Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

lafiya Hauwa'u? Mike faruwa ne?”.
    Tamkar jira take ya tambayeta sai ga hawaye sharrr. Zumbur ya miƙe daga ɗan zaman da yay a hannun kujera yace, “Subahanallahi, wai mike faruwa ne? Ko wani abun ya faru acan inda kukaje dubiyan?”.
      Hawayen ta share, tace, “Lallai Alhaji akwai matsala wlhy, dan ALLAH inason na sake komawa asibitin nan yanzun”.
      “Ki koma asibiti kuma? Akan wane dalili to?. Kimin bayanin dazan gane mana”.
      Wasu hawayen ta sake sharewa. Muryarta na rawar tahowar sabon kuka tace, “Alhaji yarinyarnan da mukaje dubawa wadda Nazirun ya kaɗe wlhy kamar Zinneerah, kai inamji a jikina itace duk da kuwa rabon dana ganta tun tana ƙarama”.
        Shima kansa da mamaki yace, “Zinneerah dai tamu dake a Danya?”.
      Cike da ɗanjin nauyinsa ta gyaɗa kanta, dan shi mutumne mai kara, duk da ɗan uwantane dama can, auren zumincine akai musu bayan aurenta ya mutu, ya sota tun tana budurwa ALLAH baiyi zata zama matarsaba a lokacin sai da ta fito yace shifa yana sota har yanzun. Da farko taso ta tirje dangi sukai mata caa akan rashin dacewar hakan. Dan kowa yasan irin son da ya nuna mata. Haka dole ta haƙura akayi aka kawota nan Kano gidansa dan dama can anan yake zaune shi shekara da shekaru, to gashi yanzun har ALLAH ya azurtasu da ƴaƴa uku duk maza. Tana kuma samun kulawa da soyayyar mijinta mai tsafta da saka kwanciyar hankali, ga Uwargidanta mutuniyar kirki, Saude ce dai sai a hankali, dan dama tun farko fitinar Sauden tasata son zamewa daga auren nasa.....
       “Wai tunanin mi kuma kika tafi haka ne?”.
      Kallonsa tai da sauri tana sauke ajiyar zuciya. Ya ɗan girgiza kansa kawai yana miƙewa. “Kinga ki kwantar da hankalinki tunda dai tana asibitin babu inda zataje, bara na kira Nazirun anjima yazo sai mu koma insha ALLAH dan wannan ba al'amarin da za'ai wasa bane”.
     Cikin jin daɗi tace, “To Yaya ALLAH ya saka da alkairi”.
       “Saboda ƴarki ce ke kaɗai kikemin godiya kenan?”.
       Ƙasa tai da kanta tana murmushi. “A'a kayi haƙuri bankai canba”.
        Fita yay yana murmushin shima. Saude dake laɓe a jikin Window ɗinta tana irga mintunan shigarsa ɗakin taja tsaki ganin ya fito yana murmushi. Afili tace, “Shegiya munafika, zanyi maganinki a gidannan wlhy. Oho ita dai maman sadiq bama tasan tanaiba, dan bayar fitar maigidan fitowatai ta ƙara gawayi a wuta ta ɗora ruwan abinci, dan dama tunkan su fita tayi miya shiyyasa bata damu da tsegumin Sauden ba ashe.

★★★★

          A asibiti kam shiru-shiru Khalipha bai dawoba har lokacin yin barcin ranar Zinneerah yayi tasha magani ta kwanta. Bata tashiq farkawaba sai bayan sallar la'asar. Ganin lokaci yaja ya sata miƙewa aɗan harzance ta shiga toilet ɗin dake a ɗakin. Alwala tayo ta fito, bayan idar da sallar ne Salima ta shigo dan bata abinci kamar yanda Khalipha ya rataya mata alhakin yin hakan ga Zinneerah. Itako bala'in son da takema Khalipha yasa bata iya ƙetare buƙatarsa a rayuwarta, shiyyasa take bama Zinneerah kulawa sosai dan duk zatonta yanada alaƙa da zinneerah ɗinne musamman dataga an kawo zinneerah ɗin ɗaki na musamman ita kaɗai an ajiye.
        Zinneerah na tsaka dacin abincinne Salima na mata hira tana ɗan murmushi sukaji sallamar Khalipha bayan yayi ɗan knocking. Saurin jan hijjab Zinneerah tai ta saka, Salima ma ta gyara zamanta dana ƙaramin hijjab ɗinta tana amsawa.
       Shine ya fara shigowa ɗakin tamkar ɗazun, sai Naziru biye da shi, wani da suke tsananin kama da Nazirun na bayansu, sai dai a kallo ɗaya zaka fahimci ya girmi Nasiru ɗin dan ba yaro bane.
       Sai matan ɗazun biye da su a baya, amma banda matar Naziru. Matar ɗazun da taji suna kira da Maman Sadiq ta ƙaraso gaban gadon sosai batare da tama saniba. Hannu takai bisa kumatun Zinneerah jikinta na wata irin tsuma da karkarwa. Ko shekara dubu tai bataga wannan halittarba tayi imani da ALLAH randa suka haɗu saita gane abarta. Tunda tabar ƙauyen Danya cikin gushewar hankali dana tunani har zuwa yau ɗinnan bata daina kwana da mafarkintaba da tashi da tunaninta kuma. Ta kai ƙasa durƙushe hawaye na silalo mata a kumatu. Tabar ƴarta da ƙarancin shekaru hannun kishiya mai ƙarancin imani dana tausayi badan ranta yasoba, sai dan anfi ƙarfinta kawai. Yau kuma sai gata a inda bata taɓa zatoba ko tsammani a shekarun girma....
       “Zinneerah!”.
Ta ambata da wani irin rawar murya dana harshe.
     Ganin Zinneerah ta kasa magana sai kallonta kawai da takeyine kamar ɗazun ya saka Naziru faɗin, “Maman Sadiq ki kwantar da hankalinki, insha ALLAHU itace ma”.
         Idanunta da hawaye ke kwarara ta ɗago ta kallesa, taɗan saki murmushin ƙafin hali tana miƙewa tsaye sosai. “Nasiru indai har yanzu ba ƙwaƙwalwata ce bata gama dai-daitaba to wannan kam Zinneerah ce, dan naji hakan a jikina duk da kuwa bata amsa sunan dana kirata da shi ba”.
        Maman Halima da sukazo tare yanzunma ta matso gaban gadon itama ta zauna kusa da Zinneerah da alamu suka nuna tamkar bata a cikin hayyacinta. Sai da ta riƙe mata hannune tai firgigit alamun ta dawo cikin hayyacinta. Ƙasa tai da kanta saboda wani irin bugu da ƙirjinta ke mata ainun, Maman Halima ta katse shirun ɗakin da faɗin, “Ƴammata minene sunanki?”.
     Babu wanda yay tsammanin zata amsa. Sai ji sukai a bazata tace, “Zinneerah”.
      Wata irin nannauyar ajiyar zuciya maman Sadiq ta sauke, yayinda ɗunbin mamaki ya kashe Khalipha da  Naziru, musamman da suka tuna randa sukaita ƙwaƙwar jin sunan nata amma tai musu shiru..
     “Masha ALLAH Zinneerah daga ina kike? Ina nufin a wane anguwa iyayenki suke?”.
     Shiru kamar bazata amsa ba yanzu. Sai kuma zuwa can tace, “Ba'anan nake ba”.
        Cike da zumuɗi maman Sadiq tace, “Daga wane gari kike?”.
      Ɗagowa tai tana kallonta na tsawon kusan mintuna biyu, sai kuma ta maida kanta ƙasa tana sauke ajiyar zuciya. Cikin suɓutar bakin da bata shiryaba tace, “Danya”.
      Gani kawai sukai maman sadiq ta zube kan kujerar roban dake a gaban gadon ta fashe da kuka tana faɗin, “Wlhy itace, Zinneerah tace”.
     A yanda tai maganarne ya sakasu jin wani irin tausayinta ya ɗarsu a rayukansu, cike da son jin ƙarin bayani Naziru yace, “Zinneerah kekam miya kawoki hanyar jigawa keda ke a jihar katsina?”.
       Hawayen dake sakko mata ta share tana girgiza kanta. “Nima ban saniba, na samu kaina ne kawai a haka”.
         Sai yanzu ne Alhaji yay magana. “Lallai da alama kamar bata cikin hayyacintane ta baro gida fa kenan”.
      “Tabbas hakane Alhaji, kenan har yanzu Asabe bata canjaba ko kuma Zinneerah ma tayi gamo da abokiyar zama irin Asabe a gidan aure.” Maman Halima ta faɗa saboda ganin ciki a jikin Zinneerah duk da kuwa ta saka hijjab.
      A karon farko shima Khalipha da tun ɗazun baice komaiba sai kallonsu ya sauke numfashi. Gyara tsaiwarsa yayi a jikin bangon daya jingina yana kallon Zinneerah da keta satar kallon maman Sadiq da suke tsananin kamanni. janye idanunsa yay ya maida ga Naziru yana faɗin, “Inaga tunda har an fahimci bakin zaren ayi haƙuri haka har zuwa lokacin da za'a sallameta daga nan ɗin insha ALLAH. Sai dai ya kamata ku sanar mata wacece ita a gareta dan na kula ba fahimtarku takeba kamar”.
     Sosai duk suka gamsu da bayaninsa, suka zazzauna aka shiga gaisuwa da tambayar jikin Zinneerah ɗin, wanda Khalipha ya ƙara musu bayani game da matsalar dake tare da ita akan buƙatar hutu bisa ga lalurar cikin jikinta. Sun shiga mata addu'ar fatan sauka lafiya.
      Maman Halima dai ce da har yanzu ke zaune a kusa da ita tana riƙe da hannunta ta nuna mata wadda aka kira maman Sadiq. “Zinneerah wannan ɗin mahaifiyarki ce, duk da nasan baki santaba kamanin dake a tsakaninku da duk bayan da mukeyi a wajennan zai tabbatar miki hakan, kai namasan zakiji a jikinki koda ba'a faɗaba dan mahaifiya tafi gaban wasa ai.”
         Kafeta da kallo kawai Zinneerah tayi tamkar wadda ta suma a zaune. Sai da Maman Halima ɗin taɗan taɓatane ta kawo numfashi, sai kuma ga hawaye sharr. Batare datace komaiba tai ƙasa da kanta, daga haka bata sake ɗagowa ta kalli kowa a cikinsuba.
     Sosai hakan da Zinneerah tayi ya taba zuciyar Maman Sadiq. Dan ta fahimci kamar Zinneerah ɗin fushi take da itane kokuma kalar nata murnar kenan oho. Kowa ma dake wajen da irin fahimtar da yayma shirun na Zinneerah. Murmushi Alhaji yayi, cike da sanin yakamata da hangen nesa irin na manya yace, “Kubata lokaci kamar yanda likitan nata ya faɗa ko”. Sai kuma ya juya ga Khalipha batare da ya jira amsarsuba. “Likita yaushene zaku sallameta?”.
       Murmushi Khalipha yayi yanaɗan sosa gefen goshinsa. “Alhaji banine likitanba dai, amma insha ALLAH zuwa nan da kwana biyar haka akoda yaushe za'a iya bata sallama tunda jikin nata yana ƙyau, dama matsalar kamar daga cikin jikintane yasa aka riƙeta”.
      “To masha ALLAH, ALLAH ya kaimu, ya kuma bata lafiya”.
    A tare suka amsa da amin. Daga haka sukai musu sallama domin tafiya badan Maman Sadiq tasoba. Sai dai taji daɗin abinda Maman Halima ta faɗa akan cewar itace zata dawo ta cigaba da jinyar Zinneerah ɗin har a sallameta. Kowama yaji daɗin hakan har Khalipha.     
        

★★★

       Tun daga wannan ranar jiyyar Zinneerah ya dawo hannun Maman Halima, Khalipha ma bai janye daga mata hidimaba, hakama Naziru, ga Alhaji ma ya ƙaru. Sai ga Zinneerah ta sake zama ƴar gata, sai dai abinda kebama kowa mamaki har yanzu taƙi barin damar da zasu fahimceta game da komanta. Hatta haɗuwarta da mahaifiyarta sun kasa gane mike a ranta. Dan taƙi cewa komai, ta kumaƙi nuna murnarta a fili ko damuwarta. A duk yanda Maman Halima ke janta a jiki dan son jin wani abu gameda rayuwarta da Inna taƙi sakin jiki da ita, duk da kuwa ta fahimci babu wata mummunar manufa ga Maman Halima ɗin. Sanin yakamatane kawai irin na matar.
      Tun daga ranar Maman Sadiq bata sake zuwa asibitinba, sai dai ranta fal yake da damuwar yanayin Zinneerah a kanta. Tadai danne ne kamar yanda mijin nasu ya bata shawara akan ai haƙuri da komai har Zinneerah ɗin ta dawo gida.

        Itakam Zinneerah bawai farin cikine batai da ganin Mahaifiyartaba. Har ranta ita kaɗai tasan daɗi da take a ciki, sai dai wani ɓangare na zuciyarta ya sakata jin ciwo da zargin mahaifiyar tata ta watsar da itane akan sani kenan. Dan duk wanda zai kalli Maman Sadiq ɗin yasan tana a cikin kwanciyar hankali a gidan aurenta na yanzu.
       A ganinta idan ba tana saneba yaya za'ai ta watsar da ita tsahon shekaru batare data taɓa waiwayar inda take ba, hakama danginta. Wannan dalilinne ya saka yin kamar batai farin cikiba. Sai dai a randa abin ya faru tasha kuka a ɓoye, still rashin ganin kuma Maman Sadiq bata sake zuwa asibitinba ma ya ƙara taɓa mata zuciya.

       Ana gobe za'a sallamesu Khalipha yazo mata da zancen da yasata tasha kuka sosai, dan har saida ta kaita da zazzaɓi mai zafin gaske. Ba komai yaja hakanba sai jin Khalipha ɗin zaiyi tafiya. Ashe dama yana karatune a wata ƙasa can daban, hutu yazoyi gida shine yake ɗan zuwa nan asibitin yana rage zaman banza saboda asibitin nada alaƙa da shi. Yanzu kuma hutunsa ya ƙare, yaso ace sai an sallami Zinneerah yaji cikakken labarinta sannan. Amma sai Yayansu yaƙi saurarensa da ɗaga masa ƙafar ƙarin kwana ukun daya buƙata. Ya tabbatar masa da dole-dole saiya koma makaranta gobe idan ALLAH ya kaimu. Shiko a duniya baya taɓa iya ƙetare maganar Yayan nasu saboda ƙauna da girmamansan da sukeyi akaf gidansu koma yace family ɗinsu.
      Kuɗaɗe masu yawa da sayayya yayma Zinneerah ya kawo mata cike da damuwa. Bayan ya mata nasiha akan yanda zata kula da kanta yace ta bashi lambar mijinta koda ya tafine zai nemsa suyi magana ta waya. Shiru Zinneerah bata iya cemasa komaiba akan wannan magana. Ya sake mainaita mata, nanma shiru tai sai hawaye dake gudu a kumatunta.
         Ƙyaleta Khalipha yayi, dan a tashi fahimtar kawai ta bashi cewar Zinneerah kodai rabuwa tai da mijin nata kokuma bata buƙatar ana alaƙantata da shi bisa wani dalili na ɓacin rai. Dan haka ya ƙyaleta kawai saboda ya amsa lambar Naziru. koma miye zai dinga ji daga garesa kawai.
      Haka dai Khalipha yay mata sallama ya wuce ya batta da kukan zuci. Dan hatta Maman Halima da bata daɗe da saninsaba yaron da halayensa sun sakashi shiga ranta sosai.
      Dalilin tafiyar Khalipha gaba ɗaya yinin ranar a rashin daɗin rai Zinneerah tayisa a asibitin, harma tanaji ta ƙagara a sallamesu gobe idan ALLAH ya kaimun, gara taje gidan maman tata taji nata dalilin itama na guje mata datai ta barta cikin wahalar rayuwa..
         Haka dai a daddafe suka kai washe gari, inda ALLAH ya taimakesu aka basu sallama tunda safe. Dan haka Nasiru yazo ya kwashesu dan yakai gidan yayan nasa inda mahaifiyar Zinneerah ke rayuwa a yanzu matsayin gidan aurenta..............✍

    
   
*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*

Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.

*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_

*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_

*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_

*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_

*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_

Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.

Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

*_08085405215_*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  0903 234 5899

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_TYPING📲_*


*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*


*_Page 10_*
________________________

*_Hummmmm!!. Wai wai wai, wani aiki sai: GIDAN ƘAMSHI💃🏻💃🏻💃🏻🥺_*

*_INA MATA ƳAN ƘWALISA MA'ABOTA SON ƘAMSHIN GIDA DANA JIKI?_*

*_INA MATAN DAKAN SO DUK INDA SUKA DOSA KO SUKA BARI SAI SUN BAR MUSU TARIHIN ƘAMSHINSU_*


*_TO MATAN ƘWARAI KUZO GA WANI SIRRI DAZAN BAKU DAGA FITACCEN GIDAN ƘAMSHIN NAN DA BAIDA NA BIYU A KANON DABO😁_*

_Ina magana ne akan GIDAN ƘAMSHI da ke a Jihar KANON DABO MAIDUGURI ROAD MARIRI_.

*MUNA SIYAR DA TURARURRUKAN WUTA SET NA AMARE, MUNA KUMA BADA SARI.*

*AKWAI KUMA SABULUN GYARAN JIKI MAIDA TSOHUWA YARINYA, BUDURWA TAURARUWA, MATAN ƘWARAI ANNURIN HASKAKA GIDA. SHIMA DAI AKAN SARI, DOZIN KO KATON*

*AKWAI KUMA ZUMAR ƘARA ƘIBA GA MATAN DA KESON SU GANSU DUMURMUR SUNA JUYAMA OGA KAYAN...😉🙈💃🏻 kundai gane*.

*_Mata ku garzaya GIDAN ƘAMSHI domin ƙamsasa kanku kuma kar aci kasuwar sama babu ku😁_*

*ZAKU IYA SAMUN MU TA WANNAN LAMBAR WAYAR: 07033778564 DOMIN JIN ƘARIN BAYANI*.

*KO A KANO MAIDUGIRI ROAD MARIRI*.💃🏻💃🏻👍🏻


______________________

*Page 10*

............Tunda suka iso gidan Zinneerah keta kalle-kalle. Basai an faɗaba a ganin gidanma kasan mahaifiyar tata yanzu kam tai gaba, kuma tana cikin jin daɗi da kwanciyar hankali. Bawai ƙaton gida baneba irin na masu kuɗi, babbane dai kam amma gini irin na mai rufin asirin ALLAH. Dan da Alhaji Bashir Ɗanmusa kam yayi kuɗi sosai, sai dai daga baya ya fuskanci ƙalubalen karayar arziƙi, tun daga nan ne dai har yanzu bai koma yanda yake daba, amma ko a hakan Alhmdllh dan yana iya ɗaukar nauyin komai na gidansa harma ya taimakawa ƴan uwa da maƙwafta. Hatta da motar da Nasiru keja a yanzu haka shine ya siya masa ita. Sannan duka ƴaƴansa suna karatu gwargwadon ƙarfinsa danshi mutumne maison ganin zuri'arsa ta samu ilimin addini dana zamani.
        Zinneerah ta samu tarba maiba mamaki a gidan na kawunta, kuma mijin mamanta. Hakama yaran gidan duk da ba saninsu tayiba suma basu santaba sunzo sun zagayeta sunata kallo. Bata wani sake da kowa ba dan har yanzun damuwar tafiyar Khalipha bata saketa ba. Tanajin raɗaɗi da zafi a ranta wanda ita kanta batasan dalili ba.
      Duk da a yanayin da take na rashin sakin jiki hakan bai hana Mama Sadiq nuna zumuɗin ganintaba, danma tana ɗan kawaicine wa Maman Halima kasancewar Zinneerah ƴar fari ce, sannan kuma yanda Maman Haliman ke nuna kara ma ta cancanci a ɗaga mata ƙafa ai. A yanzu hakama duk da tare suka dawo a ɗakinta ta sauketa. Sai dai an kawo kayan Zinneerah ɗakin Maman Sadiq ɗin alamar anan zata zauna.
       Da ƙyar Maman Halima ta lallaɓa Zinneerah taci abincin da Maman Sadiq ɗin ta tarbesu da shi, bayan ta ɗan tsatstsakura aka kaita tai wanka, tare da bata kaya sabbi fil da Maman Sadiq ɗin ta ɗiɗɗinka mata a ƴan kwanakin nan gudun kar'a sallamosu tazo babu sitirar da zata saka, dan a yanzu haka gidan nasu ƴammatan dake sa'annin Zinneerah duk ƴaƴan Saude ne, Saude kam ba bari zatai su bama Zinneerah kayaba, ballema yaran suma sun rigada sun haddace karatun uwarsu suma kishi suke da su, danma sunajin tsoron ubanne, suma kansu su Maman Sadiq ɗin kuma basu basu fuskar rainiba suna ɗan shakkarsu.
         A zahiri Maman Sadiq cike take da murnar kusantowar ɗiyar tata kusa da ita duk da batasan dalilin barowarta gidaba har yanzun. sai dai ƙasan ranta cike yake da fargabar yanda Zinneerah taƙi sakin jikinta ita. Haka dai ta daure ta danne damuwarta a ƙasan zuciyarta bayan sallar isha'i da Zinneerah ta dawo ɗakin nata bisa rakkiyar Maman Halima. Alhaji yayi tafiya, hakama Saude bata gidan, tana can gidansu bikin ƙanwarta akeyi, yaran natama suna dawowa Islamiyya da yamma yau suka bita can. Dan haka gidan ya kasance daga ita Maman Sadiq sai Maman Halima. Sai yaran Maman Sadiq uku duk maza ƙannen Zinneerah data haifa anan. Abubakar Sadiq, Abdul-Salam, sai Aliyu auta. Itako Maman Halima yaranta duk matane, huɗu sunyi aure ma, sai biyu yanzu a gabanta ƴan biyune sa'annin Sadiq. Sai itama Saude nada biyar, yanzu haka akwai ƴammata biyu da suka isa aure, sai ɗaya zasuyi kusan sa'a da Zinneerah, da ƙannensu biyu ƙanana suma kusan sa'annin su Sadiq ɗin dai.
      Sosai Saude take kishi da Maman Sadiq saboda tazo gidan ta haifi ƴaƴa maza su basu haifaba, taso su haɗe kai da Uwargidan da suke kira maman Halima amma taƙi, dan dama itama ɗin can ba zaman lafiyarne a tsakaninsuba, to mizaisa ta yarda su haɗe su cuci wani bayan ALLAH shine mai badawa. Kuma koda Maman Sadiq tazo gidan batazo musu da raini ba, su duka girmamasu takeyi dan mace ce mai sanyin hali, sai dai idan ka ƙureta kam zaku kwasa da ita. Shiyyasa duk haukan da Saude zatai a gidan ko kallonta batayi, sai idan ta kaita maƙurane ta yaɓa mata maganar da zatai kwana da kwanaki tana damunta a rai.....
         Numfashi Maman Sadiq taɗan sauke da duban Zinneerah dake a takure gefe tana magana dasu Sadiq  dake zagaye da ita a hankali. Tanajin misu Sadiq ɗin ke faɗa, amma batajin na ita Zinneerah ɗin. Gashi kuma ta duƙar da kai bata ko kallon sashen da take.
      “Abdul!”. Ta kira sunan yaron nata na tsakkiya da yafi kowa ƙiriniya a yaran, dan a yanzu haka kusan rabin jikinsa na manne da na Zinneerah ne, gashi dama suna kamanni sosai da ita.
     Kansa ya ɗago ya dubeta, “Na'am Mama”.
      “Ku tashi aje ai shirin barci hakanan, duk kabi ka katantaneta bakaga halin da take ciki bane”.
    Baki yaron yaɗan tura gaba da faɗin, “Ayya mama ki barmu muyi barci tare da ita, muna sonta sosai”.
      A karon farko Maman Sadiq taga Zinneerah ta saki murmushi tana shafa kan yaron, sai dai bataji mita faɗaba sai da yaran suka haɗa baki wajen cewa, “Muma ai muna sonki sosai” ne ta gane cewa tai tana sonsu itama.
      Murmushi tayi tana maijin daɗi da farin ciki a ranta, ta sake faɗin, “Karku damu ai tana nan tare da ku babu inda zata, kuje ku kwanta akwai islamiyya gobe idan ALLAH ya kaimu”.
     Badan sunso ba sukaima Zinneerah sallama suka nufi ɗakin barcinsu. Shiru falon yayi na tsahon mintuna. Ita dai Maman Sadiq kallon Zinneerah ɗin takeyi cike da nazari, itako kanta a ƙasa tana wasa da zanen carpet ɗin dake shimfiɗe a falon.
      “Zinneerah.”
Ta kira sunanta cike da rauni.
     Karon farko Zinneerah ta ɗago ta dubeta, sai kuma taɗan risinar da idonta. Murmushi mai ciwo Mama tayi, ta sake faɗin, “Taso ki dawo nan”.
    Babu Musu Zinneerah ta miƙe zuwa gareta. Sai dai kamar bazata zauna inda ta nuna mata ɗinba, sai kuma mita tuna oho ta zauna a hankali gab da Maman nata. Mama dake cigaba da kallonta ta riƙo hannunta cikin nata tana gyara zama da fuskantarta sosai. Hakanne ya saka Zinneerah maida kanta ƙasa idanunta na cika da ƙwalla.
      Itama Mama idanun nata cike suke da ƙwallan, cikin rawar murya tace, “Kiyi haƙuri Zinneerah, kiyi haƙuri kiyi haƙuri. Na fara da baki haƙuri ne saboda dalilai masu yawa. Nasan har ranki kina kallona ne matsayin uwa gareki mara adalci. wadda ta wofantar da ke ta manta da rayuwarki. Wlhy Zinneerah ba hakan baneba. Ni mahaifiyarki ban taɓa mantawa dakeba koda na daƙiƙa guda. A kowane sakanni kina maƙale a raina da zuciyata. Hawayena basu taɓa jinkirin fitowa ba a duk sanda na tunaki. Duk wanda ke tare dani yasan hakan Zinneerah. Nisantarki da nai itace babbar jarawar da har yanzu na kasa cimmawa wajen cinyeta, sai dai Alhmdllh, tunda yau gani gaki a yanda ban taɓa tsammataba ko tunani. Inason ki daure ki cire komai a ranki ki saki jiki dani ko hakan zai ragemin raɗaɗin ciwon gyanbon dake maƙale a zuciyata kinji”.
        Hannu Zinneerah tasa ta share hawayen dake sakko mata daga idanu zuwa kumatu, cikin rawar harshe tace, “Amma miyasa baki taɓa zuwa gareniba mama”.
     Murmushi Mama tayi itama tana sharar nata hawayen. “Zinneerah bana cikin hayyacinane, koda na baro ƙauyen Danya a yanayin ciwon hauka na barosa, sai dai Alhmdllh ALLAH ya taƙaitamin wahala maimakon na nufi wani waje saina nufi gida. Bayan isowata gida ƴan uwana sunje har Danya danjin miya faru dani amma mahaifinki yaƙi saurarensu, yama nuna bai sansuba baisan daga ina suka fitoba. Asabe kuma taci musu zarafi da musu korar kare. Duk da sunji zafin abinda akai musu sun buƙaci tahowa dake dan a gida na barki ni. amma mahaifinki ya hanasu, yama ɗora musu da cin zarafin dayafi na farko. Wannan shine dalilin yin fishinsu, amma basu haƙura akan wataran zasu amsoki ba. Ansha fama wajen nemamin magani sosai,  har takai mai gidannan dake a matsayin yayana yaje Ɗanmusa yaga halin da nake a ciki, shine ya fahimci sihiri ne tattare dani. Shine yasa aka kawoni nan kano wajen wani mutumi mai bada magungunan musulinci. Ya kashe kuɗi bana wasaba wajen ganin hankalina ya dawo tare dani, bayan wani tsahon lokaci aka dace na samu lafiya. Daga nanne ya nema aurena. Duk da banso hakanba aka tirsasani harna amince. Sosai kina maƙale a raina tunda na dawo hayyacina Zinneerah, sai dai bansan miyasaba ko sha'awar nufar hanyar Danya banayi, kai hasalima duk sanda nai yunƙurin son naje sai ciwona ya motsa min. Ƴan uwana kam bansan daliliba kowa ya bar zancen amsoki ko zuwama inda kike. Hakan na damuna a cikin rai, amma inajin kunyar yima wani magana ace na zaƙe da yawa, amma kiyi haƙuri Zinneerah ki yahe mani kinji”.
        Kuka sosai Zinneerah keyi fiye da farko. tausayi da ƙaunar mahaifiyarta na sake shigarta cikin jiki da ɓargo. sun daɗe a haka kafin Mama ta koma
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On MAKAUNIYAR KADDARA
avatar
aisha-4-4-6

9 months ago

Reply

I want to download the book

avatar
maimuna-2-6

7 months ago

Reply

Thanks

Please Login or Register in order to submit comment