Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

bakasan halin da yake ciki ba shi ba mutuwa yayi ba balle ka fidda rai. Hamida tana zuwa wani sa'ilin in ta taso daga makaranta don Webe mata kewa Hakan kuwa yana yi mata daWi sosai haka ma mamanta ta zo yi ma Amma jajen Maman Sir Ahmad ma, kowwa dai ma™ota da ake zaman mutunci da su da abokan arzi™i. Allah sarki duniya.


&&& &&& &&&
Farkawa nai da wani irin magagi gashi dai inajin Alamun motsi kuma na tashi amma na kasa buWe idona ga jikina yayi min wani mugun nauyi daidai da Wan yatsana bana iya motsawa ina so na tashi amma kamar an Wora min wani mugun dutse mai nauyi ina ta so na motsa baki na na kira ´an gidan mu amma ba dama sai na ha™ura da yun™urin da nake na zubawa sarautar Allah idanu.
Wata iriyar ™ara na ji mai matu™ar razanarwa kamar harbin bindiga kamar kuma ™arar fashewar wani abu, ashe wai in kaji ™i gudu sa gudu ne be zo ba dan kuwa a firgice na farka ina zare idanu gaban yana tsananta faWuwa (ashe Wazun da na farka uban baccin da nayi ne na kasa tashi Shi ne nayi DANNAU zaka ji Kaman ka mutu baka iya kowani kataSus.
Kallon inda nake na fara yi da tunanin mai ya kawoni ™wa™walwata ta shiga tariyomin tun daga dawowata a makaranta sha™a min abinda akai da sani a wannan motar har zuwa halin da nake ciki a yanzu, Innalillahi wainna ilaihirrajiun na fara ambata inajin wasu zafafan hawaye na tahomin musibar da ta same ni kenan? Allah ka fini sanin halin da nake ciki ubangiji ka bani ikon cinye jarrabawar nan na cigaba da duban Wakin Babbane sosai akwai wardrobe da mudubi sai ™aton gadon da nake kai bayan tiles an malala capet sannan akwai toilet a ciki komai dai na bu™atar rayuwa, ban gama wannan tunanin ba naji ana taSa ™ofa alamun buWewa sannan aka bankota da ™arfi kamar za'a Salla na mi™e a zabure don neman wajen Suya sai akai rashin sa'a babu. wani shirgegen ™atone ya shigo fuskar sa ba ko Wigon rahma a murtike gashi ba™i ga tsayi ™iba Kam nasan se an haWa biyar Wina basu kaishi ba komai dai ya ji jikin wannan bawan Allah ba fasali ba kyan gani.. ™arar rufe ™ofa shi ya dawo da ni hayyacina ashe abinci yazo kawo min har ya fita. kifa Kai na nayi cikin cinyoyina ina ci gaba da kuka yanzu Kuma rayuwar da zanyi kenan? me wa´annan mutanen suka raboni da iyayena su min? ba dai kidnapping Wina sukai ba? to ai kidnapping ma sai ´a´an masu kuWi ake yima, to ni iyayena ina suka ga wannan ma™udan kuWin da ake biya? kai badai kidnapping ba saidai just sun sato ni ne sunada wata manufa a kaina, Allah sarki iyayena nasan suna can hakulansu a tashe barin ma Ammata wasu hawayen masu zafi suka silalomin da naga dai wannan bazata fissheni ba na mi™e da ™yar naja ™afafuna zuwa ban Waki na Wauro alwala na fito na tada kabbara ina tunanin ana bi na salloli da yawa dan ban masan iyakaci ba na tayar na fara. da agogon Wakin na ke laakari lokacin sallar magriba da Isha ya yi nai salla ta,
