Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels


WATA SAKAYYAR............1

NA

FATIMA DAHIRU FUNTUWA BINTA

Godiya tatabbata ga Allah mai kowa mai komai dayasake hadamu cikin wannan littafin.tsira da Amincin Allah dukara tabbata ga shigabammu Annabi Muhammad (S A W) da sahabbansa da iyalan gidansa baki daya.
WATA SAKAYYAR..........kamar yadda kukaji NA ambaci sunan littafin dashi,labarine mai dauke dajan hankali da darasi da Harkallah.duk acikin wannan 'yar karamar kwakwalwar tawa zanshirta wannan labarin,mai dauke da wa'azantarwa.
Kabi ahankali mai karatu,don Allah idan kaga kuskure acikin kalaman dazanyi amfani dasu acikin wannan Dan littafin kasanar dani,kagyara Mani,domin kuwa labarine mai dauke da wa'azantarwa.
Idannayi amfani dawata Kalmar wadda batayi maka/maki ba,ayi hakuri,banyi amfani dawannan damar don inbata ran wani ko wataba,kuma banwuceyin kuskure koyin badai daiba.
Nidai fatana akoda yaushe shine,kadauki abinda yakeda kyau acikin labarin,abinda yake bamai kyauba kawatsar dashi.

WATA SAKAYYAR SAI A WURIN ALLAH!!!!!!!!!!!!!!!

Zaune take tana ninke kayan yaranta dasuka dawo makarantar Islamiyya,tana shiryasu acikin jaka,Abakinta kuwa istigfari kawai take karantowa,domin kuwa yazama jikinta,koda yaushe bakinta yana cikin ambaton Allah.
Haka takammala gyaran kayan sannan tazauna bakin gado,ta canza istigfarinta takoma karanta HASBIYALLAHU WANI'IMALWAKIL.
Zuwa can sallamar kawarta tajiyo,maman Hafsat tashigo dakin tare dafadin,kina zaune kenan?nayi sallama naji shiru,Maman bata nanneko?
Tace e taje barkane dakuma wata tarewa,da diyar kawarta keyi,tunda Azaharma tabar gidan.
Maman Hafsat tace kebakije tarewarba kenan?koda yakema kebason zuwa sha'aninnika kikeba,kice tarewa taje?kaih! 'Yankwanakinnan dai anata aure,kinsan kuwa Hasana ta gidan malam Haruna itama sati mai zuwa ake daura mata aure?
FA'IZA tace aure kuma?to INA wancen auren datayi?
Maman Hafsat tace wancan auren ayya mutu,gashi har zatasake wani.
Fa'iza tace ikon Allah ita kuma irin tata kaddarar kenan,aure-aure,itakau kome kejamata saurin kashe aure?
Maman Hafsa tace sabodataga idan takashe auren tanasamun wani mujin dawuri,amma data ga idan takashe auren tana daukar shekaru wani mujin baisamuba,aibatayi gigin kashe aurebtaba,amma kinsan Allah Faiza,da Hasana tafito gidan muji adaddafe take gama idda,tamkar mazan najiranta.
Faiza tace ni wannan Abu har mamaki yake bani,kiga wasu matan nan danan da aurensu yamutu saikiga sunsamu wani mujin sun aura,kuma kaga bakyau suka fikaba,ba ilimi suka fikaba,ba natsuwaba,NA rasa irin wannan Abu Allah dai yasa mudace.
Maman Hafsat tace wallahi kuwa,amma kema fa'iza yakamata ace kinsan abinda kike ciki yanzun,zamannaki yayi yawa agida,shekara da shekaru tunda Aurenki yamutu!har yanzun gashi shiru.
Faiza tace lokacine,idan lokacin yayi saikiga nayi auren.
Maman Hafsat tace kaih!!amma duk dahaka shirunnaki yayi yawa,infa kika zaunafa saikita rayuwa ahaka,kina cewa lokacine,amma za'a iya cinkaro da wata matsalar dazata iya hanaki yin aure,gara kinemi magani idan wata matsalarce arabaki da ita,haba!!shekara goma ko kare baitaba zuwa yace yana sonkiba!kuma sannan harkiyadda da cewa bakida wata matsala!wallahi wata lalura NA iya hana azoace anasonki.
