Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

BUDURWAN SIRRI
Littafin Shuraih Usman
Ebook created by Shuraih Usman
Ebook publish by http://hausaebooks.cf
Publish date: 2018 at www.hausaebooks.cf

BUDURWAN SIRRI
Gajeran labari
Marubuci Shuraih Usman
@hausaebooks.cf
@shuraih 99%
Page 1
.
Gargadi:- wannan littafi mallakar shafin hausaebooks ne don Allah kada wani ko wata ya juya wani bangare ko barin littafin na batare da iznin wannan shafi ba
.
Na fito daga gida ina sauri zan karasa wajen wani abokina domin na karbi wayata , nan na tsaya a bakin hanya ina neman lift, ban dade da tsayawa ba kuwa na samu wani dan anguwarmu yazo wucewa na tsayar da shi
.
"Abasu kala, dan Allah kabani wayana mana ya kanamin irin haka ne kaifa kasan in babu wannan waya toh fa abubuwa da yawa zasu rikirkice domin kuwa akwai document dina da yawa aciki
.
Kuma mutae da yawa suna jirana"
Na fada a lokacin dana ke tsaye a shagon su umar
shagon hada takalmane wanda wani dan cirani yazo ya bude cikin ikon Allah sai kuwa jama'a sukai ta saka yaransu cikin wannan shagon har takai yanzu wannan shago ta shahara wajen hada takalma
.
Umar wanda fuskarsa ya baci da dusar takalmi ya dubeni yace cikin muryar wasa " 99% wallahi wayanka tana gida , kuma yanzu dai kaga ina gugan takalma ne , babu yadda zanyi na saki gugan nan na je gida yanzu"
.
Kwafa kawai nayi cikin bacin rai na fice daga shagon sannan nayi natafiyata , don kuwa ba karamin haushi yabani ba,
Nan na tuna yadda ya dauki wayar ina barci da safe , inda idanuwana biyu ne a lokacin toh da babu abunda zaisa na barshi ya dauki wayar
.
Gida na nufa cikin takaici da jimamin wannan abu da umar yayi mani, kamar daga sama sai naji wata zazzakan murya tana kiran sunana
"Shuraih shuraih!! Shuraih!!!"
.
Cikin sauri na juyo don naga wacce take kirana amma cikin mamaki da zunzurutun al'ajabi sai banga kowa ba hakan ba karamin kidimani yayi ba amma sai na dauka tamkar kunnena ke yaudarana
.
Hakan na cigaba da tafiya ina isowa gida na wuce zuwa daki na , ina shiga naje na kwanta don kuwa yanzu lokacin hutu ne babu abun da nakeyi agida hakan yasa na ke dan rubutu da gajerun labarai na littatafan hausa na ringa post na su a social media,
.
Toh gashi dan iskannan ya dauke wayar kuma ya hanani,sai yawo da hankali yake yimini,kwanciya nayi bisa wata lallausar kujera dake girke a dakina, nan na kumshe idanuwa na domin kuwa barci nake bukata da nayi
. . . . . . .
.
"INNA LILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJI'UNN"
Na fada alokacin dana farka na tsinci kaina cikin dokar daji babu gida baya babu gida gaba,
.
Na mike tsaye cikin tu'ajjibin wannan lamari ina mai tsananin mamaki da Al'ajabi don a tunani na ma mutuwa nayi,
.
Toh amma da mutuwa nayi ai dole, naga mala'iku hakan ya tabbatar mani. Ba mutuwa nayi ba ,
.
Tayaya ni da na kwanta acikin dakina bisa kan shimfidata sannan na farka na ganni cikin dokar daji ai dole wannan abu ya rikita ni,
.
Babu abunda ya sake rikitani game da wannan daji face gani danayi wannan dajin sam bai yi kama da irin dajin dana saba gani ba,
Don kuwa yanayin irin wannan daji a talabijin na saba gani cikin finanan kasashen waje
.
Ni shuraihu inkiya 99% sai dana firgita ainun da yanayin wannan daji na nemi waje na zauna ina ta tunani kala kala acikin zuciyata, can sai nayi karfin hali na tashi na tunkari gabas donni a tunanina, wai kodai barayi suka shigo gidanmu suka kamani suka zo suka ajjiye anan,
.
