Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

AUREN KWANGILA!




1








Littafin






SUMAYYAH ABDULKADIR
Babbangoro2015@yahoo.com
Takorikabara@gmail.com

SADAUKARWA
Sadaukarwa ne ga duk makaranta littattafan TAKORI. Wadanda na sani da wadanda ban sani ba, masu jimirin bin rubutuna daki-daki shekaru dai-dai har goma sha biyu!Tun daga kan SIRADIN RAYUWA har zuwa yau da Allah ya hada mu a AUREN KWANGILA, yabawarku da karfin gwiwar da nake samu daga gare ku ne ya sa har muka kawo yau. Ina rokon Ubangiji ya hadamucikin alherin sa, har zuwa ranar da muka daina numfashi.


GARGADI
Ban yarda a karanta wannan littafi a gidan rediyo ba tareda iznina ba, ban yarda a juya shi ta kowacce siga ba ko rubuta shi a social media, yin hakan zai gurfanar damu gaban kuliya kuma abin tuhuma ne daga Lawyer na barrister Sadiq R Wali. Wadanda bansan inda kuke ba kuma zamu hadu a kotun Allah ranar da bawa bashi da abin biyan hakkin dan uwansa sai kyawawan ayyukan sa.


MANUFA
Manufar littafin tana cikin littafi na 3 da na 4. Don haka kada kayi korafi ko sharhi har sai ka dangana da karshen labarin. Taku har abada; Takori



AUREN KWANGILA-1
January, 1996
K
yakkyawan gidan ginin zamani na nan a tsakiyar hamshakiyar unguwar Asokoro cikin babban birnin tarayya, Abuja. Ba shi da girman da ya wuce kima, amma fasahar da aka zuba wajen gina shi abar kwatance ce, sannan hawa daya ne babu hawan bene (flat house). Ainahin ginin gidan a tsakiyar gidan aka yi shi, inda furanni suka zagayeshi suka yi masa rumfa har samansa, rufin da aka yiwa gidan brown ne ire-iren rufunan gidajen kasashen ketare. Kamar yadda rufin gidan yake brown haka fentin gidan ma yake ruwan madara da ruwan kasa (milk&brown). Daga can gefen dama na gidan an gina guest rooms wato dakunan saukar baki wadanda maigidan yayi su ne musamman don saukar ‘yan uwansa dake Kanon Dabo idan sun zo. Gidan ya kawatu da furanni kala-kala dogaye da gajeru masu sanyi da kamshi da kyawun gani hadi da kayatarwa a harabar gidan da kewayensa. A kasa kuwa ‘grass carpet’ ne sun kwanta sun yi lumm, masu taushi da sanyi hadi da sanya nishadi a zuciyar mamallaka gidan.
Da ka shigo get din gidan dakin maigadi za ka tadda a baryar dama, daf da get din. In ka kara yo gaba kadan rumfar adana motoci ce, ga su na a jere sai numfashi da sheki suke yi, mulmulallu kuma kosassu rufe cikin tamfol, adane reras cikin rumfar ba tareda kowacce ta gogi ‘yar uwarta ba, samfur din kowacce daban dana ‘yar uwarta, motoci ne da wadanda suka ci suka tada kai ke yayi a wancan zamanin.
Wannan kayataccen gida dana bata lokaci wajen wassafo muku, mallaki ne na Professor Dr. Hamza Dakata, wanda ke rike da mukamin (parmanent secretary) na ofishin shugaban kasa mai ci a wancan lokacin, shekara ta alif dari tara da casa’in da shidda wato (1996).
Matar gidan, Hajiya Maryam Hamza Dakata, na zaune cikin daya daga cikin luntsuma-luntsuman kujerun da suka kawata falon. Saboda girmansa kujeru saiti uku ya ci ba tare da kowanne seti ya san da zaman dan uwansa ba. Wato a kowacce kusurwa ta falon akwai setin kujeru kala daban da ‘yan uwansu, haka kilishin da ke shimfide a kasansu (carpet) kala daya yake da setin kowanne setin kujera. Sai aka yi labulaye mai ratsi da kalar dukkan kujerun falon.
