Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[7/21, 10:52 PM] Mummyn Yara: *RAYUWAR MACE*
_Hafsat Rano_
Free Page (2)

***
A kofar dakin Umma ta tarar dashi, ta nuna masa falon da hannu sannan ta wuce falon Abban. Yana tsaye yana kai kawo a tsakiyar dakin tana shigowa ya bi ta da ido dan yasan abinda ya kawo ta.

"Alhaji.."

Da sauri ya dakatar da

"Maganar ba zata chanja komai ba, muyi mata addu'a kawai bamu san me Allah ya tsara ba."

"Amma dai hakkin mu ne mu nema mata miji na gari, wanda muka yarda da addininsa da nagartar sa, amma Adam fa? Ya cika wannan sharadin?"

Zama yayi a nutse bayan ya cire babbar rigar jikin sa da hula sannan yace

" Mu bar wa Allah komai, ya fimu sanin komai akai, ba zan taba iya hana Yaya Asabe abinda take so ba, ba kuma zan taba kin danta wai don munin halin sa, ni ma ban fi karfin Allah ya jarraba ni da irin sa ba."

" Yanzu shikenan muna ji muna gani saboda kawai muna so yar mu tayi aure za muyi mata zabin tumun dare!?"

" Idan da rabo sai kiga ta dalilin ta Allah ya shirye shi, sai tayi kokari ta sauya masa DABI'AR sa tunda mace tana da matukar tasiri a rayuwar namiji."

Wani abu ne yazo ya tokare wuyan Umman, bata tare da masu ganin cewa mace zata iya gyara wa namiji Hali bayan ta same shi da girman sa, kawai idan kaji an ce haka toh fa lallai an shirya zalintar macen. Tana tsaye ya zo zai fita daga falon, ya kalle ta yana gyara hular kansa sannan yace

" Karki nuna mata wani abu da zai sa taki auren, muyi mata addu'a kawai dan babu abinda zai sa a fasa sai dai idan Yaya Asaben da kanta tace sun fasa, amma muddin bata ce ba, toh babu makawa sai anyi."

Kasa tanka masa tayi har ya fice, ta zauna dabas a wajen tana jin da gaske an cuce ta, ta kuma tabbatar da biyu Hajiya Maman tayi dan ta nuna mata ta isa da Abban da ma duk wani abu da ya dangance shi.
Da k'yar ta mike daga wajen ta fito bayan ta jawo masa falon, ta isa dakin Asma'un ta tarar da ita tana sallar azahar, sai kawai ta wuce dakin ta domin ta gabatar da tata sallar.
Tana idarwa Asma'un na shigowa, bata ce komai ba ta hau gadon umman ta kwanta rigingine tayi shiru tana tuna abinda ya faru bayan taje wajen sa. Kadan ya rage be rungume ta ba da ta shigo, ya hau surutan da ta kasa gane komai akai, haka ya karaci babatunsa ya tafi bayan yace mata zai dawo da daddare.

"Umma wai me ya faru?"

"Aina da?"

"Ya Adam, ban gane ba wallahi. "

" Kinsan kowanne bawa da yadda Allah yake kaddaro masa rayuwar sa, sannan duk dan ta yayi ma iyayen sa biyayya toh fa ba zai taba tabewa ba, mahaifin ki ya yanke shawarar aura miki dan uwanki Adam... "

A yadda ta mike daga kwancen sai da ta bawa umman tausayi,

" Umma Adam kuma? "

Kai ta daga mata

" Innalillah wa inna ilaihi rajiun, umma wallahi tallahi bana son shi, bashi da hali me kyau wallahi Umma, wallahi Allah bana son shi dan Allah Abba yayi hakuri. "

Duk ta gigice ta rikice, hawayen da Umman take ta rikewa ne suka soma saukowa tayi saurin maida su tana karfafar kanta.

" Menene haka? Me kike haka? Ashe ba zaki iya yiwa mahaifin ki biyayya ba?"

" Umma Adam fa? Umma dan Allah kice yayi hakuri wallahi ba zan iya ba. "

Wani kallo umma ta watsa mata

" Ki nutsu ki saurare ni, kinsan waye mahaifin ku, kin kuma san wacece Hajiya Mama a wajen sa, kukan ki da magiyar ki ba zasu taba sauya masa abinda yayi niyya ba sai dai idan su suka ce sun fasa, dan haka ba ruwana wallahi, ba zan bari ki hadu da fushin mahaifin ki ba, kiyi masa biyayya ku rabu lafiya nima na rabu da nawa lafiya, kuma in sha Allah zaki ga ribar biyayya. "

Daga haka bata kuma cewa komai ba, ta fice ta bar ta a dakin tana jin yadda take kuka wiwi, wayar ta ta dauka ta kira babbar 'yarta hadiza ta sanar da ita komai sannan ta kira sauran yan uwan Asma'un da sukayi aure, kafin kace me sai gasu a gidan gaba dayan su, duk kansu kowa be ji dadin labarin ba, amma kuma sai Umma ta hana su fuskar da zasu kushe abun dan ta riga tasan halin Abban su sarai zai iya saba musu akan maganar, sannan tunda tasan babu fashi gwara kawai tayi kokarin ganin basu bawa Asma'un kofar da zata bijire wa mahaifin nasu ba.
Lallashi da ban baki suka dinga yi mata har suka samu ta dan nutsu amma bata bar kuka ba. A haka Abban da yan mazan suka dawo suka tarar dasu, Abban ya danyi fadan dalilin zuwan su haka sai suka ce ai zuwa sukayi su gaishe su, ya ji su ne kawai amma ya riga ya san umma ce ta kira su akan maganar.
Bayan sallar magriba Yaya hadiza ta samu Abban da maganar, ya nuna mata babu fashi su dai kawai su tayata da addu'a, haka ta baro dakin jikin ta a sanyaye bayan ta roke shi ya barta su tafi da Asma'un ya amince amma iya sati daya kawai dan sati uku ya saka bikin tunda babu wani shiri da za'a yi dan kowanne bangare a shirye suke dama.
Mijinta ne yazo ya dauke su wajen tara, a hanya take bashi labarin abinda ya faru, ya dan juyo yana sake bawa Asma'un baki yana tsokanar ta, ta dan yi murmushi kawai amma ita kadai ta san yadda take ji a ranta.

***Washegari bayan an makaranta sun tafi umma ta shirya Abbati ya kaita chan Mandawari gidan su ta samu Hajiyar su da maganar auren Asma'un da lokacin da Abban ya saka, duk basu ji dadin hukuncin Abban ba, da kuma rashin bawa Asma'un dama ta fadi ra'ayin ta dan kawai ana ganin kamar ko an barta ma ba wani ne zaizo neman auren nata ba.

"Toh yanzu dai ya riga ya gama yanke hukunci, namu kawai shine mu bi ta da addu'a, Allah ya basu zaman lafiya ya kade fitina."

Hajiyan tace bayan sun gama magana da Umman.

"Amin, ni na rasa ta ina zan fara ba, sai a aika su miko su sanar da su umman Asiya da su Aunty Falila da gidajen su kawo muntari."

"Eh yana shigowa zan aika shi, sati uku kamar yau ne ai, duk sai a sanar da dangi, Allah ya basu zaman lafiya."

"Amin." Tace a sanyaye.

***Bangaren gidan Hajiya Mama shiri take na ban mamaki, tuni zancen ya karade dangin su bangaren Abban da kuma bangaren Baban su Adam din, mutane da yawa suna tausayawa Asma'un saboda dai sam babu hali na nagarta da zai saka ka dauki yar ka, ka bawa Adam din, ciki kuwa har da yan uwa makusantan su Abban dan wani kawun su sai da yayi wa Abban magana kasancewar kowa ya riga ya san nutsuwa da kamala irin ta Asma'un dan kaf yan uwanta babu kamarta, duk da su ma basu da matsala amma kuma ita din daban ce, magana da koman ta a nutse take yin sa, bata da rawar kan yan mata dan ba zaka taba tunanin ta je jami'a ba ma, bata dauki duniyar da zafi ba haka kuma bata da son kyale kyalen duniya. Haka ya saka mutane suke ganin kamar akwai zalunci a dauke ta a hada ta da Adam wanda ake tunani hatta giya yana sha bayan mugun halin sa na neman mata da yayi shura akai, amma yadda Abban yayi biris da duk wannan ya saka kowa ya shafa ma kansa lafiya aka shiga bin su da addu'ar fatan alkhairi.

Zuwan Adam din uku tare da zugar abokai baya samun ta karshe dai ranar da yazo ya tarar da Abban nan yake gayawa Abba ai yazo baya samun ta, nan fa Abban ya shiga dakin Umma yayi ta mata fad'a sannan ya dauki waya ya kira Yaya hadizan yace ya fasa sati dayan gobe gobe ta dawo gida. Jiki a sanyaye ta amsa masa da toh, bayan ya kashe sai kuma yaga kamar ya zafafa da yawa, sai ya sake kiranta yace ta kyale ta zuwa satin amma zatayi bako gashi nan zaizo yanzo. Nan ma dai toh din tace ya kashe ya koma ya samu Adam din ya yi masa kwantancen gidan Yaya Hadizan sannan ya bashi number wayar Asma'un da ta Yaya Hadizan yace idan yaje ya kira. Bakin sa tamkar gonar auduga ya karba suka dauki hanyar gidan Yaya Hadizan baka jin komai a motar sa ife ifen su irin ma gogaggun yan duniya, burin sa kawai ya nuna musu kalar matar da zai aura ya san ba karamin taya shi farin ciki zasuyi ba, hutu kam zai huta a wajen sosai, yadda yake ji ma kamar sati ukun yayi masa mugun yawa amma haka zai hakura ya lallaba ya cigaba da maneji da su Fido kafin ranar da zai gwangwaje.

Gidan bashi da wahala suna zuwa suka gane, ya dauko wayar sa zai yi kira sai kuma ya fasa ya fito da kafar sa ya karasa gate din gidan ya kwankwasa da dan karfi saboda karar Gen, be jima yana bugun ba mijin Ya Hadizan yazo ya bud'e masa, ya bashi hannu suka gaisa sannan yace ya shigo ciki

"Owk tare muke da guys suna mota bari nayi musu magana."

"Owk." Yace ya wuce ciki ya bar musu kofar a bude, ya samu falon ba kowa an gama jera ruwa da lemo akan dan centre table din, ya dauki remote ya rage volume din tv daidai lokacin da suke shigowa, su hudu ne dukkan su sanye da kananan kaya daya ma daga ciki wandon sa da kad'an yafi guiwar sa, askin kansu kuwa kai kace gobara akayi a wani gefen kan nasu babu kyaun gani, hannu ya basu suka gaisa sannan ya wuce ciki cike da al'ajabin dalilin da zai sa Abba amincewa bayan ya san waye Abban da nagartar sa.
Da k'yar da ban baki Ya Hadiza ta sakata fita dan bata son fushin Abba akanta zai iya hadasu daga ita har Asma'un yayi musu tatas. Hijabi ne burmeme a jikinta har kasa, ta dauko facemasks ta dora akan fuskar ta sannan ta tura kofar falon kanta a k'asa ta shiga. Wata iriyar kunya ce ta kama Adam din da ya ganta da shigar, shi da yaso suga kalar matar da zai aura amma shine zata je ta burma uban hijabi kamar wadda zata zaman makoki.
Dariyar shakiyanci suka fara yi suna kallon sa, ya hade rai sosai yaki kallon ta, a k'asa chan ta rakube ta gaishe su suka amsa cikin dariya dan su basu ga abinda yake ta musu kozozoto akai ba.

"Our wife kina lafiya?"

Daya daga ciki yace yana kunshe dariyar sa.

"Lafiya lou."

Ta amsa a takaice kanta still a k'asa ba zata iya cewa ga adadin su bama balle kamar su, uban gayyar kawai ta gani sanda ta shigo taga ya wani diririce kamar wanda yayi karya aka gano shi, bata kuma kallon sa ba ta zauna. Tana jin su suna ta shakiyan ci suna tsokanarshi amma ko uffan be ce musu ba, sai da suka gama suka fita, ya taso yazo daidai kanta, ya saka hannu ya fuzge facemask din, ta kalle shi da sauri

"Wannan wane irin wulakanci ne na kawo guys dina su ga matar da zan aura shine zaki sako wannan buhun sannan ki wani toshe fuskar ki dan tsabar iskanci."

"Kamar ya? Me yasa zasu ganni ko su din muharramaina ne?"

"Shit! A 21th century dama akwai mata villagers irin ki? Ke baki san civilization ba? Ko baki ga alamar mijin da zaki aura wayayye bane?"

"Ban san duk wannan ba, abu daya na sani shine abinda addinin musulunci ya koyar dani."

Ta murguda masa baki tana jan facemask din zata mayar ya fuzge da karfi sannan ya buge mata baki

"Karki yarda kice zaki min rashin kunya wallahi, dan zan taimaka miki na aure ki, naga ma ai neman kai ake dake na taimaka nace zan aura, so watch your mouth wallahi, kuma na sake zuwa kika zumbulo min irin wannan Hijab din sai na cire shi ta karfi wallahi. Nonsense!"

Ya juya da sauri ya bar falon har da buga kofa, kasa ko da kwakkwaran motsi tayi, bakin ta da ya buge na mata zafi sosai, sai kuma maganganun sa da suka yi mata mugun ciwo, da gaske taimaka mata yayi? Kuma neman kai ake da ita shine ya tausaya mata zai aure ta. Wani kuka ne yazo mata, ta gwammace ta mutu ba aure akan ta auri mutum irin Adam, jinkirin aure ai ba shine zai saka mutum yayi wrong choice ba, gwara ma ace ka aura baka sani ba, amma wannan kowa ya san halin sa.
Ta jima a wajen tana kuka sosai, kafin ta tashi da k'yar bayan ta goge hawayen ta shiga ciki.


RAYUWAR MACE COMMENT GROUP LINK. Meson comment group sai ya shiga link din nan

https://chat.whatsapp.com/EcH31iWkbGnD9DWC8SsuLR










_ZAFAFA BIYAR!! ZAFAFA BIYAR!! ZAFAFA BIYAR!!_

_ASSALAMU ALAIKUN MASOYA MAKARANTA LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

_BARKAN MU DA SALLAH, ALLAH YA MAIMAITA MANA, AAMIN_

_KU MATSO KUSA, ZAFAFAN NAKU SUN SAKE ZABUROWA DA ZAFIN SU KAMAR YADDA KUKE KAUNAR SU._

_WANNAN KARON MA SUNZO DA WANI SALO MAI NUTSUWA HADI DA ZAFAFAN DARUSSA NA RAYUWA KANA DA FADAKARWA AKAN RAYUWAR YAU.. BANGAREN KOGIN KAUNA KUWA BAA MAGANA. DOMIN WANNAN KARON SUN SAKE TAHOWA DA ZAFAFAN KAUNANNAKI MASU NARKE ZUCIYOYI._ WANDA ZASU ZO MUKU IN SHA ALLAH

_KADA KU MANTA ZAFAFAN NAKU DE SUNE KAMAR HAKA_

_SAFIYYAH HUGUMA: TAZO DA NATA SALON MAI SUNA: *KUFAR WUTA*_πŸ₯°

_BILLYN ABDULL TA ZABURO DA WANI TAKEN MAI SUNA: *BAQAR INUWA.*_😍

_MAMUH GEE ITAMA WANNAN KARON TA SAKE TAHOWA DA: *NOORUL-ALB*_πŸ₯°

_HAFSAT RANO WANNAN KARON TAZO DA NATA RUBUTUN MAI SUNA: *RAYUWAR MACE*_❣️

_NANA HAFSATU (MSS XOXO) WANNAN SALON MA TAZO DA : *MASARAUTA*_😍

***_DUKA LITTAFAI BIYAR ZASU ZO MUKU NE AKAN FARASHIN YADDA SUKE KAMAR KODA YAUSHE_*

_BIYAR : DUBU DAYA (1k)_
_HUDU: 700_
_UKU: 500_
_BIYU: 400_
_DAYA: 300_

_AKWAI TSARIN VVIP SUITES GA MASU SON HAKAN. FARASHIN SU DABAN, DOMIN KARIN BAYANI SE A TUNTUBE MU TA: _

*_ZAKU BIYA KUDINKU ANANπŸ‘‡πŸ‘‡_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biyaπŸ‘‡πŸΌ

*_09032345899_*

*KATIN MTN*πŸ‘‡πŸ‘‡

09166221261

______________________

ZAFAFA BIYAR

VVIP SUITES : 3500 (PC/TA PRIVATE KAI DAYA)

VIP SUITES : 3K (VIA GROUP) A VIP GROUP ZAA DINGA TURAWA.

TWO PAGES DAILY
INSHA ALLAH!! MORNING/NIGHT. SAFE DA DARE.

*_TEAM ZAFAFABIYAR_*
[7/21, 10:52 PM] Mummyn Yara: *RAYUWAR MACE*
_Hafsat Rano_
Free Page (1)

*******
Sanye take da hijabi ruwan toka dogo har kafarta, kanta a k'asa sanda zata wuce ta daidai majalisar mazan wadda kullum sai ta bi ta wajen idan zata je islamiyya tana kuma jin yadda suke maganar ta a kullum idan tazo wucewa, tun abin na damun ta har ta iiik ya dake makale a kafadarta ta jingine ta a wajen ta nufi dakin nasa kirjin ta n I'm aw dukan uku-uku.
Shi kadai ne a dakin daga gani ya gama shiryawa fita zai kasuwa, tun bayan da manyan yayanta maza suka taso sai ya zama ba kasafai Abban yake fita ba sai ya dau kwanaki yana gida yana hutawa.

"Sannu da hutawa Abba.". Tace tana neman waje ta rabe dan ta riga ta san kwanan zancen, ya kwana biyu be mata maganar ba shiyasa ta dan samu nutsuwa a kwanakin

"Yawwa Asma'u, an dawo!?"

"Eh Abba."

"Toh Madallah, sannu da dawowa."

"Yawwa." Ta amsa a ciki tana sake lankwasa kafarta

"Kina jina ko,akwai wani da yazo ko kuwa har yanzu dai?"

"Babu kowa Abba." Tace a sanyaye dan tuni har yar karamar kwalla ta soma taruwa a idon ta.
Shiru Abban yayi be tanka ba, tamkar me tunanin abinda zai ce, bayan wasu yan dakiku ya kalle ta sannan yace

"Ko dai kina korar su ne Ma'u?"

Da sauri ta girgiza kai hawayen da take kokarin rikewa suka sakko. Kura mata ido yayi sosai sannan ya soma magana a nutse cikin son kwantar mata da hankali

Kanta a kasa tana jin Abban har ya kai karshe, cikin nutsuwa tayi masa godiya sannan ta mike ta baro dakin zuciyar ta na sake tsinkewa. Idan tace bata damuwa da rashin aure tayi karya. Tafi kowa son ganin tayi auren kamar yadda yake burin duk wasu iyaye da zarar yar su ta kai munzalin aure! Tabbas tasan duk wasu iyaye da yar su ke gaban su basu da kwanciyar hankali har sai sun ga sun aurar da ita gudun magana da abinda ka iya zuwa ya dawo. Amma kuma abu guda da mutane suka kasa ganewa shine, aure, haihuwa da mutuwa duk lokaci ne mutum be isa ya bawa kansa ba idan ba har lokacin ne yayi ba.
Da yan yatsun hannun ta, take kokarin kirga adadin kannenta da akayi wa aure kamar yadda ta saba a kowanne lokaci, ta riga ta san adadin su sai dai kirgawar na sake tabbatar mata da dole ne mahaifin ta ya dinga tunasar da ita a kowanne lokaci. Duk da shekarun ta ba wai sun ja sosai bane dududu a yanzu ne ta cika shekara ashirin da biyar sai dai yanayin yadda ake musu aure da kananun shekaru ya saka ake ganin ta tsofe a gida. Kannenta biyu da akayi wa aure karshe ,shekarar su sha bakwai dan haka idan zaa hada su da me shekara ashirin da biyar toh fa tabbas dole a dinga yi mata kallon taki aure.
Bata san kalar matsalar ta ba, dan ba zata iya tuna lokacin da wani ya tare ta ko a hanya bane. Ta kan zauna tayi ta tunanin ko dai ba zata taba aure ba a rayuwar ta? Kila bata da rabo shiyasa hakan ta kasance dan bata zargin kowa balle tace ko wani abu akayi mata. Ta bar hakan a matsayin wata jarrabawa ce a gareta wanda take fatan cinye wa.
Daga labulen dakin Ummah tayi, ta leko da kanta tana karantar yanayin ta kafin tace

β€œYa kamata a dora girkin rana lokaci yana tafiya kafin yan makaranta su dawo."

Da toh ta amsa ta mike, ta chanja kayanta zuwa karamar riga da skirt ta saka hula a kanta ta nufi kitchen rik'e da wayar ta a hannu, tana zuwa ta ajiye a saman cabinet ta dora ruwa a babbar tukunya sannan ta fito da kayan miya daga cikin ledar su ta soma gyarawa.
Maganar Abba taji a tsakar gidan nasu yana yiwa Umma magana akan dalilin dawowar sa bayan fitar sa kenan bata jin ma ya bar layin nasu

"H pollo upar fa mun hau titi sai ga kiran Yaya Asabe wai gasu nan zuwa gidan da wata muhimmiyar magana, dole nace ya juyo my dawo dan bansan wacce magana ce ba."

" Gaskiya kam, toh Allah yasa muji alkhair"

Umma tace tana bin bayan sa suka shiga falo. Daina aikin gabanta tayi ranta na sake jagulewa jin Hajiya Mama zata zo, Itace mutum ta farko da abban su yake jin maganarta fiye da ta kowa a duniya, duk wani abu da tace masa toh fa an gama shi, ko da kuwa baya so zai amsa mata. Su biyu iyayen su suka haifa itace kuma take masa role din uwa dan tun yana karami iyayensu suka rasu suka barsu su biyu.
Turo gate din gidan yayi daidai da tsayawar bugun zuciyar ta, ta window din kitchen din da hange su suna shigowa ita da shi yana rik'e da handbag dinta ya makala ta a kafadar sa kamar wani mace. Daf da zasu karaso wajen kitchen din tayi saurin dukawa saboda kar su ganta, tana jin sanda Umma ta fito tana musu sannu da zuwa Abba na tsaye daga bakin falon sa fuskar sa na nuna jin dadin ganin Yayar tashi.

"Sannun ku da zuwa." Abba da Umma suka dinga jera musu har suka dangana da falon sannan ta sauke ajiyar zuciya ta mike ta cigaba da aikin ta a nutse.
Tana cikin aikin wayar ta dake sama tayi kara, ta dauraye hannun ta a sink ta jawota tana kallon wayar, kawarta ce Safiyya take kiranta, ta daga tana saka wayar a handsfree ta ajiye ta suka koma magana.

Maganar da yaji ya sakashi dawowa da baya zuwa kitchen din, ya tsaya daga kofar yana kare wa halittar ta kallo wadda take sanye da dogon skirt da riga. Motsi taji, ta waigo sai kawai taga mutum tsaye a bayan ta har ya iso daf da ita yana kokarin taba ta.

"Lafiya!?" Tace tana matsawa da sauri har tana neman gogar tukunyar miyar dake saman gas din.

"Fine Baby, kin hadu." Yace cikin muryar sa ta yan duniya, kallon sa tayi daga sama har kasa, zuwa kunnensa dake sanye da dankunne sai wani jibgegen takalmi da yake jibge a kafar sa, wandon sa irin wanda yake a yagen nan ne ta tsakiya sai askin kansa da ya kara nuna mata ainihin shi din waye.
Yaya Adam ne, tilon namiji a yaran Hajiya Mama kuma shalelenta, tun suna yara Allah be hada jinin ta da nasa ba dan ko haduwa akayi sai yaci
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6

Please Login or Register in order to submit comment