Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yanxu xamu duba blood grp dinta sai mu gaya muku a nemo irinsa"


Daga Iya har Saddiq babu wanda ya fito da kudi dan haka Saddiq yace "Iya xauna inje gida in takko kudi kuma in canja kaya." tace "To nagode Saddiq Dan Allah ka fadawa malam" yace "To" ya fita ya nufi gida canja kayansa da suka rine da jini.


Hajia 😊



DAGA GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP 08064400100_ πŸ“šπŸ“š
[8/21, 12:07 PM] A A Dboy: πŸ™†πŸ½β€β™€πŸ™†πŸ½β€β™€πŸ™†πŸ½β€β™€πŸ™†πŸ½β€β™€πŸ™†πŸ½β€β™€πŸ™†πŸ½β€β™€πŸ™†πŸ½β€β™€πŸ™†πŸ½β€β™€
πŸ™†πŸ½β€β™€MUQADDARI NEπŸ™†πŸ½β€β™€
πŸ™†πŸ½β€β™€2018πŸ™†πŸ½β€β™€
πŸ™†πŸ½β€β™€



2⃣2⃣

RAHMATULLAH (Hajia)


Direct Saddiq dakin Iya yaje ya dakko kudi a inda tai masa kwatance, har ya juyo xai fito ya tsinkayi qarar wayarta dake qasa a yashe kusa da inda jini ya bata. Kafin ya dauka harta katse yaga missed call din Sageer hudu a jere, ya danna kira akace busy, saiga kiran Sageer ya kuma shigowa. Ya daga, ko gaisawa basuyi ba Sageer yace "Na kirane in tambayi jikin sakeena kuma tun daxu nake kira ba a daga ba yace ko lfy?" Saddiq yace "Eh to, wlh sakeena ke bleeding yanxu mun kaita asibiti sukace ta samu miscarriage yanxu na dawo ne in canja kaya xamuje a nemo jini a saka mata" a gigice Sageer yace "Sakeenan tana wane asibiti yanxu?" Saddiq ya bashi amsa da "qaramin asibiti ne na Gwale Local government" Yace "Saddiq nake magana dashi ko?" yace "Eh" Sageer cikin gigita yace "Yanxu xan yiwa wani abokina dake nan Kano magana xan bashi number Iya ka riqe wayar a hannunka xai kiraka duk abunda ya dace xansashi yayi yanxu" yace "To"


Ya fito dakin Iya kenan saiga Baba ya kalli Saddiq a firgice yace "jinin meye haka jikinka?" cikin sauri yayiwa Baba bayanin abunda ake ciki. Su Hajjo na daki sun kasa kunne suna sauraro.


Ya koma daki ya canja kaya cikin sauri ya fito, Baba ma cikin sauri ya tattaro duk kudadensa dake dakin wanda yake hadawa dan bikin Hadixa dake tahowa ya xuba a aljihu da nufin nemawa sakeena lfy dasu, tunda lfy tafi komai.


Har sun fita Baba ya dawo ya kullo dakin Iya ya datse da kwado dan yasan halin Hajjo kamar yunwar cikinsa.

Su Hajjo dake jiran su fita su shiga dakin Iya suyi mata bincike su debi abunda sukeso
suka saki tsaki a tare ganin Baba ya rufe dakin sun rasa damarsu a karo na biyu, lokacin da aka fice da sakeena a gigice suka so shiga saiga Deni ya shigo ganin idonsa yasa basu shiga ba. Ya fita kenan suna shirin shiga saiga Saddiq ya dawo yanxu kuma gashi Baba ya rufe.


Cikin haushi sukaje kicin suka juye miyar da sakeena takeyi kafin su bata magani ta suma. Miyace tayi jajur sai qamshi take ga kuma naman kasuwa da qasusuwa sunji. Hajjo tace "Amina dau taliya kije ki dafa mana muci da miyar yau banxa ta fadi na huta cefane." Ta miqe taje ta dafo taliyar ta juyo musu a tray suka xuba miyar da namamomin sunaci suna santi. Amina "cewa take duk kudin mijinane shegiya ake tatsemun shi, ai wlh naso Baba yabar dakin nan a bude da shiga xanyi in yashe duk abunda nasan daga aljihun Sageer ya fito har suturar alfarma da take sakawa tana taqama dayimana kallon raini" Hajjo tana tauna qashi tace "Hmmm ai jin dadi ba qarya bane, yanxu dan Allah inkanacin wannan ya xa'ai ka tsufa? Shiyasa daga Malam har Hafsatu gashinan sunyi shar dasu sun murje balle sakeena da take yini ciye ciyen kayan otal, ranar fa ina xaune ta dunga aiken a siyo mata kayan kwadayi akanti saida ta kashe dari bakwai tana xaune a guri daya sannan naga da yamma Saddiq ya shigo mata da ledar wannan kaxar me kabeji, nasan shima kwadayine yasa yake tare dasu shege"


Amina tayi kwafa tace "Aikam ya kusa ya dawo tsaginmu ana kawo kudin aurena da Sageer, tunda duk wannan siyayyar mu xai dunga yowa. Ke kuma Hajjo gobe kije ki kaiwa malam number wayar dana kwafo tunda Allah yasa cikin ya xube kuma no tasamu. Ni badan bama wlh kiransa xanyi inji wannan sassanyar muryar tasa" Hadixa data cika baki da tsokar nama tace "To kirashi ki rusa aikin jaka, ke wlh ci da xuci gareki dole fa ki bari sai randa malam yace ki kirashi sannan xaki kira"



Acan asibiti kuma sunje anbada sample na jinin sakeena B+ ne aka auna Baba da Saddiq jinin Baba ne yayi dai dai da nata aka yimasa tests irin wanda akeyi kafin a dau jini dan tabbatar da wanda xai bayar bashi da kowace irin cuta. Ana cikin test din abokin Sageer ya kira waya, Saddiq ya fita ya taho dashi.



Yaxo aka tattara komai ya biya kudin kana ya karbi transfer. Cikin 15 minutes saiga Sakeena a wani private hospital me tsadar gaske da kuma kulawa. Suna xuwa suka karbeta aka shiga da ita akabar su Iya Baba kuma yaje akaja jininsa leda daya shima aka bashi gado da wasu lemuka yasha akace ya huta.


Sun dade a dakin likitar mace ce akan sakeena sai nurses, kimanin 2 hrs suka fito anwa sakeena duk abunda ya dace har wankin ciki in case of akawai wani bangaren cikin da bai fita ba. Suka canja mata kaya xuwa riga da wando blue na asibitin aka daura mata jinin Baba tare da alluran bacci suka barta suka rufo dakin. Sunwa su Iya bayanin cewa, an tsaida xubar jinin kuma anmata wankin ciki da allurar bacci wacce xata iya daukanta 46 hrs tanayi saboda haka a kyaleta ta huta kar ayi hayaniya tana bacci me nauyi.


Sunkai godiya sosai Iya ta buqaci xuwa gida danta shiryo, likitan tace, babu komi tana qarqashin kulawarmu kuje ki kintsa a nutse.



Baba daya danyi bacci ya tashi shima ya fito suka tari Napep suka tafi, Iya dai sai santin asibitin take cewa take "Yanxu Saddiqu duk girman gurin nan da tsaruwarsa asibiti ne haka kamar hotel? Kaga dakin kuwa harda fa fridge da su TV din bango da AC? Kai masu kudi dai sai abarsu yanxu kaida kaje neman lfy ina ruwanka da wani jin dadi? koda yake kuma ai yafi kulawa gashi cikin qanqanin lokaci sun mata komi har wankin ciki wanda dana gwamnati ne saika kwana ka yini kana kai kawo ba ai maka ba" Saddiq yace "Yawwa yanxu kika dawo hanya, ai Iya komai na masu kudi dabanne a qasar nan har lfy, shiyasa yanxu kowa ya dage yakeson yayi arxiqi kodan yafi qarfin wulaqanci, marasa hankalin cikinmu kuma suke neman arxiqin ta kowanne irin hali wato yaki halak yaki haram."


Lokacin da sukaje gida har ankira magrib, Iya ta gyara dakinta inda jini ya bata ta tsaftace shi, taje kicin don ta dora shinkafa suci ita dasu Baba tunda tasan sakeena tayi miya, ta tarar babu miya sai tukunyar da aka cika da bawon gyada aka rufe mata, ko ba a fada ba tasan wanda xaiyi hakan. Ta kunna rusho ta dora ruwan xafi sukai wanka ita da saddiq da Baba sukai sallar magrib da isha. Tana tunanin abunda xata dafa me sauri saboda komawa asibiti saiga Abokin Sageer ya turo sallama da saddiq, ya fita sai gashi da ledoji niqi niqi wai yaje asibiti ne ya tarar sun taho shine Sageer ya masa kwatancen gidan yace ya kawo, kuma idan Iya ta shirya yana jiranta zai maidata asibitin.



Suka bude ledojin daya kayan shayi ne rankatakaf har da wanda basu sani ba, daya ledar kuma abinci ne take away na tuwon shinkafa da sakwara sai su farfesun nama da kaji gasassau. Abincin ko mutum goma xasu iyaci balle su uku.


Iya tai hamdala tace "Sageeru kenan sarkin hidima dan ruwan mutunci" ta xubawa Baba ta miqa masa ta xubawa Saddiq ma, itama taja taci abunda xata iya, sukai nak ta jona ruwan tsafi a kettle ta cika sabon tea flask din sakeena wanda aka dawo dashi daga Kaduna. Sukaci kajin suka ture, abunda taga xai ajiyu a ciki tasa a freezer ragowar kuma ta bawa Saddiq tace ya miqawa su Hajjo. Ya danso yayi turniya tace "Nifa ba gaba nake dasu ba, kuma ko babu komai dole suna da haqqin maqotaka dani dan haka babu ruwanka kayi abunda na sakaka." ya karba yaje ya kai musu, da sauri Hajjo ta fusge ledar dama tunda aka shigo dasu take leqe. Ta bude suka kewaye suka faraci kamar basu taba cin abinci ba.


Iya ta debo kayan sakeena da nata kayan sukaiwa Baba sallama suka shiga motar abokin sageer ya suka tafi.


Suna tafiya Iya na saka masa albarka yace "Haj ai duk sageer ne ya turo kudi ai muku ni babu ko sisi na kuma shima yana tafe inya samu sauqin aiki a office" Iya tace "Duk da haka dannan inyayi hidimar kudi ai kai kuma kayi ta gaba ko?" yace "Hmm Hajiya ai dan anyiwa Sageer haka ba wani abu bane, tare mukai aiki da shi a Imo state kafin ayi mana canjin gurin aiki shi ya koma Lagos ni kuma Kano, mutumin kirki ne sosai inda ni na nemi taimakonsa nasan bayan yayi da gabarsa sai yayi da aljihunsa."


Ya kaisu asibiti ya tayasu shiga da kayan cikin dakin da sakeena ke kwance ita kadai, harda ruwan roba da maltina ya shigo dasu yayi musu sallama yace sai da safe xe dawo duba jikin. Suka tarar har jinin ya qare an daura mata ruwa. Sadduq ya kwanta a 3 sitter, Iya kuma tasa bargo a qasa ta kwanta. Tace da Saddiq kashe mana wannan abun sanyin, ina asanin mutum ya kwanta haka sanyi nata huda masa bargo, ni banga wani abun burgewa a AC ba." Saddiq yana dariya ya rage sanyin AC ya miqe kashe fitila ya kwanta.



Su Hajjo suna tsaka da brush da kaji suna santi lamarin daya qara musu kwarin gwiuwar fafatukar farautowa Amina xuciyar Sageer ta kowane irin hali saiga Deni. Shidinma yunwa yakeji ya kasa samun kwanciyar hankalin shan koda ruwane tunda yaga halin da sakeena ke ciki, sai yanxu daya bisu motarsu baya yaga asibitin har dakin kuma ya hangi sakeena daure da drip ta kofa lokacin da abonkin Sageer ke riqe da kofar dakin yana musu sallama sannan yaji hankalinsa ya kwanta ya juyo gida, amma fa ya firgita kwarai da sabuwar alaqar Saddiq da sakeena har xasu kwana daki daya dashi a asibiti, sauqinta ma da Iya.


Ya xauna yace "Abun dadi kuka samu haka?" Amina ta dakko plates Hajjo ta saka masa sakwara da miyar ganye dayan kuma ta xuma masa kaji da kayan ciki. Yasa cokali ya faraci a xatonsa saurayin Hadixa ne ya kawo mata dan yaga kayan da yawa.



Hajjo tana sakace naman haqorinta tace "Hmm! Allah kai mana arxiqi tsiya taji kunya, shiyasa yarinyar nan tai tas da ita, Allah ne yasan dadin da yake bata acan Lagos din shiyasa ta xo mana kamar Baturiya" Deni ya dago a firgice yace "Wace yarinyar kenan?" cikin rashin lura da halin daya shiga tace "Sakeena mana, ai Sageeru ne ya aiko da wadannan kayan a kawo mata sukaci suka rage suka bamu" ya tashi ya fita da gudu ya saka hannunsa a maqogwaro yayo aman abincin daya faraci tas, ya kuskure baki ya fice waje kan dakali ya xauna. Yana tunanin kenan sageer ne ya canjawa sakeena wancan asibitin me tsada? Shi a xatonsa iyalan Alh Dalhatu ne. Tab da sauran rina a kaba, kenan fa yana sonta har yanxu? Ga kuma Saddiq shima yaga xaqewarsa tayi yawa. To wai sakeena ita kadaice mace ne da idon kowanne namiji ke kanta? Me take dashi na musamman data ke jan hankalin maxa dashi? Yasan dai akwai dubban mata a kusa da nesa da suka damata kuma suka shanye a kyau, to danme maxa ke binta haka? Ya rasa yadda xaiyi ya fidda sakeena a ransa, ta tsaya mai kyam gashi dai shirin aurensa ake da Surayya wacce yake ganin tayi dai dai da tsarinsa amma kuma sakeena tana cikin ransa da ita yake kwana yake tashi. Barin xuciyaraa yace "masa dandai kuna gida daya ne, da xarar kayi aure ka tare a gidanka ka fara amarci da matarka yar gayu xaka mantata" ya yadda da hakan ya ciro wayarsa ya kira Surayya suka fara hira.


Hajjo da Hadixa suka kalli juna jin kakarin aman Deni. Hadixa tace "Tab aiki ya sameki Hajjo bakiga ta xama Ya Deni fa wlh har yanxu yana son sakeena" Amina batace komai ba sai dariya da tayi dan abun yayi mata dadi, Sakeena da Deni, ita kuma da Sageer period.

******* ****** ******** **


Sakeena sai da tayi kwana biyu tana bacci, ranar na biyun da asuba ta farka da salati a bakinta ta shafo cikinta da hannu tace "Ina cikina?" Iya dake sallah ta sallame taxo ta riqeta tace "sannu sakeena bari kikayi xuwa nayi nasame ki a sume" tace "Maltina kawai nasha sainaji fitsari naje nakasayi naji marata na ciwo" Saddiq yayi sallama yaje ya kirawo nurse suka shigo tare. Ta xarewa sakeena drip din, tace "xan shiga toilet" ta kamata suka shiga tanacewa da Iya "Hajiya kiyi xamanki xan mata komi."



Ta shiga tayi wanka da brush, nurse din ta kamota suka fito. Saddiq dake xaune ya tashi ya fita ya basu guri donta shirya. Nurse din ce ta taimaka mata ta kintsa tasa doguwar rigar cotton material black nd orange, nurse ta gyara gadon ta hau ta kwanta jikinta duk ciwo yake batasan bacci ya dauketaba ma. Iya ta iddar da sallah tace "Sakeena tashi daga baccin nan haka kici abinci, mutum ya kwana biyu sur yana bacci besa ko kwayar hatsi a cikinsa" Nurse tace "Kyaleta Hajiya tayi ya isheta allurar da akai matace kuma bata da yunwa a jikinta saboda ruwan da ake qara mata"


Bata farka ba sai kusan 11 na safe. Tana bude idonta Sageer ta fara gani a tsaye kanta cikin suit baqaqe da alama be dade da sauka ba. Ya hasketa da murmushi tai masa kyau sosai ta rame sai farinta daya qaru saboda jinin data xubar, material din jikinta ya qara haska farar fatarta, ta runtse ido bataji dadin ganinsa ba, itadai taqi jinin Sageer tunda yayi sanadin data rasa Deni. Idonta a rufe tace "Meya kawoka? Waya gayyato ka? Koban fada ba kasan mun rabu cikin qaddarar daya hadamu ya xube saboda haka ka shafamun lfy ka fice daga rayuwata" Salatin da Iya ta saka yasa Sakeena yin shiru, idonta ya rufe batasan Iya da Saddiq na dakin ba. Iya tace "Yanxu Sakeena Sageerun kikewa wannan futsarar? Yaushe kika xama marar kunya bansani ba?" Sageer babu alamar yaji haushi a fuskarsa yace "Yi haquri Iya a cikin ciwo dake" Sakeena ta kalleshi ta murguda baki.


Ta yunqura xata tashi xaune, bayanta ya riqe ta kasa, Sageer ya yunqura xai dagata cikin tsabar futsara tace "Wlh inka tabani Allah ya isa" ya janye hannunsa da sauri. Ta kalli Saddiq dake xaune kafin ma tai magana yaxo ya dagata xaune ya jingina mata filo a bayanta. Ya hada mata tea ya fara bata da cokali tana sha. Sageer ya koma kan kujera jikinsa a mugun sanyaye ko ba'a fada ba yasan Saddiq son Sakeena yake yayin da sakeenan bata lura ba ta daukeshi kamar dan uwanta ciki daya, shi kuma gashi cikin azabar soyayyarta wanda baiga ma fuska gurinta ba balle ya amayar mata ya samu sauqi, kullum da soyayyarta yake kwana yake kuma wayar gari, Maitama haushinsa yakeji akan hakan.


Yananan xaune gurin har ta gama shan tea din Saddiq ya xauna gefen gadon suna hira, shi kuma Iya tana bashi labarin yadda ta dawo daga barka ta samu sakeena kwance a sume.


Hankalin Sageer be gama tashi ba sai da yamma tayi ya dawo asibiti ya tarar da Bar Adam yaxo duba sakeena da kayan dubiya cikin ledoji yana xaune kan kujera a gabanta suna hira yayin da Iya ke waje a xaune. Kishi ya turnuqe Sageer ya kasa dannewa ya hade fuska ganin sakeena ko mayafi babu jikinta gashi rigar jikinta ta matseta daga qirji. Adam ya miqa masa hannu ya share bai bashi ba ya daga masa hannu kawai, Bar Adam yayi dariya cike da duniyanci ya harbo jirgin Sageer yacigaba da hirarsa da sakeena yana bata wani extra ordinary caring. Koda ya tashi tafiya cewa yayi "Ni xan wuce honey sai jibi xan dawo me xan taho miki dashi?" tayi murmushi kawai tana daga masa hannu.

******** ******* *********

Satin ta daya a asibiti aka sallameta ta warke tayi tas da ita, kuma har xuwa wannan lokacin Sageer yana Kano wanda sakeena ta gundura da ganinsa kamar a kanta yake ta matsu ya tafi.


Suna dawowa Iya ta dora qatuwar tukunyar wanka acewar sakeena ta danyace dole ai mata wanka koda na sati biyu ne. Ranar da suka dawo da yamma aka fara wankan sakeena ta tsorata sosai gani take ruwan xai qonata. Amma tayi mamakin da taji ruwan babu xafi yacce take xatonsa. Akai aka gama Iya ta bata xuma a kwalba me yaji tasha cokali biyu. Ranar tayi bacci me dadi duk ciwon jikin da take dana baya ta nemeshi ta rasa. Da asuba Iya ta kuma yimata wankan da towel kamar jiya, sai tafi jin dadin na asuba saboda an danyi ruwa tsakar dare garin da sanyi. Tana fitowa tasha xuma ta shirya ta kwanta.


Batasan iya tsawon lokacin data dauka tana bacci ba taji Iya na tashinta taxo anyi baqo. Ta wanke fuskarta ta nufi dakin Baba inda tajiyo muryar Iya. Taja tsaki a xuciyarta data tarar da sageer ne, tanemi guri ta xauna darajar su Baba dake gurin ta gaisheshi ya amsa yana tambayar jikinta. Yace "Baba jamb ce na saiwa Sakeena, kuma dama tunda Iya ta bani lbrin sakeena da burinta na karatu nayi alqawarin daukar nauyin karatunta amma saina bari saita haihu to kuma Allah yayi Dan baxai taka qasa ba shine yanxu na siya mata gashinan saiki cike a mayar dan ankusa rufewa. Kuma ga waya na kawo miki saboda karatun yanxu dole sai da waya, ya dora kudi akan kwalin wayar yace kisa recharge card" Sakeena duk da bata ko san ganin sageer saida taji wani irin sanyi a ranta daya dauki nauyin karatun ta wanda ta fiddaran samun hakan. Iya da Baba kuwa sun kasa magana saboda mamakin halin sageer. Sakeena tayi godiya kamar xata ari halshe.


Ta kwashe kwalin wayar da JAMB dinta tai dakin Iya, tanaji Iya na cewa tunda tafiya xaiyi saiya tsaya yaci abinci. Ta kaimasa dakin Baba yaci alkubus da stew sosai ya gama ya fito wanke hannu, Amina na jikin window tana leqensa yayin da shi kuma yake leqen sakeena, su Hajjo da Hadixa sun fita tun duku duku. Sukai sallama dasu Baba ya rakashi har qofar gida yana qara yimasa godiya.



Yana tafe yana tunanin sakeena da kuma tunanin yanxu shikenan da gaske sun rabu? Amina wacce ta rigashi fitowa tasha gabansa, ya tsaya yana dubanta da kuma tunanin inda yasan fuskarta. Ta tsuguna har qasa ta gaisheshi cikin magagin sonsa, ya amsa ba tare daya tuna inda yasan face dinta ba, ta karbi jakarsa ta goyo har tana hadawa da hannunsa tace "Kawo in riqe maka in rakaka tasha" yace "A a taxi xan hau ta kaini airport jirgi xanbi" tayi murmushi tace "Baka ganeni ba ko?" a taqaice yace "Gaskiya kam" tace "Amina sunana a gidan su Sakeena nake ni yar gidance nice auta" jin haka ya hade rai, sai yanxu ya tunata ashe wannan yar iskar yarinyar ce wadda tai aljanun qarya a kotu, wadanda su da uwarsu suka tsani sakeenan sa suka sata a gaba.



Ya tsaidata ya ciro kudi ya irga 10k ya bata yace "Ki koma gida haka nagode kar a nemeki" ta washe baki ta karbi kudin tayi godiya tace "Bari in baka number ta" yace "Bani da buqata" bai jira cewarta ba ya tare Napep ya shiga. Amina ta buga tsalle kamar ta manta a waje take, ta shinshina kudin da suke qamshin turaren Sageer ta lumshe ido ta kuma nutso a kogin sonsa ta nufi gida cikin wani irin farinciki.


Sakeena dai yinin yau babu bacci ko aikin kunun aya, Saddiq na tashi daga bacci ta tasashi gaba ya hada mata wayarta Tecno wacce yace sabuwar xuwa ce ko a unguwar mutum biyu keda irinta sai ita ta uku, suka saka layunkan da sageer ya hado dasu MTN da 9mobile kuma duk da kudi a ciki da yawa yayi mata sub, Saddiq ya tuttura mata applications da games ya bude mata watsup din da taketa buri da facebook. Yace ta bari tayi caji sai ta qara kunnata, da kyar ta yadda ta sakata caji don ta matsu ta fara watsup (ina ruwan otondoπŸ˜„) Suka fara cike jamb form, sai dai gurin saka jami'ar da mutum keso Sageer ya cike sunan wasu universities wanda ko Saddiq be sansu ba balle sakeena. Ta xabi course suka gama Saddiq yace inxai fita xai kai mata Rumfa college yayi submitting.


Ta dakko wayar ba tare data cika ba tace ya nuna mata yadda ake chatting din, yana dariya yana koya mata, ta dakko numbers din qawayenta na skull Saddiq ya mata serving wadanda suke chatting aciki sunansu ya fito, saiga number din Anty Bilki a cikin wayar da alama Sageer ne ya saka har datasa number din. Tai mata magana tace sakeena ce, ai saiga Bilki ta kirata suka sha hirar yaushe gamo. Bilki ta bada number din sakeena aka sakata a grps. Yinin ranar dai yini yai akan waya abunda bata gane ba ta kira Saddiq ya nuna mata. Da yamma bayan angama wanka hartayi tsugunan da Iya kesawa tayi akan garwashin wuta da wani turare saiga umman sageer ta kira Iya a waya, suka dade suna hirar barewar cikin sakeena kafin ta buqaci abata sakeena tayi mata sannu da jiki tace kuma xataxo biki kano watan gobe xata biyo ta dubata.


Da yamman dai su Hajjo suka dawo, Amina ta taresu da xumudi da labarin qarya wai ta raka Sageer har airport kuma sunyi xance harya bata dubu goma ta nuna musu kudin, suka qule daki suka qaraci murnarsu Hajjo ta jinjina kyautar 10k a lokaci daya ta fitowa da Amina saqonta na gurin malam turaren hayaqi ne xata dungayi har tsawon kwana 41 kamar ibada πŸ€” kuma karta sake ta tayiwa sageer magana koda ta wayane sai adadin kwanakin gama turaren sun cika. Ta karba da kwarin gwuiwa duk da tana hango wahalar yin 41 dayx ba tare da koda jin muryar sageer ba wanda sonsa ke azalzalarta.


Sakeena dai kusan kwanatai akan waya har ta fara karatun novels din da Anty Bilki ta tuttura mata, da safe bata koma bacci ba, tana gama karatun qur ani da kuma na littafan addinin da Iya ke koya mata da asuba ta kama aikinta na sharar daki da gyarawa ta taya Iya dan abunda tasata ta debo wankinsu xatai Iya ta hanata tace ta barshi akai wankau jego take karta shiga ruwa. Ana gama wankan jego ta kimtsa ta dau waya ta fara chatting. Sageer da bewani damu da harkar social media ba tun jiya yake online yana kallon sakeena itama online duk da be mata magana ba itama kuma batai masa ba amma ganinta online kawai ya isheshi farin ciki.


Yauma dai kamar jiya ta yini chatting da kuma game din "Word

Please Login or Register in order to submit comment