Idan ka dubi Hajiya Maryam sai ka ji kamar ka sace ta ka gudu sabida kyau da iya ado. Kai ba za ka ce ita ta haifi yara maza guda hudu da ke zagaye da ita tana koya musu aikin makaranta na yi a gida ba (homework). Kallo daya za ka yi wa yaran ya ishe ka kimanta irin hutun rayuwar da suke ciki su da iyayensu, domin dukkaninsu girmansu ya haura shekarunsu.
Babban, wanda ke amsa sunan Abdul’azeez shekarunsa goma sha uku. Yana amsa sunan “Yaya Azeez” daga bakin kannensa. Sai mai bi masa Isma’el da kannen sa biyu ke kira “Ishma” shekarunsa tara. Daga Isma’el sai Usman shi kuma shekarunsa bakwai a duniya tsiransu babu yawa. Hajiya Maryam ta jima bata kara haihuwa ba bayan haihuwar Usman, sannan ta haifi autan ta Haleem wanda har yanzu bai kai ga shiga makaranta ba, dan shekaru uku.
Lokaci zuwa lokaci Hajiya Maryam kan daga kai ta dubi agogon bango, sai kuma ta sauke ta ci gaba da nunawa Azeez aikin makarantarsa (home work), da gani za ka fahimci dakon wani abu take (jira); tana tsammanin shigowar maigidanta ne daga yanzu zuwa kowanne lokaci. Ya ci a ce ya shigo gida tun dazu shi da ba ya kai wa magriba a (office) in ba da wani kwakkwaran dalili ba. Idan hakan ta faru ma zai yi waya ya gaya mata. Amma yau shiru.
Usman ya sosa mata inda ke mata kaikayi da cewa.
“Wai Mammah ina Daddy ya je ne har yanzu bai dawo ba? It’s almost past eight fa (takwas har ta wuce)”.
Hajiya Maryam ta yi ajiyar zuciya, “Kada ku damu. Bari in lalubo shi a waya, watakila aiki ne ya tsare shi”.
Ta shiga latsa wayar hannunta, wadda a lokacin (mobile) ake kiranta, rike ta sai masu kambun susa, ta kai a kunnenta, amma har ta yi burarinta ta gama Daddyn bai dauka ba. Ta kira ya kai sau goma ba amsa. Cikin danne tashin hankalinta ta dubi ‘ya’yan nata wadanda suka tsura mata ido kamar a kwayar idonta suke son gano mahaifin nasu. Sai ta rasa me za ta ce musu, duk suka yi shiru.
Daidai sanda aka murda kofar falon aka shigo, duk suka maida hankalinsu ga kofar don a zatonsu Daddy din ne. Maimakon shi din, mai aikinsu ce, Jamila.
Ta shigo cikin ladabi ta tsuguna a gaban uwargijiyarta.
“Mammah abincin dare ya kammala, na shirya komai a (dining)”.
Mammah ta nisa, “To sannu da aiki Jamila, muna jiran shigowar Daddy ne kafin mu ci abincin”.
Jamila ta ci gaba da durkuson bata tashi ba kanta a sunkuye. Mammah ta lura akwai magana a bakin Jamila.
Cikin kulawa ta ce “Ya aka yi ne kuma Jamila?”
Jamila ta muskuta cikin matsanancin ladabi, kanta a kasa.
“Na zo in yi muku sallama ne, gobe zan koma gida kauye”.
Gaban Hajiya Maryam ya fadi, don tana jin dadin zama da Jamila, yarinyar na da hankali, tsabta da ladabi. Ta yi masu aiki kala-kala daga garuruwa daban-daban, amma ba ta taba yin mai aikin da ta ke jin dadinta irin Jamila ba. Shekarunsu uku kenan tare tun haihuwar Halim aka samo mata ita daga kauyen Kura. A tsayin shekarun nan ba ta taba yi mata wani abu da ba ta ji dadinshi ba. Yi-na-yi-bari-na-bari da alheri da kyautatawa ke shiga tsakaninsu. Ta daure ta ce.
“Lafiya za ki tafi gida? A sanina lokacin zuwanki gida bai yi ba? Cewa nake yau watanki daya da dawowa?”
Jamila cikin matsananciyar kunya ta ke magana.
