa kuka, ya rasa yanda zai yi da ita dan
kuwa Barde sam be iya rarrashi ba. Ta d’au lokaci mai tsayi ta
na rera kuka gaban sa, tin ya na iya ba ta baki, har ya mata
shiru dan kuwa shi dama Magana wahala ta ke masa. Sai da
ta yi shiru dan kan ta, sannan ya dube ta, kana ya ce
‘’ban san kud’irin mahaifina ba, sai bayan da bakin alk’alami ya
bushe, sai da aka d’aura min amre da kauna gun ki Fatima….’’
Jin haka Gimbiya K’amariyya ta kai duban ta gare shi, ta ga ya
k’ara ma ta kyau da kwarjini na kwaran gaske, wai kuma an
d’aura ma sa Bintu! Bintu dai d’iyar bayi! Ji ta yi kamar ta
bud’e baki ta fad’a masa gaskiya komai ta fanjama fanjam,
tunawa da ta yi da na ta Mahaifin ya sa ta a dole ta na ji ta na
gani ta yi shiru, babu mamaki shi ya na da wani shiri ne na
daban. Murya na rawa ta ce
‘’ina cikin damuwa Yarima, ina mafita?’’
Kallan ta yake na wasu dak’ikai, kafin daga bisani ya saki
ajiyar zuciya mai karfi gami da sauke kafad’a, kana ya ce
‘’Allah shi ne mafita, shi za mu kai kukan mu gare shi, hallo
bana yiwa Mahaifina musu, ban ta6a ba K’amariyya shi ya sa
ma ki gaya aiwatar da wanga lamari ba tare da ya tuntu6e
niba, yanzu ban da tsumi hallo ba dabara, amma ina so ki sani
ina son ki, kwaran gaske’’
Cikin hawaye K’amariyya ta ce
"me zai hana ka sanar da Mahaifin ka gaskiya kamar yanda na
sanar da nawa Mahaifin?’’
‘’ban da wannan ikon K’amariyya, da ina da shi da tuni na
aiwatar da hakan’’
Cewar Yarima Barde ya na amai girgiza kai. Nan Gimbiya
K’amariyya ta fusata, ta tashi da sauri za ta fita. Yarima Barde
ma tashin ya yi, ya dakatar da ita ta hanyar fad’in
‘’kar ki yi fushi K’amariyya, kunar za ta min yawa, badan
wacce aka d’aura min jinin ki ba ce kuma kauna gun ki da na
ce duk duniya babu wacce na tsana face ita, sam ba za ta
sami kulawa bare wani abu wai soyayya daga gare ni ba
saboda soyayyar ki, hallo babu yanda zan yi dole haka zan
zauna da ita har Allah ya kawo karshen zaman, dan darajar
Mahaifan mu da Masarautun mu’’
Kallan sa ta ke yayinda hawaye ke gudana daga idanun ta, a
hankali ta furta
‘’ina ma ka fatan alkhairi Yarima Badde’’
Sannan ta juya a hankali ta na ficewa. Tsayawa yayi ya na
kallan ta yayinda ta ke ficewa daga rayuwar sa, idanun sa sun
yi jajur, ji yayi k’afafun sa sun kasa d’aukar gangan jikin sa, a
hankali ya zauna zuciyar sa cike da tunanin yanda rayuwar sa
ta sauya a wuni d’aya. Shi ba mutum ba ne mai san mata,
mata ne ma ke san sa da bibiyan sa. Tin da Allah ya had’a shi
da Gimbiya K’amariyya, ita ce mace ta fari da ya ji ya na kauna
zai kuma iya aura. Amma yau gashi an ma sa Katanga da ita
ta hanyar aura ma sa kanwar ta. Yatsun sa ya tusa cikin sumar
kan sa sanadiyar sarawa da ya ji kan sa na yi, ya na fad’in
‘’lahaula walakuwata illa billah!’’

Bintu ɗiyar bayi ce (book 2) Chapter 6
Admin 001 Sayyadi Sadiq
@Whatsapp 08146934644
Khadija Sidi..✍🏼
6⃣
Ko da Gimbiya K’amariyya ta koma d'akin ta, sai ta sallami
bayin ta gaba d’aya sannan ta kulle d’akin ta haye tsakiyar
gado ta na rusa kuka. Bintu kuwa d’akin Hajja Kilishi bayi ke
jera kaya da aka d’inka ma ta na alfarma, yayinda Hajja Kilishi
ta sa ta gaba sai bayani iri-iri ta ke mata akan kayan da kuma
yanda za ta na amfani da su, da yanda ake son zaman na ta
ya kasance a fadar Fabarusa kasancewar Sarki ya janye
makwanin biyun da ya kamata a kai Bintu ga Masarautar
Fabarusa.
Bintu da ba cikin hayyacin ta ta ke ba, babu abun da ta gane
kawai dai amsa ma ta ‘’um’’ ta ke. Da wuri Hajja Kilishi ta
bawa Bintu umarnin kwanciya saboda sammakon da za su yi a
washagari. Yanda ta ga rana haka ta ga dare, haka ta kwana
cikin zulumi sai da asuba wani bacci mai nauyi ya sace ta.
Ba ta jima ta na bacci ba, Hajja Kilishi ta aiko d’aya daga cikin
Bayin da aka bawa Bintu, wato Ladiyo ta tada ita gudun kada
su makara. Nan ta ke tseguntawa Bintu cewar Gimbiya Binta
har ta wuce Nigeria makaranta bisa ga umarnin Takawa. Kuka
Bintu ta saka ta na mai fad’in
‘’Na shiga uku ni Bintu, wallahi ni Bintu na ke ba Binta ba,
d’iyar bayi na ke ba d’iyar Sarki ba, ashe dai ba zan kammala
makaranta ta ba, wayyo Inna ki zo ki taimake ni na shiga uku
na lalace!’’
Da ladiyo ta ga haka, kawai sai ta fice, jim kad’an sai ga ta
dawo biye da ita Hajja Kilishi ce rai 6ace. Tuni ta hau Bintu da
fad’a, ta na fad’in
‘’Wai ashe ba ki da tawassali Fatima? Ba ki yarda da k’addara
ba? Idan ba ki fasa kuka ba ba ba ki nuna mana ba a isa da ke
ba’’
Jin wanna kalame na Hajja Kilishi tuni Bintu ta shiga taitayin
ta, sai ajiyar zuciya ta ke kawai. Hajja Kilishi ba ta gushe ba ta
cigaba da maganar ta kamar haka
‘’Ki d’au kaddara ki yi fata Allah ya sa hakan shi an alhairi gare
ki, yoto ai alkhairin ne ma. Ina ke ladiyo ?’’
Ladiyo ta matso kusa tare da fad’in
‘’Ran ki shi dad’e’’
‘’Maza ku shiga bayan gida ku had’o mata ruwan wankan
amare’’
Cewar Hajja Kilishi.
‘’An gama ran ki shi dad’e’’
‘’Ke kuma Hansai maza shirya kayan Gimbiyar ta ku, Ina
Maman Cangwai ne? maza ku sheda mata ta ta kawo maganin
d’ar nan da lalle domin yiwa amarya wankan lalle’’
Hansai na mai duk’ar da kai ta ce
‘’Ranki shi dad’e ai tuni Maman Cangwai na can rariya, fitowar
Bintu kawai ake jira......’’
‘’Bintu ki ka ce!!’’
Hajja Kilishi ta daka ma sa tsawa. Hansai ta zube k’asa jiki na
6ari ta ke fad’in
‘’Tuba na ke ranki shi dad’e, na tuba ran ki shi dad’e ki min rai
aradu na tuba’’
‘’Kwarankwatsi ki na rasa ran ki muddi ki ka kuskure asirin
Masarautar ga tonu sanadiyar kuskure irin wang, shasha
kawai, me an sunan Gimbiyar ga?’’
Hajja Kilishi na magana ne a hasala kamar mai shirin bugun
Hansai. Ita kuwa Hansai idanun ta ke kawo ruwa.
‘’Gimbiya Bintu.....’’
‘’Gimbiya Fatima, ban yarda kin kira ta Bintu ko Binta ba!’’
‘’An gama ran ki shi dad’e, godiya na ke’’
Cewar Hansai. Allah Allah ta ke Hajja Kilishi ta sallame ta ko ta
sami sarari. Jin Hajja Kilishi ta ce ta yi maza ta idda umarnin
da aka ba ta, Hansai ta tashi da sauri ta fice. Kan ace me?
Tuni aka shiga hidimar shirya Bintu, sai ga ta ta fito tsaf da ita
cikin fararan tufa tun daga sama har k’asa. Hajja Kilishi ce ta
d’auko wani dank'areriyar sark’a na gwal tare da yari da
warwaro ta ce a sanyawa Bintu na ta gudunmawar kenan.
Haka ma Inna Salti ta turowa Bintu goma ta arziki, ciki har da
farrar god'iya. Sauran matan Sarkin ma suma ba a bar su baya
ma, sai da su ka yi tattaki domin
nuna bacintar su dan kuwa abu na kishiyoyi sai da ya so ya
zama gasa.
Rana ba ta k’arya, sai ga shi ana fitar da kayan Bintu zuwa
motocin da ke jere domin kai amarya ga Masarautar Fabarusa,
yayinda dattijiwar da ta zo amsar amarya, me suna Uwalanze
ke zaune ta na jira. Wasu dattijai mata guda biyu, wanda su ke
tamkar kakanni wajan su Gimbiya K'amariyya ne bisa ga al’ada
su ka zo raka Bintu wajan Sarki domin su yi sallama a
matsayin Mahaifin ta, sannan su damk’a ta ga mutan
Fabarusa.
Bintu na ji ta na gani su ka sa ta tsakiya, gud’a ke tashi su
kuwa tsofi fad’i su ke
‘’Allah Ya ba da sa’ar tafiya Gimbiya Binta, Allah ya sa a dace
d’iyar arziki’’
Ba su zame ko ina ba sai turakar Sarki, in da su ka tadda
Jakadiya tsaye bakin k’ofa ta na jira. Da isar su ta mu su iso
zuwa gaban Sarki da ke daman abun da ta ke jira kenan.
Gaban Sarki su ka aje Bintu dan idan aka d'auke dattijiya mai
suna Gwaggo Munari cikin su, duk a na su zatan Gimbiya Binta
ce. Sai da su ka kai gaisuwar su ga Sarki sannan su ka juya su
ka bawa Sarki waje domin su gana da d’iyar sa.
Murya na rawa Bintu ta furta
‘’Barka da safiya ran ka shi dad’e’’
Shiru be iya amsawa ba, tsabagen tausayin Bintu da ya ji ya
lullu6e shi, gami da nadamar hukuncin da ya aikata bisa ga
san zuciya. Daga bisani ya nisa tare da fad’in
‘’Da wata murya za mu amsa mi ki Fatima? Da wata murya za
mu amsa mi ki d’iyar arziki? Da wani baki za mu amsa mi ki
wanga d’iya da ke gaban mu? Yau mun yi kad’an mu amsa
gaisuwar wagga d’iya, wacca jama’a su ka ku6uta da ga
yunwa saboda ita. Sanadiyyar wagga d’iya, mutan Sa’ayrasa
na godiya gare mu, mu kuma godiyar mu gare ki ya ke, Allah
ya saka mi ki da alkhairi sa’’
Shiru ya yi na d’an wani lokaci sannan ya cigaba
‘’Mungode kwarai hak’ik’a mun yi dana sanin abin da ya
wakana a Masarautar mu, hallo mu na fatan hakan ya zama
alkhairi a gare ki. Ki tsaya tsayin daka domin tabbatar da rufin
asirin mu, shakka babu kin mana abin da ‘ya’yan mu ba su ma
na ba. Tashi ki tafi d’iyar arziki, mu na addu’a albarkar Allah
ya bi ki duk in da za ki kasance’’
Jiki na rawa, amma Bintu ta kasa tashi ta kuma kasa magana.
Jakadiya ce ta lek’o, ganin yanayin da Bintu ta ke ya sa ta yiwa
Dattijan nan magana su shigo su tafi da Bintu Sarki ya gama
ganawa da ita.
A 6angaran Hajja Kilishi su ka tadda Dattijiwar Fabarusa wato
Uwalanze. Nan aka damk'a hannun Bintu gare ta bisa alada da
amana. Bintu fuska k’udundune cikin alkyabba kuka har da
majina, Uwalanze ta ja hannun ta, biye da su d’aya daga cikin
wannan dattijan ne da su ka kai ta ga Sarki, dama kuma ita
d’in ce cikin su ta san gaskiyar lamarin wato Gwaggo Munari.
Kai tsaye motocin Fabarusa su ka numfa.
Motoci ne na gani na fad’a wanda ke tashe wannan k’arnin.
Mota ta farki cike fal da dogaran Fabarusa, sai ta biyu wacce
ke rufe ruf da bakin gilashi, ita ce motar da su Yarima Barde ke
ciki. A ta ukun Bintu ke zaune tsakiyar Uwalanze da Gwaggo
Munari. Sai ta hud'in kuma bayin da aka bawa Bintu ne, wanda
idan ka d'auke Maman Cangwi ko wacce daga cikin su tafe ta
ke da na ta kullalliyar akan Bintu. Mota ta biyar ma dogaran
Fabarusa ne ciki. Nan su ka d'auki hanyar Fabarusa.
A hankali Bintu ta ji ana ta6a kafad'ar ta, maimakon ta tashi
sai ma dad'a lumshe idanu ta yi ta na mai murmushi,
kasancewar mafarkin da ta ke mai dad'i, wai ga ta a
makarantar su, tare da Aisar su na zantawa ya sa ta ji sam ba
ta so ta farka. Gwaggo Munari ce ta katse mata jin dad'i ta
hanyar jijjaga kafad'ar ta, wannan karan da d'an karfi domin
kuwa sun jima da isa Masarautar Fabarusa, yanzun haka kofar
fada su ke, Uwalanze har ta fice daga motar amma Bintu na
nan ta na baccin asara.
A firgice Bintu ta tashi jin jijjigar ta wuce hankali, ga busar
algaita da ke tashi, har da hayaniya da wak'e dake tashi daga
bakin mutan Fabarusa da su ka cika kofar fada domin ganin
isowar amaryar Yerima Barde.
Ganin alamar Bintu ta tashi, Gwaggo Munari ta shiga gyara ma
ta alkyabba yanda fuskar ta zai rufu da kyau, ta na fad'in
"Ko ke fa Gimbiya d'iyar Sarki mai dole, ai ke kuwa bacci be
same ki ba"
Kalmar nan ta Gimbiya da jama'a ke kiran Bintu da shi sam ba
ya mata dad'i, gani ta ke tamkar ana raina mata iyayen ta, ya
ga wanda su ka haife ta amma fin k'arfi zai sa a raba ta da su?
In dai haka zama Gimbiya ya ke Allah wadar da irin na
Sa'ayrasa.
Ta na kan wannan tunani ne gilashin motar ya sauka, yayinda
Jakadiyar Fabarusa ta bayyana a gare su, kana ta ce
"Gide mutan Fabarusa, na cikin gari hallo da na fada, kwan mu
da kwarkwatar mu, mun hito domin tarbar amaryar zaki,
Yariman mu abin alfaharin mu. Mu na neman alfarmar
bayyanar wagga Gimbiya ta Sa'ayarasa, da ta kasance
Gimbiyar Fabarusa da ga ranar jiya har illa MashaAllahu"
Gwaggo Munari na mai murmushi ta amsa mata da
"Gimbiyar ta mu, wacce ta kasance fure a gare mu, wacce
babu shakka za ta wadata ku da kyawu gami da kamshi da ke
tattare da ita, Gimbiya Fatima ta Sa'ayrasa ta amsa kiran
mutan Fabarusa"
Jakadiya ta rangwad'a gud'a, tuni waje ya kaure da
hayaniya,yayinda mata da yara su ka hau wak'a su na tafi, fad'i
su ke
"Mun nema! An ba mu! Mun k'aru!
Mun nema! An ba mu! Mun k'aru!"

Bintu ɗiyar bayi ce (book 2) Chapter 7
Admin 001 Sayyadi Sadiq
@Whatsapp 08146934644

7⃣
Sidiya ce...✍🏼
Jakadiya ta bud’e kofar motar ta in da Bintu ta ke. Bayi mata
guda goma shabiyu, wanda su ka kasu gida biyu sahu su ma
jere kan sa sunkuye gaban motar su na jiran fitowar Bintu
domin taka mata baya. Idan Bintu ta motsa toh dutse ma ya
motsa, sai da Gwaggo Munri ta fito sannan ta zagayo gare ta,
hannun Bintu ta lalabu cikin alkyabba, sannu a hankali, cikin
azanci kai ka ce Gimbiyar ce da gaske ta fito da Bintu. Tuni
bayin nan su ka zube gwiwowin su biyu a k’asa cike da
girmamawa. Mata da yara masu waka ba su fasa ba. Cewa su
ke
‘’Mun nema! An ba mu! Mun k’aru!
Mun nema! An ba mu! Mun k’aru!!’’
Jakadiya kuwa ba ta fasa gud’a ba. Tuni hayaniya da sowar
jama’a ya rud’a Bintu, har sai da Gwaggo Munari ta fahimta
ganin yanda ta cize waje d’aya ta kasa tafiya. Cikin rad’a
Gwaggo Munari ta

Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3Chapter 4Chapter 5

Please Login or Register in order to submit comment