Har na ™udire a raina bazanci wanan abincin ba na satar mutane to da dare ya raba naga ba sarki sai Allah haka na daure na janyo abincin na cuccusa duk da mai rai da lafiya ne tunda ko a gida bana cin kamarsa amma yakiyimin daWi a bakina kwata kwata, ina gamawa na koma kan gadon na kwanta sannan na fara harba tunanin ta yaya zan fita a wannan gidan? duk da ba abu ne mai yiwuwa ba don daga gani gidan akwai matakan tsaro ba na wasa ba, gashi ko da na shiga ban Wakin banga window ba ba sai wata ´ar mitsitsiya shima a can sama wannan babu ta yanda zaai ma ka ce zaka haura, ga Wakin da nake duhu ne ma ko ina labulaye zagaye saidai in an kawo nefa zaa ga haske amma even haka ko ina duhu ne, to da irin wannan tunane tunen barci Sarawo ya sace ni.
Washe gari haka na tashi cike da damuwa na saba na tashi na ganni a Wakina cikin gidanmu amma sai naga saSanin haka, na mi™e nai sallar asubahi na tsananta kai kukana ga mahaliccina ina nan kan daddumar wani baccin ya kuma kwasheni ban farka ba sai ™arar bugo ™ofa da naji wannan Basamuden najiya ne ya zo kawo min abinci (haka na raWa masa sunan don yai kama da su) yana direwa ya juya tareda rufe ™ofar da kwaWo tamkar a Prison na koma na kwanta da sakin kuka don yanzu shi ne abokina in na gaji na daina in na huta na Wora.
Haka rayuwata ta shigaba da juyawa a wannan gidan me kama da kurkuku a wajena kullum sai an bani abincin safe rana dare in aka kawo sai a tafi da kwanikan, wannan mutum ne dai da yake zuwa kawomin Kuma ba um ba um um haka zai kawo min ya ficewarsa, ba wanda ya taSa zuwa wajena haka ban taSa ganin ™yallin waje ba ban san a ina nake ba sai wannan Waki da nike ciki kullum kuma tunanina yaya zan sami mafita? ta yaya zan fita? ni ba abin in ce zan ro™i wanan mutumin ba ko dayake shi ya sato ni ma fa? ta yaya zan ro™eshi ya fidda ni in banda abuna?.
˜arar buWe ™ofa naji, me kawo abinci ne ya shigo yau ba shi kaWai ba tare da wasu yake suma manyane madaka ™ato su uku, naji an daka min tsawa na mi™e a zabure aka nuna min ™ofa "muje" suka sani agaba muka fita ashe Wakin ma a bene nake akwai wata ´ar rela gaban benen nan naga wasu mutanen zaune ashe ma ba su kaWai ba ne zasukai kusan su goma, haka aka tasa ™eyyata tamkar wadda tai sata zuwa gaban Ogan nasu akasani nai kneeldown a gabansa,
Yana hakimce kan kujera ya kaWa ´an yatsunsa biyu aka mi™o masa sigari ya fara zu™a yana fitar da haya™in ta hancinsa da bakinsa, baya yai da kansa ya jingina shi jikin kujerar da lumshe idunsa da sukai jaa yana cigaba da busa haya™in, ya kai almost 10mint bai cewa kowa komai ba haka suma tunda suka ™ame ™wa™™waran motsi ba mai yi ballantana kuma ni ´ar tahalikar baiwa.
[9/21, 11:46] Safiyya: SA˜AR ZARE

BY
NA'EEMARH SADAU=ØŸÜ kowa

(3E 'DDG 'D1-EF 'D1-JE
FREE BOOK=ØØÜ

ELEGANT ONLINE WRITERs
'þ


Page 7ã __8ã
&&& &&& &&&
komai da zai sa a so mace Baby na dashi ga kyawunta dai-dai gwargwado tana da shi Masha Allah, da wannan tunane-tunanen ya tashi ya Wauro Alwala ya shimfiWa sallaya domin lokacin yin nafilarsa yayi yaita sallolinsa da adduoi har kusan ™arfe 3 kafin yai shirin kwanciya.
amma sai me?? cikinsa yaji ya masa wani mugun karta da ™ullewa ya dur™ushe a wajen yana karanta duk adduan da tazo bakinsa amma ina ba sau™i kaman ™ara masa ciwon ake yi ya zube a wajan Muhd ne ya farka.saboda mutsu²n da yake ya tashe shi yana jijjigashi "Ahmad! Ahmad!" amma Ina ciwon yafi ™arfinsa baya iya amsawa da gudu ya fita Wakin Mama ya kwankwasa suka fito a guje hankalinta a a tashe ta janyo mayafi ta zata fita Muhd ya tareta "ina zakije?" ta ce "Muhd ™yaleni ma™ocin mu zan kira malam shehu ya kaimu Asibiti" ya ce "aa bara naje" ya buWe ™ofan da sauri ya fito. (Malam shehu mutumin arzi™i tun rasuwar babansu Sir ya ke kula dasu dukkan damuwarsu yakan taimaka musu,)ana faWa masa kam bai yi ™asa a gwiwa ba ya fito da adaidaitan suka zo suka kama Sir shi da Muhd suka shigar da shi, dan takai ta kawo baya iya mi™ewa ma. wata ™anwar Babansu ce inna Harira ce ta farka jin hada-hadar da ake ta ce "lpy?" Mama wadda ta fara kuka take faWa mata Ahmad ne ba lpy zasu wuce Asibiti da zata bisu malam shehu ya ce aa dai tambari ta zauna kafin a ga abinda Allah zaiyi ta ce "to Wannan Allah ya baka lpy ya tashi kafaWunka", suka shiga baya Muhd na ri™e da shi Mama na kusa dashi malam ya jasu sai Asibiti.
TASHIN HANKALI WANDA BAA S AMASA RANA!
Sun isa aka wuce da shi emergency lokacin akwai likitoci masu aikin dare nan fa aka karSeshi suka du™ufa wajan duba lpyar tasa. Sun shafe sama da awa biyu Sune har kusan asubah amma abin ya ci tura don gaba Waya ma jikinsa ya ™ame ruwa ma sun saka masa ya™i shiga, Wayan likitan ya fito suna zaune sunyi jugum jugum.. "ina mamansa?" tami™e da sauri duk suka bita suka shiga yana shimfiWe ta ™arasa da gudu tana jijjigashi tana kuka da kiran sunansa "Ahmad! Ahmad! Wina ka tashi kai kaWai ka ragemin banida kowwa a duniyar nan sai kai dan Allah Ahmad!" ya ri™e hannunta tsam da ™yer yake iya buWe bakinsa "mamanah..! ki yafemin mamana zan tafi in barki ba da son raina ba..zan barki ke kaWai mamana.." ya faWa cikin wani yanayi mai wuyar fassaruwa, wani sabon kukane mai tsuma zuciya ya taho mata.. "Ahmad bar faWa bazaka mutuba karka tafi ka barni kaji Wana..." "Mamah... Kicewa Babby..." saikuma tari mai ™arfi ya sar™afeshi yanason magana ba dama malam ya matso kusada shi suka ri™eshi likitoci duk suna tsaye sun rasa ta cewa don sunsan cewa wannan Kam (laa budda) malam ya fara masa kalmar shahada shima ya maimaita Ash'hadu an laa ilaha illallah wa ash haWu anna muhammadan rasulullulah! (SAW).
KULLU NAFSIN ZAA'EQATUL MAUT..!=Ø-Þ. Duk mai rai zai WanWani Wacin mutuwa. Allah ya karSi ran bawansa ba don ya fimu sonshi ba.. malam yai kabbara Allahu Akbar Allah sarkin girma da Waukaka.Ahmad Allah yai maka rahma, halinka ma gari ya bika Mama kam ganin abin da gaskene ansa farin kyalle an rufeshi ta zube a gurin wani irin kuka ya kufcemata... Abin gwanin ban tausayi, Muhd Wanda shima duk jarumtarsa hawayena suka taho masa ya dur™usa "Mama kiyi ha™uri dan Allah Mama.. yama kasa cigaba da bata ha™urin. Malam ne ya ™arasa karSo takardun don sun ce sai sun ™arasa cikewa zaa badashi aka gama komai da komai nurse's aka turoshi a gadon marasa lpy aka sashi a mota sukai gida. Suna zuwa ana fara Sallar Asuba aka shigar dashi gida lokacin duk an tattsahi suka ji wannan mummunan labari malam da Muhd sukai masallaci aka faWawa Liman in an idar a faWi rasuwar. QQ
Ana idar da sallar Asubah aka faWi sanarwar Al'umma kowwa ya razana mutumin da ake shirin Waura aure anjima?? Allah me iko ™aadiran Ala man yasha'u.. nan fa rasuwa kan gari ya waye ta baza gari akai masa wanka akai masa suttura kan da safe aimasa sallah.
A firgice na farka don yau sai takwas na tashi ko sallar Asbah banyi ba..na mitssike idona.... Ina jimamin me ya sameni ko rashin kwanciya da banyi da wuri ba? nai addua a hankali na sauko akan katifar, bakowwa a Wakin duk an fice, na Waura Wankwali na da fitowwa.. mutane nagani anyi tsaye jugum_jugum gabana ya faWi na ce "lpy? ba wanda ya iya min magana illa kallo da aka bini da shi. Wakin Amma nai da gudu na faWa ban ko tsaya sallama ba ita da wata kanwarta sai yayyena Baa ma yana ciki, idonta yai jaa alamun tayi kuka nasha jinin jikina na ™arasa kusa da ita "Amma lpy? Waye ya rasu?" nanma ba wanda ya iya ban amsa na juya na ce "inasu Al'mustapha?" zuciyata tai rauni dan naga an™i min magana sai ido,
Can na tsinkayo muryar Baa "Mamana ki nutsu.. ki sa ha™uri da tawakkali a ranki dan nasan kina da shi to ki daWa akan wanda nasani.." nasiha ya shiga yimin me ratsa jiki da shiga rai.. amma ni ina.. nayi nisa don bana fuskantar me yake cewa na matsu naji me ke faruwa, "Ahmadu ne Allah yayi Masa rasuwa!"
Komina naji ya tsaya cak! kaina..kwakwalwata.. gangar jikina.. tunanina.. bugawar zuciyata.. kai badan bama zan iya cewa harda ruhina ya daina aiki na some seconds kamar ba ni ba na tafi.wata duniyar ta dabam, wadda ba mutane komai yanata juyamin naji hayaniya sama sama ana wai a zubamin ruwa najiyo ihun su yaya Indo shikenan nima na bi Sir.
˜arfe goma daidai, lokacin da akasa za'a Waura masa Aure, yai dai-dai da lokacin da za'a sallaci gawarsa mutane sun halarta sosai fiyeda yanda ake tunani saboda abin ya haWe 2 Waurin auren wasu da zummar hakan sukazo sai Kuma aka riski mutuwa, anan massalacin ™ofar gidansu akai Masa sallah kafin a Wauke shi zuwa gidansa na gaskiya. (Allah ka ji™an iyayenmu da yan uwanmu da duk alummar musulman da suka riga mu gidan gaskiya, in tamu ta zo ya sa mu cika da eemani ameen). haka aka dawo akacigaba da karSar gaisuwa ´an gidanmu da wanda suka zo biki duk an taho gidan makokin, Baa ma dashi aka kaishi.
Suna ta karSar gaisuwa dan ya samu mutane ba kaWan ba kowwa.kuma shaida halinsa yake ba a taSa kamashi da wani hali Mara kyau ba ga HA˜URI kawaici kowwa nasa ne, Walibansa na safe da yamma.duk sunzo hakama malaman abokan aikinsa mutanen gari kowwa dai Masha Allah, Haka aka shafe kwana3 ana zaman makoki kafin a fara tafiya sai WaiWaiku Wanda zasu kai bakwai.
&&& &&& &&&

A hankali na ke iya buWe idadanuna saboda nauyin da sukai min tun Ina gani dishi² har na soma gani tarwai gaba Waya,farin Waki ne sosai ko Ina haske Kuma shuru alamaun ba kowwa sai ni na Waya juya Waya Sangaren saboda jin hannuna a Waure amma ina... na ji bazan iya ba saboda nauyin da naji kaina yayi min har bazan iya sarrafashi ba haka ma jikina.
Na lumshe idanuna ahankali na mayar da su na rufe ™wa™walwata ta fara tunani me ya kawoni nan, na fara tunani tiryan tiryan, (tun tashi na daga bacci zuwa fitowata ganin mutane jugum-jugum shigata Wakin Amma da ganinsu duk a tsaye sannan na tuna anyi mutuwa Sir..!) kaina na shiga ™o™arin dafewa sakamakon sarawa danaji yana ™o™arin yi, Hasbunallahu wa niimal wakeel! Innalillahi wainna ilaihirraji'un! Haka na dinga maimaitawa azuciyata domin bakina yayimin nauyi bana iya buWe shi magana naji sama² a kaina ashe har nurse's sun shigo ban sani, suka ™araso kusa da ni damin sannu najiyo ma muryan su yaya indo harda Amma, na sake buWe idon a hankali Waya nurse in ta ce "maza ta kira Doctor," ta fita da hanzari sai sukai kiciSis ma da shi a bakin ™ofa a kai saa shi ma zai shigo lokacin "Doctor ta farka",,, ta ke faWa masa.. ya ™arasa shigowwa da sauri ya iso bakin gadon, hannuna da Nurse ta ke ri™e da shi nake ™o™arin zame wa saboda ji na duk a WaWWaure, ya ™araso da mata magana akan ta sakeni nai ko™arin yun™urawa na tashi ya dubeni da kulawa ya na tambayata ya jikin nawa..kai na iya gyaWa masa alamun sau™i don banajin zan iya buWe buWe baki na.
Magana yayi musu suka Wagani da jingina ni jikin fillow yayi min gwaje² da aunawa ya tabbatar ba wata matsala sannan ya ce za a iya bani shayi na sha kafin a ba ni wani abincin saboda hanjina ya warware, haka ko akayi dama akwai a flask Yaya fatima ta tsiyayomin ta haWaminshi akai min brush sannan nasha shayin shi ma ba don raina yana so ba ina gamawa na koma na kishingiWa.
Har yanzu ban iya cewa kowa komai ba duk suka fice don banaso hayaniya Doctor ya ce anaso a Wan barni na huta, jin shurun da nai yasa na daWa faWawa cikin kogin tunani, Allah sarki malamina bazan sake ganin kyakyawar fuskarsa ba murmushinka komai ma mutuwa tayimin yankan ™aunah! ta rabani da masoyina farin cikina mutum ne ha™uri me kawaici ban taSa ganin mutum kalan Sir Ahmad ba.. wani kuka naji ya taho min tun daga ™ar™ashin zuciyata na ko fasa shi don banajin zan iya ri™eshi na Wau tsayin lokaci ina kuka ba me rarrrashi na, ko dayake koma an rarrasheni bana iya jin zanyi shuru saboda bana bu™atar hakan haka ko nayishi ma'ishi har naji ba daWi don gaba Waya kaina yamin nauyi jikina kaman zazzaSi ke son rufe ni.
Sallamar Amma na ji da wata innarmu ™anwar Amman sun shigo Wakin suka ™araso da zama bakin gadon "Ummina kukan ne? shi fa kukannan da kike babu inda zai kaiki face ma ya daWa miki cuta, shi fa wanda kike kuka a kansa ana sa masa rai da rahmar ubangiji addu'a zakiyi masa ita ce manufa kidaina kukan man dan Allah kinji?,"
Bansan sanda na faWa jikinta da sakin wani kukan ba "Amma shikenan bazan sake ganin Sir ba ya tafi ya barni da tabo a zuciyata ba?.
[10/13, 06:43] E*O*W: SA˜AR ZARE

BY
NA'EEMARH SADAU=ØŸÜ

(3E 'DDG 'D1-EF 'D1-JE
FREE BOOK=ØØÜ

ELEGANT ONLINE WRITERS
'þ

Page 13ã __14ã

Sai da ya gama Sata lokacinsa sannan ya samu damar Wagowa yana bina da wani shegen kallo da idanunsa da sukai uban jaa tamakar wanda ya zuba gauta sai da ya gama ™aremin kallon tsaf! from head to toe sannan ya samu daman yimin magana "ke!.." gabana naji ya wani irin faWuwa saboda jin muryasa mara daWin Amo ga tsoratarwa ga mai saurarenta na Wago idona da kallonsa, banyi na biyu nai maza na sadda kaina ™asa saboda bazan iya juran kallon wannan mummunan mugun mutumin ba, karo na biyo ya sake kirana "ke!.. kinsan dalilin kawo ki nan?.. duk da nasan baki sani ba but I should ask uh..", kin sani ko baki sani ba..!? Ya dakamin tsawa jikina na Sari na girgiza kaina a hankali alamun ban sani ba "alright yanzu zaki sani, na kawo ki nan ne domin samu da aka anbamu kwangilar mu kasheki!! Amma inaso kafin nan sai nayi amfani dake na mayar dake Karuwata!
Jikina ya hau kyarma saboda jin kalamansa da ya ke zazzagamin ji nai kamar ya watsamin garwashin wuta, ni za'a satoni daga gaban iyayena don a kashe? Kan wane dalili? Wayasasu wannan aikin? Sannan zaiyi wannan fasadin dani? a dinga tafka Sarnar da fasadi a ban ™asa da ni? Abinda ubangiji ya hana?laifi mai matu™ar girma? ZINA!? Bansan lokacin da na mi™e ina ina girgiza kaina ba wani kuka yana tahomin "ina... ba dani ba bazan taSayin wannan abin da kuke so ba bazan taSa baku haWin Kai kuyi wannan abin da ni ba wallahi! Saida ka kasheni ko da hakan zai zama sanadin Waukan raina bazan taSa yi ba" maganganun bansan kalan wanda na dinga saki ba saboda raina a tunzure yake na manta ma a gaban wa nake, wasu jajayen taurari naga suna giftani kafin ganina ya soma dishi-dishi naji fuskata tamkar ta bar jikina saboda saukar wani zazzafan mari da naji yayimin dirar mikiya saboda bansan ta inda ya fito ba sannan na sake jin wani a cikin su ya daka min tsawa! yai arresting Wina da Gun,
"ke! Bastard! Stupid girl! Kinsan a gaban wa kike? fitsari naji yana ™o™arin ziraromin na Kuma zubewa a wajen wani kukan ya kuma ™wacemin.
Cikin isa da gadara ya mi™e tsaye ya janyo P-cap inshi gaba "Gaza ™yaleta.. any way yanzu kinsan abinda ya kawo ki nan don haka da amincewarki da ™in amincewarki duk ba matsala ba ne a wajena zan baki 3dys kije kiyi tunani.. sai kuma ya Waga kafaWunshi alamun I don't care.. ya fara sauka step Win a gaggauce suka rufa masa baya ni kuma Basamuden ya tisa ™eyana zuwa Wakin yasa kwaWo ya gar™ame da bin bayansu da gudu.
Gadon na faWa ina sakin wani marayan kukan, ba na komai ba ne illa na tausayin kaina da nake ganin irin rayuwar da nike ™o™orin faWawa dukda na ma kaina alwashin bazan taSa yi ba, amma wa'innan mutanen sunfi ™arfina nesa ba kusa ba ni nasan da wanan, amma ai Allah fi ™arfinsu yana tare dani.
I know that kukan nan bazai taSa fissheni ba dan haka bansan sanda na mi™e ba naje na Wouro alwala na shimfiWa
sallaya na fara jero nafifili da adduoi don samun kuSuta daga hannunsa wa'innan azzaluman,bansan iya tsayin lokacin da na Wauka a zaune ina addu'a ba,
&&& &&& &&&
Gidanmu kam tashin hankalin da aka shiga bazai misaltu ba saboda yanzu zancen da ake an shafe tsawon sati 2 kenan ba ni ba labarina duk inda aka san za'a sameni gidajen ´an uwa, abokan arzi™i, ™awaye (dukda ba su ne da ni ba) anje amma ba a sameni ba, ´an sanda sunzo don yin binciken mutuminnan amma ba'a sameshi ba duk inda aka san zaa ganshi anje babu shi babu alamarsa, to haka abin ya zama sai addu'a aka cigaba da yi da kuma ro™on Allah akan Allah ya bayyana ni.
Da safe hayaniyar su ce ta tashe ni na mitsike idona ina tashi da ™yar don idona haba Waya ya kumbura ga shatin en yatsu WoWar a kunci na da mamaki nake daWa kasa kunena duk da na saba da jin hayaniyarsu wani lokaci insunyi operation sun dawo, amma na yi mamaki don ban taSa jin haka ba abin yayi yawa, tsoro ya fara shigata jin abin nasu ma kamar faWa, anata zage zage da Waga murya abinka da maza tamkar ana ya™i, ban ankara ba naji an banko ™ofata da ™arfi uwa za'a Sallata na mi™e da hanzari me kawo min abincine, ya daka min wata uwar tsawa "ke fito!!
ai be ™arasa faWa na dirgo a gadon Allah ya so ni da hijab a jikina wanda nai sallar Asbah, ya tisa keyata da fita dani.
sun kusa su talatin a falon wasu a zaune wasu tsaye wasunsu sanye da mask a fuskokinsu kowane ri™e da ™atuwar bindiga, shi ma uban gayyar tasu yana tsaye ya Wora ™afansa a kan table, dakin yai tsit! tamkar basu suka gama ihu yanzu ba,
Ana shigowa da ni ya tsaya daidai kan ™afafunsa, ya fara Magana cikin kausasa murya da matu™ar Fushi a kan fuskarsa ya ke musu magana "kai Rabe da Bagudu asase ku tafi da ita, oska! team Winku maza ku je please bana son ™ara buWe idona naganku oya," kafin ya rufe baki kusan su ashirin suka mi™e radadada suka fara sauka a benen da gudunsu ya rage sauran mu sha Waya su bakwai za su fita da shi su huWun da ya ware duk da ni ya juyo kanmu asase! Kar kumin hauka wlh ka sake kuka samu wani saSani by mistake ko ka bari mutanen nan
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5

Please Login or Register in order to submit comment