“Ki yi hakuri Mammah (yadda take ji ‘ya’yan ta na kiranta), ni ma ba da son raina zan barku ba. Domin hakika ku mutane ne na kwarai wadanda suka san hakkin dan Adam da darajar da Allah ya yi masa komai kaskancinsa. A wannan zuwan nawa gida na samu miji da muka daidaita, iyayenmu suka yi magana da juna. Na yi wa iyayena alkawarin bayan wata daya zan dawo a daura mana aure. Tunda na dawo nake so na fada miki kunya ta hanani sai yanzu da lokacin ya zo”.
Jikin Hajiya Maryam ya yi sanyi. Tabbas duk son da ta ke mata ba za ta hana ta yin aure ba kam a kan neman duniya. Murya a sanyaye ta ce.
“Toh Jamila. Na yi miki murna. Allah ya sanya alkhairi, Ya kuma hada mu da alheri. Jira ni ina zuwa”.
Ta mike ta yi dakinta ta dauko rafar kudi a jakarta, turamen atamfofi Holland guda uku da mayafai da takalma da jaka uku-uku ta zo ta zubewa Jamila. “Ga kudin aikinki na wata uku a gaba, wannan kuma gudumawata ce Allah ya sanya alkhairi, Ya bada zaman lafiya”.
Idanun Jamila suka cicciko da kwallah, ta sa hannu biyu ta karba tana godiya. Ta tashi ta koma sassansu na ma’aikatan gidan.
AbdulAzeez ya dago kai daga kan littafinsa, duk maganganun da suke yana jinsu amma bai dago ba sai yanzu da Jamila ta bar falon, yace,
“Mammah garinsu za ta koma?”
“Eh, aure za a yi mata Abdul’aziz”.
Usman ya ce, “Ba za ta dawo ba?”
Nan ma ta daga musu kai, ta ce, “Eh”.
Damuwa ta nuna sosai a fuskar yaran, don sun shaku da Jamila. Tana kula da su sosai, tana jansu a jiki.
Haleem ya ce, “To Mammah, wa zai dinga goya ni?”
Ta yi murmushi, “ai ka wuce goyo yanzu Haleem. Kada ku damu, za mu samu wata. Addu’a za ku yi Allah ya sa mu samu mai irin halayenta”.
Suka daga hannu duka suka ce, “Ameen”.
Isma’el da bai yi magana ba, sai yanzu yayi dogon nazari irin na yara masu tsinkaye sannan ya ce.
“To yanzu Mammah wa zai dinga yi miki wanke-wanke da sauran ayyukan data ke yi?”
Ta yi murmushi, “Ni zan yi da kaina Isma’el, kuma ba da jimawa ba za mu samu wata...........”
Ba ta kai ga rufe bakinta ba suka ji horn din motar Daddy. Ai a guje, in ba ka yi ba ni wuri, Maryam da yaranta ba ga uwar ba, ba ga ‘ya’yan ba, kowanne so yake ya fara isa ga Daddyn. A tare suka isa daidai lokacin da direbansa ya yi fakin a babbar kofar shiga falon, wadda ta kasance ta gilashi (sliding door) suka taro shi zuwa cikin falon don ta nan yake shiga, sauran mutane kuwa sai dai su zagaya su shiga ta kofar kicin.
Bakinsa kamar zai tsage don fara’a, ya bude hannuwa suka shige ciki har uwar. Da alama cikin farin ciki yake mara misaltuwa. Da alama akwai soyayya da shakuwa mai yawa a tsakanin wannan family. A haka suka shiga falon yana dauke da Haleem. Sai jero masa tambayoyi Isma’eel da Usman suke yi na ina ya je yau bai dawo da wuri ba? Shi da ma babban wato Abdul’aziz magana ba ta dame shi ba, uban ya kamo hannunsa suka zauna tare cikin kujera,
“Come on Babban Yaya. Wa ya taba min kai na ga kamar kana fushi?”
Abdul’aziz ya kwantar da kai a kirjin Babansa cikin damuwa.
“Daddy ka yi dare ne duk mun damu. You know we care for you too much (ka san mun damu da kai sosai)”.