Sai wata zuciyar tace dani yo imma barayinne suka kama ni mene ne dalilin da yasanya suka kawoni wannan waje, nan dai na cigaba da tafiya ina ganin ababen mamaki, dogayen bishiyoyine suka cika wannan daji bishiyoyin kuma zaka gansu sai kamshi suke tamkar itatunan sandal,
.
Su kansu ganyayen wannan bishiyoyin korayene ababen sha'awa, sannan kasan wannan daji wasu irin ciyayi ne wayanda ban taba ganinsu ba , su wayannan ciyayi sun kasance jajaye, kuma koda na taka su sun durkushe take zasu sake dagowa
.
Koda na kara gaba sai na hadu da wani abun mamaki wanda yai matukar tayarmun da hankali
Ba komaine na gani ba illa wata korama, wadda ruwanta yake zubowa daga saman wani katon dutse , shi wannan korama ruwansa garai garai ne dun kuwa koda na matso kusa da ruwan sai na ga hoton fuskata ya bayyana acikin ruwan tamkar an dauki hotona ne aka manna ajikin ruwan
.
Tsaban tashin hankalin dana tsinci akaina aciki a wannan lokacin yasa na kurma ihu, domin kuwa dauka nayi ko mafarki nake hakan yasa na cizi hannuna, a bisa mamaki sai naji zafi ya ziyarci hannanuna hakan ya tabbatar mani da cewa ba mafarki nake ba
.
Irin wannan koramar sam babu shi a kasar hausa, kuma na riga dana san a irin garuruwan da ake samun wayannan koramun, don kuwa na kanga hotunansu a jikin gorunan swan water da talabijin
.
Motsi naji daga bayana hakan ya tabbatar mani da a akwai wani halitta a bayana koda na waiga sai naga daga cikin wani surkukin ciyayi mitsin yake fitowa, nadai takure na matse sannan nayi na maza na daure don ganin mene ne ya ke fitowan
.
Abubuwan dana ga suna fitowa daga cikin wannan surkuki su suka saka naji cikina ya tsure, idan da ba dun ina da karfin haliba toh da babu abunda zai hana ban saki gudawa a wandona ba, amma duk da haka sai dana tsiyayo fitsari wanda ni ban ma san na tsiyayo ba
.
.
Kai friends ku taimaka ina cikin firgici
Shin ko kunsan mena gani alokacin toh ku jirani sati mai zuwa a cigaban wannan labari wanda zai runga zuwa maku duk sati Ranar Asabar da safe tare dani Shuraih Usman inkiya Shuraih 99%
.
Wannan kirkirarren labarine daga 99%
Ku tsumayeni a page 2
Daga:- hausaebooks wepsite
Da keffians News Teller
BUDURWAN SIRRI
Gajeran labari
Marubuci Shuraih Usman
@hausaebooks.cf
@shuraih 99%
Page 2
.
Gargadi:- wannan littafi mallakar shafin hausaebooks ne don Allah kada wani ko wata ya juya wani bangare ko barin littafin na batare da iznin wannan shafi ba
.
Ba komai nagani ba face namun daji danginsu su Alfadari, Giwa, barewa,Zaki,maciji,damisa,kura kai duk dai wani dabba da kuka san yana rayuwa acikin daji, cikin gungunsu suka nufo ni ai koda ganin haka sai na juya da nufin na fada cikin wannan kogi dayake gabana
.
Amma me zan gani wasu kyawawan kananan kifaye na gani masu zakwa zakwan hakora lokaci lokaci zakaga suna kikkirta hakwaransu, abun yabani mamaki wai ace kifaye da hakwara amma sai na tuna wani american film din dana kalla mai suna PIRANHA
.
Koda naga haka sai nayi wani gefe da gudu don na tsere ma wayannan dabbobi da suka biyo ni da mugun nufi, gudu nake iya karfina don na ceci rayuwata daga hannanun wayannan dabbobin sai dana kai wajen mintin arba'in ina tsala gudu acikin wannan jeji amma wayannan dabbobin sai bina suke duk inda na shige, abunda zai baka mamaki da wayannan dabbobin shine
.
Su ba gudu suke ba don kuwa tafiya suke amma yadda kasan suna gudu domin kuwa duk lokacin dana waigo yayinda nake tsala gudu sai na hango su a kusa dani,
Acikin wannan gudun danake yine, nazo gaban wani katon kogon dutse, batare da wani nazari ko shawaraba na afka cikin wannan kogon,
.
