Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

xata fita ta kuma tsinkayan muryarsa yana cewa "ke! Ki daina wannan saurin haka don banason munafurci duk wanda ya ganki kice masa daga dakin dadironki kike kuma in anjima inxakixomun karki xomun kina wannan saurin, yanga xakiyimun yanda zansan mace ce ke ba namiji ba"



Babu shiri ta canja salon tafiyarta a hankali don ta samu su rabu lfy.




Baba, Iya da kuma Hajjo sukai baya da sauri jin ana shirin fitowa daga dakin, bayan sun gama jin komai. Suna kaucewa sakeena na fitowa tai cikin gida da sauri a tsorace take sosai. Ta shige uwar dakin Iya ta qudundune a gadon gabanta na faduwa. Iya ta dubeta tace "sakeena naga kin kwanta kin fasa mana wankin ne?" cikin qinqina tace "Iya bani da lfy ne sanyi nakeji har cikin bargona baxan iya ko fita tsakar gida ba balle wanki"




Iya ta dunga kallon sakeena da tausayi ta fuskanci a mutuqar tsorace take, to ita kanta uwar sakeenar a tsorace take da kalaman Deni balle sakeena.



Lallai wannan yarinya sakeena da xurfin ciki take, wato badan Baba da yake shirin fita yaji tashin magana daga dakin Deni yaxo ya kirasu ita da Hajjo dan jin abunda suke fada ba da ita kadai xata shanye wannan tashin hankalin?



Iya na xaune ta rasa mafita? Sai aikin tunani daga taji anshigo gidan ta furgita don tana zaton Deni ne zai shigo daukan sakeena a gabanta kamar yadda yayi alqawari. πŸ˜‚πŸ˜‚πŸ˜‚




Hajjo na can daki tana ta zarya cikin rashin gane takameme wane abu xatai, kuka ko dariya baqin ciki ko farin ciki. yayanta sai tambayarta suke tai musu shiru.




Baba kuma gaba daya yafisu tashin hankali a matsayinsa na namiji kuma shugaba a gida wanda in abu mai kyau ya faru xai xama nasararsa in mara kyau ya faru xai masa laifinsa. Ya tufka ya ware, ya kuma tufkawa ya warware kafin ya yanke abunda yake ganin zai zama masalaha da kuma yiwa duk bangarorin biyu adalci wato Iya da Hajjo dan haka ya qulle daki ya fita.




Iya tai saurin fitowa jin qulle qofarsa tace "Malam yanxu inka fita Deni yaxo daukan Sakeena kamar yadda yayi alqawari ya xanyi dashi? Gida babu namiji kuma kasan yafi qarfinmu, ka rufamun asiri ka dubi girman amanar dana dakko ka xauna a gida karka fita Deni ya batawa sakeena rayuwa" kafin ya bata amsa Hajjo ta fito cikin masifa tace "ban haifi dan iska ba Hafsatu, kowa yasan Deni natsatstsan yarone kafin xuwan sakeena gidan nan dan haka inma iskancin ne sakeena ta fara sakashi a hanya." Iya cikin nata masifan itama ta tasowa Hajjo "Hajara ai kinji da kunnanki yanda lalataccen danki kewa sakeena tayin xuwa dakinsa dan aikata masha'a saboda haka saiki fadan waye dan iska a cikinsu?"




Baba ya tsaya yana nazarinsu duk su biyun, Allah yasa gidan babu kowa, su Amina anfita office (yawan bin maqota) yayin da sakeena ke qulle a uwar dakin Iya. Baba ya daka musu tsawa da cewa "Duk wacce ta kuma magana be yafe mata ba" sukai shiru a tare. Yasa kansa ya fita.




sai ranar asabar xan kuma posting in shaa Allah.

Hajia ☺
[7/31, 2:09 PM] Reine Ghana: πŸ™†πŸ½β€β™€πŸ™†πŸ½β€β™€πŸ™†πŸ½β€β™€πŸ™†πŸ½β€β™€πŸ™†πŸ½β€β™€πŸ™†πŸ½β€β™€πŸ™†πŸ½β€β™€πŸ™†πŸ½β€β™€
πŸ™†πŸ½β€β™€MUQADDARI NEπŸ™†πŸ½β€β™€
πŸ™†πŸ½β€β™€2018πŸ™†πŸ½β€β™€
πŸ™†πŸ½β€β™€



9⃣

RAHMATULLAH (Hajia)



Har dare sakeena bata yadda ta fito tsakar gidaba ita kadai, ko bandaki zata shiga sai tace iya ta rakata, yayin da iya ke rakata ta tsaya a kofar daki har sakeenar ta gama abunda xatai ta fito sannan su tafi. Iya kuma bata tambayi sakeena meye dalilin hakan ba kuma bata nuna mata tasan komai ba. Baba ya dawo gida be nemi kowa ba kuma bece da kowa komai ba.