Fa'iza tace ga Allah nadogara,shi zayyimin maganin komai,imma iska gareni ko wani sihiri akayimani,idan Allah yakawo lokacin auren dole iskarnan takauce tabarni inyi aure,inkuma sihirine wallahi Allah shi zayyimin maganinsa sihirin yakarye,ba wurin Wanda zanje nemanmagani,zawarci dai bani kadai bace bazawara.
Maman Hafsat tace aikaji matsalar taki,koda bake kadai bace bazawara,aisauran zawarawan,ana zuwa ace anasonsu,koda ba aurensu za'ayiba,ammake matsalar takifa,koda wasa bawanda yataba cewa yabasonki,Tabbas!!ansan aure lokacine,to amma arika cewama anasonka Aida dadi,bamayi jimgimba,duk yadda akayi wannan matsalar taki akwai abinda kefaruwa dake.
Duk yadda akayi wannan matsalar taki akwai abinda kefaruwa dake bahakananba.
Faiza tace:Tonidai inata Addu'a kodayaushe,imma wata matsalarce Allah yakawarmin da ita,idan kuma jarabawace daga lillahi Allah yabani ikon cinyeta.
Maman Hafsat tabita da Ameen,dai dai sanda akakira sallar magariba,faiza tatashi tadauki buta tayi alwalla,tareda umurtar 'ya'yanta suma suka dauki butoci,sukayi alwalla.
Maman Hafsat kuwa tayi sallama dasu tatafi gida,itama tayi tata sallar.
Misalin karfe goma sha daya nasafiyar ranar Asabar,su faiza suka taso makarantar islamiyya,tare suka jero da Maman Hafsat,suka tafo kamar yadda suka saba tafiya da dawowa makaranta atare,,suna tafe suna taba firarsu,musamman akan darasin da akayi masu,a ranar.
Maman Hafsat tace kaih!yau naji dadin karatun muallimah!nafahimcesa sosai,amma kinga Nahawu haryanzun bana fahimtarsa,wahala yake bani,wani lokacimma da malamin yashigo yafara karatun,yana farayimana li'irabi,kawai sai inma bacci nake,sabida tsabar bana fahimta,amma kinga Hadith da Alkur'ani,wannan har kosawa nake ranar yinsu tazo.
Faiza tace shima nahawun nace kirika zuwa,Wanda akayimaku inkara yimaki bayani,watakila nikirika fahimtar nawa.
Maman Hafsat tace gaskiya kwakwalwata bazata iya daukar Bahawuba,bata daiki Tajweed bama yaza'ayi tadauku Nahawu?
Fa'iza tace aikaji matsalar taki,saurin karaya gareki,bawanda aka haifa da iyawa,kowafa koyo yayi,kirika dagewa kina jarabawa.
Maman Hafsat tace kedai bashshi kawai,hidimar 'ya'yama ta isheni,tunda banyi karatun da yarintataba,kekau ai malamace,shiyasa da karanta kike ganewa.
Wai Fa'iza yamaganar Addu'oin da malam yabayar?
Faiza tace:INA amfani dasu sosai,kinsanni bana wasa da Addu'a,kodon wannan rayuwar danake ciki,Allah yakawomin sauyinta,inayin addu'oi sosai.
Maman Hafsat tace hakane,amma kinsan wani Abu fa'iza?koda kina yin Adduar kirikasa malamai sutayaki,kinsan Baki dayawa,wani daya roki Allah saikiga cikin gaugawa Allah yabiya bukatar,wani kuma yaytayin addu'ar amma kaji shiru,Allah natuba.