Yana shafa lallausar sumar kan yaron, yana murmushi ya ce, “In ka ji shiru alheri kenan. Amma ba zan fadi wannan albishir din da ke bakina ba sai dukkanmu mun ci abinci mun koshi kada farin ciki ya hana ku cin abinci”. Ya fada tare da mikewa rike da hannun Abdul’aziz din. Da, mafi soyuwa a zuciyarsa, cikin ‘ya’ya maza hudu da Allah ya ba shi.
Gabadaya suka hau kujerunsu na cin abinci suka fara ci cikin nutsuwa. Sai da suka kammala suka yi hamdala suka koma bisa kujerun falon, sannan Daddy ya dubesu daya bayan daya yana murmushi ya ce.
“Tun safe muna dakin (meeting) da (President), Ambassadan kasar Saudiyya ne ya yi (retire) kuma cikin ikon Allah ni aka baiwa kujerarsa. So ku soma shiri, nan da sati biyu kacal za mu koma birnin Jeddah da zama”.
Usman da Isma’el suka soma tsalle, amma abin mamaki ban da Abdul’aziz. Shi kamar ma damuwa ya shiga. Daddy na lura da shi ya kara jawo shi jikinsa, “Ya ya dai Azeez? Kai ban ga kana murna ba”.
Ya yamutsa fuska kadan, kana a hankali ya ce, “Daddy I love Nigeria. Bana son matsawa daga cikinta zuwa kowacce kasa. Na fi son in girma, in rayu, in yi karatu a cikinta in tallafe ta watarana. Kowa ya samu ci gaba, sai ya gudu daga cikinta. (I want to be exempted) daga masu yin hakan”.
Daddyn ya tsura masa ido yana al’ajabi, wai yaro dan shekaru goma sha uku ke wannan maganar. Shi ne da wannan ‘patriotism’ din (kishin kasa). Ya san kuma abin da ya fada haka yake har zuciyarsa. Shi din kuma ya kasance wani mutum mai girmama ra’ayin ‘ya’yansa. Ya tattara hankalinsa waje guda wajen baiwa yaron amsa.
“Ba za ka iya taimaka wa kasarmu ba Abdul’azeez sai ka karantu ka gogu kayi koyi da kasashen da suka riga suka gyara nasu kasashen suka ci gaba. Sannan komawarmu kasar Saudiyyah falala ce mai yawa Azeez. Ga ka kullum kusa da dakin Allah ka je ka roki duk abinda kake so. Ga makarantu na musulunci ba irin namu ba. Ga abinci mai albarka ga kwanciyar hankali. Abubuwan alherin suna da yawa, kuma ai ba dauwama za mu yi ba a can zama ne na kayyadadden lokaci. Ka saki ranka ka ji? Mu je mu gina sabuwar rayuwa”. Ya fada yana bubbuga kafadun yaron.
Ga mamakinsa budar bakin Abdul’azeez sai cewa ya yi, “Daddy I’m okey with my life here (ina jin dadin rayuwa ta a nan). Ina son school dina (Regent). Bana so in rabu da ita da abokaina, tunda dama (boarding) nake yi sai in dinga zuwa muku hutu in an yi hutu karshen kowanne ‘term’.
Hajiya Maryam da tun dazu ba ta saka musu baki ba, sai yanzu ta ce, “Abdul’aziz kafiyarka ta yi yawa, duk abin da Daddy ya gaya maka ba ka amince ba ko me?”
“Na amince Mammah. Abin da ya fada, haka ne. Babu kasa irin Saudiyyah. But I love my country, Nigeria (ina son kasa ta Najeriya) anan nake so in rayu”.
Iyayen duka suka dube shi baki a sake. Daddy ya sanyaya murya,
“Za ka iya rayuwa babu mu Abdul’azeez?”
“Zan iya Daddy, na ce maka ai duk hutu ina tare da ku ko in tafi Kano. I just want to live and study in Nigeria (kawai ina so in rayu, in yi karatu a Nigeria ne).”
Ya gyada kai cikin girmama ra’ayin yaron nasa.
“Shi kenan Abdul’azeez tunda haka ka zaba. Mu ma mun amince”.
Sai a lokacin suka ga murmushin Abdul’azeez.
****
Tun a cikin satin Hajiya Maryam ta soma shirin tafiyarsu Jeddah. Damuwarta daya rashin mai aiki. Jamila ta tafi tun a washegarin ranar da suka yi magana. Ta so a ce da Jamila za su yi wannan hijira mai albarka, ita ma ta samu sauyin rayuwa. Ga shi aure ya raba su yadda ba ta da damar sake zama da ita har abada.
