Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[16/06, 9:00 pm] JAKADIYAR AREWA:        ƘANWAR MAZA
                

Na Aisha Adam (Ayshercool)

MIKIYA WRITER'S ASSOCIATES





https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels

Ku yi subscribing  YouTube channel ɗin
@Cool Hausa Novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro.
Ku yi following ɗina a arewabooks a kan account ɗina na ayshercool7724
Ko watpad Ayshercool7724 kowanne a cikin manhajojin za ku iya samun litattaiafaina da na yi a baya, da wanda nake yi a yanzu na gode.


*Ina fatan yadda na fara lafiya, Allah ya sanya na gama lafiya. Ƙirƙirarren labari ne, idan akwai abin da ya yi kamanceceniya da rayuwar wani ko wata arashi ne*


Page1

Bismillahirahmanirrahim



Daji Ajiyar Allah! La'asar sakaliya, a lokacin da hasken rana ya fara disashewa, ta doshi yamma za ta faɗi, duhun magariba na ƙoƙarin shigowa ya maye ragowar hasken da ranar ta bari kan ta ƙarasa faɗuwa.
Gamayyar bishiyoyi ne, dogaye da da madaidaita, haɗe da ciyayi da ga mabanbantan tushe, suka haɗu suka yiwa dajin ƙawanya. Zai iya kasancewa abin sha'awa ga wanda ya zo yawon buɗe ido, idan har bai san mai dajin ya ƙunsa ba.
Ga wanda ya san abin da ya ƙunsa kuwa, zai kasance wuri mafi razani, firgici da kuma tashin hankali.
Gudu take yi a tsakanin rayuwa da mutuwa, tana rungume da wani zani a ƙirjinta, babu yadda za ayi daga nesa ka gane me ta rungumo haka take wannan uban gudun.
Ƙafafuwanta babu takalmi, jikinta babu mayafi, duk da yanayin garin babu zafi, amma laɓɓanta sun bushe tamkar dutsen da ya shekara ruwa bai zuba a kansa ba, babu alamar tana gane in da take jefa ƙafarta. Duk da wannan mawuyacin hali da take ciki, ta bawa abin da take rungume da shi muhimmanci sosai da sosai.
Cikin rashin sani, tayi karo da wani abu da ita kanta ba ta kai ga tantance ko meye ba, sai dai ƙarfi da nauyin abun ya sanya ta faɗi ƙasa, take ta saki wani marayan kuka, a lokacin da jini ya fara zuba daga ƙeyarta.
Sai a lokacin abin da take rungume da shi ya tsala kuka, saboda firgitar da ya yi shima.
Jariri ne ɗanyen goyo, cibinsa ko faɗuwa bai yi ba, jikinsa duk busashshen ƙazantar haihuwa da alama yaron ya kwan biyu, amma ko ruwa bai taɓa gani ba balle a wanke wannan ƙazantar!.

**************



Cikin garin Kano, unguwar ɗorayi tinga, misalin ƙarfe huɗu na yammacin ranar Alhamis, wani matsakaicin gida ne, cikin rukunin gidajen dake ɗan ƙaramin layin,  kallo ɗaya zaka yi wa gidajen, ka san na masu ƙaramin ƙarfi ne, duba da yanayin kwatoci da kuma kasancewar gidajen awon igiya, ba magudanan ruwa, babu layuka masu kyau, kowa da in da fuskar gidansa ta kalla, haka zalika kowa in da ya ga dama yake sako kwatar gidansa, wasu da gyara wasu babu, ga gidajen 'yan ƙanana tamkar wani zai hau kan wani.

"Wai ba zaki fito ki je mini aiken ba, har sai gawayin ya ƙare tukuna?" Cewar wata matashiyar dattijuwa, da take zaune a gaban kurfoti, hannunta riƙe da mafici tana firfitawa, gefe ga farantin silba ɗauke da garin tuwon masara a kai.

Wata  yarinya ce ta fito daga wani ɗakin da yake bayan matar, hannunta ɗaya riƙe da hijjabinta, ɗaya kuma sai matsar hawaye take yi.

Matar ta kalleta ta ce "Kukan me  ki ke yi?"

Aikuwa kamar mai jiran ƙiris, cikin sangarta yarinyar ta ce "Ba Huzaifa bane ba ya....

"Ni yi mini shiru, haka dai kuka iya faɗa kamar kuna ganin hanjin junanku, idan na hana ki zuwa in da yake ai ba zaki hanu ba, maza ki ɗau kuɗin nan ki je mini gidan Laure, ta baki kuka ta sittin, daddawa ta arba'in sai manja na naira ɗari ki kawo mini canjin, na yi maza in kaɗa miyar nan kan magariba".

Kwaɓe fuska yarinyar ta yi ta ce "Wai yau ma miyar kuka za ayi Innalillahi wa innalillahi raji'un"

Baki buɗe ta bi Yarinyar da kallo, cikin hasala ta ce "Idan na kaɗa kukar kar ki sha, zaki ɗau kuɗin ki fita ko sai na yi fatali da kanki a wurin?"

Ta durƙusa ta ɗau kuɗin, ta zura hijjabinta ta nufi hanyar fita, a ranta tana jin gara ace yau babu abin da zasu ci, da wannan tuwon kamar na ibada.

Cike da kashedi matar ta ce "Idan kin ga dama kuma ki je ki zauna, kar ki yi sauri kiga yadda zan yi da ke, ko ki biyewa yara ki tsaya shashanci a hanya"

Ba to ko waiwayo ba, ta yi gaba abinta tana kalle-kalle.

Gidansu ƙawarta Habiba ta fara biyawa, ta tarar da maman Habiba a tsakar gida ana yi mata kitso, ta durƙusa ta gaida Maman Habiba, sannan ta ce mata wurin Habiba ta zo.
Habiba ta fito daga ɗakinsu tana kallonta tana murmushi, ta ƙaraso in da take tsaye ta ce "Ruma ina zuwa ne?"

Cikin muryar Raɗa Ruma ta ce "Dan Allah Habiba aron tayar Sani zaki bani, Mama ce ta aikeni so nake nayi sauri na je na dawo".

Habiba ta ce "Kaii, Ruma kin san Sani yafi kashi ɗoyi, kar na baki ki je ki salwantar da ita, daga ni har ke mu shiga uku".

Ruma cikin ƙwarin gwiwa ta ce "Wallahi ba zata salwanta ba, ke dai ki aramini, so nake na yi gudu na ne na dawo".

Habiba ta ja Ruma soron gidansu, ta duba saman kejin kajin da ke cikin ɗan tsukakken zauren gidan, ta ɗaukowa Ruma tayar Sani ta bata ta ce "Dan Allah Ruma ki kula, kar wani abu ya samu tayar nan, ki yi maza mi garata ki je ki dawo"

Ruma tayi murmushi ta ce "Kar ki damu, yanzu zan fyalla naje na dawo, ina son tayar nan ta sani dama ya bar mini, 'yar dandaɓasa da ita, yanzu zaki ga naje na dawo".

Habiba tayi murmushi ta ce "To shikenan, yi sauri kafin ya dawo".

Ruma ta dafe kan taya, ta garata ta dinga zura gudu ta lunguna kamar wata namiji ba mace, ba ta tsaya da gara tayar ba har sai da ta isa gidan Laure.
Ta yo sayayyarta ta gama, ta fito ta kuma garo taya zata tafi gida, can ta hango wasu 'yan makarantar allonsu, a ƙofar gidan Hanne mai markaɗe suna 'yanta, ba tare da ta tuna da kashedin Mama ba, ta ajiye kayan aiken da canjin haɗi da tayar da ta aro, ta shiga aka hau 'yanta da ita.

Kasancewar ƙwararriya ce a harkar shagala da iya rinto, nan da nan wasa ya ɗau zafi, ganin tana ta cinyesu a 'yantar ta hanyar rinto, sai wasa ya koma faɗa, daga nan aka hau dambe, a wurin Ruma ta kifar wa da wata markaɗenta ga ta da ƙarfi kamar doki. Da ƙyar wani mutum ya raba faɗan, Ruma ta haɗa yaran mutane ta zane musu jiki, sai da mutumin yayi mata barazanar zai gayawa yayanta, sannan ta haƙura da damben.

Yarinyar da suka yi damben, ganin an musu asarar markaɗe, an kifar ga duka, ya sanya ita da ƙannenta suka fasawa Ruma Manjan da ta sayo wa Mama, suka kwashe canjin aiken, suka farke ledar aiken suka gudu, daddawar ma sai da ƙyar ta tsinto wasu, an fasa ledar kuka duk ta watse.

Ta kwashi sauran kayan, ta tafi gida, tana tafe tana tunanin wace ƙaryar za ta jirgawa Mama, dan ta kaucewa faɗanta, dan a duniya ba ta son faɗan Mama, gefe guda kuma tana tunanin irin dukan da zata naɗawa Safiya idan suka haɗu a makaranta allo, saboda abin da suka yi mta.
Lokacin da Ruma ta isa gida tuni an fara kiraye-kirayen sallar magariba, domin wasu masallatan har sun tayar, sai a lokacin ta sake shan jinin jikinta, tsoro ya ziyarce ta.

A soro ta rakuɓe tana leƙa cikin gidan, ta hango Mama a gindin rariya tana alwala, Mama ta ɗaga ido tayi mata kallo ɗaya, ta mayar da kai ta cigaba da alwalarta.

Cikin sanɗa Ruma ta shiga tana satar kallon Mama, ta ji mai Maman za tace mata, amma ta ji ba tace mata komai ba.
Ta lallaɓa ta ajiye abin da yayi saura na aiken, ita ma ta faɗa banɗaki tayi alwala.
Ta lallaɓo falo, ta tsaya a bayan Mama ta tayar da sallar ita ma.
Mama ta idar, ta tashi ta fita tsakar gida, ta duba abin da Ruma ta kawo mata na aiken, taga irin aika aikar da Ruman ta yo.
Ta dawo falon tana jiran Ruma ta idar da salla ta dirar amata, amma Ruma ta ƙi idarwa, ta hau nafifilin babu gaira babu dalili, matar da wataran sallar ma sai Mama ta haɗa .mata da duka take yi, amma yau sai gashi har da nafila.

Can da Mama taga abin nata bana ƙare bane ba, sallar taƙi ƙarewa, ta damƙo wuyanta ta baya ta zaunar da ita, ta kalleta cikin haɗe fuska ta ce "Gidan uban wa ki ka je dana aike ki?"

Cikin tsoro Ruma ta girgiza kai ta ce "Ba ko ina Mama"

"Ƙarya kike yi, zaki gaya mini ko sai na murɗe miki wuya, tun la'asar na aike ki amma sai magariba kika shigo mini, gidan uban wa kika je?"

Cikin zazzare ido Ruma take jujjya kai tana rantse-rantsen rashin gaskiya, "Wallahi Mama ban je ko ina ba"

Cikin tsananin Fushi, Mama ta ce "Ba zaki gaya mini ba!"

"Mama wallahi dagaske nake"

"Assalamu alaikum" aka yi sallama a tsakar gida.

Mama ta amsa sallamar tana huci, wani matashin saurayi ne ya shigo ɗakin, yana faɗin Mama na dawo".

Mama ta ce "Sannu da zuwa"

Ya amsa da yauwa, ya dubi Mama dake tsaye a kan Ruma, Ruma sai wulƙita ido take, kamar ta zagi sarki.

"Mama meyafaru ne?" Yayi Maganar yana son jin ba'asi.

Cikin ɗacin rai Mama ta ce "Saboda tsabar iskanci na yarinyar nan, nan da gidan Laure, ta je ta sayo mini kayan miya, tun bayan la'asar sai yanzu ta shigo mini gida, babu aiken babu dalilinsa, kuma babu canjina, nayi-nayi ta gaya mini in da ta tsaya amma taƙi faɗa sai rantse-rantse take yi".

Ya kalli Ruma ya ce "Ba zaki faɗi inda kika tsaya ba, kuma ina canjin? Ko zuwa ki ka yi ki ka kashe mata kuɗi tunda kin saba"

Cikin tsiwa da rashin kunya, Ruma ta ce "Ban sani ba, kai kuma waye ya saka da kai, zaƙin zaƙafere mai gida feraye kabewa, ai ba da kai ake yi.....
Kan ta ƙarasa Mama ta rufe bakin nata da duka, da sai da tayi zaton bakinta ya fashe.

Ja da baya tayi da sauri, ta dafe bakinta tana yarfe hannu, saboda ta ji zafin dukan nan sosai da sosai.

Ya jinjina kai ya ce "Mama ƙyaleta, ba dai bata da kunya ba, kar ki wahalar da kanki, ki bari mai sunan Baba ko Haidar su shigo, sai su tuhumar miki ita".

Jin abin da ya faɗa ya sanya Ruma ta yi wata irin zabura, ta ce "wallahi Mama gaskiya na gaya miki, dan girman Allah kar ki gaya musu, canjin ne suka zube a hanya, na faɗi ƙasa man jan ya fashe dan Allah kar ki gaya musu".

"Wallahi Mama ƙarya take yi, kin san dai ƙaryarta ba ta salla, ki tuhumeta bari mai sunan Baban ya dawo zaki ci ubanki".

Cike da gamsuwa Mama ta ce "Ai hakan za ayi tun da ba ta da mutunci"

Ya fakaici idon Mama ya yiwa Ruma gwalo.

"Mama kin ganshi ko yana mini dariya, dan Allah kiyi haƙuri"

Banza Mama tayi da ita, ta bawa Huzaifa kuɗi ya kuma yi mata wani cefanen.

Rumaisa ta koma gefe tayi tagumi, zuciyarta na ta zullumin halin da zata iya shiga, idan har aka sanarwa da Mai sunan Baba ko Haidar abin da ta yi, gashi ko giyar wake ta sha ta san ba zata iya gayawa Mama haƙiƙanin abin da ya faru ba.
Salati kawai take yi, tana roƙon Allah ya rufa mata asiri, kar Mama ta gaya musu, ƙasan zuciyarta kuma tana yi wa Huzaifa Allah ya isa da ya bawa Mama shawarar ta haɗata da su Haidar.

Ta na tsaka da tunanin, ta jiyo Mama da Huzaifa suna hirarsu a tsakar gida, kamar ba ita ta gama faɗa ba.
Suna yi mama tana ƙarasa aikin miyarta.
Sallama aka yi a tsakar gida, Ruma ta rikice, dan kusan muryoyinsu duk kusan iri ɗaya ne, ta ɗan nutsu ne da ta tuna mai sallamar muryarsa ba ta kai ta su Haidar fashewa ba, kuma shi dama sanyin hali ne da shi.

Jiyo Mama tayi tana faɗin "Fodiyo, an dawo"
"Eh Mama, ya gidan?"

"Alhamdilillah, sannu ka je ka watsa ruwa kafin nan na gama miya"

Usman da Mama ke kira da Fodiyo ya ce "To Mama, ga wannan" yayi maganar yana ajiye mata leda.

Miƙewa Ruma tayi tana leƙa window, tana son gane me ye a cikin ledar da Fodiyo ya kawo.
A ranta ta ce "Allah ya sa kifi ya kawo, idan kifi ne a bani kasona, dan idan aka saka a wannan baƙar miyar ban sha.

Ba ta kai ga gano meye a ledar ba, idanunta suka sauka a cikin na dodonta, da ya shigo gidan ko sallama bai yi ba, gani tayi tamkar yayi mata wani irin mugun kallo, ko dan dai a tsorace take ne oho.
Mai sunan Baban Mama kenan, Umar faruk.
Cikin takunsa na ƙasaita ya ƙaraso tsakiyar tsakar gidan, sannan ya yi sallama.

Hannu Ruma ta ɗora a ka, muryarta ƙasa_ƙasa ta ce "Na shiga uku, yau kashina ya bushe ƙayau idan ya san me nayi".

Tun daga sallamar da ya yi, bai cewa kowa komai ba, shi ma ya ajiyewa Mama ledar da ke nasa hannunsa, ya wuce ɗakinsu.
Bai jima ba ya fito tsakar gida, ya ɗau buta zai yi alwala.
Ruma ce ta fito kamar munafuka, ta ɗan risuna ta ce "Yaya Faruk sannu da zuwa"

Ɗaga ido ya yi ya kalleta, bai amsa ba ya mayar da kansa ya cigaba da alwala.

Cikinta ya ɗuri ruwa, ta ɗau tsintsiya ta tafi falon Mama ta hau shara a daren, kai da gani ka san sharar ba ta domin Allah bace ba.
Huzaifa ya faki Idon Mama ya bi Rumaisa falon, ya dinga leƙata yana tuntsura mata dariya.

Ba dan tana cikin yanayi na tashin hankali ba, babu abin da zai hana su kafsa faɗa da Huzaifa a daren nan, amma ta san biyewa Huzaifa su yi faɗa alhalin Faruk yana gidan nan, wata babbar matsalar ce, mai zaman kanta, dan ƙarshe sai tayi kuka.

"Ba zaki fito ki ɗebi Abinci ki ci ba?" Mama tayi maganar cikin ɗaga murya, yadda za ta jiyota.

Daga ɗaki Ruma ta ce 'Mama na ƙoshi"

A ƙufule Mama ta ce "To uban me ki ka ajiye da zaki ci, ba zaki fito ki ci Abinci ba?"

Ruma ta ɗan tura baki tayi shiru.

Usman ya ce "Ai kin san kin yi maƙiyin nata tuwo, mussaman miyar kuka da ma wata miyar ce ba wannan ba, ƙila ta ci"

Mama ta ce "Abin da nake da shi ba shi zan dafa na bata ba, zan fasa girki ne dan ba ta cin tuwon?".

Cikin kakkausar muryarsa Umar ya ce "Ki ƙyaleta, tun da a cikinta zata zuba, ta kwana da yunwa mana".

Mama ta gyaɗa kai ta ce "Ai shikenan"

Muryarsa kawai da ta jiyo, sai da ta sake shiga cikin tashin hankali, tsananta addurta ta yi, a kan Allah ya rufa mata asiri kar Mama ta gaya masa ta yi mata laifi.

'yan mazan nan suka kewaye Mama, suna ta hira kowa da abin da yake ce mata, banda mai sunan Baba, da  yake duba wayarsa, ba tare da ya tanka musu ba.

Jin suna ta hira, Mama ba ta gaya masa tayi laifi ba, ya sanya take ta murna, tayi maza ta yi sallar isha'i ta shimfiɗa katifar ta ta kwanta.
Ta cigaba da Addu'a a cikin zuciyarta.

"Assalamu alaikum" aka yi sallama a tsakar gidan.

Suka amsa baki ɗaya, Suka zubawa yaran da suka shigo ido mace da namiji.
Duk da akwai wutar lantarki da fari Mama ba ta gane yaran ba sai daga baya.

Suka gaida Mama da su Umar, Mama ta kallesu ta ce "Habiba ya aka yi me?"

Habiba ta ce "Ruma tana nan?"

Umar yayi caraf ya ce "Yaya aka yi?"

Kasancewar sa mutum mai tsanain kwarjini, sai da Habiba ta ɗan ruɗe sannan ta ce "Dama ɗazu ne da aka aiketa ta zo ta ce na bata aron taya, zata jewa Mama aike, to tayar ta Sani ce, ta ce zata dawo da ita kuma haryanzu shiru".

Mama cikin mamaki ta ce "Taya kuma?"
Habiba ta jinjina mata kai.

Gaba ɗaya Ruma ta manta da ta je ta aro taya, sai yanzu da ta ji maganar Habiba, dan tun da aka kwashi damben nan a nan ta yasar da tayar ta yo gida.
Ɗora hannu tayi a ka ta ce "Na shiga uku, Habiba shikenan kin kasheni".

Mama ta ce "Kina ina zo nan, mara kan gado, babu yadda ban yi dake ba a kan ki gaya mini in da kika tsaya, amma kika ce ke baki tsaya ko ina ba, ashe yawon aron taya kika tafi ko, ko ina sai kin nuna hali ƘANWAR MAZA, ina ke ina taya ban da hauka, zaki fito ki basu abarsu ko kuwa?"

Jikinta na tsuma ta fito ta tsaya daga bakin ƙofar falon Mama, tana satar kallon Umar, amma taga kamar ma bai san me ake yi ba.

"Ma.m.maama.. wallahi dan nayi sauri ne, ya sanya na aro tayar, kuma wallahi na manta na barota a wajen gidan Hanne mai markaɗe".

Mama ta riƙe haɓa kawai, tama rasa me zata ce gaba ɗaya.

Huzaifa ya ce "Wannan yarinyar idan kina da rabon yin hankali Allah ya shiryeki, ina ke ina taya kina mace?"

Mama ta kalli in da Habiba take tsaye ita da ƙaninta ta ce "Dan Allah ku yi haƙuri, tun da ta fita nima nake zaman jiranta, ban aiketa ta je ta karɓi kayan kowa ba, da safe in Allah ya yarda zan turata ta je ta dubo muku" Mama tayi ta basu haƙuri, suka juya suka tafi.

Mama ta zauna ta dasa mita, ta in da ta shiga ba ta nan take fita ba, su Usman na tayata, ita kuwa Ruma da ta san ba ta da gaskiya, sai ta ƙule a kan katifarta, zuciyarta sai bugawa take tana jiran jin me Yaya Umar zai ce, amma shiru bai ce komai ba.

Har suka watse daga tsakar gida, Mama ta shigo ɗakin, ta sameta ta rufe ido tana baccin ƙarya, still Mama ta cigaba da mita, sai da Ruma ta ji kamar ta tashi ta barwa Mama ɗakin ta huta, saboda Mama mitarta ba ta ƙarewa sam, gefe guda tana yiwa Allah godiya da Dodonta bai yi magana ba.

Wani irin bacci ne mai daɗin gaske yayi awon gaba da ita. A cikin baccin nata babu zato babu tsammani sai ji tayi an yi sama da ita da hannu ɗaya.

"Wayyo Allana, Innalillahi wa innalillahi raji'un, warin hannuna na hagu zai karye Mama!" Sai da ya dungurar da ita a tsakar gida, suka yi ido huɗu, ta ga wanda yayi mata wannan aikin.
Jikinta ne ya hau kyarma, dan idonsa kawai idan ransa a ɓace yake abin tsoro ne.

A ƙasan zuciyarta ta ce 'Shikenan tawa ta ƙare, Allah ya sa na cika da kyau da imani!.

Ayshercool
08081012243
[16/06, 9:00 pm] JAKADIYAR AREWA:                    ƘANWAR MAZA

      BY AISHA ADAM (AYSHERCOOL)



Ku yi subscribing YouTube channel ɗin mu, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro.
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Arewabooks @ ayshercool7724
Watpad@ ayshercool7724




P2






Kasa ɗauke idanunta tayi daga kallonsa, saboda azabar firgici da razanar da ta yi.
Ya janyo kujera ya zauna a gabanta, ya ɗan ƙura mata ido, sannan cikin kaushin murya ya ce "Gidan uban wa kika tafi da ta aikeki, tun la'asar ba ki dawo ba sai magariba?" Yayi Maganar yana tsareta da ido.
Kasancewar akwai wutar lantarki, ya sanya fes take kallon fuskarsa da idonsa.

"Ba magana nake yi miki ba, ki ka tsare ni da ido?" Ya daka mata tsawa.

Zabura tayi ta yinƙura za ta yi magana,amma ya sake cewa "Kuma wallahi kika yi mini ƙarya sai na ci ubanki a daren nan"

Jiki na rawa ta fara zayyane masa yadda aka yi tun bayan fitarta.

Huzaifa tun da  yaga Yaya Umar ya shiga ɗakin Mama ya jiyo kukan Rumaisa, ya sha jinin jikinsa, dan ya san yau sai yadda Allah ya yi.
Mama kuwa girgiza kai kawai ta yi, jin Yadda Ruma take faɗar gaskiya saɓanin ɗazu da ta yi mata ƙarya.

Umar ya ce "Namiji ce ke da zaki tafi aron taya?" Ta sunkuyar da kai tayi shiru.

"Kuma me nace miki a kan dambe a hanya, karya ce ke?"

Ta girgiza masa kai alamar a'a.

Ya ɗora da cewa "Wato ke duk wani abu da za'a gaya miki sai dai ya shiga ta kunnenki na dama, ya fita ta hagu ko?"

Ita dai tayi shiru tana rarraba ido.

"Kyaci ubanki, tashi ki kama kunnenki tun da ba zaki yi hankali ba".

Maraicewa tayi zata fara yi masa magiya, amma da yayi mata wani mugun kallo, ba shiri ta miƙe ta durƙusa ta hau kamun kunne.

Gaba ɗaya Huzaifa ji yayi bai ji daɗi ba, maimakon a hukuntata tun a lokacin amma sai da aka bari ta fara bacci, za a sakata kamun kunne, ya tsaya ta ƙofa yana leƙen tsakar gidan ya san yanzu zata galabaita, gashi babu wanda ya isa ya hana Yaya Umar abin da yayi niyya sai Hassan ɗin sa wato Abubakar Sadik, shi kuma baya nan.

Umar ya nutsu yana duba litattafansa, Rumaisa kuwa sai tangaɗi take tana neman ta faɗi, amma yayi banza da ita, dan ta san idan ta faɗi ko ta tashi ba zata iya ɗaukar wani hukuncin ba.
Tun tana kuka ƙasa-ƙasa har ta fara yi da ƙarfi, saboda azabar gajiyar da ta yi.
"Tashi" ya faɗa ba tare da ya kalleta ba. Ta ɗago duk ta haɗa uban gumi, ga hawaye da majina duk a fuskarta.

"Kukan uban me kike yi?"

Cikin kuka ta ce 'Yaya na gaji ne, dan Allah kayi haƙuri ba zan
DOWNLOAD
DOWNLOAD

4 Comments On KANWAR MAZA
avatar
shemau-shafiu

4 months ago

Reply

Anayi munajin dadi

avatar
maryam-2-7-4

4 months ago

Reply

Anayi munajin ddi

avatar
maryam-2-7-4

4 months ago

Reply

Yyu kyau

avatar
hauwau-8-4

2 months ago

Reply

Dan Allah qarashen fa

Please Login or Register in order to submit comment