Fa'iza tace wallahi kuwa hakane Maman Hafsat,Nice sallar dare,nice duk wata Addu'a,kosunayen Allah da akabamu zanrike inje intayi,shekara da shekaru,INA wannan halin,amma bawani canji,yadda akedai haka ake,ko Alama!koda wasa!!wanima yace Faiza INA sonki wallahi babu,Addu'ar dai yinake-,yinake,don dai ba'acewa kayi kagaji,amma wallahi Maman Hafsat harna fara sarewa,dacewa anya kuwa zan kara aure?shekara goma koda wasa wanima yace yanasona ba'ataba ba,duk dadai akwai wadanda sunmafi shekara goman suna zawarcin,amma susai inga niyyar Aurenne basuyiba,tunda anazuwa ace anasonsu,amma nifa? Babu Wanda yataba zuwa yace yanasona,Addu'ar nan nayi-nayi har yanzun shiru,yadda kikasan ba a kar...............
Kaih!karmadai inyi sabo,ya Allah kakawomin iyakar wannan zawarcin!wallahi nagaji Maman Hafsat, ace duniyarnan babu Wanda zaizo yace yanasonka,sai kace muguwar haja,inda ace inada zawarawa zanrika samun wani Abu daga wurin su,amma dai dai da omo ko sabulu banida Wanda zayyimin kyautarsa,sai dai innina nemi kudi nasiya dakaina,ga yara inada su,banida mai tallafamini sai Allah,wannan Abu yana dagamin hankali,shiyasa hankalina yatashi nakeso inyi aure,amma ace INA mace Nike daukar hidimar kaina data 'ya'yana,aiwallahi akwai wahala.
Maman Hafsat tace gashi kuma wannan Dan banzan mujinnaki ko.............
Faiza tayi saurin cewa mujin watadai!!karki kara kiranshi da mujina,wallahi ko firarsa banaso anayimin,wannan Azzalumin!;Wanda baisan ciwon kansaba!!kanada 'ya'ya bakasan yasukeba,bakasan cinsuba!bakasan shansuba!!baruwanka da ciwonsu!!don yanzunfa 'yata khadija batasan Babantaba,saidai acemata tanada Baba,amma bata taba ganinsaba,baima zuwa ballantana musa ran zayyi mana wani Abu kodon 'yayannan,duk gaba daya hidimarsu yasakar Mani,HAKIKA WATA SAKAYYAR SAI A WURIN ALLAH!!!!!
Maman Hafsat tace kema kuma danaki laifin,dabaki taba daukar 'ya'yanki kin kaisu wurin ubansuba,suganshi suga danginsu.
Faiza tace Allah yakiyaye!!shibaidamu dasuba,sai nice zan kwashesu inkaisu,salon inje ace Neman gyaran aure nake,ba kisan gulmar garinba kenan,danaje za'ace gatanan kila so take yamaidata dakinta,anga zaman zawarcin baci,Allah yakiyaye bazaniba!
Nadaiyya alkawarin duk ranar danayi aure zanje inkaisu,amma ayanzun banida aure,ace sonake yamaidani,AA Allah yasauke.
Maman Hafsat tace toke baki tunaninma koshine yayi maki wani saddabarun donya hanaki aure?tundafa badon yanaso kuka rabuba.
Faiza tace:gaskiya bazai iyaba,bazan dauki alhakinsaba,Nina zauna dashi,nasan halinsa,nasan abinda zai iya,nasan abinda bazai iyaba,ban taba tunanin cewa wai sihirine akayimani aka hanani aureba,tsofon mujina bazaitaba yimin Asiriba,kawai dai nafi dauka cewa lokacine bayyiba,to amma abinda yafi damuna shine,inrika ganin Alama,ma'ana arikacewa anasona mana,amma kodaya bamai tayani,idanna tuna wannan inyi kukana ingaji.
Maman Hafsat tace tokisa atayaki da Addu'a mana,yanzun anan cikin unguwarmu ga malam shehu mai Almajirai,koshi kikaje kikayima bayani,in Allah yataimaka saikiga karshen abin yazo.
Faiza tace nifa gaskiya bana son fara shiga malamannan,saboda.....................
Maman Hafsat takatseta dacewa to aisaikita zama!abin baidameki bane!!baki gaji dazama gidankuba,bakisan Annabi (S A W ) yace malamai magada Annabawa bane,yadda zasu roki Allah nan danan aga biyan bukata,kesaikiyi shekara kinayi,batayi matsayin tasu tarana dayaba,domin kuwa su bakin su koda yaushe cikin ambaton Allah yake,sallolin nafila basa yankemasu,kuma kedakanki kinsan muyi Hadisinnan.
( daga abi Huraira Allah yakara masa yadda yace:manzon Allah (S A W ) lallai Allah madaukakin sarki yace:duk Wanda yayi gaba da masoyina,to yayi shirin yaki dani,kuma bawana bazai taba kusantuwa dani da abinda nafisoba,kamar abinda na farlanta akansa,kuma bawana bazai kasance yanayin nafilfiliba,harsai nasoshi,to idannasoshi,zan kasance masa jinsa dayakeji dashi,in kasance masa ganinsa dayake gani dashi,inkasance masa hannunsa dayake tabawa dashi,inkasance masa kafarsa dayake tafiya da ita,kuma idan yarokeni wallahi zan amsamasa,idan yanemi taimakona wallahi zan taimakesa.Bukhari yaruwaito.
Faiza kokin mantane?acikin Arba'una Hadith yake,Hadisi na Talatin da Takwas,abinda yasa nakeso kisa atayaki da rokon Allah domin bakisan bakin waniba,wani zai iya kasancewa daya daga cikin waliyyan Allah,idan har akayi sa'a shine to daya roka Allah zai amsa,kinga nan danan sai bukatarki tabiya.
Faiza tace to tunda har Allah yafadi suffofin waliyyan,sai kawai inkara dagewa da sallolin nafila,konima zanzama daya daga cikin su,amma ince wani yarokar Mani Allah,aikamar natura Dan sakone,inroka dakaina mana,kinsan kuwa zuwa dakai yafi sako.
Dai dai nan Maman Hafsat tadafa kyauren kofar gidansu,tatsaya,domin kuwa suzo dai dai inda zata shiga gida,sai kuma tatsaya tace:
Tsiyata dake faiza taurinkai,duk yadda akayi dake baki yadda,amma tunda kince haka,mubari idan munkoma makaranta muyi tambaya: SHIN YA HALATTA MUTUM YASA AYIMASA ROKON ALLAH,ATAYASA ADDU'A???????
To idan mukaji amsar da malam yabamu,komunaso kobamaso saimuyi amfani da ita,Allah dai yasa mudace ,sai anjima.
Sukayi sallama tashiga gida,faiza kuma tawuce nasu gidan.
Ranar Asabar misalin karfe uku narana,Maman Hafsat tashigo gidansu faiza,mahaifiyar faiza tagani zaune tana yankan kubewar miya,ta gaisheta sukadan taba fira Maman Hafsat tace INA Faizar naga bangantaba?
Mama tace tana kitchen tana hada wuta,sannan takwala mata kira.
Tafito tareda fadin aiwai Maman Hafsat CE?shigo mana.
Maman Hafsat tace AA bashigowa zanyiba,dama nazone infadamaki yau ake auren Hasana,Dana gayamaki,daurawa datarewa,kushirya idan anyi sallar la'asar
Whatsapp number 09162526909
Kishirya idan anyi sallar la'asar,kizo gidammu muwuce.
Faiza tace to shikenan,Allah yakaimu.
Cikin wasa da tsokana Maman Hafsat tace,gara dai kirika FIFA,ba kodayaushe kina cikin gidaba,daga gida sai makaranta,kuma kiyi kyalliya sosai,don kema sonake ashekararnan azo naki auren,saboda mungaji daganinki agida,kifayo kwalliya hada jambaki!
Abinma sayyabata dariya,mama tace Allah yakawo muji na kwarai aimuna fata,itama tatafi dakinta tahuta hakanan,kowa dai dairin kaddararsa,ita kuma Hasana irintata kaddarar kenan,aure da anyi baya zuwa ko INA,Allah dai yasa mudace.
Maman Hafsat tace Ameen,tare dafadin faiza inajirankifa,yanzun zankoma gida inyima yara wankane sutafi islamiya naga uku tawuce,yanzun kinji la'asar,tamike tsaye tareda tafiya tana kara cewa:faiza kisanyo kayanki wadanda sukafi kowanne kyau,kisha turare,kidau make up sosai,Allah yahadaki da wani dan gayun.
Sumama da faiza dai dariya suke,maman Hafsat tatafi gida.
Misalin karfe biyar na yamma,Faiza tashiga gidan maman Hafsat.
Kin dai shiryako?nasan ki danawa wurin shiri.
Maman Hafsat tace nashirya mana,nadaukama bazakiba,tunda gashi har biyar takusa.
Faiza tace zani mana,kinsan taron bikin yanzun saida yamma,shiyasa natsaya nakintsa sosai.
Maman Hafsat tace kingakau yadda kikayi kyau faiza!!dama kin iya irin wannan kwalliyar kike zaune haka?haba da walakin,Aida kina daukar wanka da kwalliya,haba dayanxun ba wannan maganar akeba,tafada tana dariya,tareda kara fadin:
Hala kinwuto 'yansa idonnan har sun kafa majalisa? 'Yan zaman zana'ida bagawa.
Faiza tace keko maman Hafsat kinsama wadannan bayin Allah ido,daga suna zaman kan hanha shikenan saikice sa ido suke?
Maman Hafsat tace aiko kallon matan mutane kawai kezaunar dasu,in mace zata gitta insuka fara kallonta harsai tabace,har wani lekota suke,auu!!canzakiga sun saki haba suna kallon mata,sunsan kowace mace a unguwar nan,sunsan gidansu,in budurwace sunsani,inbazawarce sunsani,in matar aure CE sunsanta sunsan waye mujinta,hakan kuma bai hana subita dakallo harsai sundaina ganin ta,karmadai inkinyi kwalliya,mace intazo dai dai saitinsu har tuntube take tana hardewa,koke NA tabbatar sun kalleki,yadda kikayi wannan kwalliyar,daka wuce kuma ahau labarinka,baza'a dainaba,sai kuma inhan hango wata tazo wucewa sai asaki tata fitar akama tata.
Faiza tafashe da dariya,tace gaskiya maman Hafsat akwai ki da sharri!!Tonidai basu kalliniba,ballan tana ince sunsamin ido,ni tunda nake wucewa tagabansu lafiya lau nake wucewa,BAN TABA GANIN SUNA KALLONABA,harma indaga ido inkallesu,sai inga kowama hidimarsa yake baidamu daniba,ammake kullun saikince sunsamaki ido.
Maman Hafsat tace tokeko wace irin mace CE dabasa kallon ki?wadanda kowa yayi masu shaidar kallon matan tsiya,amma kekice basa kallon ki?
Maman Hafsat takuma cewa wasa dai kike.Allah natuba indai balalura garekiba,to komindai munin mace intazo wucewa saisun kalleta,ballan tanake.
Faiza tace abar Maganar,dauko hijabinki muwuce,yamma karayi take,suka fita gidan baki dayansu.
Ranar Lahadi suna cikin Aji,misalin karfe goma nasafe.
Malamin dakeyimasu Tajweed yashigo,yafara karatu,yanayimasu bayani.
Maman Hafsat ta nutsu sosai dukda wannan darasin yana bata wahala sosai,domin kuwa ba fahimtarsa takeba,amma awannan lokacin hankalinta da idanunta nakan malamin,da abinda yake karanta masu,ita iyakar gaskiyarta yau saita iya karatun nan tafahimceshi
Bayan malam yakammala karantawa,yayi masu bayani sosai,sannan yajefo tambaya,kamar haka.
(Idan aka samu nunussakina sai mimunmushaddada tabiyo bayanta,ya akekiran wannan hukuncin?)
Budar bakin maman Hafsat da karfinta irin yau tafahimci karatinnan,tace:
NUNUN MAKIYYA!!!
Gaba daya aji akafashe da dariya,hatta shi kansa malamin saida tabashi dariya......
Hattashi kanshi malamin saida tabashi dariya,yace gaskiya baki tare damu,in inakaratunnan ina hankalinki yake zuwa?tunda muke Tajweed kintabajin na ambaci wani hukunci da nunun makiyya?
Tace malam naji kacene,nunun daurarriya sai mimun tabiyo bayan ta,toshine nace nunun makiyya,aikaga ganunun ga mimun,ita mimundin batana nufin makiyya bane??
Malam yace maman Hafsat idan ina tambayar 'yan aji kidaina samin baki,wannan karatun anyishi maimaicine ake,amma haryanzun baki fahimtaba,kiyimin shiru.
Faiza tace wallahi maman Hafsat kekike bada amsar nikejin kunya,wane irin nunun makiyya?dama akwai nunun makiyya a Tajweed?To bama kigane Tajweed ya za'ayi kigane Nahawu?
Barikiji,idan mimun mushaddada tabiyo bayan nunussukun,ana kiranta.
(Al-idgamun nunussakinati bi gunnah)
Maman Hafsat tace to shikenan narike wannan.
Faiza tace Allah yasa da gaske.
Bayan malam yakammala karatun zai fita,maman Hafsat tace ya mu'allim!inada Tambaya.
Yace to naji,ammafa kiyi tambaya ta hankali,nasan halinki.
Tace Shinyahalatta mutum idan wata damuwa tasameshi yasa atayishi da Addu'a?
Malam yace sosaima kuwa,domin kuwa bakasan ta bakin Wanda za'aamsaba,kamar ninan idan wani Abu yasameni zan iya zuwa wurinku Ku dalibaina,ince kutayani da Addu'a,wannan yahalasta,shirkace ba'ayadda da itaba,misali zuwa wurin Boka,sabo dawata 'yarbukata taka,kakwashi jiki kaje wurin boka wannan haramunne,sai dai katashi kayi sallar nafila ko Azumi,sallar dare karoki Allah,kuma kina iyasa kawarki ko malaminki kokuma duk Wanda kika yadda dashi,kice matsala kaza tadmsameki atayaki da Addu'a.
Duk sanda mutum yayi Addu'a"Allah yakarba,koda bakaga biyan bukatar akusaba,wani lokacin Allah yana jinkirtawa,kayi fatan wannan jinkirin yazamemaka Alkairi.
Kuma ba'acewa angaji da rokon Allah haryanzun bukata bata biyaba,wata kila wannan bukatar dakake nema ba Alkairi bace agareka,idan kayi Addu'ar sai Allah (S W T) yajuyar maka da Adduar tawani bangaren,karshenta akwai wani Abu dazai cutardakai,ko wani mummunan Abu zaisameka,to sanadiyyar wannan Addu'ar da kakeyi,sai Allah yakawar maka da wannan mummunar kaddarar.
To kunga Amfanin Addu'a kenan,don haka kodayaushe mudage dayin Addu'a .
Allahu a'alamu.
Dukkan 'Yan ajin suka bude baki sukace:mungode ya mu'allim!!
Bayan wasu 'yan watanni suka samu hutun makaranta,don haka Faiza tayi shirinta tatafi kauyensu,inda aka haifi mahaifinta.
Taje lafiya,Gidan yawane sosai,dakin gwagwgwo Hauwa tasauka,dama nan take sauka idan tazo garin.
Gwagwgwo Hauwa matar yayan Babantace,mace CE maikirki sosai,suna zaune atsakar gida misalin karfe Tara na safe.
Saiga wani yaro bai wuce Dan kimanin shekara gomaba,yashigo gidan,yana rataye dawata jakar fata,acikin ta magunguna yake sayarwa kala-,kala,na gargajiya,yana Talla yana fadin.
Kusai maganin miyagu.
Maganin sammu.
Maganin ketara.
Maganin makaru.
Maganin baki.
Maganin kambun baka.
Maganin..............
Kafimma yagama fadin sauran magungunan,Hansai datake tsaye tana surfen masara aturmi,tace Yaka mai maganinnan kona miyagu masiya.
Yaro yashigo ya kwance magunguna anata siye,mutane dayawa acikin gidan sun anshi maganin.
Ita kuwa Faiza kallon ikon Allah kawai take,watakan su yanzun dasuketa rububin siyen wannan maganin,ko amfanin mezayyimasu oho?anje anyo sassake-sassake adaji ance masu magani sundage sai wani siye suke,Allah yakyauta.
Aka kammala siye,yaro yakalli Faiza yace kebazaki siyaba?
Tace me zanyi dashi?Allah yakiyaye!!
Yace baiwar Allah ki amsa zayyimaki amfani,domin kuwa akwai matsala ataredake,kinada lalura sosai ajikinki,mai wahalar magani,ammani idan ki kabani abin sadaka zan iyarabaki da ita,kuma...............
Takatseshi dacewa Dallah Dakata!!nikarkayimin janye-janye!lafiyata lau!!INA zaman zamana lafiya.....
Takatseshi dacewa Dalla Dakata!!nikarkayimin wani janye-janye!lafiyata lau!INA zaman zamana lafiya kakiramin lalura!!kai duk cinikin dakayi acikin gidannan bai ishekaba,dole saikaci dani?Allah yasauke!!!
Yakara kwantar dakai yace:baiwar Allah ki amsa zayyimaki amfani,domin kuwa kinada lalura mai wahalar magani,amma awannan karon dazaki amshi maganina Allah zairabaki da ita.
Tace kai yaro! Dukfa dadin bakinka bakacin kudina,ni inatare da Allah bawanda ya isa yacutar dani,don haka kadama kayimin janye-janye,kace iska gareni ko sihiri akayimani,ko magani zan amsa,zan amsa awurinkane?
Yabude baki yana dariya zayyi magana,
Hansai tace karabu da ita ba amsa zatayi ba,su 'yanburnine ba amfani sukeyi da irin wadannan magungunanba.
Yace to shikenan.
Masu siye sukagama siye Yakama hanya yatafiyarsa.
Misalin. Karfe Tara nadare,suna zaune acikin dakin Gwagwgwo Hauwa daga faiza sai Gwagwgwo Hauwar,sunata fira,anan Gwagwgwo Hauwa ketambayerta.
Wai Faiza bakiso kiyi aurene?kokinfiso kizauna kita renon 'ya'yanki?yakamata ace kinyi aure yanzun,shekara kusan goma kina zawarci,yakamata kiyi aure tunda yaran suna iyayima Kansu komai,saiki barma innarkisu,Allah shike rayawa,tunda yanzun mazan baso suke ajemasu da Dan waniba,yakamata kifitar damuji kiyi aure hakanan,tin kafin afara yimaki surutu.
Faiza tace wallahi Gwagwgwo nima inaso inyi auren,Allah ne baikawo mujinba.
Gwagwgwo Hauwa tace cikin zawarawanki zaki fidda daya,kada kitsaya zaben wani mai kudi,rufin Asirinki aidakin mujinki,kindaima Sani tunda kinada iliminnan,kuma haryanzun kinazuwa islamiyya,kinsan lada da falalar datake game aure,Mara aure baya samunta,yadda zakuyi aikin lada keda me aure bafa za'abaku lada dayaba duk abinda zakiyima mujinki ladane,kiyima kanki fada kiyi aure hakanan.
Gaba daya jitayi idanunta sunciko da wasu zafafan hawaye,azuciyarta tace don basusan nafisu damuwa dason yin auren ba,shiyasa take fadin haka,ni kaina kodayaushe Addu'a nake Allah yakawomin muji nakwarai.
Kawai saikuma tayanke shawarar tasanar da ita dalilin dayasa
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4

Please Login or Register in order to submit comment