Koda dare yayi abun dariya Iya ta saka sakata a daki duk kuwa da xafin da ake ita keda girki amma ko dakin Baba bata kallaba ita kawai ta tsare sakeena kar Deni yaxo ya jata kamar yadda ya fada. Shima Baban Iya haushinsa takeji saboda da taga hankalinsa a kwance yake be damu da furucin Deni ba ko daukan mataki akansa kodan ba diyarsa Deni ke yunqurin batawa? Wannan shine tunanin Iya.


Haka sukai bacci ita da sakeena cikin zafi amma duk da haka iya tana baccin tana farkawa dan sai takejin kamar ana buga kofar dakin, daga qarshema saita tashi ta dauro alwala tahau nafila da roqawa sakeena miji nagari.



Wayewar gari Monday gidan ya dade kamar yadda aka saba, Sakeena ta nufi aiki Deni kasuwa, Saddiq makaranta yayin da yayan gata su Amina ke gado ana bacci Baba ma ya fita sai Iya da Hajjo a tsakar gida kowacce na harkokinta.




Sha biyu da rabi Sakeena ta shigo gidan jikinta a sanyaye qalau, tun jiya da abun ya faru xuwa yanxu jikinta a sanyaye yake ga wata irin faduwar gaba data sakata a gaba amma duk tana danganta hakan da tsoratarwar da Deni yayi akanta. Ta xauna ragaf a gaban Iya dake kwance. Iya tai mata sannu dan a zatonta gajiya ce ta sata wannan sanyin jikin. Tace "sannu Sakeenatu ta miqa mata kwanon awara tace maxa ci kafin a qare abincin rana" taja kwanon gabanta tanaci tace "Iya ina kika samu awara haka?" Iya ta bata amsa da cewa "Zahra ce taxo ta kawo mana ita fall samira shine aka kasa aka bamu" Sakeena tace "Allah sarki shiyasa naga dakin naki kaca kaca ashe anxo da qawayenki" Iya ma tana dariya tace "eh yan qaniya suncimun gyada ba sun barmin dakin kaca kaca"



Tana gama cin abincin ta share dakin Iya da yayan Zahra suka bata sannan ta fita alwala. Ta leqa dakin Hajjo suka gaisa da Zahra a mutunce har tana tambayar sakeena aiki, Zahra da Deni a yayan Hajjo kam sune basu da matsala dan sun dauki Iya a matsayin uwarsu. Ta tambayi zahra ina yaran tace "su Amina sun fita dasu maqota" Sakeena ta qarasa bakin famfo tana alwala yayin da tabar Zahra da Hajjo sunata qus qus dinsu a hankali badan zargi babu kyauba da saitace xancensu da Deni ake fadawa zahran.



Kafin La'asar Baba ya dawo, ya kira Zahra suka dade a daki sannan suka fito yana yiwa yan jikokinsa yayan Zahran wasa. Koda xata tafi har daki ta tarda Sakeena wacce tunda taga 5:30 tayi ta qule uwar daka saboda da tasan koda yaushe Deni kan iya dawowa ita kuwa yanxu tsoronsa take fiye da komai a duniya. Tana dariya tace "Anty Sakeena kece haka a uwar daka a dai dai wannan lokacin? Ai da kin fito tsakar gida kinsha iska" Sakeena ta maimaita kalmar da zahra ta fada "Anty Sakeena" a zuciyarta, kafin ta bata amsa da cewa sanyi nakeji shiyasa na shigo uwar daki Anty Zahra" tace "to shikenan dama tafiya xanyi nace bari naxo nai miki sallama" Sakeena kanta ya kuma daurewa amma dai sai tai tunanin ai zahra karamci gareta ba wani abu bane dan taxo mata sallama kuma ta kirata da Anty. Tace "to nagode Anty zahra da qalau nake dana rakaki titi" tai saurin cewa "a a bakomi keda bakijin dadi yi xamanki su Amina sa rakani. Allah ya qara sauqi kinji" tasa kai ta fice




Kiran sallar magrib da sallamar Deni cikin gidan lokaci daya suka shiga kunnen Sakeena, qirjinta yayi wata irin bugawa har saidata dafeshi. Sai data tabbatar Deni yabar gidan ta fito a gurguje tai alwala ta koma daki.



Ga al'adar gidan bayan sallar magrib ake haduwa a babbar tabarma a tsakar gida aci abinci, in kuma lokacin sanyi ne ko damina sai a shiga dakin Baba. Wannan shine abunda Baba ya kafawa gidansa. To yau dai da jiya Sakeena duk bata halarci xaman cin dinner tare da su ba acan daki Iya ke kai mata.




Kowa ya tasa kwanon tuwonsa a gaba yanaci yayin da Sakeena ke uwar daka a xaune cikin wata irin fargabar da batasan kota mece ba. Baba ya kalli Iya yace "ina Sakeenatu?" ta bashi amsa da cewa "tana daki" ya kalli Amina yace "jeki ki rawon ita" Iya tayi Hamdala a zuciyarta dan bata raba daya biyu Baba tsakani xai yiwa Sakeena nan da Deni saboda in xaiyi magana me mahimmanci a wannan lokacin yakeyi saboda kowa na gurin. Wanda ita tun jiya take dakon ganin Baban yayi haka. Ta qara gyara xama ta fallarawa Deni harara wanda ya tasa tuwo a gaba ko hannu besa ba.



Acan daki kuma Amina tana fadawa sakeena kiran Baba ta juyo tana mitar cewa kinyi abu ya dameki ko xama cikin mutane kin kasa, waya fada miki xakici ribar soyayya da dan masu gida?



Ta gaishe da Baba sannan ta koma jikin Iya ta rabe saboda ganin Deni a gurin wanda yake kallonta ko kunyar idon mutane bayaji. Iya ma ta qara janyo sakeena jikinta saboda tsaro πŸ˜„



Baba yayi gyaran murya ya fara magana bayan ya wanke hannunsa da ruwan da Hajjo ta miqo masa. "Sakeenatu kiyi haquri, saboda wasu fitintunu danaga suna shirin tasowa wanda ba lallai na bayyana miki suba da kuma gujewa fadawa halaka a jiya nayi miki karanbani, bayan na fita da rana na halarci daurin auren yar abokina bayan ansallaci azahar kenan, NA DAURA MIKI AURE" sakeena tayi matuqar qoqari wajen danne firgitar da tayi, aure kuma? Saboda me? Akan me? Ko Baba ya gaji da xamanta a gidansa ne? Ko kuma biyan bashi yayi da ita don yasan xatai masa biyayya sabanin yayansa wanda ta haqiqance baxasu yarda ba? To inko hakanne baxata karya yardar da Baba yayi akanta ba. Mutan gidan kuwa gaba daya kallon Baba suke a firgice ta bangaren Iya da Deni kenan wadanda suke kallonsa kamar sun warke daga cutar makanta da alama maganar ta dokesu. Ta bangaren Hajjo da ragowar yayanta kuwa fuskarsu wasai suna murnar cewa fa anrabu da qaya duk da suna baqin cikin sakeena ta rigasu aure amma suna da yaqinin Baba ba wani mijin kwarai (me kudi) ya samowa Sakeena ba. Saddiq kuwa cikin farin ciki ya furta "game over"




Muryar Sakeena ta katsewa kowa nasa tunanin inda tace "To Baba nagode Allah ya saka da alkhairi, Allah ya biyaka Allah ya bani ikon bin wanda ka auramun." tana gama fadar haka ta miqe xata shiga daki. Tana tunanin shiyasa tun jiya take a sanyaye tana jin faduwar gaba ashe aure ne ya hau kanta.




Muryar Baba ta katseta yace "Dawo Sakeena ban gama maganata ba, ban kuma fada miki wane na aura miki ba" ta dawo kamar yadda ya umarceta ta tsuguna tana murnushin qarfin hali tace "Baba basai ka fadamun ba, wlh kowanene ka bani xan soshi xan masa biyayya dan nasa baxanka cuceni ba kuma baxan biyaka dawainiyar dakai a kaina ba. Ka ciyar dani, ka shayar dani, ka tufatar dani, ka tsare mutuncina da lafiyata sannan ka bani ilimi da tarbiyya, to ni kuwa in ban maka biyayya ba ai nasan baxan gama lafiya ba" Baba ya jinjina kai cikin yabawa da fasahar harsher da hikima ta sakeena sannan yace.




"Kamar yadda na fadamiki, bayan idar da sallar azahar a jiya lahadi na xama waliyinki a inda limamin masallacin unguwar nan ya xama wakilinsa na daura auranki da Nuraddeen bisa sadaki naira dubu ashirin ajalan ma'ana bashi wanda xan biya nan da qarshen wata innasamu kudina kamar yadda addini ya umarceni inwa dana aure."




Wannan karon sakeena kam bata iya danne razanarta ba, a firgice ta dago tana kallon Baba. Yayin da Iya da sauran yaran gidan suka hada baki wajen tambayar Baba "wane Nuran?" Baba yana murmushi yace "Ai acikin bayanina nace muku dana Nura ko? In bashi ba wa Allah ya doramun nauyin yiwa aure?" sukai dubansu ga Hajjo dan ganin wane yanayi take ciki. Suka sameta fuska jiqe da hawaye wani na korar wani. A tare suka kuma kai dubansu ga Deni dan ganin shi kuma ya yadauki lamarin, suka tarar dashi ya duqa yana sujudu shukur (sujjadar godiya)




Baba ya kuma dorawa da maganarsa "Nuraddeen ga amanar Sakeenatu nan na baka, ka dubi Allah ka riqe da kyau ka tuna itafin marainiyace marashiyar uwa da uba bata da kowa yanxu sai kai duk nauyinta yanxu Allah ya dora maka, nasan baka dashi amma ka xage dantse ka kare mutuncinta da martabarta. Na sanya tare warku xuwa qarshen watan nan kafin nan na hada abunda Allah ya horemun xan kama muku inda xaku xauna da sauran hidimomi. Nura ka karbi amanar dana baka?"




Deni ya matso ya riqe hannun Baba duk biyun yace "na karba Baba in shaa Allah xan riqe sakeena da mutunci da amana baxan ci amanar da kabani ba. Allah ya saka maka da alkhairi, kuma nima kafin qarshen wata xan adana abunda nake samu inyi nawa shirin." Baba yace "to Masha Allah naji dadin jin hakan" ya juya gurin sakeena yace "sakeenatu kinji zabin da nayi miki, ina fata kin karba kamar yadda kika alqawaranta tun kafin kiji waye mijin" Ta kuma qasa da kanta tace "Na karba Baba, koda wani ka auramun xan maka biyayya bare kuma tsatsonka Allah ya xaunar damu lafiya kuma ya hada tsakaninmu da alkhairi" Baba farin ciki ya kuma bayyana a fuskarsa, ya dubi su Iya da Hajjo yace "kunji ra'ayin ma'auratan yayanku, mexakuce?"



Shirun mintuna biyu ya biyo baya kafin Iya ta fara magana "Allah ya sanya alkhairi Allah yasa abokan arxiqin junane" Hajjo ma a sanyaye ta fara magana "Allah yasa albarka Allah ya kade fitina" Baba ya amsa da Aminnn kuma Allah yayi muku albarka.




Deni ya matsa gaban Hajjo yace "Hajjo ga matata nan sakeena, itama yanxu yarkice kamar yadda nake danki kisa mana albarka" tayi murmushin yaqe ta shafa fuskarsa tace "Allah yayi muku albarka Deni" Qannansa suka hau harararsa kamar idanunsu xasuyo waje, shi kuwa besan sunayi ba sai washe baki yake.





Deni shiya fara tashi daga gurin, ya nufi bakin famfo, Hajjo da Iya kowacce ta nufi dakinta xuciya babu dadi, Baba ma ya shige nasa dakin akabar sa idawan qannan miji da ganin yanayin da sakeena da Deni zasu kasance.




Sakeena ma ta miqe ta nufi dakin Iya, Deni dake tsaye a gurin famfo ya kafeta da Ido itama akai sa a ta kalleshi. Ya ware mata hannayensa yana mata murmushi yana nufin taxo, kallonsa take babu ko qiftawa yayi mata kyau sosai cikin polo shirt da Blue Jeans haka kawai taji baxata iya watsa masa qasa a idoba, a hankali ta nufeshi cikin slow motion ta fada jikinsa suka qanqame juna suka saki ajiyar tare. Ai su Fiddausi daganin haka duk suka baje kowa ya nemi hanya πŸ˜„ Saddiq kuwa cewa yayi a fili gayan nan fa zaija kaya shege.



Deni dai ya tafi wata duniya tunda yaji sakeena jikinsa, ido lumshe yanata yawo da hannayensa a tsakiyar bayanta. Yayin da ita kuma tayi luf a jikinsa tana shaqar qamshinsa. A hankali ta janye daga jikinsa cikin jin kunya tai qasa da kanta, yasa hannu ya dago habarta yana qarewa kyakykyawar fuskarta kallo. Yace "Sakeena kinga hukuncin Allah ko? Cikin ikonsa ya nufemu da xama abu daya. Ki yafemun abunda nai miki abaya dan Allah" tai murmushi batace komai ba ta juya ta shige dakin Iya.




Abincin da bataciba kenan a daren tahau gado ta kwanta, ta rasa takameme me takeji akan wannan aure, farin ciki ko baqin ciki? Amma dai ta tabbatar da soyayyar Deni tananan a ranta daram babu abunda ya ragu. Iya tanata yimata magana bataji ba har saida Iyan ta burkitota sannan ta farga.




Iya ta fara magana cikin bacin rai "nifa sakeena sam wannan aure naki bai kwantan ba, tayaya malam xai daukeki ya danqaki hannun mutanen da basa qaunarki? Ai yasan Hajjo da yayanta bazasu taba sanki ba. Kuma dan ni be daukeni wata abuba bai nemi shawarata ba balle in fadawa yayyenki da kuka hada uba, wannan hadin sam beba" Sakeena ta waro ido tace "Iya kece babba dan Allah tunda ita Hajjo bata nuna komai ba ke karki fara nunawa, karku batawa Baba rai aikin gama ya gama tunda an daura aure" Iya takai mata bugu tace "dan ubanki keda nazo ki goyamun baya mu yaqi abun shine xaki gwale ni? Kinason Deni ko? Soyayyarsa ta hanaki hango abunda na hango miki" Sakeena tace "Iya kiyi haquri duk abunda kikace inyi xanyi amma ki tuna ya Deni yanxu mijinane ko ina sonsa ko bana sonsa hakan baxai amfaneni ba" Iya ta kuma harxuqa ta kama kunnen sakeena ta murde tace "To dan ubanki wannan rawar kan da yake akanki inkika bashi hadin kai ya gama dake tun a gida wlh xai wulaqantaki saboda haka ki kiyayeni ko doguwar gaisuwa ban yarda kuyi ba ke dashi" Sakeena ta runtse ido saboda xafin murdar kunnen da Iya tai mata tace To Iya naji xan kiyaye" ta saki Kunnan sakeena ta nemi gurin kwanciya tana mitar wannan aure.



Deni kuwa yayi ficewarsa waje cikin nishadi ya nufi majalisarsu baki har kunne duk inda ya xauna saiya fada musu yayi aure jiya. Abokai suka dunga tayashi murna tare da yimasa iya shege irin na abokai. A cikin daran dai yayi bacci me dadi cike da mafarkan sakeena, ya dunga dariya shi kadai wato dai aure lokacine in lokacinka yayi koda shiri ko babu shiri sai kayi. Duk da sakeena ba irin kalar matar da yake mafarkin aura bace amma yayi mutuqar farin ciki da aurenta kuma da xuciya daya ya dauki aniyar riqeta.



Acan daki kuma Hajjo ta xauna ta zabga tagumi yayinda yan majalisarta wato yayanta suketa aikin xugata tare da tsinewa auran Deni da Sakeena. Ita kuwa Hajjo duk da bata qaunar auren ko kadan amma kuma batayi wani baqin ciki sosai ba, dalili kuwa shine : danta ya isa aure amma kuma bashi da aikin yi balle ya riqe iyali kuma baxata taba so ace Deni ya lalace ba ma'ana yafara bin matan banxa saboda rashin halin yin auran to tunda ga Sakeena bashikenan ba sai yayi auran kare kansa daga zina da ita inyaso duk randa yayi arxiqi saita uxxura masa ya qara aure irin wacce takeso kuma tayi duk yadda xatai ya sallami sakeena. Ta dakko maganar Zahra ta dazu bayan ta fada mata yadda sukaji Deni na yiwa sakeena tayin xuwa dakinsa, zahra ta bata shawarar cewa bataga amfanin hana Deni auren sakeena ba tunda yana sonta inda tace "Hajjo tunda saurayi kamar yaya Deni beji kunyar idionku ba ku iyayensa beji kunyar idon qannensa ba furta cewar ai masa aure ai kinsan tura takai bango shiyasan illar da rashin auren yake masa kuma in kukaqi yi masa duk abunda yaje ya aikata kuna da xunubi, kuma Hajjo da ace yau ga yayan Deni shegu na yawo ba gara ace ga yayansa na halak ba amma uwarsu bata da asali? Nikam banga illar auren sakeena ba koda bata da asalin tunda tana da halin kirki kuma ai Deni talakane wanda bashi da kudin aure kamar yadda sakeena take yar talakawa wacce ba a da kudin yimata kayan aure to basai ku barsu su rufawa juna asiri ba?" wannan shine shawarar da Zahra ta bawa Hajjo daxu da rana.