Ai koda shigata cikin kogon sai wani narkeken dutse ya mirgino da kanshi ya kulle bakin kogon ta yadda ko digon haske baya iya shigowa cikin wannan kogo,
.
Take duhu mai tsanani ya mamaye wannan kogon don kuwa ko tafin hannuna bana iya gani nan nacigaba da karanto addu'o'I kala kala duk wacce tazo bakina karantawa nake, har saida na karance gabadayan addu'o'in dana iya haka na runga jawo ayoyin kur'ani maigirma har zuwa wani dan lokaci
.
Koda naga an dauki dan lokaci banga komai ya faru ba sai na dan fara tafiya amma bakina babu abun daya ke furtawa face karatun kur'ani,
.
Tafiya nake ban san inda nake nufa ba, nidai nasan ina tafiya domin kuwa duhun daya mamaye wannan kogo baya bari naga maine ne agabana, na tsinci kaina tamkar wani makaho
.
Ni dai babu abunda nake furtawa face karatun kur'ani mai girma, koda na cigaba da tafiya acikin wannan kogon ina cin karo da duwatsu akalla na fadi yafi sau goma
.
Don kawai sai ina kan tafiya sai naji nayi karo da dutsi take zakaga na fadi gefe, a haka sai da hannuna na dama ya samu targade,
Kukan zuci nake sosai ina tunanin lokacin da akeyimana wa'azi a islamiya zaka ji ana cemana muyi aiki mai kyau don kuwa akwai lokacin da mutuwa zata riskemu,
.
Sam sam bana son na mutu yanzu amma kuma gani nake tamkar tsakanina da mutuwata banfi zira'I daya ba zuciyata tana ta karantomin abubuwa da yawa na cutarwa da ka iya wanzuwa a cikin wannan kogon
.
ni ma'abocin karanta littatafan yakine nasha jin labarin yadda kogo take, kuma a yadda naga dutsin nan ya mirgino da kanshi yazo ya rufe kofar fita daga wannan kogo hakan ya tabbatar mani da cewa wannan al'amari akwai TSAFI acikin sa
.
Amma haka na dake na cigaba da addu'a da karatun kur'ani a zuciyana, kai in takai takawo ma har hadisai ma karantowa nake
.
Haka na kasance a cikin wannan kogon har na tsawon wajen sa'a daya wato awa daya sannan na fara tafiya, babu abunda yake zuwa zuciyana face tunanin ALJANNU
.
Don nasan inba lamari na Aljani ba babu ta yadda za'ayi na kwanta a gida cikin dakina bisa kujera mai laushi sannan na farka na ganni cikin kungurmin daji sannan ga wasu halittu na neman su halakani
.
Haka naci gaba da tafiya kwatsam ba zato ba tsammani sai cikin kogonnan ya gauraye da wani haske wanda koda Allura ne yafadi akasa toh za'a iya ganinsa
.
Hamdala nayi sannnan na gode ma Allah daya rabani da sharrin Duhu ya Allah karemu daga sharrin DUHU,
.
Toh sai a sannan naga ashema kogon nan cikinsa tamkar wani gidan hamshakin attajiri ne ko kuma mashahurin sarki , domin kuwa ganin kogon nayi a kawace da tsarin gida,
.
Shi dai wannan kogo dana afka sam daga ciki baiyi kama da kogo ba sai dai akirashi da fada domin kuwa wani kayataccen fada ne a ciki, nan na zama dan kallo nama daina mamakin yadda akayi na zo wannan daji na koma mamakin wannan fadar wanda tafi min kama da ALjannar duniya, sai a sannan ne na lura da komai dake cikin fadar fadan ya kawatu iya kawatuwa don kuwa tun da nake a duniya ban taba ganin wani fadan dayai rabin wannan kawatuwa,
.
Duk da na kasance masoyin kallon fina finan kasa shen waje irin na su yaki, toh ko a fina finan ban taba ganin irin wannan fada ba
.
Babbar fadace katuwa wacce zata iyacin wani karamin gari akarshen fadar wata kujerace ta zinare a girke wannan kujerar an kawata ta ainun don kuwa wasu irin takubba masu tsananin walkiya da kashe idanuwa aka sossoka su ajikin kujerar
.
A saitin kujerar daga gaba wata shimfida na gani itama kalarta kalar zinari an shimfidata takai har karken fadar, kai nan dai na tsaya ina ta kalle kalle ,
.
Wani abun mamakin kuwa shine babu kowa acikin wannan fada sannan kuma ga a kowanne kusurwa na fadar an ajjiye wasu irin gumaka masu siffar mutane cikin shigan yaki,
Koda na kare masu kallo dakyau sai na gane ashe wayannan kaman sojoji suke,
.
Nayi ta yawata wa acikin fadar har kafafuwana suka fara kuka, nan na zube kasa ina mai dafe da kafafuwana, sai a sannan idanuwa na suka kai ga wata, kofa wacce sam ban lura da ita ba yayin dana shigo cikin wannan fada,
.
Koda na ga haka sai na daure na mike tsaye na tunkari wannan kofa, ina isa bakin kofar na sanya hannu na bude , ko musu kofar baiyiba yabata wata kara "kikkir kikkirrrrrr" alamar ana bude kofar, kofa kofar ta gama wangamewa ta budu nan take nai arba da abun da ya tashi tayar mani da hankali ainun,kwakkwalwata ta kusan daina aiki,idanuwa na sukafara lumshewa a hankali tamkar me gyangyadi,gaba dayan lakar jikina ya mutu,!!!
.
Zazzakar muryace ta biyo baya "shuraih! Shuraih!! Shuraih!!!
.
SHIN A TUNANIN KU wai me nai arba da shine da har na rikice haka
BUDURWAN SIRRI
Gajeran labari
Marubuci Shuraih Usman
@hausaebooks.cf
@shuraih 99%
Page 3
.
Gargadi:- wannan littafi mallakar shafin hausaebooks ne don Allah kada wani ko wata ya juya wani bangare ko barin littafin nan batare da iznin wannan shafi ba karkashin jagorancin Shuraih Usman
.

na daure na mike tsaye na tunkari wannan kofa, ina isa bakin kofar na sanya hannu na bude , ko musu kofar baiyiba yabata wata kara "kikkir kikkirrrrrr" alamar ana bude kofar, kofa kofar ta gama wangamewa ta budu nan take nai arba da abun da ya tashi tayar mani da hankali ainun,kwakkwalwata ta kusan daina aiki,idanuwa na sukafara lumshewa a hankali tamkar me gyangyadi,gaba dayan lakar jikina ya mutu,!!!
.
Ba komai nai arba da shi ba face wata tsaleliyar kyakkyawar budurwa wacce saboda tsananin kyawunta ne nama kasa sarrafa kaina,
.
TABA RAKALLAHU AHSANUL KHALIQEEN, lallai Allah yayi halitta , ita dai wannan kyakkyawar mace wacce ta kasance bantaba ganin ta ba sai ayau, shekarunta ba za su wuce goma sha tara ba, tsananin tsabar kyawunta nema yasa har wasu dausayin fararen haskene ke bibiye da ita,
.
Na tabbata ko da cikin duhu ne mai tsanani wannan budurwa ta miko hannunta toh take duhun zai bace haske ya maye gurbinsa,
"Shuraih! "
Zazzakar muryarta wadda tafi na komai dadi aduniya ta katse mani tunanina , a irin salon yadda take kiran suna na, ji nake babu wanda ya iya kiran suna na face ita, koda wannan zazzakar muryar tata kawai mutum zai saurara toh da sai ya gwammaci ya saurara fiye da abashi kyautar makudan dukiya
.
Firgigit na dawo cikin hayyacina tamkar wanda ya farka daga barci na dubeta baki na sai kakkarwa yake amma na kasa fadan komai dakyar da sidin goshi na iya fadin "nnnna - m"
.
Murmushi tayi wanda ya kusa zautar dani don kuwa alokacin da gefen kuncinta suka lotse sai naga tama fi kyawu bisa kan da,
.
Koda taga halinda na shiga adalilin wannan murmushinn da tayi sai ta kyalkyale da dariya, ai saboda dadin sautin wannan dariya nata ban san lokacin dana sulale a kasa sumamme ba,
Iya abin da masarrafin kwalkwata ya iya dauka shine daukewar dariyar wannan budurwa daga nan kuma ban sake sanin meke faruwa ba
***
.
A hankali nafara bude idanuwana, mutane ne nafara ganinsu dishi dishi akaina, na mike na zauna sai a sannan ne kwalkwalwata ta dawo aiki hankalina ya dawo jikina
.
Na dubi mutanen da suke gefena suna yimini sannu, sai naga ashe ma yan mata ne kyawawa, sanye da fararen dogayen kaya, sai a sannan na lura da dakin danake ciki
.
Karamin dakine an kawata shi da kayan ado na mutanen da, zaune nake a kan wani luntsumemen katifa, wadda yake bisa wani katakon gado, na budi baki na ce wa yan matannan "su waye ku, a ina nake sannan waya kauni nan?"
Wata daga cikinsu tace ainan kana gaban birnin sin ne cikin garin LAJUJ
.
"Ina ne kuma garin lajuj, na tambayesu" na tambayesu cikin mamaki
Wacce ta bani amsa da farko ta sake cewa "ai garin lajuj garine na Aljanu don kowa daka gani anan garin aljanine, mutum dayace kawai ba aljana ba, amma itama ba mutum ba ce, kuma itace ta kawoka wannan birni namu, "
.
Cikin rudewa na mike a firgice ina neman hanyar gudu don kuwa na riga dana gama firgita da maganarsu,
Na nufi kofar fita daga dakin cikin gudu na kama mabudin kofan na murda take kofan ya bude
.
Ban jira komai ba na nausa a guje, wata doguwar hanya na gani ta mike santa wannan hanyar na zura a guje, ko waigowa baya bana yi,
ban dade da fara bin hanyarba sai na hangi wata kofa karshen hanyar, wannan kofa abude take,
.
Turus naja na tsaya a yayin dana shige cikin wannnan daki da yake da wannan kofa,
.
Zaune take akan wata luntsumemiyar kujera haryanzu wannan murmushin nata yana nan a fuskarta,
Ta dubeni tai mani nuni da wani kujera tace na zauna
.
Babu musu naje na zauna akan wannan luntsumemen kujera wanda saboda tsabar laushinsa sai danayi tsammanin ko bulalliyar kujerace,
.
Zamana keda wuya sai na cigaba da kallon kyakkyawar fuskarta wadda banki nayi shekaru talatin ina zaune ina kallo ba, karar budewan kofar dakin shine yaja hankalina inda na maida dubana ga wajen
.
Daya daga cikin matannan ne ta shigo tana dauke da wani faranti a hannunta mai dauke da akushi sai wani tambulan na zinare, tazo ta ajjiye a gabana
.
Tana ajjiyewa tayi ficewarta kyakkyawar budurwan ta dubeni tace "ga abunci nan kaci in kama sai muyi magana, "
Ba musu na bude akushin wanda yake rufe sai nayi arba da dafaffiyar kaza, sai a sannan ne ma cikina ya fara kuka na tuna cewa wunin ranar ban ci komai ba , kuma banji yunwa ba sai yanzu
.
Toh dama ina cikin wannan hali ina zanji yunwa, cikin kankanin lokaci na gama da wannan kaza banbar komai a cikin akushin ba sai kasusuwa, nan na kora wani lemu mai tsananin zakin gaske sannan nayi hamdala ga Allah
.
Koda ta fahimci na iddar da abuncin sai ta fara magana da daddadan sautin muryanta wanda kan iya zauta mutum, "shuraih ka sani cewa ni sunana haseena tun ranar dana fara ganinka shekaru biyar baya naji zuciyata ta kamu da tsananin sonka, naji babu wanda nake so aduniya sama da kai,
Tun a wancan lokacin na so na sanar dakai irin zunzurutun son dana ke maka Amma naji tsoron Abu daya, Wato naji tsoron SALMAN"
Haseena tayi shiru ga barin magana llokacin data sadda kanta kasa,
.
Na tsinci kaina acikin wani irin Ni'ima wanda tunda nazo wannan duniya ban taba tsintar kaina a ciki ba, wai ni take so tabbas abun da Al'ajabi
Cikin dakewa irin ta maza na dubeta bakina sai rawa takeyi nace HAS-sss Ena ta dago da kanta ta dubeni fuskarta na murmushi a gareni in ka ganta tamkar wata ran daren goma sha biyu
.
Nan da nan naji na samu kaina ina mai cemata "lallai babu mutumin da zaiyi arba dake baiji cewa yana sonki ba, tun dana fara ganinki nima zuciyata take bugawa ban taba gani ko jin labarin wata mai kyau irin nakinnan ba,, I na sssoosssonki Haseena"
.
Tayi murmushi sa'annan ta kama hannuna ta mike tsaye tace zo muje na gabatar dakai a wajen mahaifana, naji abun banbarakwai amma na dake nace mata masoyiya kafin muje mai yasa ba za kidan bani labarin wannan birni naku ba mai matukan ban Al'ajabi
.
Haseena ta dubeni da wani kayataccen kallo sa'annan Tace "habibina mai zai hana"
Muka koma muka zauna akan luntsuma luntsuman kujerun dake makare a cikin dakin
.
Haseena ta dubeni tace "shuraih sunan wannan birni namu LAJUJ kuma wannan birni bayana kan Duniyarku bace ta mutane
Wannan birni na Lajuj birnin Aljanu ne amma mun kasance musulmai kamar kai, mahaifina sunansa Nasaruddin kuma shine sarkin wannan gari namu.....
..Rayuwa haka take wakana yau lafiya gobe akasinta, dazu-dazu lafiya yanzu-yanzu rashinta
Allah ka baiwa dukkan musulmi marasa lafiya masu lafiya kuwa Allah ka kara masu ,,,,
Its 99% awakening from three 3 days sickness
Yo sai mun Hadu MAKO mai zuwa
Daga - www.facebook.com/hausaebooks
.
Marubuci:- Shuraih Usman
Typing:- Shuraih 99%
Hakkin mallaka (m) hausaebooks page
BUDURWAN SIRRI
Gajeran labari
Marubuci Shuraih Usman
@hausaebooks.cf
@shuraih 99%
Page 4
.
Gargadi:- wannan littafi mallakar shafin hausaebooks ne don Allah kada wani ko wata ya juya wani bangare ko barin littafin nan batare da iznin wannan shafi ba
.
Haseena ta dubeni tace "shuraih sunan wannan birni namu LAJUJ kuma wannan birni bayana kan Duniyarku bace ta mutane
Wannan birni na Lajuj birnin Aljanu ne amma mun kasance musulmai kamar kai, mahaifina sunansa Nasaruddin kuma shine sarkin wannan garin namu,
.
Mahaifina ya kasance jinsin aljanu ne , amma kuma daya tashi aure sai ya tafi naku duniyar ya auro jinsin bil'adama wacce ta kasance itace mahaifiyata, sai da mahaifi na ya yai shekaru biyu a duniyar mutane sannan Allah ya baiwa mahaifiyata haihuwa, amma cikin rashin sa'a data haifeni sai ta koma ga mahaliccinta
.
Mahaifina yayi kuka sosai akan rashinta, domin kuwa a kullum da dare baya samun bacci sai tunaninta yake sakamakon irin zunzurutun shakuwan dake tsakaninsu, da kuma matsanancin soyayyar da suke wa junansu
.
Tun daga wannan lokaci gaba dayan son da mahaifina yake yi wa mahaifiyata sai ya dawo kaina, ya dauko ni muka dawo wannan duniyar, amma lokaci lokaci yakan daukeni muje duniyar mutane na dan wani lokaci sannan mu dawo wannan duniyar
.
Abum Al'ajabin daya kasance dani shine ni ba Aljana bace haka nan ni ba mutum bace, kuma ni Aljana ce Ni mutum ce,.." Har zan yi magana sai ta daga mani hannu alamar nayi shiru, ta dora da "tsananin kyawuna ne ya sanya aljanu da yawa ke muradin suga sun aureni, amma sam mahaifina ni baya son na auri Aljan ,
,
Daga cikin masu son su aureni akwai Salman salman shine sarkin yakin wannan birni namu
Gaba daya mutanen wannan birni namu sona matukar tsoronshi da shakkar shi, saboda duk birnin nan babu wanda yakai shi jarumta , wannan nema yasa da yawa daga cikin masu neman aurena suka janye sakamakon tsoron salman da sukeyi
.
a Al'adar wannan
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5

Please Login or Register in order to submit comment