Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

shiga dakin umman Amir ta fada mata Deni yabar sakeena aiki kuma ta mata godiya. Umman Amir ta tabbatarwa da Iya gobe xata raka sakeena gidan aikin. Deni da sakeena suka raka Iya har bakin titi ta tafi.



Wannan shine mafarin fara aikin sakeena gidan Alh Dalhatu inda take musu aikin girki rana da dare, tana xuwa qarfe goman safe in Deni ya fita ta dawo qarfe shidan yamma Karin ya dawo. Da alqawarin xa a dunga biyanta 5k duk wata.



Hajia☺
[7/31, 2:15 PM] Reine Ghana: πŸ™†πŸ½β€β™€πŸ™†πŸ½β€β™€πŸ™†πŸ½β€β™€πŸ™†πŸ½β€β™€πŸ™†πŸ½β€β™€πŸ™†πŸ½β€β™€πŸ™†πŸ½β€β™€πŸ™†πŸ½β€β™€
πŸ™†πŸ½β€β™€MUQADDARI NEπŸ™†πŸ½β€β™€
πŸ™†πŸ½β€β™€2018πŸ™†πŸ½β€β™€
πŸ™†πŸ½β€β™€



1⃣2⃣

RAHMATULLAH (Hajia)


Ranarta ta farko a gidan aiki ta kasance kamar ranar da kowane irin ma aikaci kan tsinci kansa a gurin aiki. Bata fita da wuri ba domin ranar Saturday ne sai da Deni yayi musu wankin kayansu tas ya shanya sannan ya fita itama suka fita da umman amir wacce xata rakata.



Gidan babu nisa sosai tsakaninsu dan haka a qafa suka isa, tun daga gate sakeena ta gane ba qaramin hamshaqin mai kudi bane me gidan. Da suka shiga ciki kam har xuwa falo sai ta tsinke da ganin irin kayan alatun da aka qawata gidan dasu. Ita ada can ta dauka gidan anty Bahijja shine aljannar duniya domin shine qarshen gida me kyau a tunaninta amma kuma data shigo nan sai taga ai ko boy quarters din gidan data hango ta kere gidan Bahijja a tsaruwa.



Suka tadda matar gidan a falo tana danna waya. Umman Amir ta gabatar da sakeena bayan sun gaisa ta kuma fada mata kamar yadda sukai a baya aikinta iya kacinsa rana da dare saboda tana da aure. Matar wadda taji suna kira Mama ta kalli sakeena a tausashe tace "diyata sakeena ina miki fatan akkhairi da fara aiki a qarqashina, xan daukeki ya kema ki kalleni matsayin uwa. Inada yara guda 3 Babban namiji ne sunansa Ahlan sai qannansa Hassana da Usaina yan biyu ne. Yawanci basa tashi breakfast sai 11 nasan lokacin kinxo saboda haka kowanne xai fada miki abunda yakeso ki masa, banason qazanta kuma banason lattin gama abinci saboda mijina kullum cikin baqi yake duk da bai cika xama a gari ba sai qarshen wata amma yana yawan samun baqi wanda suke xuwa domin duba wani abun ko kawo Ahlan kudin ciniki da sukai da Alh. Karkimun rashin gaskiya karki dau abunda ban baki ba duk qanqantarsa, inkikai hakan xakiji dadin xama dani ni kuma xanyi iya yina inga na kare mutuncinki baxan bari a wulaqantaki ba. Kin yarda?" Sakeena ta sunkwui da kai tace "in shaa Allahu Mama xan kiyaye baxaki kamani da lefin cin amana ba nayi alqawari" Mama ta washe baki jin sakeena ta anbaceta da mama tace "Barka da xuwa gidan Alh Dalhatu" ta kwallah kiran Habiba. Taxo ta durqusa tace "gani mama" ta nuna sakeena tace "ga yar uwa na samo muku, itane xatana girki yanxu saboda haka aje a nuna mata komai xata fara aiki yanxu a kuma samar mata da time table na girki a gwada mata yawan abincin da ake" Habiba ta amsa taja hannun sakeena suka tafi tabar umman amir suna hira da mama.



Sakeena sai da ta kuma tsinkewa ganin girman kitchen din da kuma injinan da aka shaqare kicin din dasu kamar baxa a mutu ba, Habiba ta dunga nuna mata komai dallah dallah, da alama itace me wanke wanke. Sakeena batai girman kaiba yawanci bata san amfanin injinan ba ta dunga tambayar Habiba yacce ake amfani dasu ita kuma tana nuna mata dake ta jima a gidan.


