Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ku ji mu da Ladiyo da yasasshen zance, tuwo ne towo
ba a sake masa suna, maza d’auko mu tai ko ba komai na
sha iska’’
Cike da farin ciki Ladiyo ta da’aukowa Bintu d’aya daga cikin
kayan ta na bayi, kan kace me sai ga Bintu ta koma gidan ta
na da, wato shigar kayan bayin Sa’ayrasa, Ladiyo har ta na
mata tsiyan ya ta ga kayan sun kar6e ta sun zauna jikin ta
sosai, ko da shike daga jikin ne.
Bintu na duban kan ta cikin madubi, idanun ta cike da kwalla
ta ce
‘’Allah Sarki wata rana, aradu Ladiyo na fi san rayuwa ta a da
akan wagga sabuwar rayuwar’’
‘’yo to Bintu ina ga cigaba ki ka samu, wani sa’ilin sai na ji
dama ni ce ke aradu da kin ga yanda ake tsiya da mulki. Mu
tai dan Allah kar wani abun ya zo ya sa mu fasa hita’’
Bintu na me goge kwalla ta bi bayan Ladiyo. Daga waje su ka
tadda bayi mata wanda Goggon nan ta bawa Bintu zaune.
Ganin su sai da Bintu ta ja da baya gudun kar da su waye ta.
Ladiyo ce ta yi maza ta ja hannun ta tana mai fad’in
‘’barkan ku da dare’’
‘’barka dai Ladiyo, an fito shan iska ne?’’
Su ka amsa mata amma idanun su na kan Bintu. Ladiyo ta ce
‘’eh Gimbiya na da muradin a bar ta ita kadai’’
Kai su ka jinjina su na mai musu fatan dawowa lafiya. Har sun
yi gaba su tsaida su ta hanyar fad’in
‘’ba ku ji ba’’
Cak su ka tsaya, Bintu na mai rawan jiki, cikin ran ta fad’i ta ke
‘’shikenan sun gane ni’’
Ita kanta Ladiyo mutawar tsaye ta yi ta na jiran tsammani.
D’aya daga cikin bayin ce ta matso gare su kana ta ce
‘’Ladiyo wagga baiwar ban waye ta, shin ko ita ce Lantana?’’
Ta na magana ne yayinda ta ke k'ok'arin ganin fuskar Bintu
wacce ta 6uya cikin duhu. Ladiyo na mai sosa k’yeya ta ce
‘’ah ah wagga Batula sunan ta’’
‘’Batula?’’
Baiwa ta sake maimaitawa, Ladiyo ta jinjina kai kafin ta ja
hannun Bintu su ka yi gaba ta na fad’in
‘’bari dai mu je mu dawo....’’
Ko da su ka k’urewa ganin bayin sannan su ka karya kwanar da
za ta sada su ga lambu, har lokacin gaban Bintu be dena
fad’uwa ba, haka kuma Ladiyo ba ta fasa mitar gulma irin na
bayin Fabarusa ba.
Hankalin Bintu be kyauta ba sai da ta tsinci kan ta cikin lambu.
Lambu ne mai ban sha’awa wanda ya sha ado da bishoyin
kayin marmari iri daban daban. Hasken wata da yayi fari kal a
tare da hasken lantarkin da ke daga cikin kowacce kusurwa na
cikin lambun ba k’aramin k’ayata shi yayi ba. In ban da koken
tsuntsaye da na kwari babu abun da ke tashi cikin lambun.
Tuni Ladiyo ta shiga raba ido ko Allah ya sa ta ga wannan
mutumin, ita kuwa Bintu wani dutse ta samu ta yi zaman ta kai
ta na fad’in
‘’kai Ladiyo wagga lambu ba dai ni'ima ba, ni dai na yi wajan
zama daga nan’’
Ladiyo na mai raba idanu ta ce da Bintu ita dai za ta d’an taka
to, yanzu za ta dawo. Nan bisa dutse ta bar Bintu yayinda ta
kutsa cikin lambu domin neman wannan mutumin.
Barde kuwa da daman shi Ladiyo ke nema zaman Lambun ne
ya ishe shi, gaba d’aya ya kasa samin nutsuwa. A hankali ya ke
shawagi cikin lambu, wani irin wari ya ji yana bak'untar hancin
sa sannu a hankali, tun ya na iya jurewa har ya kasa ya yanke
hukuncin ficewa daga Lambun gaba d’aya dan kuwa warin ya
fi k’arfin na mataccen dabba. Ko da ya d’auki hanyar fita daga
Lambun nan ya ji wari na k’ara gabato shi. Nan bisa dutse yayi
kaci6us da ita kishingide, idanun ta runtse tamakar mai bacci,
hakan nan wani irin wari da tun da yazo duniya be ta6a jin irin
sa ba ya daki hancin sa har sai da ya ja baya da sauri wanda
k’aran sautin motsin na sa ya sa Bintu bud’e idanun ta yayinda
ta kai kallan ta ga kyakkawan buzun da ke tsaye gaban ta,
hannayen sa biyu bisa hancin sa da alama yana k’ok’arin kare
hancin daga jin wari ne.
🐫🐪🐫🐪🐫🐪

Bintu ɗiyar bayi ce (book 2) Chapter 14
Admin 00 Sayyadi Sadiq
@Whatsapp 08146934644

1⃣4⃣
Sidiya ce...✍🏼
Barde kuwa a nasa 6angaran komawar sa turakar sa har da
amai. Hankanlin sa be kwanta ba sai da ya amayar da
dukkanin abun da ke cikin sa. Abun da ya ke bashi mamaki be
wuce yanda yaji dan adam ya na wari kamar na mushe ko
kuwa ja6a ba, daga ganin shigar ta ya san baiwa ce sai dai ba
irin kalar shigar bayin Fabarusa ba ne, ko koma baiwar wata
masarauta ce dole ya sa a nemo masa ita a sallame ta daga
cikin fada ta je ta nemi magani gyambon da ke jikin ta idan dai
ba so ake kar shi har lahira ba. Da wannan ya sami mafakar
rashin zuwa ya ga amaryar sa, yayi kwanciyar sa abun sa.
Washagari da sassafe Jakadiya ta je masa da karin kumallo
na musammam bisa ga umarnin Sarki Abdulrahman. Wanda
Yarima Barde ya san ba komai ba ne illa tambayar
‘’shin ka je wa matar ka?’’
Saboda haka ko da Jakadiya ta tashi tafiya sai Yarima Barde
ya bata sak’o zuwa ga Gimbiya Fatima, ya na mai fad’in
‘’a shedawa Gimbiya Fatima, bayan gaisuwa da fatan ta na
lafiya, ta saurari zuwan mu bayan fad’uwar rana, kada ta
tsawaita buri ba ma buk’atar komai daga gare ta’’
Kalaman da Barde ya k’arasa da su be hana Jakadiya
rangwad’a gud’a ba, dan kuwa ta san tabbas idan aka juri kai
zuga gabas wata ran ta zo da ruwa. Ai kuwa ko da sak’on
ziyarar Barde ya riski su Bintu, nan fa Bintu ta ga ta kan ta dan
kuwa tun da safiyar Manman Cangwai ta shiga gyara ta da su
turarukan wuta, tsimi ne da cukwid’i kai har da wanda ma ba
a sa ta ba, domin fa Maman Cangwai ita ta na da nata
manufar na musammam cikin ran ta na game da Bintu, sai dai
sa6anin sauran ita kad’ai ke san Bintu da alkhairi.
In dan ban da fad’uwar gaba babu abin da Bintu ta ke, bini bini
ta ke duba lokaci ta na mai fargabar fad’uwar rana da abun da
za ta zo mata da shi na daga ziyarar Yariman Fabarusa. Haka
kuma kaman nin wannan da ta gani cikin lambu be dena mata
gizo ba, da za ta sami dama ko shakka babu ta na komawa
cikin lambu ko Allah ya sa ya k’ara bayyana a gare ta.
