Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

 ↫ NI DA FATALWA! ↬

{gajeran labari}

Part {1}

@KINGBOY ISAH



NOTE:
IN KASAN KANA/KINA DA TSORO KARKA/KI KARANTA. DOMIN LABARI NE MAI CIKE DA ABUBUWAN TSORO DA NA DARIYA. IN KUWA KA KARANTA KAYI MAFARKIN FATALWA BA RUWAN KING.LOL


"Habib da gaske wai fita zakiyi ka barni ni kadai? Wallahi na gaya ma akwai fatalwa a gidan nan, ni fa na ganta da idanuna dan Allah in dai fitarka ta zama dole to ka barni in tafi gida da yamma in ka dawo daga wajen aikin sai ka biya ka dauko ni kaji angona tsoro nake ji". Tsaki naji yaja abunda bai taba mun ba tun kafin ma muyi aure balle yau da na zama amaryarsa yau duka kwana takwas nayi a gidan nasa. "Khadija naga alamun so kike ki bata mun rai kuma nima in bata miki. Wai ku mata me yasa komai sai kun canfa shi ne? Shegen tsoro ne ya miki yauwa amma ba wani fatalwa a gidan nan, ni a rayuwata kwata-kwata ma ban yarda cewa akwai fatalwa ba. Ni zan tafi kuma wallahi in kika yarda kika sa kafa kika fita daga gidan nan ko? Zakiyi mamakin hukuncin da zan yanke". Yana fadar haka ya shige motar sa ya fita sannan ya dawo ya rufe get din. Da sauri na karasa bakin get din na zukulkula kubobi hade da kule get din. Zuciyata cike take da tsoro amma ya na iya? zaman aure ya ja mun. Shima Habib sai da nace ya nema wani gidan- ya nema wani gidan amma yaki gida kusa da makabarta ai dole ma fatalwa ta takura ma. Tsaye nake tsakar gida ni kadai nake zancen zuci. Ta wutsiyar idona na hangi kamar wani farin abu ya shigar mun daki. Hakan tasa na nufi dakin a tsorace na bude labule. Sai da na leka ko'ina a falon naga ba kowa sannan na sauke ajiyar zuciya. Domin bana mantawa sau biyu naga fatalwar nan kuma fararen kaya ne a jikinta. Jikin socket ma naje na ciro wayata na bude data na kwanata kan kujera sofa, na shiga whatsapp na fara chat da kawayena domin shi ne kadai nake tunanin zai deben kewa. Message naga ya shiga na bakuwar number nayi saurin shiga hoto ne aka turo ba sallama ba komai. Na sa hannu na danna kan hotan don ya bude. Ihu na kwada hade da yin wulli da wayar. Domin kuwa hotan wannan fatalwar ta jiya ne na gani. Da gudu nayo waje daga cikin dakin. Fitowata yayi dai-dai da sallamar wata mata. Turus na tsaya ina maida numfashi ina kare mata kallo wani dogon farin hijabi ne dogo a jikin matar gata doguwa. Girman idanunta kadai abun tsorone gata dattijuwa. Cikin tsoro muryata na rawa na amsa sallamar. Sai ji nayi tace "Sunana Indo ni makwabciyar ki ce ga gida na nan gaba da gidan ki. Gani nayi an kawo amarya yau har kwana takwas nace bari na leko mu gaisa". murmushin karfi da yaji nayi cikin karfin hali nace "Bismillah to mu shiga ciki". Gabana ne ya fadi da na tuna cewa na fa kulle gidan nasa kubobi da jamuluck amma ta ina matar nan ta shigo anya kuwa ba fatalwar bace? na tambayi kaina da kaina tambayar da bata da amsa. Sofa na nuna mata nace ta zauna ni kuma na daukko mata juice a cikin kofin glass a tsorace na kawo gabanta na ajiye sananan na koma Can kuryan falon kan archair na zauna domin a matukar tsorace nake da matar nan. "Amarya banga angonba ko ya fita ne". abunda matar nan tace kenan da muryarta marar dadin saurare. "Eh dazun ya fita office". Na bata amsa. "Kina nufin ke kadai aka bari a gida? bakisan akwai fatalwa a gida nan ba". Tuni tsoro biyu suka farmake ni. Ga tsoron matar nan ga kuma ta kara tabbatar min da zargina."Fatalwa kuma Inna Indo? ashe da gaske akwai fatalwa dama sau biyu ina ganinta na fadawa Habib amma yace wai tsorata nayi". "Ba tsorata bane bari kiji na baki labarin gidan nan". Na kara gyara zama hade da mika hankalina gare ta, ta fara da cewa, "gidan nan gida ne mai hatsari nan baya da shekara biyar aka gida shi. kinga ai katanga daya ta raba ku da makabarta ko". Nayi saurin girgiz kai Alamun eh. "To da nan gidan da kike ciki makabarta ne an taba binne wata mata ce a saitin gidan nan. Matar nan kuma itace take fatalwa taki barin a zauna a gidan nan. Fatalwar nan tana da matukar hatsari gata da siffofin tsoro na tabbata mijinki ma bai san cewa haka gidan nan yake". Wani sabon tsoro ne ya sake ziyartar zuciyata lokaci guda, na daga kai ina kare wa gidan kallo. A raina nace ko habib yana so ko baya so wallahi sai ya canza min gida. taya zan zauna a gida Ni da fatalwa?...................

Autan writers ne...

https://www.facebook.com/groups/1232550283531628/







↫ NI DA FATALWA! ↬

{gajeran labari}

Part {2}

@KINGBOY ISAH

note;
Mai tsoro kar ta karanta!...

Maganar matar nan ce ta dawo dani daga tunanin da nake, "Shin kinsan me ya faru da matar da ta fara zama a gidan nan kuwa?". Na kada kai alamun Aa. "Itama amaryace kamar ki tun ranar da aka kawo ta gidan nan fatalwa ta fara firgita ta. Wata rana da daddare mijinta baya nan ya tafi wajen aiki bai dawo ba har dare wajen magariba. Tana zaune a falo ita kadai tana kallon tv kawai sai gani tayi wuyar dakin ta dauke, nan take fanka ta fara wulwulawa da karfi. Yarinyar nan tsoro ya kamata kawai gani tayi TV ta kawo ciki kuwa wata doguwar mata ce mai dogayen faracina domin farcen ta na hannu har kasa yake tabowa gashin kanta kuwa baki ne wulf amma yana da tsayi sai hakora zako-zako abun tsoro". Ina jin haka tuni na makalkale kafafuna kan kujera na kame waje daya kamar ni ce naga fatalwar. "Kina ji nan take sai fatalwar nan ta cikin TV ta kyalkyale da dariya mai firgitarwa yarinyar nan ta kwalla ihu ta yunkura zata tashi amma sai taji kamar an daure ta. Fatalwar nan ta daka mata tsawa tace "Ina zakije? ko ina zaki ba zaki guje mun ba sai kin gaya mun dalilin da yasa kuka shigo mun gida. Yarinyar nan ta fashe da kuka tace "Dan Allah kiyi hakuri wallahi bansan nan gidan ki ne ba" fatalwar nan ta bushe da dariya kawai yarinyar nan sai gani tayi fatalwar ta zuro hannu daga cikin TV zata kama ta kawai sai ta sulale kasa a sume". A firgice nace "Wayyo Allah na Fatalwar ta kashe ta?". Matar tayi murmushi tace ai ita bata kashe mutum sai dai ta basa wahala domin tana ganin yarinyar nan ta suma sai ta barta. shi kuma mai gidanta wata rana yayo dare karfe goma ya nufo gida sai sauri yake domin shi kanshi tsoron unguwar yake kasancewar dare yayi ga kuma duhun dare. yana cikin tafiya kwatsam sai ganin wani abu yayi fari tass a gaban shi. Da ya lura da kyau sai yaga kamar mutum ne a kwance cikin fararen kaya hakan yasa ya tsaya cik ya fara cewa "Waye a nan? waye ne". amma sai yaji shiru hakan tasa ya dan rabe da nufin yabi ta gefe ya wuce bai sani ba ashe fatalwa ce, Ya kusan wucewa kenan ta mirgina ta rike masa kafa a lokacin ta dago fuskarta abun tsoro da gashi baja baja ta fashe da dariya marar dadin saurare. suna hada ido kuwa ya kwallah ihun neman agaji amma ina ba wanda ya kawo mai dauki domin kowa yasan halin unguwar nan ba a zuwa da dare daga bakin isha'i duk wanda ya fito to ba shakka sai ya hadu da fatalwar nan". Ai tuni jubi ya kwaranyo min. naji tsoro ya dabai baye ni. Nace "To Inna Indo ya kike ganin za'ayi domin nima na ganta wata abun tsoro mai fararen kaya jini na zuba a idonta". Wata irin dariya naji Inna ma'au ta kyalkyale da ita wacce har sai da ta ban tsoro ma. "Kwarai yarinya kin ganta domin nima ina ganinta sosai jarumta nake kawai ina nuna mata rashin tsoro. Yanzu dai mafita daya ce ku tattara ku bar gidan nan in ba haka ba komai zai iya faruwa daku kullum kina cikin tsoro ne da fargaba. Yauwa yar nan ni bari na tashi na shiga gida gobe ma zan zo in dan debe miki kyauwa". Inji Inna Indo ta fadi haka hade da mikewa ni tuni tsoro ya kamani ita kanta tsoronta nake domin hijab din jikinta yayi kama da likafani gashi fari har kas. Tana tashi tayo waje nima na dau wayata na biyo ta da sauri domin in rufe kofar gidan. Wani sabon tsoron ne ya kara ziyarta ta domin gani nayi Babu Inna Indo gashi banji karar bude gida ba haka kuma na duba naga kubobi a makale kamar yanda nasa su dazun. Bansan lokacin da kuka ya kubce mun ba. da sauri na kira number Aunty na Hauwa. dake tana gida sun sama sabani da mijinta. "Hello amarya kinsha kamshi sai yau aka tuno damu wata amarci yasa an manta da mu ma". itace mai fadar haka kuka taji na fashe da shi ina fadin "Aunty Hauwa Dan Allah kizo yanzu akwai matsala wallahi". "Kuka kike khadija? Me ya faru ne? Innalillahi gani nan zuwa". Daga ji hankalinta ya tashi amma kin kashe wayar nayi domin tsoron da nake ji ya baci. Ban koma daki ba ba dadewa sai gata ta iso a napepk nayi sauri na bude mata kofa ta shigo tana tambayana. ban mata magana ba sai da naga mun shiga falo nace "Aunty Hauwa Wallahi gidan nan akwai fatalwa. Ni na ganta da ido n kuma yanzu wata mata ma ta shigo itama abun tsoro, take bani labarin akwai fatalwa. A gidan nan shiyasa na kira ki dan wallahi bazan iya zama ni kadai ba. dama sai da nace wa Habib ya barni na tafi gida yaki". Aunty Hauwa ta kwashe da dariya ta dade tana yi na tambaye ta me take wa dariya? wai ni take wa dariya domin ita ma wai bata yarda akwai fatalwa ba ni kuwa na kyale ta nace naji din. Haka muka wuni duk inda tayi ina biye da ita bana bari ta bace mun a gani ko kadan. Da yamma Habib ya dawo daga aiki suka gaisa da Hauwa bayan sun gaisa ne take bashi labarin zuwana da kuma irin tsorona nan fa suka hadu su biyun sukai ta mun dariya ni kam kallon su kawai nake domin ni kadai naga abunda na gani. Aunty Hauwa tace zata tafi gida na kuwa tashi hankali nace wallahi bazata tafi ba sai dai ta tsaya a nan in yaya habib ya tafi aiki ta ringa taya ni hira. Da kyar na samu na shawo kanta ta yarda da hakan a kan zata tsaya ta kwana din. Wani irin dadi naji da kaina naje na gyara mata dayan daki wanda dama saboda baki aka tanade shi. Da dare bayan munci abinci mun dade a falo muna hira sai wajen sha daya tukun muka shiga daki nida Habib Aunty Hauwa kuwa mayyar kallo tace sai ta tsaya ta idasa kallon wani indian film da ake a bollywood wani irin kuka kuka kamar na jariri ta fara ji kafin wutar dakin ta dauke dif lokaci guda kuma sai ta dawo. Wata irin firgita Aunty Hauwa tayi da ta tuna cewa Khadija ta fa gaya mata akwai fatalwa a gidan nan.................

ZANCI GABA


https://www.facebook.com/groups/1232550283531628/



↫ NI DA FATALWA! ↬

{gajeran labari}

Part {3}

@KINGBOY ISAH


*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*

[WARNING; MAI TSORO KAR TA KARANTA. IN KUMA TSORON BA SOSAI BA TO KI KARANTA DA RANA]

Ai tuni ta fara karkarwa, Kuuwwuuuuuu! karan da taji ya wuce shiff! ta gefan kunnenta kenan da sauri ta waiga sai bata ga komai ba. Tuni ta fara karkarwa amma tsabar maita taki hakura da kallon. Ji tayi an shafi bayanta da hannu. Bata san lokacin da ta saki dan kara ba. Karan yayi sanadiyar fitowar mu ni dai dama a tsorace nake ina kankame da Habib domin ko sanda muka shiga daki ma a like da shi nake kamar cingum. "Aunty Hauwa lafiya naji kinyi kara". Habib ya tambaye ta, Rau-rau tayi da ido ta hade tsoron ta hade da kakalo murmushi "Lafiya lau wallahi wani abu ne akayi a film din nan da ya burgeni shine fa nayi karar jin dadi". Habib yayi murmushi "Lalai aunty Hauwa ke ko gajiya ma bakya yi da kallo? Yanzu fa karfe sha biyu da rabi. Mu dai tuni mun kama gobe". Habib ya fada hade da komawa cikin daki. A yanayin da naga Aunty Hauwa na tabbata a tsorace take naje nayi mata tambayar duniyar nan amma tace wai ba tsorata tayi ba. na lurs dai bata so na gano ta tsorata watakil dan kar na rama dariyar da tayi mun. Tayi nayi na nufi dakina dama gidan falo ne sai dakuna uku wanda ko wanne akwai bandaki a ciki sai kuma kitchin. nace Aunty Hauwa in zaki kwanta dai kiyi addu'ah ni dai na gaya miki halin gidan nan". Aunty Hauwa tuni har jubi ya fara keto mata domin ta tsorata matuka kallon take amma bata fahimtar abunda ake yi ma. hakan yasa ta kashe TV din ta tashi ta nufi dakin baki inda Na share mata domin ta kwanta. Ta fara tafiya ta je tsakiyar falo kenan nepa suka dauke wuta dif hakan yasa ta tsaya cik! tayi saurin latsa switch off na wayar tana karkarwa amma sai wayar ta subuce daga hannunta ta fadi kasa. Aunty Hauwa tsoro ya kamata kamar zata fashe da kuka tsabar tsoro ta tsugunna ta hau laluban waya. Karar tafiya taji kamar anyo wajenta hakan yasa ta fara cewa "waye waye". amma shiru bata ji ance komai ba. "Me kike nema a cikin duhun nan". abunda taji an fada da muryar mace kenan a zaton ta ni ce hakan yasa tace "Khadija wallahi wayata ce ta fadi shine nake nema domin duhu yayi yawa bazan gane hanyar dakin ba". Dai-dai wannan lokacin nepa ta dawo fuw! aka kawo wuta bisa mamaki sai gani tayi bata ga kowa ba da sauri ta dauki wayarta ta ruga daki a guje tana shiga bata tsaya dubawa ba ta banko kofa jamuluck ya shiga. Juyawar da zatayi sai tayi arba da wata doguwar mata siririya wacce take sanye da wata doguwar riga fara sai wani mayafi da ta yafa a kafada gashin kanta duk ya barbazu a bayanta dake matar ta juya ne Aunty Hauwa bata ganin fuskarta. Nan take gabanta ya fara dukan uku-uku duk illahirin jikinta ya dau rawa. "Wace ce". Aunty Hauwa ta fada cikin muryar tsoro dake fitowa a hankula. Shiru taji Matar batayi magana ba. Ta sake maimaita tambayar har sau uku, a na hudun kawai sai matar ta juyo fuskarta fari fat kamar wacce ta shafagari amma kuma idanunta ko kadan ba fari a ciki baki kirin da su ga wani irin gashin gira dogo da Aunty Hauwa bata taba ganin kalarsa ba tunda take. "Ni ce Fatalwa Indo". Abunda matar ta fada kenan. "Wayyo Allah na dan Allah dan annabi fatalwa kiyo hakuri ban san nan dakin ki bane. Na rantse yanzu zan fita". Kulululu cikin Aunty Hauwa ya kada sai zawo kafin kace me tuni ta jika zanin ta da fitsari. Ita sam ta kasa yin addu'ah kamar an mantar da ita kuma ta kasa bude dakin ta fito a guje. Kawai sai ihu take. Fatalwar nan kuwa ba abunda take sai kyalkyala dariya. Ni da Habib muna daki har barci ya fara daukar mu muka jiyo ihun Aunty Hauwa can kasa-kasa. Dake ni na fara tashi nayi sauri na tada Habib nace ihu nake ji. Yace "kwarai kuma kamar a gidan nan ma". Da sauri ya tashi ya yo falo ni ma da nake a tsorace a guje nabi bayansa. Mukaje kofar daki mukayi mukayi Aunty Hauwa ta bude amma ta ki budewa ihu take har muryar na shakewa. Da gudu Habib ya koma domin ya daukko makolin dakin nima kuwa na bishi dan bazan yarda ya barni ba wannan yanayi. Muna dawowa mukaji Aunty Hauwa ta daina ihu. Habib na budewa muka tarar da Aunty Hauwa bakin kofa a yashe a kasa ga dukan Alamu dai suma tayi Habib ya debo ruwa ya yayyafa mata ta farko. Hade da sakin razanannen kara. Sai kawai gani mukayi ta tashi ta baza a guje ta fito daga dakin tayi hanyar kofa. Da sauri Habib ya riko hannuta. "Ina zaki Ke Hauwa lafiya kuwa". Habib yake yake tambayar ta cikin tashin hankali. Ita kuwa kokarin kwacewa take kamar mai aljannu sai kuka take tana fadin "Wayyo Allah ka barni in tafi gida fatalwa wallahi bazan kwana a gidan nan ba". Nima tambaya nake lafiya lafiya amma ina hankalinta ya matukar tashi ga dukkan alamu dai tayi matukar razana ne. Habib ya juyo yana tambayana wai ko tana da iskokai ne ai kuwa ta gallamai cizo a hannu dan dole ya sake ta ta ruga da gudu waje na bita a guje ina fadin ta dawo. Kafin ta kai gate naga taja wani uban birki ta saki razanannen kara. Ta juyo a guje, Nima ihun na saki na juya a millon sakamakon ganin abunda ta gani. Fatalwar nan ce zaune cikin fararen kaya tasa wani abu wanda shima kamar gawa ce dai cikin likafani sai dariya take hasken glof din tsakar gida ya haska mana ita. Sai gamu muna tsere da Aunty Hauwa da da take niyar bude gida ta gudu. Ina zuwa na rukunkume Habib ina fadin "Fatalwa Fatalwa". Aunty Hauwa ma da gudu ta zo ta makalkale ni. Habib yace "Wai ku wane irin mutane ne in ma fatalwar ce ba zakuyi addu'ah ba sai ihu?. oya ku sake ni naje na ga miye". Ai maimakon in sake sa ma kara rukunkume shi nayi.Aunty Hauwa da sai maida numfashi take hauwaye kam sun cika fuskar share-share. itama kara matse ni tayi kam. Nace "Dan Allah karkaje Habib Fatalwa ce". Tsaki yayi yace "Oya to muje dakin iyayen tsoro ku kama karanta ayatul qursiyyu. Ai tun kafin ya rufe baki Aunty Hauwa kamar an kunnata ta fara karantawa. A haka muka tafi daki kamar yara Ni ina rike da Habib Aunty Hauwa kuwa na rike da ni. Mukaje wajen kwanciya aunty Hauwa ta kwanta a kasa tace Alquran ba mai raba ni da ita. Habib yace to mu kwanta a kan gadon shi zai kwanta a kasa. Ni ma nace wallahi ba zan rabu da kai ba, ni da Aunty Hauwa ai duk jirgi daya ya kwaso mu tunda itama fatalwar ta rainata. Ba yanda baiyi ba a kan shi ba zai kwanta gado daya ba da Aunty Hauwa Amma abu yaci tura domin nima nace bazan rabu da shi ba itama kuma bazata rabu dani ba. ganin muna shirin yin kwanan zaune ga barci a idanunmu sannan ya aminta ya kwanta can gefan ni kuma na rungume shi aunty Hauwa itama ta kankame ni. ya zmana ni ce a tsakiya. Aunty Hauwa a jike take sharaf da fitsari amma tsoro baza zai barta ta canza ko nawa ne bama. rokon Allah kawai take gari ya waye ta bar mana gidan. Cikinta ne yayi kara kulululuuuu "Aunty Hauwa lafiya kuwa". Tace "Wallahi zawo ne kuma bzan iya shiga toilet ba ni kadai wallahi tsoro nake ji. g zawan ya matse ni"..............


ZANCI GABA


https://www.facebook.com/groups/1232550283531628/



↫ NI DA FATALWA! ↬

{gajeran labari}

Part {4}

@KINGBOY ISAH


*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*

(*KUYI HAKURI JIYA KUN JINI SHIRU WAYA TA CE TA SA MAN HAWAN RUWA. HAR YANZU DAI BAI SAUKA BA*)

Nace "Aunty Hauwa ki daure ki matse shi wallahi ni dai in kika fita fatalwa ta kamaki ba ruwana" Karan tusa naji. Aunty Hauwa kaman tayi kuka "Wallahi ya matsen Dan Allah muje ki rakani na rantse in ba haka ba a wando zanyi". Da sauri Habib ya mike zaune yace "Khadija maza tashi ki raka ta". Na tashi zaune nace wallahi ni dai bazan iya zuwa ni kadai ba dole sai dai a tafi da kai domin nima tsoro nake ji". "Khadija kina da hankali bn dakin zan bi ku?. Dallah kinga ki tashi ki rakata muje na jira ku a kofa. Haka muka tashi a tsorace sai waige-waige muke. Aunty Hauwa na tura kofan ban dakin tayo baya da gudu. Habib yace "Miye kuma?" "Faa.... tall... wa". Ta fada cikin in'ina Habib da shima zuwa yanzu ya dan fara tsorata a hankali yaje ya tura ban dakin ya tura kafar haggun gaba ya dan like kamar marar gaskiya, ganin ba komai ya juyo yayi tsaki yace "Kawai tsorata kukayi amma ba

Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3

Please Login or Register in order to submit comment