Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

cookies" wacce Sadddiq ya koya mata Iya na yimata fadan idonta ta dakko glasses dinta tasa tace "Kinga nasa glasses ba komi da xai faru" koda Deni ya tashi bacci yaxo giftawa ta dakin Iya xai shiga toilet ya hangi Saddiq da sakeena xaune kusa da juna suna duba waya suna dariya. Baqin ciki da wani irin kishi ya qulle masa xuciya ya quduri aniyar daukar mataki akansu.


Da yamma bayan angama wankan jego tana xaune tana yankawa Iya kubewa a kujerar tsakar gida tana sauri ta gama taje tadau wayarta taci gaba da game dinta na word cookies ta wuce inda Saddiq ya batta kamar yadda ta cika masa baki kan ya fita.



Taji anshigo gidan lokacin babu kowa a tsakar gida sai ita, a xatonta Saddiq ne tana cigaba da yanka kubewar tace "Saddiq albishirinka? Naje Banana level 9" jitayi kawai an chafke mata maqogwaro an hadata da bango ana neman kaita lahira.



Ta waro idonta ta cikin medical glasses dinta taga Deni ne ya shaqeta idanunsa jawur ya fara magana "Ni xaki yaudara? Wato kin cuci banxa ko? Shin sakeena meyasa na kasa cireki a xuciyata? Meyasa da kikai aure akan aurena a Lagos da kika dawo hayyacinki baki xubar da cikin jikinki kin dawo mun haka ki buyemun abunda ya faru mucigaba da xama? Meyasa kike axabtar da xuciyata?" Dakyar sakeena ta kwallah qara tace "Iya xai kasheni"


A tare Iya da su Hajjo suka fito tsakar gida sukayi arba da Deni shaqe da sakeena tana qoqarin banbare hannunsa daga wuyanta ta kasa. Iya cikin daga murya tace "Nura cika mata yuwa" Hajjo kuma cewa tai "Deni meya gama ka da ita kai da xakai aure kwanaki kadan masu xuwa?" Babu wacce ya kula a cikinsu yacigaba da yiwa sakeena maganganu. Iya dataga yana neman kai sakeena lahira ta dakko bokitin qarfe ta daga ta kwantara masa a baya tace "Cikata dan ubanka babu abunda ya hadaka da ita yanxu, inka manta in tuna maka ka saketa kuma ta gama iddarka, inamaka albishir cewar kai da sakeena har abada domin ta gama auren wanda besan darajarta ba kuma riqaqqen mayaudari irinka" ya cika sakeena badan xafin kwala masa bokitin da Iya tayi ba sai dan xafin maganarta ta cewa shi da sakeena har abada kuma shidin yaudarar sakeena yake.


Sakeena dai tunda ta samu ya cikata tai bayan Iya tana haki cikin tsoron Deni. Deni ya kalli Iya yace "Yanxu Iya nine ke yaudarar sakeena? Meyasa kowa ya budi baki yake cewa ba sonta nake ba yaudararta nake? Meyasa babu wanda yake duba girman lefin data yimun nayin aure yayin da ni kuma nake xaman jiranta? Meyasa data dawo hayyacinta bata nemi saki gurin wancen tsinannan ba ta xubar da cikinsa ta dawomun a sakeena matata muncigaba da xama?" Iya tana nunashi cikin bacin rai tace "Sageer ba tsinanne bane don yafita qaunar sakeena ko aranar daya fara ganinta a rayuwarsa sai da yayi mata abunda a gaba daya xamanka da ita na fin shekara bakai mata ba saboda haka wlh ka rabu da yata ko kuma nayi qararka kotu shege butulu me mance alkhairi"


Hajjo itama ta harxuqo cikin takaici abunda Deni yayi da kuma xafin maganganun Iya taja Deni itama ta turashi bayanta kamar yadda sakeena ke bayan Iya tace "Ya isheki haka Hafsatu karki qara yiwa Dana baki akan wata banxa sakeena wacce bata da cikakken asali, wannan bala'i da masifa ya isheni akan wannan yarinyar, muna xamanmu lfy kikaje kika dakko mana riqon wannan annobar ta hargitsa mana gida. Tunda sakeena taxo gidannan xaman lfy yayi qaura, ta hargitsamun xaman lfy, ta kashemun aurena, ta silarta na rasa kadarata(gona) da nake taqama da ita sannan ta rabani da xaratan yayana maxa guda biyu da nake tsanin so kuma nake ji dasu sannan na dora duk wani buri nawa akansu" Hadixa ta dafe goshi (🤦🏽‍♀)) jin Hajjo ta fadi matuwar aurenta da suketa boyewa.



Iya tace "Da mutuwar aurenki da kuma rasa kadararki har xuwa kan rabuwa da yayanki duk babu ruwan sakeena aciki mugun halinki da baqar aniyarki ce ta janyo miki dan dai ke dabbace shiyasa baki ganeba, mugunta ai futsarin fako ce. Sannan karki qara kiramun yata da annoba domin sakeena xuwanta gidannan alkhairi ne daga kan mijinki har xuwa kanki da yayanki babu wanda bataiwa rana ba har aikin da Deni ya samu kike taqama dashi kuma kika rabashi da sakeena saboda aikin ai itace silar sama masa aikin, saboda haka Hajara kece annobar gidannnan ba sakeena ba" Haka dai kowacce ta shigarwa danta fadan ya koma nasu suka cigaba da amayar da abunda ke cikinsu yayin da Deni da sakeena kowanne ke bayan uwarsa a labe.


Deni ya fito daga bayan Hajjo, be wani damu da kukan da Hajjon keyi ba ya tsaya gaban Iya idonsa jawur yana nuna sakeena yace "Saddiq ko? Shine next target dinki ko mayaudariya? To wlh kodai ki samawa kanki lafiya kiyi cutting relationship dinku ko kuma in kashe shi akanki, na shirya tsaf dan fara xubar da jini akanki" ya juya ya fice yabar Hajjo tana ihu da salati a hade.
Iya ta juya saiga Baba a tsaye yana kallonsu da sauri ta nufeshi tace "Yawwa malam wlh kaiwa danka tsakani da sakeena a gidannan ko kuma ayi babban tashin hankali" ya dubeta da takaici yace "Akwai tashin hankalin daya wuce wanda kukai yanxu Hafsatu? Kuntara yayanku kuna hauka a gabansu maqota na jinku kun taunamun asiri kun taunawa kanku, kuma harke da nake yabonki?" Jikinta yayi sanyi ya kewayeta ya wuce daki.



Deni ya dauki mota ya fafareta ya bata wuta ya dunga sharara gudu a titi shi kansa besan inda xashi ba tunanin yake me xurfi wai shin da gaskene abunda mutane da abonkansa ke yawan fada na cewa yaudarar sakeena yake? Kowa ya bude baki abunda yake fada kenan, yawancin abokansa na cikin unguwa sun daina kulashi tunda ya saketa acewarsu beyi hallaciba yadda tasha wuya dashi kafin yayi arxiqi yaxo yayi arxiqin ta silarta sannan kuma Hajjo ta hanata jin dadi shi kuma ya saketa bayan yar wata qaddara ta afka mata. Hatta wasu abokansa na gun aiki wadanda sukaji tarihin soyayyarsa da sakeena sun fita harkarsa. Tambayar kansa yake wai da gaske yaudararta yake ko kuma mutanene suka fahimceshi ba dai dai ba? Wlh shi harga Allah son sakeena yake da wani irin matsanancin kishinta duk da lokacin daya aureta batayi daidai da tsarinsa ba amma kuma ya kasa rejecting dinta, sai yanxu data xama irin macen da yakeso me tsafta da kyale kyale sai Sageer ya fado rayuwarsu duk da ya temaki sakeena yayi mata abunda be taba yimata ba shi Denin amma kuma ta silarsa aurensu ya qare. Haka ya dunga tunani yana driving babu gurin xuwa.

****** ****** ***** *****

Saura sati biyu biki Deni ya kawo kayan lefe daya hada a gidan abokinsa akwati biyar da kit shaqe da kaya donsu gani a kuma kai gidansu Surayya. Suka baje kaya ana gani Hajjo ta gayyato tsirarun qawayenta da suka rage na cikin unguwar wadanda suke kulata aka kuma kira dangi aka yini ana ganin kaya da kuma habaici da yaba bajintar da Deni yayi duk da ba haka taso ba so tayi ya bata kudin hado kayan tayi cuwa cuwarta aciki ta samu kayan fitar biki. Ba'a gayyaci Iya ba kuma itama ko an gayyaceta baxataje gani ba saboda tunda akai fadan Deni da sakeena suka fara xaman gaba.


Deni da Baba sunso a bawa maxa sukai lefen amma Hajjo ta kafe tace sai mata don a qara gano mata gidansu Surayya kuma su samo tukuici. Ta hada gayyar mata da dangi da kuma yayanta mata kaf dan tsabar qauyanci aka tafi rijiyar xaki gidansu Surayya.


Basu wani dade ba sosai ba sai gasu sun dawo jiki a sanyaye suka baje xancen da suke tafe dashi a tsakar gida duk da kwabarsu da Hajjo keyi suyi shiru su shigo daki. Yan kai lefe dai sunje kuma sunsamu gidan su Surayya makeke fiye da yadda Hajjo ke xato amma koda aka gansu sai aka canja fuska aka dunga fesa fresheners wai sun cika falon babu iska sannan kuma aka raina lefen da suka kai a gaban idonsu aka dunga saka masu aiki suna daga kowacce atamfa anai mata kudi a wulaqance. Aka gama wata qanwar uwar Surayya ta dunga xarar kayan lefen tana rabawa yan kawo kayan a matsayin tukuici. Ana gamawa aka dauke baskets din da suka gani a gurin shaqe da snacks da drinks da aka tanada don basu aka shige daki aka barsu jiki babu kwari suka taho. Wata qanwar Hajjo tace "Deni kam ya samo diyar masu arxiqin da kike buri amma babu alamar suna da mutunci" zahra tai tsaki tace "Arxiqin da babu mutunci da daraja dan adam ai tsiya ta fishi" Yan kai lefe suka watse bayan angama fada da Hajjo akan wai sai sun bata atamfofin da aka basu ai Deni ne ya siya. Su kuma suka hanata sukace ladan wulaqancin data turasu akai musu.


Sakeena da Iya na jinsu Iya tana dariyarta a fili tana cewa "Allah kenan tunkan aje ko ina ya fara fidda haqqin marainiyar da aka azabtar" Sakeena dai ta dan saurarawa waya ta maida hankali kan bitar karatun jamb da Baba ya samo mata pass questions. Ta janyewa Saddiq sosai saboda furucin Deni na cewar xai kasheshi, Saddiq besan anyi haka ba yaga kawai ta dauke masa wuta wanda hakan ke axabtar dashi. Ta samu no Hassana a wayar Iya suna xumuncinsu sosai harda Usaina dake qasar waje, saura yan kwanaki kadan ayi jamb abunda bata ganeba ta tambayi Baba yayi mata bayani.


Washegarin kawo lefen Deni aka kawo na Hadixa shi amma maxane suka kawo, suka gama shewarsu da alama sunsamu yacce sukeso. Amina dai tana ta aikin bankawa kanta hayaqi safe da yamma kamar yadda malam ya sakata ga kuma soyayyar sageer dake qara xurfi a xuciyarta.


Acikin satin dai aka kawo IV na bikin gaba daya sakeena tana ganin IV hawaye ya wanke mata fuska duk da Iya na gurin ta tuna nata auren ko arxiqin IV bata samu ba balle lefe ko kudin aure saboda ita din marainiyace bata da gata Iya ta bata haquri da kalamai sanyaya ta share hawayenta.


A cikin satin dai rigima ta kuma tashi akan Deni ya kama gidan haya da zasu zauna da Surayya sunje sungani sunce yayi musu kadan, shi kuma yace iya qarfinsa kenan in sun raina afasa auren don haushinsu yakeji tun akan wulaqancin da sukai akan lefe duk yadda Hajjo taso a boye xancen kar yaji sai da zahra ta fada masa. Ganin ya kafe ga kuma yarsu tana sonsa sosai kuma dama ta dade a qasa babu miji hakan yasa Babanta ya basu gida makeke a goron dutse, Deni beso hakan ba saboda gudun raini amma Hajjo tayi tsalle ta dire tace saiya karba don haka takeso Deni yayi aure samfurin aureni ka huta.


Angama rigimar Deni ta Hadixa ta kunno kai anje anga qerarran gida Yusuf yayi akayi ta fafa da fangima da nunawa mutane gidan a waya. Baba ya hada tanadin da yayi wanda bashi da yawa sosai saboda qurarren lokacin da aka saka, ya hada da kudin aurenta ya basu suyi siyayya. Ananfa balli ya tashi Hajjo tai tsalle ta dire tace sam dole yayi hubbasa saboda gidan arxiqi xa akai Hadixa ya kawo kudi sosai su taru su rufa mata asiri, shi kuma yace Iya qarfinsa kenan. Ta tari Deni da xancen ya sayi kayan daki da kujeru kamar yadda yayi abikin Fiddausi yace bashi da kudi saboda shima nasa auren wanda qarya yake yayi hakanne saboda haushin Hadixa da tsanarta da yayi saboda itace kanwa uwar gamin data taka muguwar rawar watsewar aurensu da sakeena.


Wannan abu ya mugun dagawa Hajjo da Hadixa hankali murna ta koma ciki yayin da Hadixa ta maida kuka abincinta safe rana da dare.


Dakyar Hajjo tai buga buga aka samarwa Hadixa saitin furniture na kan titi guda daya da kujerun hannu sai yan kwayoyin tukwane guda uku da yan tsirarun kayan kicin da ko buhu basu cika ba aka bar kudin sadakinta da xa a kawo a matsayin kudin siyan katifa, a falelen gidan da yusuf ya gina wanda xaici kayan gado kusan set 4. Hadixa tana arba da kayan a matsayin kayan dakinta ta yanke jiki ta fadi. (Hmm yanxu kika fara gani 😏)



Ana saura kwana 3 asoma biki sakeena ta tafi xana jamb a airport road, tun safe sai yamma ta dawo a gajiye liqis. Ta tarar Iya ta hada musu kaya jaka biyu da rashin fahimta tace "Ina xaki Iya?" tana dariya tace "Baggadano xamuje muyi musu sati daya banaso ai bikin nan muna nan saboda gudun fitina" Sakeena ta dane Iya tana ihun murna, kamar tasan bata son ko xancen bikin ayi balle kuma ta gani.


Da sassafe ranar Laraba suka daga Baggadano (Dawakin Tofa) sakeena murna kamar me, rabonta da garin tun shekaru kusan 7 abaya.


Sun isa Baggadano da rana akai murna da xuwansu fiye da xatonsu saboda an gansu fes. A dakin Inna sukai masauki daya dakin matar Dahiru ce ciki sai dayan na ragowar maxan da basuyi aure bane. Aka kewayesu ana murna aka gaggaisa aka dunga aikin shigo da kwanikan har daga gidan yan uwan sakeena mata da sukai aure, garin yacigaba sosai ya tashi daga qauye ko ina ga wuta nan da aiyukan raya qasa anayi. Sun miqe sunci sun qoshi sun huta gajiya. Xuwa dare kaf yan gidan sun dawo harda mata na gidan aure sunxo ganin sakeena wacce labarin kyan datayi ya cika garin.


Suka hadu a tsakar gida iskar damuna na kadasu anata raha kamar babu wani abu marar dadi daya faru abaya. Iya ta fada musu duk abunda ya faru tun daga kan auren sakeena har xuwan da sukayi nemanta nan da kuma yadda lamarin ya kaya daga baya. Kuma tayi hakanne saboda Baba ya umarceta ta fadamusu gaskiya dan ta iya yiwuwa sunji xancen a radio duba da yadda abun ya fasu, sannan kuma yan uwantane bata da kamarsu Kamar yadda yace koda basa sonta. Suka jinjina duk jikiinsu yayi sanyi Yakubu yayanta yace "Wlh wani abokina ya karanta a jarida ya fadamun na qaryata ashe gaske ne" shi kuwa Labaran dake yana da xafi cewa yayi "Ai wlh Iya da tun a lokacin kika fadan dasai nakai qarar uwar mijin ta sakeena" Iya dai ta taushesu ta basu haquri da fadamusu ai komai ya wuce kotu ta raba maganar. Suma suka nemi yafiyar sakeena akan abunda sukai mata abaya aka shirya hakan yayiwa Iya dadi sosai sun dade suna hira kafin Dahiru ya kori masu auren a rufe gida.


A ranar sakeena tai kwanan farin cikin da rabonta dayi tun tana gidan Deni suna xaman soyayya. Wai yau itace a mahaifarta cikin yan uwanta suke xaune lfy ana riri tata? Lallai Allah maji roqon bawa kuma addua bata faduwa qasa banxa, sai dai wata ana jinkirin amsa maka ita.


Washegari Inna da kanta ta dafa musu ruwan wanka da alama duniya tayi mata nata karatun ta saduda. Sukayi suka shirya aka dunga aikowa da su sakeena kwanikan abinci. Haka suka yini baqi kafin yamma tayi Musa qaninta ya rakasu maqabarta kabarin Nura da kuma iyayen sakeena harda kakanninta. Sukai musu addua kuma ta biya kudi aka daga wasu qaburbura da suka fara ruftawa saboda damina.


Taji dadin kwanakinta a Baggadano sosai taci abincin gargajiya ko adafa mata abunda ranta yakeso ita da Iya sannan Yakubu da beyi aure ba ya goyata a machine dinsa suyi ta xaga qauyen koya kaita gona gurinsu Dahiru ta tayasu aiki suna kwabarta amma takance babu komi yaya mutum ai baya manta asalinsa. Iya ta xage tana dafe dafen mugunguna da itatuwa ita da Inna suna saka sakeena ciki ta xauna ta dade saiya huce ta fito wanda Iya tunda sakeena tai bari taso yimata haka amma bata samu dama ba saboda su Hajjo. Ta dage sosai ta gyare sakeena tas wacce tajita ta koma zam zam kamar bata taba jinin al adaba balle wani aure.


Tana yawan daukarsu photo da wayarta ita da yan uwanta wadanda tun suna dari dari da ita harsuka saki jiki ganin bata kyamarsu komai tare take dasu ta daqumesu suyi photo bata nuna musu ita yanxu yar gayuce ko yar Birni. Su da sukaje yin sati daya sai da sukayi kwana 10 cur saboda dadin xama da sukaji (Allah sarki kowa yabar gida) ranar kwanansu na 9 Yakubu ya goya sakeena a machine dinsa ya kaita cikin dawakin tofa ATM kamar yadda ta buqata, ta cire kudi sosai cikin wanda Sageer ya xuba mata lokacin daya bude mata acct. Suka dawo ta raba musu kudin duka daga me 10k sai me 5k suturar data xo da itama gaba daya ta rabawa yan uwanta mata da matan su Dahiru bata duba tsadar suturun ba, shiryawa da yan uwanta yafi mata komai. Suka dunga godiya suna qarawa da yiwa sakeena fatan gamawa lfy, Iya bakinta har kunne ganin yayanta sun hada kai.


Washegari cikin kewa sukayi shirin tafiya basu da wasu kaya sakeena suturar jikinta kawai ta rage mata itama Iya ta bawa Inna nata kayan da yawa. Suka hado mata kaya da yawa tundaga kan kayan gona wadanda suka isa girbi har xuwa kan kayan lambu da kaji da xabi harda Akuya da Dahiru ya bata Sadiya yayar sakeena ta karba harda kajin tace xata kiwata mata tunda tana kiwo duk da haka sun hada tsaraba da yawa Sakeena tayi musu family picture kowanne cikin matan sanye da suturar data bashi jiya. Har tasha suka rakasu gaba dayansu da fagon kayan tsaraba sai da sukaga shigarsu mota da tashinsu sannan suka juya suna waving juna Dahiru na qara jaddada in sakeena ta tashi aure afada musu da wuri suyi shirinsu, Iya ta amsa suka rabu wasu harda kwalla.(Sabo turken wawa)


Sai yamma liqis suka isa gida suka sauka daga Napep Saddiq take xaune majalisa ya taso da gudu yana tayasu sauke kayan da sukaxo dasu. Suka shiga gida yana mitar sun tafi sunyi xamansu sunqi dawowa sun barshi da kewa sudai dariya kawai suke masa. Suka bude dakin Iya Baba bayanan sai Hajjo dake girki Amina kuma tana falon Hajjo tana kallo.


Sakeena ta dan share qurar dakin suka xube, Iya ta ware kayan data sukaxo dasu kowanne ta ajiyeshi a maxauninsa. Ta ware wasu ta miqawa Hajjo da kanta tai mata Allah sanya alkhairin bikin da akai basa nan. Ta watsawa Iya harara tace "Biki anyi angama lfy bakin ciki ya koreku, kaya kuma ki riqe banaso nafi qarfinsu danni yanxu na wuce ki temakamun yayana kaf sun sami madafa kije gidan Deni kiyi kallon yadda ake auren diyar masu arziqi" Iya tace "To madallah Allah ya sanya alkhairi ya kuma kawo na yan gaba" ta juya ta koma daki. Tasa ka nono a freezer da kwan xabi sakeena ta debi guda 30 ta dafa musu sukaci aka ajiyewa Baba. Iya ta bawa Saddiq kudi ya siyo musu gayar fura tasa nonon da sukaxo dashi kindirmo ta dama musu fura sukasha a matsayin abincin dare. Baba ya dawo ya shigo har daki yana musu maraba suka sha hira Iya na fada masa yadda sukayi a Baggadano shima yaji dadi sosai. Sakeena tai masa murnar bikin Deni da Hadixa, ya amsa yana me tausaya mata. Da wuri suka kwanta saboda gajiya.


Washegari suka kuma kimtsawa sosai Saddiq ya shigo musu hira yana basu labarin bidiar da akai a bikin Deni kusan party kala 4 akai, sannan kuma aka kawo masa gara akori kura guda harda motar hawa c class. Ita kuwa Hadixa abun babu dadin ji ko kadan domin sadakinta 50k bekai a siya mata katifa ba don haka aka kaita babu katifa da sunan sai ansamu ciko xa a siyo, dangin miji suka dunga tabe baki suna mata gorin wannan wane irin aurene? Kalli wasu kaya kamar na wasan yara da kuma kujeru duk jirwayen fitsari. A gaban idon wadanda suka kaita.


Iya ta kada kai tace "Hmm Allah ya xaunarsu lfy" sakeena kuma xurfi tai cikin tunanin Deni yanacan yana amarci da sabuwar amaryarsa ya manta ta, duk yadda taso kauda abun amma ya tsaye mata karma dai yanxu da akai mata fami da taso da xancen.


Ta cigagaba da kunun ayarta a ranar da kuma karatun addinin da Iya ke koya mata, Saddiq ya dubo mata jamb a cafe taci sosai tayi farincikin haka ganin ta haura step daya na shiga jamia kuma a ranar taiwa Sageer waya karon farko a rayuwarta don ta fada masa tunda ta inda aka hau tanan ake sauka ya dauka jikinsa rawa ta gaisheshi ya amsa kamar me magana da shugaban qasa. Tace "Sakeena Abbakar Liman ke magana na kirane in fada maka naci jarrabawar Jamb na samu maki 213" ya sauke hamdala da ajiyar xuciya a tare yace "Masha Allah sakeena yanxu sai post UTME in lokaci yayi." haka ya dunga janta da hira tana amsa da kyar saboda karta gwaleshi. Sageer yana tashi office gidan Maitama ya wuce ya rungumeshi cikin farin ciki yana fada masa yau sakeena ta kirashi a waya. Maitama ya kalleshi da tausayi shi ya dauka ma qarin girma akai masa a office ashe wai duk murnar kiran wayar sakeena ce wannan.


Koda dare yayi ta kwanta bacci wajen qarfe ukun dare Iya ta tasheta tace "ke tashi bacci ba naki bane yanxu ki tashi ki roqi Allah abokin rayuwa nagari da kuma dacewa duniya da lahira." ta tashi tana magagi tayo alwala ta fara nafilfili har xuwa kiran asuba sukai sallah tare da Iya sukai karatu sannan ta koma bacci me cike da nishadi saboda tsaiwar daren da tayi. Daga wannan rana kullum sai Iya ta tashi sakeena tsakiyar dare sunyi sallah tun bataso harta saba kuma abun ya shiga ranta.


Kwana uku da kiran wayar Sageer da sakeena tayi, yana bacci wajen biyun dare kiran waya ya tasheshi, a xatonsa sakeena ce idonsa cike da bacci ya dauka, yace "Assalamu alaikum ranki ya dade ya akai?" Amina wacce soyayyar sageer taiwa mugun kamu harta gaxa dauriya yau ta kirashi cikin dare tanason fada masa abunda takeji game dashi yayin da Hajjo kecan uwar daka tana bacci, taji ya kirata da ranki ya dade wani sanyi ya ratsata badai har aikin malam yacishi ba tun kafin kwanakin turaren su cika? Ta washe baki tayi qasa da murya tace "Darling Sageer ashe ka ganeni? Wlh soyayyarka da tunaninka sun hanani runtsawa" ya wartsake jin baquwar murya don kodaga bacci ya tashi yakan iya banbace muryar sakeena. Cikin dakiya yace "Wacece ne? Bangane me magana ba" ta kuma qasa da murya tace "Amina ce mana autar Hajjo da Baba wacce ta rakaka hanya ranar dakaxo gidanmu" ya ganota yayi mamakin jinta a wannan tsakar daren da kuma inda ta samu number sa ya katse tunaninsa yace "To yaya akai?" ta sauke ajiyar xuciya tace "Sageer baxan boye maka ba wlh Allah ya jarrabeni da mugun sonka na rasa yadda xanyi, na shirya xama da kai a kowanne irin hali koda sadakine ka kawo a daura mana aure, ni budurwace, ban taba aure ba kuma saar sakeena ce ni ko shekaru 20 banyiba a duniya, na iya girki sosai ina da tsafta kuma na iya kwalliya sannan bani da tashin hankali ba halinmu daya da Babata Hajjo ba indai.. ..."



Sageer ya katseta dan ta isheshi da surutu mara kai bai kuma tambayeta ba, yace "Nagode Amina da soyayyarki gareni amma kiyi haquri inada wacce nikeso kuma na kusa aurenta in shaa Allah" Amina tai saurin katseshi idonta taf da kwallar soyayya tace "A a sageer karkaimun haka wlh ko a ta biyu xanxo gidanka inasonka jinake

Please Login or Register in order to submit comment