Tana zaune a falonta ta kira aminiyarta a nan cikin Abuja, Hajiya Halima. Mijinta (controller) ne na (Custom) ita ta samo mata Jamila. Ta gaya mata tana son mai aiki da gaggawa za ta tafi da ita Saudiyyah an yi wa Baban Halim Ambassada.
Hajiya Halima ta taya ta murna, ta kuma ce babu lokacin da za a je kauye a nemo, amma ga tata nan Habiba jiya-jiyannan aka kawo mata ita. Su tafi ita za ta nemi wata, ta turo direba ya dauke ta. Hajiya Maryam ta yi wa kawar tata godiya sosai suka yi sallama, ta ce ga direban nan tafe yanzun nan.
Alkasim direban Hajiya ya je ya dauko Habiba. Matashiya ce kyakkyawa, amma ba yarinya ba ce, za ta yi shekaru ashirin da tara Haka. Sosai ta yi wa Hajiya Maryam, don da alamu za ta yi tsafta da kuzari. Tun a ranar ko ta soma birge Hajiya Maryam da aiki kamar janareta. Ta gayawa Habiban maganar tafiya da zatayi da ita Saudiyyah ko zata je gida ta fada ta kuma yi sallama amma sai Habiba tace ita bata da kowa, ko sunan garin su ta omanta. Daga nan har birnin Sin su tafi ita bata da matsala. Yakamata ace Hajiya Maryam tayi dogon nazari akan hakan amma da yake a bukace take da neman mai aikin sai bata zurfafa maganar ba, tayi tunanin wani bacin ran ne ya fito da ita daga gida shiyasa tace hakan, tasa aka kai ta aka yi mata fasfo aka hada da nasu Daddy ya karba.
Dr. Hamza bai fiya son wadannan ‘yan aiki da maidakinsa ke kwasa ba, ta kan gaya masa ba yadda za ta yi ne ayyukan gidan sun fi karfinta bazata iya rayuwa babu su ba, amma ba sa yi mata girkin da zai ci ita ta ke yin abunta. Hajiya Maryam ta yi murna da samun Habiba sosai da alama tasu za ta zo daya, don duk halayen Jamila tana da su har ma ta zartata wasu abubuwan.
****


ASALINSU
Gidan marigayi Malam Abdullahi Dakata ba boyayye ba ne a unguwar Dakata da ke cikin jihar Kano. Gida ne da ake yi wa kallon babban gida sabida yadda ya wadata ‘ya’yansa maza da mata da ilim addini da na zamani. Sana’ar Malam Abdullahi har ya bar duniya sayar da manya da kananan shaddoji wadanda yake shigo da su daga Cotano ya zuba a babban shagonsa da ke kantin Kwari. Da wannan sana’a ya riki iyalansa, ya ba su tarbiyya mai inganci da ilmin da ake alfahari da su a yanzu. Malam Abdullahi ya dade da rasuwa a lokacin da ‘ya’yansa suka kawo karfi. Allah bai yi zai ci gajiyar ilmin ‘ya’yansa ba, wadanda duk sun fito daga cikin mace daya ne, Inna Rabi. Ya rasu ya bar ‘ya’ya hudu, maza uku da mace daya.
Babban dan Malam Abdullahi shi ne Atiku, wanda ahalin gidan ke kira Baffa Attiku, mai bin sa Adda Hafsatu, sai Abdulkarim Dakata, da autansu Idris Abdullahi Dakata. Allah ya karbi ran Inna Rabi Idris na da shekaru ashirin da biyar.
Baffa Atiku wanda ya zamo shi ne babba a zuri’ar Malam Abdullahi shi ne mahaifi ga Dr. Hamza da suka haifa da maidakinsa Inna Ramatu. Sun manyanta, amma ba za a kira su tsofaffi ba. Dr. Hamza kadai suka haifa, mai bin Baffa Atiku a maza wato Abdulkarim Dakata a yanzu haka Sanata ne mai wakiltar Kano ta tsakiya, yana Abuja da iyalansa, Adda Hafsatu ‘ya ta biyu ga Malam Abdullahi ita ce, mahaifiya ga Hajiya Maryam, Hajiya Maryam din ce babbar ‘yarta sai kannenta hudu mata Anty Luba, Anty Furairah, Anty Mariya, Aunty Murja da autan Adda Ibrahima wanda ke karatunsa yanzu a jami’ar Ahmadu Bello mataki na farko, yana karantar tsimi da tanadi. Lubabatu, Furairah, Mariya da Murja duk an aurar da su bayan kammala karatun sakandire, su da nasu iyalin duk a Kano suke zaune.
Autan Malam Abdullahi wato Idris Dakata, yana karatun likitanci ne a jami’ar Maiduguri, bai kai ga yin auren fari ba, yana amsa sunan Uncle Idris daga bakin yara da manyan wannan zuri’a mai albarka.
Adda Hafsatu mahaifiyarsu Hajiya Maryam ta yi aikin gwamnati na tsayin shekaru talatin. A yanzu ta yi ritaya bayan rasuwar mijinta ta zauna a gida ta rungume ‘ya’yanta kasancewar maigidanta Alhaji Hassan ya jima da rasuwa.
Kenan Hajiya Maryam da Dr. Hamza ‘yan uwan juna ne, ‘yar mace da Dan namiji suke. Sun tashi gida daya, sun samu tarbiyya iri daya. Aurensu ba na hadin zumunci ba ne, shi ya ce yana sonta tun tana karama. Amma ba wanda suka yi wa auren zumunci bayansu cikin zuri’arsu, kowanne daga waje yake kawo abokin rayuwarsa in ka cire Hamza da Maryam.
An yi musu aure tun kafin ta kammala digirinta na farko, shi kuma yana koyarwa a jami’ar Bayero. Ya samu muqamin Farfesa a shekarun kuruciyarsa saboda hazaqarsa wajen rubuce-rubuce da wallafe-wallafe a fanninsa na (political science). Ya rike muqaman gwamnati guda uku a Federal Government kafin Allah ya kai shi ga samun matsayin (parmanent secretary) na ofishin shugaban kasa. Wanda abokin mahaifinsa ne tun na kuruciya ya dauki mukamin ya bashi. Suka tattara suka koma Abuja da iyalinsa.
Gidan Mal. Abdullahi ya kara yin fice a unguwar Dakata ko don mukaman dan sa da babban jikansa; Parmanent Secretary Hamza da babban dan siyasa Abdulkarim, wadanda ba dare ba rana duk sanda suka zo garin Kano taimako suke yi wa al’ummar unguwar su da kewayenta ba na wasa ba.
A yanzu haka ciki gidan marigayi Malam Abdullahi babban dansa Baffa Atiku da maidakinsa Hajiya Ramatu mahaifan Dr. Hamza ne a ciki, sai Idris wanda in ya zo hutu gida a karshen kowanne zangon karatu dakinsa yana nan a soro na biyu. Adda Hafsatu ma bayan an sayar da gidan gadon ‘ya’yanta su Hajiya Maryam an raba musu gadon mahaifinsu, nan gidan ta dawo ta share dakin mahaifiyarsu marigayiya Inna Rabi ta yi zamanta kusa da dan uwanta Baffa Atiku da maidakinsa Ramatu, suna zamansu lafiya. Babu yaro gabansu sai autan Adda Ibrahim wanda ya fara karatun jami’a. Duk da haka ba ka raba dakin Adda da yara haka dakin Inna Ramatu sabida ‘ya’yan su Luba, Mariya, Furairah da Murja duk hutu suna gidan ko ranar da ba makaranta. Adda Hafsatu na baiwa Inna Ramatu girma yadda ya kamata kasancewarta matar Yayanta kuma suruka a gare ta. Amma wani zubin sukan manta surkuntar su yi ta harkar arzikinsu da kula da jikokinsu. Inna Ramatu ta rike girmanta ta hada shi da kyautatawa. Don haka ake zama na aminci da kwanciyar hankali da wadata a gidan marigayi Abdullahi Dakata. ‘Ya’yansu sun wadata su da komi na rayuwa, sun dauke duk wani nauyi na rayuwar iyayen nan nasu bakidaya. Dr. Hamza ke dauke da nauyin karatun Uncle Idris da
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment