Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

*_TARAYYA_*
_wattpad@mamuhgee_



*1*
BISMILLAHIR RAHMANIRRAHEEM

For you my ummu-khulthum.

Bayine da kuyangi bila adadin akowace kusurwa ta cikin babbar masarautar kowanne da aikin daya duqufa yanayi wasu nsu kuma a qaqqame suna gadin hanyoyin wucewa da kowace qofa ta cikin masarautar
Dukkaninsu kalar kayansu dayane mazansu da matansu kalar dark blue Wanda zaa iya kira da uniform.

Ahankali kowannansu yafara aje aikinda yakeyi yana ra6ewa gefe tareda sunkuyarda kai qasa sbd takun tahowar sarauniya Wanda sautin anklets din zinarin dake qafarta shine yake sanarda isowarta ko tahowartar tundaga nesa wanda tunda ta tashi arayuwarta ta taso agidan sarauta tasaba duk inda take sautin sarqar ke sanarda tahowarta harzuwa yanxu data manyanta sbd mulki a jininta yake.

Tana qarasowa hanyar dazata shigarda ita 6angaren mai martaba sarki ta tsaya cak batareda tace qalaba tareda juyawa ahankali tadan kalli gefenta da dama.
jakadiyarta dake gefenta tayi saurin matsowa tareda juyawa takalli kuyangin dake take musu baya kusan su shida kallo daya tayi musu suka ja baya ahankali suka tsaya tareda sunkuyarda kai.

Boyayyar ajiyar zuciya tasauke ahankali tareda shiga qofarda aka jima da wangale mata jakadiya tabita abaya aka rufo qofar.

Parlour ne mai wani irin girma da tsari dayaji adon royal chairs red and golden kamar zinari sai qyalli suke sai komai daya qawata palon yazamto shima red and golden dinne splits aircon kusan guda biyar sai aiki suke sanyi yakama palon takoina sbd wata irin dukiyace ta musamman aka narkar a palon.




Babu kowa a palon sbd palon farkone dazai sadaka da palon sarauta harzuwa turakar sarki
Ta sake tsayawa cak tareda sake sakin wata sahirtacciyar ajiyar zuciya akaro na uku zuciyarta na harbawa batareda tajuyo bangaren jakadiyaba murya a karye tace,

Wannan saqon na sultan(sarki) yana matuqar girgixa zuciyata sbd saqone daya zamto na baqin ciki agaresa,
Duk wani bawa ko bafade yakai wannan saqon abakacin rayuwarsane shiyasa nazabi nazo na isardashi dakaina,

Ajiyar zuciya mai nauyi jakadiya ta sauke tareda kallon sarauniya zaarah din cikin tausayawa acikin aranta afili tace,

Allah yataimaki sultana yakuma sanyaya ranki badan kinyi rashiba yabaki ikon isarda saqon sarkin sarakuna....

Katseta sultana zaraah tayi da cewa,

Haihuwa tazamar mana abar fargaba maimakon farin ciki.

Uwargijiyata Allah ya sassauci fargabarki amma dakin sake kin nunawa yarima farin cikinki da qaruwar dayasamu tunda shi yanaso ahakan kuma yana godiyar Allah da arzikin qaruwa daya basa
Allah ya raya abinda aka Haifa din yasa ayi alfahari da hakan gaba.

Ajiyar zuciya sultana tasake tareda furta amin qasan maqoshinta kafin ta tattaro jarumta da qarfin gwiwa ta gyara zaman gyalen kanta daya rufo dogon gashinta dake kwance har bayanta Wanda shima gashin harzuwa goshinta adone na wata kyakkyawar sarkar zinari ta kai sai aka rufo gyalen doguwar rigarta dark purple dataji adon duwatsu masu shegen kyau da kyalli gyalen naja har qasa kadan.

Ratsa dogon palon tayi jakadiya na bayanta ta nufi qofarda zata kaita ainihin palonsa na musamman tana zuwa wanda ke tsaron qofar ya wangale mata qofar ahankali tashiga jakadiya takoma gefe ta toge itama tana jiran fitowar uwar dakin tata.

Wani palon ne na alfarma babu kowa sai qarar ac dake tashi ahankali



Zaune yake cikin shiga ta alfarma
Dattijone sosai da Hutu da mulki na jinin sarauta daya ratsasa,
Kallo daya yayi mata da idanuwansa masu tsananin kwarjini da firgitarwa taso rudewa tayi saurin daidaita kanta ta tattaro nutsuwa da qarfin hali.

Qarasowa tayi cikin sanyin jiki da fargaba ta kallesa ta rufe idanuwanta dasuka fara canxawa murya na rawa tace,

Allah yataimakeka saqo daga GEORGIA.....

Idanuwan daya sake watso matane yasa taso daburcewa tayi saurin gyara murya cikin nutsuwa ta dauke idanuwanta daga kallonsa murya na rawa tace,

Yarima yabugo yasanarda saqon matarsa ta sauka ansamu 'YA MACE.

Sake dauke kai tayi sbd gudun ganin yanayinsa sbd kodagajin yanda ya dauke wuta tasan ran maza ya baci babu jin dadi ko alamar farin ciki dagajin saqonta.

Tsawon mintuna ashirin shiru
Kamar daga sama taji dakakkiyar muryarsa cikin ikon mulki yace,

Kin isarda saqon yarima Dan haka kisanardashi saqonsa ya iso
Ke kuma tukuicinki na sanarda saqonsa bazaki sakashi a idoba sai bayan shekara daya,
Karya dawo harsai matarsa tasake samun wani cikin wannan karon anan zata haihu
Zata haifi yariman da ubansa yaqi amsa.
Yana gama fadar haka ya miqe zai shige turakarsa

Dagowa tayi takallesa idanuwanta na canxawa zuwa kalar tausayin kanta dabazataga 'dantaba ko awannan shekarar
Tsawon lokaci kenan tunda yayi aure matarsa tahaifi ya mace suka koma Georgia sarki yace karsu dawo saita sake samun wani cikin tasamu tasake haihuwar mace yasake korasu yarinyar ta rasu still yahanasu dawowa harsaita haifi namiji yanxuma gashi macen ta haifa kuma yanxunma saiwata shekara kenan kusan shekara biyar kenan rabonta da danta tana tsananin kewarsa dason ganinsa.

Cikin sanyin murya tace,

Allah ya huci zuciyar sarkin sarakuna
Na karbi hukuncina matuqar hakan zai faranta ran sarkina
Saqon yarima kuma kamar yagama isa a kunnensa ne
Nabarka lafiya.

Juyawa tayi ta nufi qofar tana isa aka bude mata ta fice
Jakadiya tayi saurin Mara mata baya kanta asunkuye sbd ganin yanayin uwar dakin nata.

Suna isa babbar qofa suka fice kuyanginta sukai saurin Mara musu baya
Bayi sai zubewa suke suna sunkuyar dakai yaukam ko kallonsu bata iyayi bare amsa gaisuwarsu dankuwa ranta amatuqar dagule yake.

Tana isa sashenta cikin tsananin sauri aka bude mata qofa tashiga
Tana shiga kai tsaye hanyar bedroom dinta tayi bayan tasake wuce palonta na musamman inda babu mashigowa duk fadin masarautar daga ita sai danta yarima sai amintacciyar kuyangarta datake kamar matsayin 'ya agareta saikuwa jakadiya ko matar yarima bata taba shigowa nan palonba iyakacinta na farko bedroom dinta kuwa ko yarima baitaba shigaba bare jakadiya kuyangarta mai gyara mata kawai keshiga.

Tana shiga bedroom din taganta a tsaye jikin wardrobe din lafiyyan dakin tana jera mata sabbin kayanta dasuka iso.

Daidaita nutsuwarta da fuskarta tayi tareda gyaran murya batareda takalletaba.

Juyowa tayi da sauri tana ganin sultana zaarah tasaki wani irin lafiyyan murmushin daya bayyanarda dimple dinta duka guda biyu cikin tsananin taushin murya da tsantsar ladabi tace,

Ammy barka da dawowa.

Daga mata kai ammyn tayi batareda sakin fuskaba kamar yanda suka sababa murya a dake tace,

Ina buqatar hutu.

Cikin nutsuwa tayi saurin aje kayan ta nufi qofa zata fice jiki asanyaye sbd ganin yaudai ammyn bata cikin kwanciyar hankali dankuwa tunda safe take lureda ita bata cikin kwanciyar hankali.

UMMU-RUMANA....cak ta tsaya jin ammyn takirata tareda juyawa cikin ladabi tace,

Allah yataimaki ammy.

Bana buqatar damuwa takomai da kowa ko dogon motsi banaso kowa yafice daga nan shashen zuwa anjima saiku dawo ina buqatar Hutu.

Ahuta lafiya ammy"""tace cikin sanyi tareda ficewa jiki ba dadi sbd damuwar ammy na matuqar ta6ata sbd akoyaushe idan takalleta cikin annushuwa ganin take tamkar mahaifiyartace cikin annashuwar kasancewar mahaifiyarta babbar amintacciyar baiwar ammyn kuma jakadiyarda kafin tarasu.

Tana fitowa bban palon ammyn duk ta sallami sauran kuyangi da bayin sashen itama ta fita masu tsaron qofar shiga sashen kawai aka bari tareda nufar hanyarda zata sadata da bangarensu na bayi inda kowa keda daki mutum uku daki daya.
#mamuhgeee

*_TARAYYA_*
_wattpad@mamuhgee_



*2*
Babban sashensu na bayi da bororin masarautar ta nufa tana isa kai tsaye dakinsu ta nufa tana ganin qofar abude tasan nuratu naciki tashiga bakinta daukeda siririyar sallama.

Zaune bakin katifa taga nuratun tana qoqarin zare wandon uniform dinta zata shiga wanka ta nufi bakin tata yar katifar ta zauna tana cewa,

Yau kingamo da wuri Nima nasamu dan qaramin hutu daga ammy yanxu kiyi sauri kiyi wankan sai kiyimin koda kalbane sbd inason zanyi wankan tsarki banasan nayi da kaina a tsefe zai dameni tunda ba iska zaishaba koyaushe muna cikin uniform.

Kallonta nuratu tayi jin yanayin data qarasa zancen dashi kamar koyaushe tun tasowarsu sun bude ido sun tsinci Kansu a bayi kuma yayan bayi Wanda har gwara ita tanada mahaifiya rumana din batada uwa batada uba.

Fasa shiga wankan tayi ta qarasa katifar rumana din ta zauna tareda zame mata dankwali tace zonayi miki daga baya nayi wankan sbd nima aikine dani matuqa zanje karbo sabbin furannin dazaa jera a kwalbar ruwan dake girke palon sarauniya adama na farko gakuma aikin chanxa

Gyara zama tayi cikin tausayawa rayuwarsu tace,

Mamani tasha saqe saqin maganinta kuwa kafin tafita aiki?

Girgiza kai nuratu tayi cikin tausayin mahaifiyarta dakuma na rumana din datake qaunar mamani da zuciya daya duk da kyararta datakeyi.

Kamar rumana tasan me take tunani cikin sanyin murya tace,


RUMANA INA MAI HORAR DAKE KI RIQE ALLAH AKO WANE HALI KO YANAYI KIKA TSINCI KANKI DA RAYUWARKI,
IDAN KIKA RIQESA KIKA ZAMA MAI HAKURI DA DANGANA DA DAUKAR QADDARAR DAYA DORA MIKI MAI KYAWU DA MARAR KYAWU TO KODA KIKE BAIWA RAYUWA BAZATAYI MIKI TSANANIBA HAKAMA IDAN KIKA ZAMO BAIWA MAI BIN UMARNIN UWAYEN GIDANKI TO HAKAMA RAYUWA BAZATAYI MIKI TSANANIBA...

Nuratu wainnan sune kalaman ummana da ako yaushe suke shawagi cikin zuciya da kunnuwana wainda sune nake kallo amatsayin wasiyyarta gareni,
Ni baiwa ce uwata da ubana bayine harsuka rasu,
Banida wani gata ko martabarda zan kalli kaina amatsayin wata mace ko 'ya mai qima sbd nima zanqarasa rayuwatane amatsayin baiwa kamar iyayena,
Tun lokacinda nayi wayo

cikakkiyar mai yanci ta hanyar 'yantawa
Allah yakarbi adduata amma adaidai lokacinda yantawar batada amfani sbd tana kwance ciwon ajali Wanda yasa na yanke rai daga samun ingantacciyar rayuwa.....

Katseta nuratu tayi da cewa,

Ba'a cire rai daga rahamar uban giji rumana,
Ki zamto mai gode masa da kowace irin niima,
Ke mai saa ce sbd koda kasancewarki baiwa kinfita dabam acikin bayi sbd ke abar qaunace ga sarauniyar datafi kowace mace matsayi acikin masarautarnan sultana zaarah kasancewarki 'ya ga amintacciyar baiwarta
Ko ahaka kika duba zaki godewa Allah da wannan ni'imar.

Ajiyar zuciya tasauke ahankali tareda zare kanta ta juyo ta kalli nuratun tana tattare dogon gashinta tace,

Kibar kitson kiyi wanka kikoma bakin aikinki da wuri sbd gudun kwana gidan kason masarauta.

Tashi nuratun tayi tana jawo kayanda tafara maidawa tana cewa,

Bazan samu yin wankaba kuma sbd lokaci yashiga kuma wlh tsananin aikine asashen sarauniya adama sbd komai na sashen zaa canza har sitirunta kaf ko tsokalinda aka siyo jiya bazai shiga sashentaba sai sabo dal sbd kwanaki uku zuwa hudune suka rage ta kammala hukuncinta na sultan daya bata na ko qofar palonta na farko karta fito sai bayan shekara guda iyakacinta palonta na qurya zuwa bedroom dinta ko 'yayanta anhana shiga gurinta bare kuyangi iyakacinsu palonta na farko jekadiyarta kawai keda izinin shiga sbd kamata da laifin sa likita yaje gidan 'yarta gimbiya amatullah yayi mata allurar tsarin haihuwa suda ake fatar samun 'da namiji a zuria sbd.....

Rufe mata baki rumana tayi tana kallon qofa tace,

Ya isa idan wani yajimu kinsan rayuwarmuce zamu qarasa a kurkuku.

Saurin kallon qofa nuratu tayi ido a firgice zufa na karyo mata sbd shaf idan tafara barin baki mantawa takeda abinda zaibiyo baya sbd masarautar takasance maitsananin hukunci babu sauqi ko bata lokaci sbd tsagwaron mulki da iko ke yawo a jinin masarautar kasancewar sarkin masarautar mai tsananin zafine da zallar mulki babu sauki gurin daidaitawa kowa kansa,

Kwarjininsa ikonsa kesa ko matansa da 'yanyansa ke matuwar shakkar hukuncinsa shiyasa kowa a kiyaye yakeda umarninsa bare 'yan fada da sauran hakiman sarki.


Kusan atare suka fito daga dakinsu suka jawo dakin suka kowa yanufi gurin aikinsa
Kai tsaye rumana sashen sultana zaarah takoma inda ta tararda dukkanin wasu kuyangin sashen a qofar sashen sun jeru zai zufa suke sbd tsayuwa gashi babu ikon zaunawa haka itama tabi layinsu suka cigaba da tsayin jiran lokacinda uwar dakinsu zata gama hutawa sukoma ciki domin hidimarta.

Saida rana tafadi lis kafin ta matsa sbd lokacinda ake diba nabawa sarauniya Hutu yayi idan bata fitoba ana shiga aga lafiyarta
Matsu tsaron bakin qofar sashen sukayi saurin bude mata tashiga tana goge zufanta ta tsaya a palon farko saidatayi mintuna kusan shida atsaye AC ya butsarda ita kafin ta nufi palon gaba tashiga da sallama Mara qarfi sbd gudun yin hayaniyar da ammyn bataso.

Shigarta yayi daidai da fitowar sultana din daga bedroom dinta cikin doguwar riga maroon dataji adon sequence stones masu masifar kyau sai qyalli suke wannan karon babu adon sarqar zinari a gashinta da wuyanta kamar koyaushe saidai wasu awarwaron zinari masu kauri da girma sosai hakama babu kwalliya afuskarta kamar koyaushe sbd sultana zaarah takasance yar sarautar qasar Morocco koyaushe cikin tsananin ado da kwalliya take musamman gwalagwalai naban mamaki hakama bazaka gantaba kace tanada babban jarumin 'da sbd zamanta kyakkyawar mace mai kyawun jiki.



Durqusawa tayi cikin tsananin ladabi tace,

Barkada fitowa ammy da fatar kinhuta lafiya.

Zama ammyn tayi kan 'daya daga cikin royal chairs din palon batareda takalli rumanarba ta 'daga kai kafin tace,

Rumana 'yau banason dogon motsi bare hayaniya Dan haka kisanarda sauran ayi komai cikin qanqanin lokaci kowa ya fice kema ki kammala kije kihuta bana buqatar kowa.

Angama ammy.

Miqewa tayi taje tasanarda sauran kuyangin tadawo ta nufi bedroom din ammyn tafara gyara ta canza zanin gado sbd kwana daya 'daya yakeyi acire asaka sabo tana gama gyara koina ta sassaita AC daidai yanda ammy keso sanyinsa ya kasance takunna burners qamshi yafara tashi ta shiga toilet tayi gyaran dazatayi ta fito taje takarbo abincinta a manya manyan tururuwa ta jera a makeken royal dining din dake palon ta dawo gabanta ta durqusa a ladafce tace,

Allah yasa ahuta lfy yakuma tasheki lfy.

Ficewa tayi lokacin tuni aka fara kiran magriba daidai zata fito dake jakadiya dake qoqarin daidaita nutsuwarta tashigo.

Tsayawa jakadiya tayi a palon farko tafitarda numfashi mai zafi sbd sotake ta daidaita kanta sbd da rayuwartace amatuqar tsaka mai wuya duk tabari fargabarta tasa sultana tagano hukuncin da sultan ya yanke akan alamarin dake damun masarautar shekara da shekaru.

Tunda suka baro gurin sultan dazu tasake komawa sbd kai saqon banhakuri da tubar uwargijiyarta bisaga saqo Mara dadi data kaimasa na haihuwar mace da matar yarima tayi.

Abakin qofar fadar ta wuni tsaye cikin rana Dan nuna banhakurin uwargijiyarta Wanda saida rana ta fadi lis sarki ya aikoda izinin shigowarta.

Jiki na rawa ta zube gabansa cikin tsananin girmamawa tace,

Allah ya huci zuciyar sarkin sarakuna,
Sarkinda yafi kowane sarki adalci,
Da yardar Allah sai anmaka takwara harsai andarje a jininka,
Ba 'daya za'a samuba ba biyuba dozin ne da yardar ubangiji saika gansu saika aurensu
Allah ya sake hutar zuciyarka.

Gyara murya yayi cikin wani irin iko da umarni dake nuni magana daya yakeyi yace,

Jakadiya aje aciro 'yan mata biyar dasukafi kowa kyawu acikin kuyangun masarautarnan a killacesu afara kintsasu daga yanxu harzuwa nanda shekara daya lokacinda yarima zai dawo
Za'a kaisu sassansa amatsayin sa dakokinsa duk wadda ta haifi namiji ayimata albishirda tazama uwar sarkin wata rana.

Amatuqar kidime jakadiya zufa ya keto mata murya na rawa tace,

Angama sarki mai adalci,
Cika umarninka zaifara ne daga yanxu,
Allah dai yaqara hutar zuciyarka
Nabarka lafiya.

Fitowa tayi saida ta tabbatarda tayi nisa da sassasansa ta tsaya gefe tareda sharshe zufar daketa faman karyo mata tayi shiru tsawon mintuna zuciyarta na tumamin hukuncinda sarki ya yanke dakuma sanin waye yarima akan tsantseni matarsama da yaya akasamu yayi auren bare sa 'daka har biyar...

Sake sharce zufa tayi cikin tsananin fargaba gashi abakacin ranka matuqar sarki ya yanke umarni katsaya sanarda wani batareda ka cika umarninba Dan haka batada ikon fadawa kowa saidai kawai aiwatarwa.

Nufar sassan sultana tayi cikeda fargaba da tausayinta ta yanda hankalinta zai matuqar tashi duk randa taji zata fara shirin tarbon jikokinta na sa'dakoki.

*_TARAYYA_*
_wattpad@mamuhgee_
_Haske writers association_💡


*3*
Asma'u bilalu bulama shine asalin sunan mahaifiyarta asalinta 'yar qasar Nigeria ce ubanta bilalu dan Maiduguri sai mamarta ummu-rumana shuwah ce.

Bilalu bulama Nada tarin dukiya mai yawa hakama matarsa ummu-rumana kasancewarta tanada gadon iyayenta dasuka barmata.,
'Yarsu qwaya 'daya tak aduniya Nana asma'u wadda duk wata soyayyarsu da burinsu sun 'dorasa akanta.

Bilalu bulama Nada qanne biyu jabir bulama da salmanu bulama
Kowannensu matarsa 'daya da 'yaya uku uku banda bilalun dakeda 'ya daya,

Jabir babban dansa shine ishaq sai qannensa mata biyu hassana da husasaina,

Salmanu kuwa sunan babban dansa bulama sbd sunan mahaifinsu yaci sai qaninsa babaye da yakurah.

Kowannensu nada arziki daidai gwargwado amma ba kamarna bilalu ba sbd shi ba qaramin arziki Allah ya hore masa Wanda hakan yasa shedan yashiga kwadaitawa qannensa dukiyarsa nan kowannensu yafara qoqarin ganin ya cusa dansa gurin Neman 'yarsa Nana asma'u,

Tun kowanne natura babban 'dansa a 6oye gurin neman soyayyar asmaun hardai kowa yafito fili yanuna buqatarsa tason nemawa 'dansa auren,

Alhaji bilalu baiyi tunanin komaiba saima farin ciki dayayi saidai abun daga baya lalace sbd fada da tashin hankali daya shigo ciki sbd tuni kawuna suka rarrabe sbd alamarin ganin haka sai alhaji bilalu yace abari asma'u tazaba Wanda takeso acikin yaran dakanta sbd ya fahimci bulama shine Wanda tafiso kuma maganar gaskia yafi ishaq nutsuwa da tarbiya ga hankali amma shi bazai fadaba saidai ita asma'u tafada Wanda takeso dakanta.

Tashin farko da'a tambayeta gaban kowa ba 6oyo ta za6i bulama

Hakan datayi shiya qulla wata irin qiyayya da sabani tsakanin jabir da yayyunsa bilalu da salmanu.

Bayan auren da wata biyar aka wayi gari gidan alhaji bilalu ya qone qurmus dagashi har matarsa ummu rumana babu Wanda yafita kuma a iya binciken da akayi aka gano wutar dai kunnata akayi da man petrol.

Haka akayi zaman makoki aka watse dakyar aka samu asma'u ta dangana Wanda saida aka hada da adduoi da sauke al-qur'ani kafin tadawo daidai.

Duk inda hankalin alhaji jabir da ishaq yake yasake hargitsewa sbd sai yanxu kukaga wautarsu ta kashe su alhaji bilalu sbd yanxu duk tarin maqudan dukiyarsa yarsa zata gada tokuma ai mijinta da uban mijinta suzasu juya dukiyar kenandai alhaji salmanu yayi arzikinda ba ranar qarewarsa shikenan shi yatashi abanza.


Cikin watanni hudu shida ishaq sunkasa sukuni suna qulla yanda zasu qwato dukiyar su raba su salmanu da ita.

Ranarda suka gama qulla suka aika 6arayi gidan alhaji salmanu tsakiyar dare,

Gurin karbar takardun bulama da mahaifinsa sukai gardamar bayarwa Wanda yaja nan take aka harbe alhaji salmanu da matarsa bulama naganin haka ya buge babbansu da flower verse ya fizgo matarsa asma'u suka gudo tareda takardun dukiyar
Yakurah da babaye dama suna schools hostels suke zama.


Gudu suke sosai atsakiyar ko gani sosai basayi sbd duhun dare amma haka suke gudu hannunsa damqe Dana asma'u suna keta duk hanyarda suka samu sbd sunajinsu abayansu biye dasu.

Basu ankaraba suka gansu har sun fara barin anguwanni suna qoqarin ketawa daji amma haka suka cigaba da gudu agalabaice cikin tsananin wahala da gajiya
Can wajen gari sukaga wani kangon gida daya qone suka shige tareda boyewa.

Wani irin kuka asma'u tasaki jikinta na karkarwa
Bulama yayi saurin saka hannuwansa ya toshe mata baki sbd takun su ishaq da barayin daya jiyo yana kusantonsu.

Dudduba koina sukayi suna haskawa Allah yasa basu gansuba
Iska ishaq ya daka cikin zafi da tsananin 6acin rai yana huci yakira abbansa yafada masa

Cikin takaici da baqin ciki abban yace,

Kutafi tashoshin motar duk garinnan kudubasu banason kowannensu da rai takardun kawai nakeso Ku karbo saiku harbesu
Hakama atura su tiger duk wata station su zauna daga nesa da anhangosu sunzo station kafin sushiga aharbesu.

Aje wayar yay yakallesu yace kumuje tashoshin mota amma wasu su tsaya anan sbd nasan idanma sunanan kusa idan gari ya waye zasu fito idan sun fito Ku harbesu kawai.

Barin gurin sukayi sukuma su bulama najin haka koda gari ya waye sake lafewa sukayi sukaqi fitowa saida duhu yasakeyi suka fito cikin sanda suka fice tareda qarasa kutsawa cikin dajin suka fara gudu

Jini sosai qafafuwansu ke fitarwa sbd ko takalmi babu maishi acikinsu ga yunwa ga wahala da kishirwa amma hakanan suka cigaba da tafiya sbd komawarsu nada matuqar ha'dari yanxu.

Basu hadu da qauye ko dayaba har asuba tayi musu atsakiyar daji gashi tuni asma'u tafara riqe ciki tana murqususu cikin tsananin azaba ta durqushe agurin awahalce tace,

Bulama marata zan mutu.

Da sauri ya aje takardun ya durqusa ya tallafota jikinsa shima daqyar yake hade yawu sbd bakinsa daya bushe qyam ko yawu daqyar yake samun na hadiyewa a maqoshinsa ga wata irin rana mai tsananin azaba,

Ko tsuntsaye babu adajin sbd a bushe yake babu damshin ruwa ko kadan itatuwan dajinma duk abushe suke babu mai inuwa.

Jinin dayaga yanabiyo qafafuwantane yasa yayi saurin kallonta murya na rawar wahala yace,

Asma'u cikine dake dama bansaniba?
Innalillahi-wainnalaihirrajiun.

Ganin tana Neman fita hayyacinta yasa ya goyata tareda daukar takardun yacigava da tafiya daqyar shima sbd shima yafara daina gani daidai.

Ahaka rana takuma faduwa wani Daren yayi musu a tsakiyar jeji wannan karon kam ya tabbatarda wata duniyar suka fado sbd kalar yanayin dajin ya sauya sosai
Tun yana gani har duhu yasake yi dare Yakuma tsalawa sosai cak ya tsaya tareda yanke jiki ya fadi asma'u dake bayansa ta fado da qarfi kafin ya bude idanu daqyar Dan taimakonta sai ganin yayi kamar tana gangarawa
Bude idanuwansa yayi awahalce da sauri saiyaga Ashe bakin cliff suke mai tsananin zurfi da ruwa masu tsananin yawa yana miqewa daqyar kafin yakamota idanuwansa suka rufe yasake yanke jiki yafadi tareda fadawa shima.


********
Ahankali ya bude idanuwansa dake gani dishi dishi harsuka bude daqyar suna kallon sama,
Lumshe idanuwan yasakeyi yabudesu yaga tabbas rufin sama bukkar karace yake ciki,

Qoqarin motsawa yakeyi Dan ya yunqura yatashi aka shigo bukkar yayi saurin dagowa.

Tashin namijine kamarsa dago fari tas sanyeda kayan saqi na fulani.

Qarasowa yayi da sauri tareda dafasa yana cewa,

Yi ahankali kana kariya aqafa.

Kallon qafar bulama yayi sai alokacin yaji azaba ya lura da 'dauri amma bai damuba cikin dasashiyar murya da fargabar amsarda za'abasa yace,

Ina matata?
Inane nan?
Ina takardun dake daure ajikina?
Kwana na nawa anan?

Cikeda mamaki da rashin isashiyar hausar fahimtar me bulaman ke fada yake kallonsa kafin ya gyara masa zaman qafar mai 'dori yace,

Kayi hkr sbd bansan mezan fada makaba amsa daya zan iya baka shine kwananka takwas anan sauran tambayar anjima idan mahaifina yadawo ya amsa maka.

Yana fadar haka ya fice
Saigashi yadawo da qwaryar magani da akushin wani irin abinci kamar tuwa kamar kunu ya zauna tareda miqawa bulama yace,

Gashi kaci saikasha magani.

Kallon abincin bulama
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment