Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[8/19, 10:08 AM] Haisahhtttttt💅🏻: *👠👠💅🏻BAGIDAJIYACE👠👠💅🏻*





*©️HIKIMA WRITERS ASSOCIATION.*
*(Home of peace ,joint entertainment to educate and enlighten our readers)*



*Godiya*
Ina mika godiya ta ga Allah madaukakin sarki,mai kowa da komai wandaya bani lafiya da Aron numfashi,har nafara kawo maku sabon wannan littafin nawa ,Allah nagode maka.Allah kabani ikon ga mashi cikin koshin lafiya,kuskuren dasuke ciki Allah kayafe mana.Ammen


*Dedication*
Na sadaukarda pajinnan gareku masoyan littafin RAYUWAR AFREDARH, Allah yabar kauna...🤍🖤💜


*GARGADI*
Wannan littafin 'kagaggene daga kwalwar Hassenart ,idan kinga yayi daidai da rayuwarki ,to kisani arashine.don haka vanyarda ajuyamun littafina ta kowacce sigaba batareda izininaba,yin hakan babbar zunubine...akiyaye


*_written_ _by_*
*_Hassenart_ _Mohammed_*

*Litattafan marubuciyar:-*
-RAYUWAR AFREDARH (endless love)
-QASAITATTUN MATA
-RAMUWAR GAYYA (The shaded blood)
Now
BAGIDAJIYACE


*Wannan littafin na kudine,adon haka za'a biya #200 na katin mtn ma wannan number 09065990265 sai ayi screen shooting as evidence a dai turama number na saman.vip kuma #300 don haka biya kudinki ki karanta littafin ki hankali kwance🤗🤗 wacce tabiya kudin ramuwar gayya nayi maku rangwamen zata biya #100 ne amaimakon #200 inkuma VIP ne #200 a maimakon #300*



Bismillahir~ rahmanir~ raheem


___________________________


1️⃣&2️⃣




*Kauyen fallankin malam yahaya*
*Zuntu*


Wani irin gudu takeci uwa rainta zai fita,sakamakon ganin 'yan kungiyarta suna dab da shigewa rutsutsin wajen gonakin.kwalla ma daya daga cikin su kiratakeyi da karfi, hakan yasa suka dakata da tafiyan.
Har ta Karaso cikeda haki
"K'ure dadi nine zakuyiwa wulakanci ko?,wato da bansauriba tafiya zakuyi kubarniko?"

"Laa bahaka bane indo kinsanifa sarai lokacin birek gajerene...gashi munada yawa masu cin gwavan inba muje da wuriba za'a iya komawa aji ,ko masu gonan su zo"

"Wooo, kahe da sunhememu...hanzarta mu higa layi yanda akasa ba ,kasan gonan nan akwai hi da hammatsi" tafada da lalataccen hausan ta na gidadawan 'kauye
Layi maza uku sukayi agabanta sai rahane kawarta ta biyar sauran mazan abayansu
A hankali take tafiya sadaf sadaf cikeda tsoron karta taka kan maciji...har suka iso fili suka fito sosai iya ganin ka mai cikeda bishiyoyin mangoro da guava
Daf undo tahaye nagovan tana watse masu suna watsawa abuhu

Dagacan nesa wani mutumi dake gyangyadi karkashin bishiya da zugegen dorina a gabansa, ga dukkan alamu maigadin wajen ne,ya hango su a hankali yashiga sad'ad'awa wajenda suke,karaf kan idon indo,dirkowa tayi akan bishiyar jikake tif!

Hada baki sauran sukayi suna fadin "lafiya?"
Ai yankan hanya tayi da gudu tana gayamasu cikib waka faditake"ga mai gona ga mai gona nan...Wanda yakalla banyafeba".
Haba kafa mai naci banvakiba,shimako maigadin yadade masu baya .gudu sukaringayi tun suna jin nishad'i har indo tafara kuka ,tuni a hanyar sun zubarda buhun goban amma mutiminka yaki daina binsu, har suka shiga filin makarantan yana binsu.daidai nan aka kada kararrawa na komawa aji, ai dagudu suka hade da yara kowa yayi ajinsu.

Koda maigadi yaga sun tsira ,takaicin gudun da yayi yakeyi,atake yayanke shawarar tafiya ofishin malamai yakai kararsu
Duk ko malaman suna nan...
Discipline master ne yamike cikeda fushi yacewa mutumin "yi hakuri malam ,yanzu duk sun gama shiga aji don haka muje inzaja iya ganesu a tsintosu"

"Tabbas zangane ,wannan mai muryar chanisawan(yana nufin indo)

Aji aji yaringa zagawa dashi ,har sukazo js 3 anan tun kafin sushigo yayi idobiyu da idon indo ta windown ajin ,ido ranbadadau da kwalli. Daganinta kaga Mara gaskiya.

" malam itace wagga"yanuna ta da yatsa da sauri
Malamin bai wani damuba don yasan indai indoce zata aikata abunda yafi haka

"Fito gaban allo kowa yaganki barauniya,ina sauran?" Cewar discipline master.

Ganin ba matsera yasa tafito tana muzurai,kyar tayi da ido ma en ajin
"K'ura dadi,lafazi,rahane....kai nagaji dakiran sunayenku,malamai ai he kuhito ko"
Ba arziki suka yo waje ,don sunsan inya zakado su zafa adake sun,sukuma bi hanya itama ta narka.
dukansu saida suka fito malamin ya mikama maigona bulala yazanesu...haba kura dadi yafara gaba shine dama bai tsoron bulala, sauke masa da yafara yi ,azabar dukan yagigitashi kwara ihu yakeyi iya karfinsa,tuni idon indo ya raina fata,baya taringa yi har tajingina da gajeran windon ajin basu yi auneba saidai sukaji dirkanta cikin gonakin bayan ajinsu,kalkalawa tayi da gudu 'yan ajin akasa sukabita amma haka suka kare gudun su suka dawo don tab'ace masu.
Dabalain gudu tashiga gidan,mama na tsugune tana wankin waken alala bataji shigiwarta ba saidai taga giftawarta tayi ciki da roban waken.
Mikewa mama tayi tana tafa hannu tareda sallallami
"Auta wa kuma kika tono yau ?ina makarantab?kifito inji nace"

"Alkur'an mama banfitotwa sukamani....ke makarantan ma anbari daga yau...yasin yau ban kwanan garin nan tunda kowa ya tsaneni"

Shigowa dakin tayi ,taciro ta a bayan kofan.
"To kwantarda hankalinki kimun bayani sosai"
Hmmm inazuwa " randa tanufa ta dibi ruwa a mod'a tashiga kwankwa'da daga nesa kanajin karan wucewar ruwan.tana gama sha ta suri buta taje bakin vandakin gidan ta tsula fitsarinta yako gangaro wajen dakin yaya(kishiyar mamanta)ta kakkabe jikinta tashigo daki.
Mama nanan zuru tana jiran fitowa r ta, zama tayi kan tabarma gefen mama tayi gyaran murya tasoma koromata bayani

"Mama ina gonan gobannan danake kawo maki kinaci ,kina tond'e baki?todai yau dubunmu tacika dinko su rahane yau sunkade har buzunsu da duka...."

"Ke tsaya auta menene na duka kusiya Abu da kudinku?"

"Tab lallai ma to debosu mukeyi ,hannu nki ana ke hin dauka kudi muke basu to yasin yau ban zaman garin nan Zaria ba nufa gidan anty,bazan zauna me gari yazo akamoniba,dama gashi da jikakka tsakanina dashi....ki tashi ki shirya mun kaya don alkuran akazo kamani zance kece barauniyar zaunen ,akama dake..."

"Auta nice barauniyar ?to ba inda zaki kijamasu magana ,acan su basu saba da hayani yaba ,unguwarsu na natsatsune"

Geiwoyinta tasa a kasa tana rokonta "mama nice fa autarki indo,zakiso akashani,ji nake idan na kara kwana ajalina kekira ,konafada ruwa ko rijiya...

.....to shahararriya fito ki wanke fitsarin da kikayi ....ace kaf ,kafin gidannan kin karyesu da fitsari?komai nagida kin lalaceshi ,mudai anhaifo mana annoba"
"Bani bace annoba sunusi danki shine annoba"buge bakinta mama tayi,tasoma ba yaya hakuri

" yimana shiru baqar algunguma...ba kece kikajaba,to maza sata tawankemun kofar daki don bazan dauki cin kashiba"Tsidik tayi mata a gaba
"Ninan na isheki ,kuma tunda kika zagi uwata abakin wankin fitsarin kofar dakin ki"
Tayi shigewarta muryan daki tahaye gado,masifa taringa yi kamar zata ari baki tagaji tafita ,don takaici ya hana mama bintu magana.saida taji tsiyar ya kwanta,tashiga tasameta tayi daidai a gado tana barci hankali kwance.daka Mata duka tayi acinya
"Jai'rah tashi ki hada kayan ki kitafi zarian,konaji kunne na kwana biyu"
Aidasauri tafigi Ghana mustgo tagaudanna kayanta acikin.taje tadako tsaminta tadan gurza Vaseline guburi guburi,tayafa kanannadadden mayafintada kila baitava ganin iron ba a rayuwar sa
"Mama na shirya sallameni,karsu taso makarantan" tsaki tayi ta kwanto hannun zani taciro Dari biyar tabata,tashi ga rumbu ta jibgo kayan tsaraba irin nasu na 'yankauye tabata takai masu.mai baro tafita tanemo ya kwashe kayan ta suka tafi tasha,saida tajita a motar Zaria .kuma tacika sun hau kwalta tafara jin daidai a ranta"cab ai Yaseen sai na huta na watanni zandawo lokacin komai ya lafa...,"tunanin rayuwar ta data gudanar a garinsun yasoma dawowa kwanyarta,tartar.........


#vote
#share
#comments
[8/19, 10:09 AM] Haisahhtttttt💅🏻: 👠👠💅🏻BAGIDAJIYACE👠👠💅🏻




*©️HIKIMA WRITERS ASSOCIATION*
*(Home of peace, joint entertainment to educate and enlighten our readers)*




Wannan pajin nakune kuyi duk yanda kukaso dashi,,, kawayena,aminan arziki,abokan tsegumi da dan gulma🤪
Aisha Abubakar musa(mrz zuntu)
Zainab Isah (hajiya babba)



Written by✍🏻
Hassenart Mohammed😘


Littafan marubuciyar:-

-RAYUWAR AFREDARH (Endless love)

-QASAITATTUN MATA

-RAMUWAR GAYYA (The shaded blood)

_And now_

BAGIDAJIYACE


*littafina dashi da ramuwar gayya,dukna kudine#200na mtn ake biya ta wannan number 09065990264 inkuma vip kikeso zaki turo #300 👷ace tabiya na ramuwar gayya kuma #100 zata biya VIP #200 𣁈ajiya daure rage ciki kibiya ba tsada bane gareshi da zaisa sai anfita maki dashi kina jira aturo kisamu, inmai turowa hidima yasha masa kaifa🙃😏*



___________________________


3️⃣~4️⃣


Wani handsome sojane fari tar kyakyawa ajin farko sanye cikin farar T-shirt da gajeren wandon kakinsu, nagani tsaye acikin filin wajen training din 'yan Navy acikin makarantar NDA ta kaduna,gadai dukkan alamu dalibin department dinne .waya yakeyi cikin natsuwa...ayanayinsa da yanda yake harhad'a maganarsa zakagane shid'in bamai cika son hayaniya bane,da yawan surutu....
daidai nan wata matashiyar inyamura takaraso wajen dayake itakuma cikin complete shigan uniform dinsu na navy,amma tana d'auke da alamar 'yan shekaran farko,acikin collegin.

Tana ganin sa ta fara feck call,"hello my friend,can u hear me?...eh I told u what man can do,a woman can do beyond... Letz..."rashin sani kenan donko
Awani bala'in zuciye yaje ya shaqota ya jefata cikin wani tabon jar kasa mai dauke da ruwa kimbul,tako fada ta fuska, ji kake facccch!, yayi saurin bin bayanta kafin ta dago yataka keyarta fuskarta dakanta yalume cikin ruwan jar kasan mai kamada yanbu na training dinsu.haba wutsil witsil takeyi da kafa kamar kifi, tana kuka amma bakaji saima ruwan dake shigamata ta hanci da baki,adole tai shiru cikin sadakar da cigaban rayuwa.shikan gogan ko a jikinsa saima yacigaba da wayarsa.

Da sauri wani matashin sojan ya 'karaso wajen dasuke,rai a 'bace ya saita cinyar kafar da ya daura akanta ,ya kaimasa tokari da sauri yad'an goce, cikin sauri yayi azamar janyota ya watsar gefe,sannan ya soma magana
"Farouk yaushe kazama maras imani ?,kashata zakayi komene,jibe tafa wannan tama suma...taimaka mukaita asibiti"

"...kai baka da hankali,nine zanyi punishing mutum kuma inzo inkaishi inda zai samu relieve?... Bayan rashin kunyarda victim din taimun?Towaima me ruwan ka dani da zaka daka tar dani eyee haidar?,kamata yayi kabarni inbata lesson tukuna,i want to confirm her that,what man can do, a women can never ever do...even if they can die and resurrected hundred times,so now banwaje mtseww"
bai jira tacewarsaba ya ja tsaki ya bar wajen.girgiza kai aliyu yayi ,yakira juniors dinsu dasuka zo wucewa yasa suka taimaka suka dauketa zuwa asibitin cikin makarantan.



**********

Indo kam an sauka a tashar kofar doka cikin zeetown lafiya, mai Babur tayi kiran sa tayi masa kwatancen inda zai kaita ,yadaukar mata buhun tsara barta,yasa agaba , tsohon Ghana must go dinta abaya sannan itama tahaye bayan.tiiiiiiii haka yakwasheta har GRA .daidai kofar wani gida dayafi duk sauran gidajen gurin tsaruwa ya ajeta ,taciro #200 tabasa yanda sukayi ciniki,kamar mumina Wanda tasaba biyar masu ocada hakkinsu,yo ehmana matarda saidai ta dirka tafalla a guje tace inkanada zarra kabiyota ka amsa?!

Tadad'e tsaye kafin tasami almajiri tarokesa ya shigar mata da kayan.
Tundaga bugun gate d'in, gatemen din su kasan sunyi ba'kin mahaukata.
Don haka dasauri nakusada kofar ya bude cikeda fushi dafatan kama kowaye ya Zane....ganin ta yasasu saranda don yasan watan aikin su ya tsaya,baxai taba manceta da balainta ba,sakin baki yayi galala yana istigfari aransa inyayiwa Allah laifine ,donko hadaka da indo gida daya babbar jarabawace..."
Bai ida zancen zucinba yaji takarashe hankado gate din ji kake,garararaf to ufo ciki abunta,a firgice ya juyo yana kallonta
"Malam inkagama kalle kallen ba yaro waje yahuce,haba mutum haka sai kallon tsiya ba aiki?, Sam anty bahuyi sahan mai gadiba...wannan ai shai yarinka koron masu bakin alkhairi"
Fuuuu tayi ciki da katon ghana mustgo dinta akai.
Dasauri ya amshi buhun hannun almajirin,yabi bayanta dashi don Sam baiso yazama na farko dazasuna soma rikici.


Babban kofar dazai sadaka da asalin cikin gidan tashiga kai tsaye,tasoma kwarara sallama
"Assalamu alaikum sallama nake,gaba kuwa gaisheku take,ina antyn tambayrku nake"
"Barkanki da zuwa...anty na ciki" taron masu aikin suka hada baki wajen bata amsa.
Cikeda fargaba daya daga cikin housemaid din ta amsheta da Jakarta ,har cikin falon.
ACikin falon ,Hassana da Husseinane zaune akan kujera Hassana game take a laptop dinta Hussaina na charting da wayarta ta like kunnenta da earpiece, sai Ahmad dan karamin kaninsu dabazai gaza 10years ba,dake kan dinning yana shan Golding morn.ga karan t.v dayacika falon ,din haka Sam basu ji shigowar taba saidai sukaji dirkan buhu akan center Carpet din ,take kurar kuka da barkonu yatashi alamun sun fashe ta cikin buhun.daidai nan indo tasoma magana
"Kai dan uwarku bakuga muhane bane hiyyeee"
Ai tari suka dauka atare,don Hassana harda hawayen azaba don direct yawuce mata ta kofofin hancinta.
dasauri tarufe laptop dinta tabar shinan tahaura sama da gudu,sauran 'yan uwannata suka dafe mata baya

Tsaki tayi tasama kujera tabaje tanajiran azo atarbeta,shiru har kusan Rabin awa. Sannan ne Hassana tadawo falon,tasungumi laptop dinta tanufi hanyar komawa dakin su

"Ke ina uwartakune,ne ne?"
"Kai indo kin cika fitina to tana dakin abbey kuma har yanzu ba tafito ba tukun, sai kijira in akayi azuhur zasu fito ai"

"Caftsi,kenan zaman cikin nan zantayi?,aiko na gaji saidai ko naje dakinku najirata....yaa shafii kafii" takarashe maganar ta tareda yunkurawa tayi hanyar wajen steps din.Ai azabure Hassana tayi ciki da gudu kamar wacce ta ga horror, tashige dakin su tamurza key da sauri.
Jingina tayi da jikin kofar tana hakiiy.

"Ke lafiyarki kuwa?" Hussaina takaraso tana tambayarta

"Inafa lafiya, laluwa bala'i zata shigo mana daki"bugun kofar suka somaji da karfi
"Mtseww to meye ?,ke wannan tsoron ne zaisa tarainaki....kina ganinta da lodin kayannan ,kinsan tafiyanta ba yanzuba...kuma kinsan abbey baison hayaniya ,ji yanda take bugun kofa?" Janyeta tayi ajikin kofar tamurza key din ta bude tashigo,duk suka koma gadon su suka zauna

"Ke to meye na guduwa ,harda sa makulli saikace kinga mu da fatalwa?"
Hussaina ne tasoma magana cikeda kambamawa
"Wanemu anty ayeeshar...jakadiya er saleh,sa baki dariya sai yak'e ,kowa yace zaiga dariyansa ya mutu ,margamargan dutse kinfi gaban aljihu....barkanku da zuwa bakin zuntu"...........

" aiho ai na aza baku marhabin danine ,dasaina koma inda nafito ".
Allahumma ameen, Hassana tace a hankali

" wanemu anty ,salan kija mana fushin ummy....ai murnar ganiki muke...(ta waigo da fuskarta wajen Hassana) ai ma ringa samun dadadan labaran ban dariya awajeta ko !"

Gyada kai tayi kawai batace komaiba.turo kofar akayi,ummyne da abbey suka shigo yi mata sannu da zuwa,din dinki shigewarta

"Barkaana ,barkaana daganinku mutanen zuntu...kun iso lafiya?"
Dadyne yake magana tareda tafa hannu wa fuskarsa cikeda fara'ah

"Barkankadai alhajinsu 'yan biyu...munsameku lafiya"
"Lafiya klou,ya wajen su mama....Hassana yabakusata tai wankaba"ya tambaya cikin sigar tsokana

" yoooh inbanda abinka alhj yazasu martaba ni ,haikashe fatsima uwarsu?...dadai itane zasu bata...to kusani matsayin mu daya da fatsime dan iyayen Ku,gatanan tsaye Ku tambayeta "tafada tana zazzare ido kamar uwarsu

" ayi hakuri dai ranki yadade...kuruciyace"abbah yafada cikin sugar zolaya dafatan kwantarda tarzoma

"Hmmm...wai ina mutumina ne aliyu haidara,hoja mazan hwama" tafada tana washe dafaffun hakoranta

Ummyy ta amshe maganar"Nana aisha tashi muje dakina ...sweetheart kubiyota da Jakarta...aliyu na makaranta ,but munasa karan zuwansu a satinnan"

"Eyyah Allah yakawoshi lafiya donjin gidannan nake uwa maka barta dabayanan" tafada tana karkade 'Yar zaninta tamike tabi bayan ummy ,Abby ma yafita.




#vote
#share
#comments
[8/19, 10:10 AM] Haisahhtttttt💅🏻: 👠👠💅🏻BAGIDAJIYACE👠👠💅🏻


*©️HIKIMA WRITERS ASSOCIATION*
*(Home of peace,joint entertainment to educate and enlighten our readers)*


This page ix wholly dedicated to my besty Hameedart 🥰
Allah yabama mamanki twins,anty habiba saura karkice ameen🤩🤩



Written by
Hassenart



Littatafan marubuciyan:-

-RAYUWAR AFREDARH (Endless love)

-QASAITATTUN MATA

-RAMUWAR GAYYA (The shaded blood)

And Now

BAGIDAJIYACE


*Wannan littafin na kudine only #200 VIP #300 , idan kinbiya na ramuwar gayyya kibiya #100 vip #200. Hanzarta kibiya kudinki kafin nagama*💃💃💃


5️⃣~6️⃣


*WACECE INDODO*


Indo Aisha diyace ga mal.abdullahi da mal.binta
Mal.Abdullahi asalin su fulanin usulne 'yan asalin garin zuntu a wani 'kauye da ake kiransa fallanki,babansa ,shi yakafa kauyen sunan shi mal.yahya ,amma shidan kauyen gabane ana kiran kauyen *fallankin sab'a dutse* to lokacin da ya bar kauyensu da matanshi ,sai yayi 'yar madaidaicin gidansu suka zauna anan.
sai ya zamana infulani sukazo wucewa zasu sauka awajen sudanyi bukkansu na wucin gadi sutashi wasu su tsaya,ahaka waje yayi tayawa har yazama gari ana cemasa fallankin mal.yahya.

Mal.yahya yana da matan aure hudu dayara Ashirin da uku ,Ashirin da daya matane biyu maza Abdullahi da Abdussalamu

Lokacin da yaran shi maza suka fara tasa wane yadaukesu yakaisu almajiranci abdullahi aka kaisa Zaria ,shi kuma abdulsalamu yafi kusa akabarsa a soba .

Abdullahi Dane mai hazaka saida yayi sauka sau uku da tishi ,abdulsalam baiyi dayaba. adon haka sai yafara sana'arn dinkin hula anan cikin Zaria ung. Albarkawa tunda ba halin komawa yabar dan uwansa bai dawoba,yina sana'ar sa yana karatun littafai don sun zama gardawa.Ahaka wata rana wani alhj Ilu dake sayan hula a wajen sa yayi masa tayin makarantan boko ,bai wani musaba don yana da sha'awar karatun dama can,yaroki mutumin da yazo ya rokar mashi malamin su in ya amince.

Bai sha wani wuyaba sakamakon toshe masa baki da kudi dayayi.
Damakarantan yaki da jahilci yasoma, daganan yawuce secondary yafara daga form 1 har 5 .lokacin har yafara sana'ar yadiddika da dinka Manyan riguna yana saidawa attajirai da masu sarauta duk da taimakon wannan alhajin

Koda yagama sakandire makarantan gaba yanema yasamu yayi diploma daganan karatun ya tsaya ,saboda hura masa wuta a kauyensu da akayi da yayi aure a lokacin tuni abdussalami yayi aure matansa biyu da 'yaya rututu.

Alhaji Ilu mai gidansa yasama da maganar, yagayama duk matsalar da yake ciki,kwantar masa da hankali yayi sosai yakarba takardunsa yasamar masa aiki a wani babban kotu dake a sabon gari.yakuma wanke 'yarsa bintu yabasa da kyautar gida.

Hankali kwance yake gudanar da rayuwarsa arziki na kara bunkasa har suka hayayyafa a lokacin da binta tahaifi yara biyune Fatima da ameena danginshi nacan suka matsa sai ya auri 'Yar uwansa yahadasu inbahakaba,'yan Zaria zasu kwashe arzikinsa inya rasu,binta tanada sanyin hali batada hayaniya samsam .

Bata matsa masaba ya auro matarsa kuluwa amma ana kiranta yaya yabarta acan fallankin bayan ya Gina gidansa me kyau acan.

Tunda binta tahaifi 'yarta Rahma haihuwar ta tsaya mata.bare kuma yaya da ko b'atan wata bata tab'a yiba.

Tuni fatima da amina sun girma har anyi bikinsu ameena a tudun wada tayi aure da yaranta uku dayake gwarne takeyi itakuma fatima tabiyo mamansune danta kenan daya alokacin sunansa Aliyu a hanwa suka fara zama da mijinta cikin danginsa.
Itakuma rahma ansamata rana da wani dan Abuja yazo bautar kasa makarantarsu,suka hadu

Sai a wannan lokacin ne ciki bul ya bayyana ajikin mama binta daabokiyar zamanta yaya .

Akuma wannan lokacin ne mal.yahya Allah yayi masa rasuwa.

Suka d'ibi jiki aka tafi gaisuwa bayan an share zaman makoki an raba gado mal.abdullahi yayi shirin komawa Zaria ,nan enuwanshi suke shaida masa wasiccin babansa dayayi akan yadawo fallanki da iyalansa da zama.

Yayi kukan bakin ciki bintama tayi ai wannan shi ake kira karkon kifi daga cikin gari sai dosun kauye?

Adole yakara fadin gininsa yayi masu wadataccen gini na sumunti ,yaje wajen aikin su aka bashi transfer yadawo kotun zuntu.

Basudawo fallanki da zamaba saida sukajira akayi bikin rahma acan zarian amarya tatare agidan mijinta a abuja

Anan fallankin tahaifi 'yarta aishatu danginta nacan nakiranta indo,itama yaya tahaifi danta namiji ana kiransa sanusi,sa'annine indo da sanusi wata biyu sanusi yabata.itakuma lokacin Fatima tana goyon 'yan biyunta sunba indo wata hudu.

A lokacin da indo da sanusine suka isa shiga makaranta babansu yasakasu a primary din cikin garin zuntu,kullum in zaije aiki zai tafi dasu.in lokacin tashi yayi yaje yadaukesu su wuce gida,a kullum cikin kawo masa kararta ake yau taci abincin wane,gobe ta Zane wane, tankwalace original duk jarabawa ita ke daukan na baya.ancancanja makarantu ba adadi amma Sam ba abunda ya sauyata nadaga kokari ko kawo kararta kan yaran mutane

Dama kuma tunda indo ta taso , tun bata wuce shekaru ukuba tayi tanbari a unguwansu to, cizon yaran jama'ah iyaye na ganin ta ,suke dauke yaransu su Goya, ga rigima.

Watarana ne anty Fatima tazo garin da 'yan biyunta,shikenan tunda yara sukazo garin suka daina shan ruwan garin ko anbasu sai sun amayar,A lokacin basufi shekaru biyar ba,take suka fara rama.da tana kawaici ne saboda alkunyar dake tsakanin ta da maman matsayin ta na 'Yar fari ,bata ko kula 'yayanta bare ita kanta.gashi basuyi sa'ar kishiyar uwaba don Sam harsuzo sutafi daga gaisuwa ba maganar da zai sake hada su.

Ganin 'yayan mutane na Neman halaka abanza ,ai ba arziki tazari keyn motarta taje nemo masu ruwan roba a cikin gari,don tasan ruwan rijiyar garinne badadi kuma ita bazata iya basu narafiba.
Cartons 5 tasiyo dasu caprison datarkacen chocolate takawo masu. Aikoba ajimaba ,yara suka murmure suka saki jikinsu.
Saidaime?tunda indo ta kyalla ido taga ruwa ,tashi ga jida ,tana bama yaran makota da almajirai kwaf daya, saida takrar da duka ,itace kwabin wasan kasa dashi ,tajika jiki ta bannatar.
tun Fatima na kawaici harta kare dai ta tsawa tar mata.
Haba dan fadarda taima ta keda wuya ,tasami karkashin inuwa tamike kafa ta runtse ido taringa kwarara ihu iya karfinta,kaf saida ta tada hankalin gidan,kowa yazo lallashinta sai aga ido a soye ba d'igon hawaye.

Tun safe har karfe biyu tayi zufa sharkaf ,kowa dayagaji dole suka shige daki suka barta ,harsaida tayi su amai sannan bacci ya sureta a wajen.

Fatima da yaran ta kam tundaga lokacin suka fara ganin babi babi na izaya,shiga dubu fita dari saita jibgesu,don dole ta tattara kawunan 'yayanta suka koma inda suka fito.

Haka rayuwa tacigaba da gungurawa ,har indo suka shiga shekaru takwas,nan akeyinta
Don ita gabadaya
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3

1 Comments On BAGIDAJIYACE
avatar
abdulkadir-lawan-yusuf

2 months ago

Reply

Tsarin labarin yayi

Please Login or Register in order to submit comment