Yarima Barde ma cikin zulumin had'u da k’anwar Gimbiya
K’amariyya a matsayin matar shi ya wuni. Rana na fad’uwa ya
shirya cikin shigar sa na saraki, biye da shi amintaccan bawan
sa ne wanda ake kira Bakar namba, su ka nufi 6angaran su
Bintu.
Lifaya fara kyal Bintu ta d’aura bayan ta sha turaruka na hayaki
da humra. Ta na daga zaune bisa gado gaban ta na fad’uwa
tsabagen fargaba ji ta ke kamar ta zura a guje. Maman
Cangwai ce ta sa ta a gaba ta na ta jera mata bayanai tare da
kashedi, fad’i ta ke
‘’kin san dai ke d’iyar Sarki ce ba d'iyar bayi ba, ki kasance
mai rowar muryar ki a gare shi, ban da yawan surutu in dai ba
ya zama dole ba, ki kasance gwanar iya kalamai duk san da
zaki bud’i baki ki yi furuci, ki tabbatar kin tauna kin juya kan ta
hito daga leban ki.........’’
Daga waje tun isowar Yarima 6angaran na Bintu warin nan da
ya ji a lambu ya fara bakuntar hancin sa, hankalin sa ne ya fara
tashi yayinda ya ji bugun zuciyar sa na dad’a k'aruwa. Cikin
wannan hali ya yi tsaye bakin k’ofar falon Bintu, yayinda bak’ar
namba ya shiga kwad'a sallama.
Ladiyo na mai amsa sallamar ta fito, ganin wanda ke gaban ta
tsaye ta yi ta na duban sa. Sanye ya ke cikin fara Jabba wanda
aka mata ado da koran zare, bisa babban rigar sa ce na
dokakkiyar shadda fara kyal sai d'aukan ido ya ke. Haka
rawanin da ke bisa kan sa irin na buzaye zuwa huffin da ke
sanye cikin k’afafun sa farare ne kyal kai ka ce shirya shi aka
yi.
Ganin ta saki la66a da su ga66a ta na duban Barde, ba ta da
niyar motsawa bare ta kai gaisuwar ta gare shi, ya sanya Bakar
numba fad'in
‘’hattara d’iyar talakawa! Yarima Barden Mahadi shi an gaban
ki’’
Tuni Ladiyo ta zu6e k’asa jin buzun nan dai ba kowa ba ne illa
mijin Bintu, fad’i ta ke
‘’tuba na ke Yarima, Allah ya huci ran Yarima, babban Barde
babban bako’’
Shi kuwa Barde ganin tufar jikin ta ne ya dad’a d’aga masa
hankali ba wai yanda ta masa ba, dan kuwa tabbasa wannan
baiwar mai wari da yayi arba da ita cikin lambu a daran jiya
irin shigar ta kenan. Idan kuwa haka ne to lalle d’aya daga
cikin bayin matar da aka aura masa ne ke wannan mugun
warin da ke neman halaka shi.
Bakar numba ne ya amsa da
‘’an gaishe ki d’iyar talakawa, ki shedawa Gimbiya Fatima
Yarima Barde na neman iso gare ta’’
Da sauri Ladiyo ta tashi har tana hard’ewa, yayinda ta ke fad’in
‘’an gama ran Yarima ya dad’e’’
Ciki ta shige jiki na rawa, ta tadda bayin da ke hidima cikin
falo wanda k'atuwar muryar Bakar numba ya sanar mu su da
isowar Barde, kowannan su ya nutsu jere cikin sahu,
musammam bayin Fabarusa wanda dama sun fi na Sa’ayrsa
sanin darajar Barde. Kai tsaye cikin d’akin Bintu Ladiyo ta
shige ta na mai zubewa k’asa gaban Bintu dan kuwa ganin
Barde ya sa ta tsorata da sa’a tare da nasarar da ke tattare da
d’iyar bayi
‘’ran Gimbiya ya dad’e, Yarima Barde ya iso ya na mai neman
iso gare ki Gimbiya’’
🐫🐪🐫🐪🐫🐪

Bintu ɗiyar bayi ce (book 2) Chapter 15
Admin 001 Sayyadi Sadiq
@Whatsapp 08146934644

GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA
YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN
SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA
NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN
ALLAH MU KIYAYE.
1⃣5⃣
Sidiya ce...✍🏼
Jin haka hankalin Bintu ya tashi, cike da fargaba ta kai duban
ta ga Maman Cangwai, wacce ta gane halin da Bintu ta ke ciki
kana ta ce
‘’ki nuna masa hanya ya iso gare ta, ni da sauran bayi za mu
tsaya daga wancan d’aki, ke kuma Ladiyo da ke ku tsaya
daga wajen kofa kafin Gimbiya ta sallame ki’’
Cikin rawan jiki Ladiyo ta tashi ta na mai fad’in
‘’an gama ran gimbiya shi dad’e’’
Ko da ta koma gun su Yarima Barde, Maman Cangwai ce ta
fito da kan ta ta sallami sauran bayi zuwa ga d'ayan d’akin,
duk da kuwa bayin Sa'ayrasa ba haka su ka so ba, su ma dai
so suke su ga Yarima Barden nan da jama’a ke yawan
ambaton sa wajan kyawu. Ladiyo a gaba, biye da Ita Yarima
Barde ne in da shi kuma Bakar numb ya tsaya daga waje, su
ka shigo falon Bintu.
Warin nan da ke d’aga masa hankali shi ya ke bunk’asa ya na
dad’a bakuntar hancin shi duk sanda ya d'aga k’afa ya sauke a
falon. Isar su tsakiyar falon Yarima Barde ya tsaya cak, ga
mamakin Ladiyo ji ta ya furta
‘’gide bayi masu shiga irin ta ki nawa ne cikin wanga turaka?’’
Ladiyo na mai susa k’yeya yayinda ta shiga kame kame ta
cikin fargabar kar dai ya gane ita ce mai bin bayan sa cikin
lambu ta yi saurin fad’in
‘’iye na’am? Mu na da d’an dama ran Yarima Barde ya dad’e,
wagga shiga ita an shigar bayin Sa’ayrasa, dukkanin mu wagga
shiga mu ka yi Allah shi da ran Yarima’’
Yarima Barde na mai duban ta ya ke d’an tuntuntuni, dan kuwa
ko shakka babu ya san wagga baiwa ta gaban sa ba ita ce mai
warin da ya gani a lambu jiya ba, duk da dai be ga fuskar
waccan da kyau ba amma ya san a jiki waccan tafi domin
kuwa Ladiyo irin k’ananan matan nan ne. Shi kuma a yanzu be
da buri da ya wuce ya gano baiwar nan da ke wari ko ya sami
lafiya domin kuwa muddun ta na nan ba zai iya zama ko da na
minti hud’u a turakar amaryar ta sa ba, abun mamaki shi ne ta
yaya bayin Gimbiya kamar Fatima za su na zama da wari har
haka ba tare da ta d'auki mataki ba? Hakan ke tabbatar masa
da k'azantar da ke tattare da ita.
Juyawa yayi ba tare da ya sake tankawa Ladiyo ba, wacce ta yi
kasake ta na duban sa ta rasa yanda za ta yi da ran ta, ganin
dai da gaske ficewar ya ke ta bi bayan sa da sauri, amma ina
kan ta cima su tuni ya d’au hanya, Bakar numba biye da shi.
Da gudun ta ta dawo d’akin Bintu in da ta zu6e k’asa ta na
kuka fad’i ta ke
‘’ki min rai Gimbiya, kwankwatsi ban san shi an Yarima Barde
ba, aradu da na san shi na da ban bi bayan shi ba, in k’arya na
ka yi aratta kashe ni’’
Cike da mamaki Bintu ta yane lifaya da ta rufe fuskar ta,
tambaya ta ke
‘’gide lafiya? Yo to minana? Mi Yariman yay mi ki da har ya
sanya ki kuka Ladiyo? Ina Yariman ya ke?’’
Ladiyo wacce duk a zatan ta Yarima Barde ya gano ta ne ran
sa ya 6aci har ya juya ya fasa ganin Bintu ta ce
‘’ Yarima Barde ya juya ya koma, ki min rai kar ya sa a tsire ni,
ina ni ina lek’en surrun Yarima Barde, ki taimaka ki min rai,
wayyo ni Ladiyo sai kuma yanda aka yi da ni d’an daudu a
kabari’’
Ganin dai Ladiyo ba ta da niyar bata cikakkiyar amsa ya sanya
Bintu tashi ta fita da kan ta, ita ma Ladiyo bayan ta ta biyo
wanda kukan ta ya sa sauran bayi fitowa. Maman Cangwai na
mai tambayar ko lafiya? Ina Yariman ya ke? shin me ya fito da
Bintu daga uwar d’aka ita kuma Ladiyo kukan me ta ke?
Kasa amsa mu su Ladiyo ta yi har sai da Maman Cangwai ta
daka mata tsawa sannan ta iya labarta mu su yanda ta bi
bayan Yarima Barde zuwa Lambu ba tare da ta fad’i jan Bintu
zuwa lambu da ta yi ba, yanzu haka ya gano ita ta ke lek’en
asirin sa.
Cikin jimami kowa ya ke duban Ladiyo wacce ta had’a zufa,
hawaye da majina. Ita kuwa Bintu waje ta samu ta zauna cikin
neman mafita, dan kuwa muddin abun da Ladiyo ta fad’a
gaskiya ne, ko shakka babu dole sai an hukun ta ta, lek’en
asirin Yarima ba k’aramin laifi ba ne, za a iya amfani da
wannan ace so ta ke ta idda wani mugun nufi kan sa ko kuwa
dai ta ha’d’a baki da abokan gaba ta na san halaka shi.
Yarima Barde kuwa da fitar sa kai tsaye gun Jakadiya ya nufa.
Ya tadda ta bisa sallaya tana lazumi kan ta zo ta shiryawa
sarki sauwar dare. Ganin Barde ta san da matsala wanda shi
ma be 6oye mata ba ya sheda mata cikin azanci ba tare da ya
fayyace mata komai ba.
‘’ya Jakadiya, a had’a fanteka na turaruka, na jiki zuwa na
kaya, a aika ga Gimbiyar Sa’ayrasa, a kuma sheda mata
Yarima Barde ma’abocin k’amshi da tsafta ne, ta gaggauta
sauya gimshikin kusurwar ta’’
Cewar Yarima Barde, wanda ya juya ya tafi ba tare da ya tsaya
amsa tambayoyin da Jakadiya ke shirin jera masa ba. Abun da
kuwa ya fi d'aure mata kai shi ne fantekar turaren da za a kai,
ga kuma batun na Barde na Bintu ta gaggauta sauya gimshikin
kusuwar ta, ko shakka babu Barde ya ji wari daga wani
6angare na Bintu ko kuwa bayin da ke tattare da ita.
Ba tare da 6ata lokaci ba Jakadiya ta aikata yanda Barde ya
ce. Cikin baitul mali ta shiga, daga cikin daular iyalan Sarki
Abdulrahman ta jido turarurruka fanteka guda, cikin bayi ta
za6i wacce ta fi tsana sannan ta d'aura mata fanteka ta tere
da bata sakon Barde zuwa ga Bintu. Jin sak'on da aka bata sai
ga baiwa a k'asa ta na yiwa Jakadiya magiya da kada ta tura ta
da wannan mugun aike, amma ina sai ma tafiyar ta yi ta barta
ta na share hawaye dan kuwa dai ta ta ce ta same ta kishiya
tara rana d’aya.
🐫🐪🐫🐪🐫🐪

Bintu ɗiyar bayi ce (book 2) Chapter 16
Admin 001 Sayyadi Sadiq
Whasssp. 08146934644

1⃣6⃣
Sidiya ce...✍🏼
Ta na tafe ta na hawaye haka ta isa 6angaran Bintu in da ta
tadda Ladiyo zaune gaban Bintu ta sha kuka ta k'oshi, daga
gefan Bintu kuwa Maman Cangwai ce zaune a k’asa, d'ayan
6angaran Hansai da lantana ne zaune. Bintu ta sallami
dukkanin bayin Fabarusa domin samarwa Ladiyo masalaha.
A gaban Bintu baiwa ta aje fanteka ta na mai rawan jiki, tun
gaisuwar da ta kai ga Bintu, bakin ta na motsi amma tsoro da
kwarjinin Bintu ya sa ta kasa furta komai. Maman Cangwai na
me duban ta ta furta
‘’ke mu ke sauraro ya ke d’iyar Fabarusa....’’
Maimakon Baiwa ta fad’i dalilin zuwan ta da kuma sak’on
Barde, sai gani su ka yi ta fashe da kuka ta na mai fad’in
‘’tuba na ke ran Gimbiya ya dad’e, ki min rai na tuba ki rufa
min asiri, tuba na ke’’
Nan fa su Ladiyo da lantana su ka shiga kallan kallo cike da
mamaki. Bintu ma mamaki ya ne ya lullu6e ta, cikin ba da
umarni ta ce da Maman Cangwai ta bud’e fantekar ta ga abun
da baiwar ke tafe da shi. Ko da Maman Cangwai ta bud’e
fanteka sai da gaban ta ya fad’i ganin turaruka iri daban daban
masu yawa ciki. A hankali ta kai kallan ta ga Bintu wacce ita
ma ta hango me ke cikin fantekar kafin ta maida kallan ta ga
baiwar, kana ta furta
‘’wannan kuma daga ina?’’
Baiwa ba ta fasa hawaye ba ta furta
‘’gide sak’o ne daga Yarima Barde zuwa ga Gimbiya Fatima,
hallo ya na mai sheda mata cewar Yarima Barde ma’abocin
k’amshi da tsafta ne, ta gaggauta sauya gimshikin kusurwar
ta.......’’
Ta k’arasa furucin na ta ne cikin rawan murya. Shiru kake ji
babu mahalukin da ya furta komai tsabagen bazata da kalamin
baiwar ya mu su, babu shakka Barde na me shedawa Bintu
wani abu daga 6angaran ta ya na wari duk da dai be fayyace
mata ko menene ba, wanda turo fantekar turaren da yayi ba
k'aramin cin fuska a gare ta ba ne, ba dan ma an riga an
d’aura mu su aure ba da hakan daidai ya ke da ya ce ya fasa
auren ta saboda wari da ya ji na daga wani 6angare da ya
shafe ta.
Sai a sannan Maman Cangwai ta gane kukan da baiwa ta ke,
dan kuwa a k’aida ya zama dole Bintu ta hukunta ta bisa ga
sak’on cin fuska da ta iya duban tsabar idanun Bintu ta sheda
mata, in kuwa ta yi sake ta rabu da ita salin alin, toh tabbas ta
siyawa kan ta raini daga kan jama’ar fada har izuwa sauran
bayin na fada babu wanda za ta k’ara yiwa kwarjini bare a ji
shakkar ta.
Jin Bintu ba ta furta komai ba Maman Cangwai ta dawo daga
gefan ta, in da ta zauna kamar me jiran umarni daga Bintu, a
kaikaice yanda baiwar ba za ta fahimta ba ta ce da Bintu
‘’hattara Gimbiya, wanga batu ba na sassauci ba ne, dan haka
zan ari bakin ki in ci albasa, ina mai neman alfarma rashin
maganar ki bisa hukumcin da zan aiwatar kan wagga baiwa ta
fabarusa’’
Ba tare da ta jira amsar Bintu ba ta mayar da kallan ta ga
baiwa, sannan ta ce
‘’bisa ga umarnin Gimbiya, ta yaba da kyautar Yarima a gare ta,
sa'annan wagga baiwa da ta kawo sak’o gare ta, zaki amshi
bulala hamsin na daga tsimagiyan Gimbiya Fatima’’
Da sauri Bintu ta kai kallan ta ga Maman Cangwai cike da
6acin ran jin furucin na ta ta yi k’ok’arin dakatar da ita, wanda
hakan ya sa Maman Cangwai saurin fad’in
‘’na yi kuskure Gimbiya, bulala sittin Gimbiya ta ke nufi, maza
Lanta tashi ku fitar da ita zuwa d’akin horo, ki kuma sheda ma
su umarnin Gimbiya kowa ya ji ya gani ya kuma sheda!’’
Baiwa na kuka ta na fad’in
‘’tuba na ke ran Gimbiya ya dad’e’’
yayinda Lantana ta tasa ta gaba, ta na mai fad’in
‘’godiya ta ke Allah shi taimaki Gimbiya’’
Su na fita hawayen da ya ciki idanun Bintu tuni ya gangaro
bisa kuncin ta tsabagen tausayin baiwa da ba ta san hawa ba
ba ta san sauka ba an k'ak’aba mata horo tsabagen rashin
adalci. Cike da 6acin ran da ita kan ta Maman Cangwai ba ta
san Bintu na da irin wannan fushin ba, ta furta
‘’akan wani dalili za a yiwa baiwa horo? Gide ita na ta ba sak’o
ba ne? idan adalci ne na lalle sai kin nuna an min ba daidai ba
ki hukunta shi Barde wanda ya aiko ta mana? Saboda ita baiwa
ce? Su bayi ba su ‘yanci? Bayi su an bola?’’
Jiki a sanyaye Maman Cangwau ta furta
‘’hakan da na yi kad’ai zai nuna matsayin ki na d’iyar sarki,
dan kuwa babu d’iyar sarakin da za a yiwa wanga cin fuska ta
kasa aikata yanda na aikata, in ba dai so ki ke asiri ya tonu ba.
Na san yanda ki ke ji, amma fa kada ki manta ko nima baiwar
ce, ina fatan za ki fahimce ni.....’’
A fusace Bintu ta tashi tsaye, ta na mai girgiza kai ta ce da
Maman Cangwai
‘’ba zan ta6a fahimtar ki ba in dai bisa zalinci ne, ba da
yawuna ki ka aiwatar da hukuncin ga ba, umarni na anan shi
ne ki gaggauta dagatar da shi!’’
A fusace ta wuce d’akin ta, wanda kan ta kai ga shiga
sallamar wata baiwa ya tsaida ita. Ta na ji baiwar na gaishe ta
amma 6acin ya sa ta kasa amsawa ta d’aga k’afa za ta shige
kenan amma jin furucin na baiwar ne ya tsada ta. Jin ta na
fad’in
‘’Yarima Sadauki ya na da murad’in ganin dukkanin bayin
Sa’ayrasa!’’
A hankali Bintu ta juyo, wato 6acin ran da take ciki ya sanya ta
rikidewa hatta Maman Cangwai, bare kuma su Ladiyo, tashi
guda ta tashi daga Bintun da su ka sani ta zame mu su wata
daban mai wuyan fasaltuwa. Ta na mai duban baiwar ta furta
‘’wa an Sadauki? A matsayin sa nawa ya ke da muradin ganin
bayin Sa’ayrasa gide? Akan wani dalili?
Baiwa ta yi jim dan kuwa ta tsorata da yanayin da ta ga fuskar
Bintu, cike da 6acin rai da kwarjini ga kuma tambayoyi na
gadara da ta mata akan Yarima Sadauki. Nisawa ta yi kafin ta
amsa mata da
‘’Allah huci zuciyar Gimbiya, Yarima Sadauki shi an Yaya ga
Yarima Barde wanda ya ke maigida a gare ki, dalilin sa na
murad’in ganin bayin Sa'ayrasa shi kad’ai ya barwa kan sa
sani’’
Bintu na mai jinjina kai ta ce da baiwa
‘’ki koma ki shedawa Sadauki ni Fatima na ce bayin Sa’ayrasa
ba za su isa gare shi ba muddin be zo mana da
gamshashshiyar dalilin sa na murad’in hakan ba!’’
🐫🐪🐫🐪🐫

Bintu ɗiyar bayi ce (book 2) Chapter 17
Admin 001 Sayyed Sadiq
@Whatsapp 08146934644

1⃣7⃣
Sidiya ce...✍🏼
Bintu na k’arasa magana ta shige uwar d’aka. Baiwa kuwa
tashi ta yi cikin jinjina maganar ta na mai gyad’a kai ta fice ta
bar Manman Cangwai da su Ladiyo cikie da mamakin sauyin
Bintu lokaci guda duk akan kishin bayi. Minti kad’an sai ga ta
ta fito sanye da lifayar nan da ta cire kafafun ta sanye da cikin
farin takalmin fata ta ce da Ladiyo
‘’wuce mu tai d’akin horo’’
Da sauri Ladiyo ta yi gaba Bintu na biye da ita, ita kuwa
Maman Cangwai bin Bintu ta yi da ido, cikin ran ta kuwa fad’i
ta ke lalle dole ta aika da sak’on neman taimako Sa’ayrasa
domin kuwa alamu ya nuna Bintu mai yin gaban kan ta ce.
Cikin sak’ar zuci Sadauki wanda ke zaune bisa daddumar da
ke shimfid'e a lambu ya ke duban baiwar da ta zo masa da
amsar Bintu gare shi. D’aya da ka cikin bayin sa ne ya furta
‘’gide Gimbiya d’iyar Sa’ayrasa ba ta da masaniya akan girman
Yarima Sadauki, ko shakka babu za ta tuba Allah shi taimaki
Yarima’’
Baiwa na mai gyad’a kai cikin amincewa da maganar na
bawan ta ce
‘’kwaran gaske, tuba ta ke ran Yarima ya dad’e’’
Murmushin mugunta Yarima Sadauki ya saki, cikin ran sa ya
na mai jaddada dana sanin da Bintu za ta yi bisa ga kuskuran
da ta yi a gare shi, tabbas ta tari aradu da ka dama dai ta bar
abin ya tsaya ga mijin ta da ya fi mata sauk’i, zai kuwa nuna
mata bakin rijiya ba wajan wasan makaho ba ne. Mik’ewa yayi
tsaye yayinda bawan sa yayi saurin matso da takalman sa
gaban sa. Cike da tak'ama ya sanya bayi na masu ram masa
baya su ka d'au hanyar fita.
‘Dakin Horo kuwa Lantana ce ta idda sak’on Maman Cangwai,
nan da nan kuwa Dogarin horo ya shiga gyara tsumagiyar sa
domin aiwatar da umarnin Gimbiya Fatima. Sauran bayi fada
kuwa tuni labari ya zaga, sun yi tattaki zuwa d’akin haro
domin ganin yanda baiwa za ta fuskanci hukunci. Kujerar horo
aka sanya baiwa ta zauna yayinda aka zuba mata ruwa bisa
cinyar ta har zuwa k'asan k'afafun ta yanda ko da zafin
tsumagiya zai sa fitsari ku6uce mata ba zai nuna ba. Waje yayi
tsit kuka baiwa kad’ai ke tashi yayinda Dogarin horo ya d’aga
tsumagiyar sa ya na shirin sauke ta bisa cinyar baiwa muryar
Ladiyo ya dakatar da shi ta hanyar fad’in
‘’dakata Dogarin horo, Gimbiya Fatima ce tafe!’’
Tsayawa yayi cak yayinda Bintu ta taho, bayi na bud’a mata
hanya haka kuma ba su fasa kai gaisuwa gare ta ba har ta iso
gaban dogarin horo. Cikin bayin kuwa

Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5

Please Login or Register in order to submit comment