Ta fara aikin girkin rana a tsorace dan kartayi ba dai dai ba ko kuma tayi be dadi ba a koreta. Tana cikin aikin taji an danno qararrawa wacce qararta har tasa sakeena firgita. Habiba dake jera kayan data wanke tace "sakeena duk sanda kikaji andanna wannan to ana kiranki ne a falo" sakeena tace "to rakani falon dan na manta hanyar" ta rakata kamar yadda ta buqata. Ta tarar da mama da wasu yan mata biyu kamar daya sak a falon suna xaune kowacce ta harde dayar taci kwalliya dayar kuma tana sanye da kayan bacci, da alama sune yan biyun. Ta duqa gaban mama tace "gani mama" ta kalli sakeena da murmushi da alama tafiyarsu xata wiyu dan tanason girmamawa tace "kinyi breakfast ko? Da akwai ragowar breakfast a kicin din kici" sakeena tace "ai nayi a gida kan na fito" tace "to dama yan biyu ke kiranki xaki hada musu abinci" ta juya garesu tace "to ga sabuwar me girkin tamu" me sanye da kayan baccin ta kalli sakeena a sheqe tace "ke sandwich xakimun sai Lipton kiyi sauri" cikinta ya qulle meye kuma sandwich? Ita a makaranta batai Food nd nutrition ba economics tayi. Tace "ke! Xaman me kike kije kiyi abunda na saki da sauri xan tafi lectures ne" cikin sanyi tace "meye sandwich? wlh ban iya ba" dayar ta sheqe da dariya tace "in kinsan baki iya girki ba kam meya kawoki nan? Sandwich dinne baki iya ba? Common sandwich?" mama ta shiga maganar da cewa "Ke usaina banason iya shege, kuyi mata a hankali mana dama wani sain kuke koremun yan aiki da iskancinku". Ta dubi sakeena tace "jeki kicin Habiba ta nuna miki littafin girke girke akwai aciki ki duba yacce akeyi ki je gida ma dashi ki dunga dubawa" tace "to"




Ta koma kicin ta fadawa Habiba saqon mama ta dakko mata tullin littafan girke girke ta bata ta kuma dakko mata sandwich bread dake qaton fridge din kicin din. Da taimakon Habiba da kuma littafin girkin wanda suke da harshen turanci sakeena ta hada dan guntun turancinta ta yiwa Hassana sandwich din ta hada a tray ta nufi falo gurin Hassana ta durqusa har qasa tace "gashi Anty" kan Hassana ya fashe jin ankirata da Anty. Ta dubi usaina tace "kinji yanda ake girmama na gaba ko? Kinqi kirana anty yau Allah ya kawo me kirana da Anty har gida" Usaina tace da sakeena ke nima ki dunga cemun Anty dan tare mukaxo duniya da ita ko da secon 1 bata girmeni ba" mama tana jinsu tana dariya. Hassana ta dubi sakeena tace "kaimun bedroom dinmu yanxu xan shiga inyi brush" ta fada tana nunawa sakeena up stairs. Usaina tai sauri tace da Hassana "Da Allah malama ya xaki turata sama dakinmu? Ko kin mata abunda Hindu ta mana, tadaukemun xobe na na English gold ban taba sawa ba? Ta cije lebe ta qara da cewa Abba yace 280k ya saya mana amma ta dauke ta barni da takaici, ita wannan din kinsan halinta ne? To wlh duk abunda naga babu sai kin biyani" mama ta harareta tace "bansan cin fuska Usaina, sakeena hau ki ajiye mata" tahau jikinta a salube, daki dayane tal a saman wanda ke nuna sukadai ne a benen. Ta buda ta shiga, a gurguje ta ajiye ta fito tana jinjina wannan uban daki da uwar dukiya duk na yara biyu kacal? Tab.





Qarfe daya da rabi ta gama girkin rana ta lodoshi a wata kura da ake turawa ta silver ta kawo falo, Habiba ta koya mata yadda ake shirya dinning, yadda ake ajiyewa kowa farantinsa a saitinss da cup. Mama taxo ta yaba kwarai da girkin bayan taci tace "da kyau sakeena diyata ashe expert ce akan girki duk da baki da shekaru" wannan yabo na mama yadan bawa sakeena kwarin gwuiwa. Ta koma kicin ta dora girkin dare duk da kwabarta da Habiba keyi na cewa ta bari sai anjima lokacin dora girki beba taxo suje dakinsu suyi kallo. Tace "barni inyi ingama Habiba inkoma gida da wuri" ta maida girkin dare, tana ta aikinta cikin gwarewa da hijabinta xurmeme. Wajen qarfe biyar mama ta shigo kicin din tace "sakeena me ake dafa manane gidan ya cika da qamshi haka." tayi dan murmushi tana wanke kifin data ciro a freezer a sink tace "Fatan erish potato ne da fresh fish nayi, sai jellof din cous cous sai kifi da xan gasa yanxu" mama ta bude food warmers din tace "um yummy" sukai dariya a tare da sakeena tace "kamar kuwa kinsan bamason tafarnuwa da yawa yar kadan ake sakawa. Yanxu dai kiyi haquri xan qara miki aiki duk da kin kusa gamawa, dan Allah zobo drink xakiwa Ahlan bayasahan lemon kwali. Kuma in akwai abunda kike buqata na girki saiki rubuta a qaro" sakeena tace "to bakomi mama yanxu xan hada zobon"




Ta dafa xobonta da pineapple da kuma cocumba tasa danyar citta ya dahu ta narka sugar ta xuba. wanda hakan shiya xama aikinta na qarshe, ta hada komai takai dinning ta shirya kamar daxu, lokacin 5:30 a gurguje ta gyara kicin din ta maida kayan datai amfani dasu, na wanke wanke ta waresu Allah Allah take ta tafi gida kar Deni ya rigata dawowa.




Mama ta sakko bayan ta gama kallon sakeena ta CCTV camera din dake dakinta wacce ita da yayanta kawai sukasan da ita a gidan. Ta yaba kwarai da tsaftar sakeena da salon aikinta yau daya kawai.



Sakko warta tai dai dai da shigowar sakeena falon ta tsuguna tace "mama na gama inbabu abunda xa ai xan tafi" Mama tace "To sakeena sannu da aiki amma beyasa bakici abinci ba daga na rana harna dare, ke banaji ko ruwan gidannnan kinsha" sakeena tai shiru tana tunani, ita wlh tama manta da abinci dan tunda taci tuwo a gida rabonta da kai wani abu bakinta kuma batajin yunwa kodan ta saba yini da yunwar ne ko kuma dan aiki yasha kanta?



Tadan motsa tace "naci abinci mama, ina gamawa na xuba naci" tayi dariya tace "banason qarya sakeena wlh ko ruwa bakisha ba" tai xukudi tana mamakin ya akai mama tasan bataci komai ba? Ta kwantar da kai tace "yanxu innaje gida xanyi mana girki shiyasa nake sauri in koma"



Mama tace "kinga inkinaso mu shirya dake in kinyi abincin rana ki dunga ci, na dare kuma ki dunga diba kina tafiya dashi gida in kinje kwaci da mijinki kin huta girki, inba baki da raayin cin abunda kika dafa xaki iya dafa duk abunda kikeso. Qin cin abunda kika dafa kan iya janyo miki xargin kin xuba wani abun aciki saboda haka cin abincin wajibine a gareki" sakeena ta bude baki cikin tsoron jin intaqi cin abincin xa ace tasa wani abun. Mama tace maxa dakko warmer a kicin ki dibi abinci ki tafi kar mijinki ya dawo ya taddaki kina qaurin girki baki wanka ba.



Taje ta dakko tana dariyar jin abunda mama tace. "maxa xuba duk abunda kikeso" ta fara diban abincin kamar na wasan yara.




Mama ta taso taxo gurin ta karbi cokalin hannunta ta fara xuba mata abincin tana cewa "kawo in diba miki, haka kawai yarinya xaki janyomin Allah ya isan Abba tahau kaina. Shidin yasha fadamun cewa in akabar koda mutum daya dake qarqashinsa da yunwa be yafe ba, saboda shima da dan aikin gida ya soma rayuwa kafin yayi nasa arxiqin dan haka be yarda a wulaqanta me aiki a qarqashinsa yana cewa mutum daraja gareshi bakasan wazai xama ba a future. Sannan banda abinki sakeena mu 4 ya xamuyi da wannan abincin daga ni sai Ahlan sai yan biyu Alh baya gari su kuma masu aiki suna nasu girkin a kicin dinsu daban. Saboda haka ki dunga sakin jiki kina diban abinci yadda zai isheku dan inba baki diba bayarwa xa ai indai mun gama ci, ni banason kwauro da dan hannu ki kiyaye kinji diyata" ta qarasa maganar tana miqawa sakeena warmer din data shaqe taf da kalolin abinci. Sakeena ta karba tana godiya ta juya ta tafi tana jinjina karammaci irin na mama kamar ba matar me kudi ba.




Cikin sauri take tafiya burinta ta isa gida kafin Deni ya dawo. tai farin ciki data isa be dawo ba, Mariya na xaune da daurin qirji tana girki a kofar daki, tabi qayattaccen flask din hannun sakeena da kallo.




Da sauri ta jona ruwan wanka, dakin fes yake baya buqatar gyara dan ta gyara kanta fita. ta dakko flask din ta shiga dakin umman Amir ta nuna mata abincin tare da yimata bayanin duk yadda ta kaya yau a gidan. umman Amir tayi dariyar farin ciki tace "ai dama na fada miki indai kika riqe gaskiya xakiji dadin xama dasu. Suna da mutunci" sakeena tace "tabbas naga hakan" ta xubawa umman Amir abincin duk kuwa da tana kwabarta ta barshi amma bata fasaba sai data xuba mata.



Har tai wanka tayi kwalliya ta shinfida musu tabarmar cin abinci ta shirya kwanikan Deni be dawo ba. sai da ta fito tana kwashe kayan shanyar da yayi musu da safe saiga sallamarsa, suka kalli juna cikin farin ciki yayi murnar ganin tabi umarninsa ta dawo kafin ya dawo.



Ta cire ruwan data jona masa takai masa yayi wanka, a gida yayi sallar magrib saboda an idar a masallaci kuma yana idarwa ya xauna gurin cin abinci alama yunwa yakeji. Itama taxo ta xauna, shiya bude flask din yayi dum ganin abunda yake ciki ya dubeta ya qara duban abincin wanda qamshinsa ya cika dakin daga budeshi sai a lokacin ya kula da food warmer din bata sakeena bace. Ya qura mata ido, ta sunkuyar da kai tana wasa da yatsunta.



Ya fara magana cikin bacin rai "Sakeena wannan abincin da kwanon daga ina" Cikin sanyin jiki tace "kaso nane na gidan aiki na taho dashi muci tare" ya daka mata tsawa da cewa "ke! rufemun baki" taja bakinta ta tsuke ta fasa yimasa bayanin da yasa ta taho da abincin.


Ya fara fada kamar xai daketa "dan kin rainamun hankali kuma na barki aiki shine xaki tahomun da abinci? Wato ga talaka dan iska wanda bazai iya daukar nauyinki ba ko? Shiyasa kika yanke shawarar fara kawomun abincin gidan masu kudi daga haka kuma saiki rainani ki daina yimun biyayya ko kifi qarfina tunda kina ciyar dani wlh baki isaba sakeena, nace baki isa ki maidani sakarai ba" ta fashe da kuka jin yadda yake magana da daga murya wanda ta tabbata ana jiyosu a tsakar gida, amma ga mamakinta kukanta bai hana Deni hargagin masifar da yake ba. Da sauri ta nufeshi ta rungumeshi ta qara sautin kukanta, sai a lokacin yayi shiru. Tana cigaba da kukanta tace "ya Deni ka tsaya ka saurareni kaji yadda akai, wlh ina sonka baxan tabayin abunda kake fada ba koya kake ina sonka kuma xan maka biyayya Dan Allah ka saurare ni" Ya qara matseta jikinsa tsam yana shafar bayanta yace "to yi haquri yimun bayani kinji, ina sonki sakeena ina tsoron kar idonki ya bude da rayuwar gidan masu kudi da cima me dadi ki gujeni" tace "ya Deni soyayyar gaskiya bata qarewa, baxan taba iya gudunka ba kamar yadda nasan baxan daina sonka ba" yayi murmushin jin dadi, tana jikinsa ta fada masa duk yadda akai.



Ya fahimceta kuma ya yadda dan bai taba samunta da yimasa qarya ba, ya sauketa sukaci abincin tare yanata santi da mamakin wai sakeena ce tai wannan girkin, ita dai yaqe kawai take, sam bataji dadin abunda ya faru ba tsakaninsu yanxu. Abincin ma tsakura kawai tayi.



Bayan sallar isha suna falo yana gugar kayansu daya wanke ita kuma tana duba littafan girkin da Mama ta bata daxu, tanayi tana hamma bacci takeji dan yau batai baccin data saba yiba na safe.



Ya gama gugar yaxo ya tada ita daga baccin data fara yace "sakeena xo muga wani film dana samo mana" tace "to" suka shiga uwar daki sukai shirin bacci ya kunna musu film din "KI&KA" na kareena kapor da arjun kapor suka fara kalla, itakam basuyi nisa ba tayi masa sai da safe ta kwanta. Shima ya kashe wayar ya kwanta a bayanta yace cikin rada "sakeena har yanxu fushin kikeyi dani?" tace "a a just inajin bacci ne" ya matseta sosai yace "ni kuma da sonake kimun irin kiss din da muka gani yanxu a film" tayi dan murmushi tace "kayi haquri sai gobe" bai qara cewa komai ba ya haye jikinta dan yau baijin xai iya haqura, batare da wani hadin kan sakeena ba ya samu biyan buqata.



Washegari ta isa da wuri da Deni suka fita tare sai da yaga shigarta gidan sannan ya tafi kasuwa bayan ya qara bata haquri dan ya lura tun jiya bata ware ba.



Dake Sunday ce duk yaran suna gida, ta shiga falo domin gaida mama da kuma jin abunda xa a dafawa su Hassana na breakfast. Ta rar da mama da wani saurayi yanata game a system yana ta ihu da tabara kamar yaro qarami abun babu ko tsari. Saurayin da xaiyi saan mijinta koma ya girmeshi wai shine ke wannan ihun dan kawai yanayin game 😏 Allah sarki ajebo.



Ta gaida mama yayin da ihun saurayin ya hana taji abunda mama ke fada. Mama ta dubeshi tace "Ahlan kaxo ka cikamun falo da ihu ka hana inji kunne, tashi ta tafi sashinka ina dalili xakaxo har gurina ka takuramun?" ya juyo yace "Haba Mom cinyeni fa akai, memakon kimun jaje." ya juyo sai a lokacin ya lura da sakeena, ya qura mata ido kana ya Kalli mama yayi mata alamar wacece da hannu? Mama ta bashi amsa da cewa "sabuwar me girkinmu ce saika fada mata abunda xatai maka na karyawa" ya juya ya qara kafawa sakeena ido yace "Duk abunda hannunki ya dafa xanci, amma anya ke a shekarunki har kin wani iya girki?" Batace komai ba sai tashi datai ta tafi domin sai takega inta tsaya bashi amsa kamar tozarta aurenta ne.




Taje kicin ta samar masa da abun breakfast ta dama masa oat ta kai masa falo kan dinning lokacin ta tarar su Hassana ma sun sakko, tana ajiyewa ya tashi ya haye table din tare da cewa "kewai bakijin xafi ne kike yawo da wannan xurmemen jalbab din? Muda muke falo cikin AC ma munajin xafi bareke a kicin gashi kin yaba wannan abun." wannan Karon ma batace komai ba ta nufi hanyar sauka daga dinning area din. Yayi caraf ya riqo hannunta yace "ke! Wanene ke ina miki magana kinmun shiru? Ki tsaya kiyi serving dina" ta fara kici kicin kwace hannunta ya kuma riqeta gam, su Hassana da suka hau dinning din yanxu suka fara dariya. Mama tanacan kan kujera tana danna waya ta hangesu ya riqe sakeena tana yunqurin kwacewa.




Tace "kai Ahlan, cikata karka qara riqeta matar aure ce, banason wannan dabia taka ta turawa" a tare Ahlan dasu Hassana suka maimaita kalmar "matar aure???" suka jiyo suna kallon mama dan tabbatar da abunda ta fada, ta qara tabbatar musu tace "wlh matar aure ce, a gidan su umman Amir suke haya da mijinta" Ahlan ya saki baki yana qarewa sakeena kallo kafin ya maida kallonsa ga mama yace "wai dama har yanxu qasar nan ba a daina Child Abuse ba? Wannan yarinyar ina ta isa aure inba xalunci ba, aiko su Hassana basu isa aure ba bare wannan yarinyar da na tabbata batafi 15yrs ba"



Sakeena dai tunda ta samu ya saketa ta gudu dan haka bataji qarshen film dinba.



A ranar haka tai aikinta a kicin yayin da Ahlan ya yini a falo duk sanda ta shigo saiya bita da kallon qurullah duk kuwa da uban hijabin dake jikinta.

***** **** **** ***** ****

A kwanaki 7 da sakeena tayi tana aiki a gidan ta fuskanci mutan gidan Kam basu da matsala tun daga kan mama har yayanta. Matsalarta daya Ahlan wanda duk da anfada masa tana da aure be fasa yimata kallon qurullah ko janta da hira inta shigo falon yin wani abun. Wannan dalili yasa bata shiga falo indai yananan kuma tana qoqarin gama aikinta kafin qarfe shida ta tafi gida kafin ya dawo office. Ita dasu Hassana babu matsala dan tasamu karbuwa gurinsu a dalilin girmamasu da take. Sau tari insuna musun kayan da xasu saka ita ke bin bayan Hassana mama kuma ta bi bayan Usaina aita muhawarar kayan da xa a saka kafin daga baya sakeena ta sasantasu cikin hikima.




A wannan kwanaki datai tana aiki a gidan yasa daga ita har Deni sun dawo hayyacinsu ma'ana sun daina kwanan yunwa sunyi kyan gani kullum xataxo musu da abinci isashshe suci har su rage, inxai kwana su ajiye inbaxai kwana ba su bayar. Abunda Deni ke samu a kasuwa kuwa sun barshi a breakfast, in aljihunsa da nauyi suyi tare inbabu nauyi kuma ya siyo abunda xaici shikadai ita intaje gidan aiki saita karya.



A ranar kwana na 8 Iya taxo musu da magriba. Ta kallesu sunyi kyan gani akan kwanakin baya tace "kai wannan mutane Allah ya saka musu da alkhairi har kunyi kyan gani. Nima yanxu hankali ya kwanta kullum ina cikin tunanin kun kwana da yunwa, dama xuwa nayi inganku ai kuwa nayi farin xuwa naji dadin ganin canji" qarshe dai da Iya suka hadu sukaci abincin da sakeena taxo dashi a kwano daya. Deni ya qara girmama Iya a xuciyarsa tunda har ta damu da halin da suke ciki shida sakeena, sabanin tasa uwar da yan uwansa da basa nemansa saboda bashi da shi kuma basasan matarsa. Suka raka Iya har titi tahau napep ta tafi.



Ita da Deni kam basu da matsala gishiri kan kaxa suna xaman lfy da soyayyarsu mai shiga rai. Inta dawo tana bitar littattafan girkin da aka bata, turancin da bata gane ba ta nunawa Deni ya fassara mata.



Tana tsaye a kicin tana aikin abincin rana, yayin da Ahlan ke tsaye yana kallonta ta tagar kicin din ta waje jikin net. Kallonta yake kamar yadda ya saba a kwanakin weekend inyana gida, ya furta "Gold a kwata" ma'ana kyakykyawar mace a gidan talauci. Sakeena ta juyo a firgice jin muryarsa da kuma abunda yace ta qara gyara hijabin jikinta tace "kana buqatar wani abune in miqo maka?" yace "no pretty kawai ke naxo kallo" ta qara daure fuska tacigaba da aikinta, wannan hali na Ahlan yana mutaqar bata tsoro duk da anfada masa tana da aure amma bai fasa kallon ta ba kamar ba musulmi ba ko kuma kamar besan abunda kalmar aure take nufi ba. Kuma tasan ko giyar wake tasha baxata iya fadawa Deni wannan batunba, saboda tanason aikinta kuma fadawa Deni yana dai dai da Third World War (yaqin duniya na uku) Ahlan yakai 18 minutes yana kallonta kafin ya juya ya tafi, ta sauke ajiyar xuciya tace "Allah kasan temakon da aikin nan ke mana ni da mijina kamar yadda kasan abunda bawannan naka yake nufi dani, Allah ka shiga tsakanimu."




Ranar laraba da wuri ta gama girkin rana wajen 11 saboda Habiba tace xatai mata qunshi da kitso ta iya. Tana gamawa suka tafi can dakinsu Habiba aka fara saka mata lallen a qafa da hannu wanda Habiba tace 2 hrs yakeyi nan da 1:30 xa a cire. Inna wata dattijuwa dake dakin itama tana aiki ne a gidan sai yaba kyan qunshin take, sakeena kuwa bakinta yaqi rufuwa yau xata burge Deni rabonta da qunshi tun na bikinsu. Ana gama qunshin aka fara kitso duk da Habiba tana cewa bata iya sosai ba amma dai yayi kyau sosai akan sakeena dake bashi da cika. Daya da rabi tanayi aka cire qunshin dan sakeena ta damu acire xatai sallah.




Masha Allah qunshin yayi jajur a farar qafarta,

Please Login or Register in order to submit comment