Maganar Amina ta katsewa Hajjo tunani inda take cewa "ai wlh karyar sakeena ta auri miji handsome kamar yaya Deni wannan aure sai mun batashi kafin qarshen watan tayi." Fiddausi ta karbe da cewa "tabbas kwancekwance xamuyi mu hada mata tuggu yanda ba yaya Deni ba har Baba sai yaji ya tsaneta" Hajjo ta katsesu ta hanyar daga musu hannu da cewa "bansaku ba" Hadixa ta matso tana leqa fuskar Hajjo tace "Hajjo? Me hakan yake nufi? Kina nufin kin karbi sakeena a matsayin surakarki kenan?"



Hajjo ta fashe da kuka jin an kira sakeena da surukarta da kuma tunawa da tayi yanxu fa duk mutan unguwa suna kallon sakeena a matsayin surukartane. Kuma duk yadda taso ta danne ta karbi hakan amma abun ya faskara. Ta qara sautin kukanta tace dasu fiddausi "bance ku kashe masa aure ba, ya kikeso inyi? Dame xanji? Da baqin cikin ya auri yar talaka mara asali kuma yare xanji koda maganganunku? Ku kun jibge kunqi aure muna hada kafada daku shi kuma talauci ya hanashi auren duk kuwa da yanaso, ko so kuke ace yayana baqin jini garesu?" ta qarasa tana gursheqen kuka. Su Hadixa jikinsu yayi sanyi ganin kukan Hajjo cikin kukan tacigaba da cewa "Allah ya tsinewa talauci domin talauci ne yasanya Dana auren yare wacce qedara ta haifa kuma nima haka xata haifamun yare, wai ni Hajjo nice xan xama kakar yare?" Ta share hawayenta ta kuma cewa "Sakeena kinyi nasarar auren Dana amma kuma baxan taba bari ki haihu dashi ba wallahil azim xaki qaraci xamanki xuwa lokacin dana diba miki kiyi gaba" Haka dai suka dunga qulle qulle ita da yayanta har xuwa lokacin kwanciya bacci.




Washegari Deni ya shigo har dakin Iya ya gaisheta ta amsa tana basarwa ya sosa kai yace "Iya ya sakeena ta kwana?" tace "lfy lau tana wanka xata tafi aiki" yadan hade rai yace "Iya ban yadda ta fita ba, na soke aikin nan daga yau ban bata izinin fita ba" Iya ta saki baki tana kallonsa daga baya ta fara magana "Deni ka dubi Allah ka barta ta qarasa xuwa qarshen watan nan tunda yau 3 ga wata kaga in anbata kudinta sai ta daina xuwa kudin xasuyi mana amfani auren yaxo mana baxata bamu shirya komai ba" yadan kau dakai yace "to shikenan Iya na yadda amma ni yanxu xan fitane ina sauri yau xamuyi baqi a shago dan Allah ko ke ko Baba wani ya rakata makarantar ya sheda musu tana da aure yanxu a kulamun da ita don Sakeena yarinya ce batasan haqqin aure ba" Iya ta bishi ta to tana masa kallon mamaki daga aure jiya har yafara saka doka? Dai dai fita daga dakin Iya sukai kacibiz da sakeena ta fito wanka daga ita sai daurin qirji don bata xaci ganinsa yanxu ba. Ya kalleta yace "inxaki fita ki saka hijab kuma ki kiyaye magana da kowane namiji kinji ko?" ta gyada kai yayi waje ita kuma ta qarasa ciki.




Iya ta harareta tace "wai meya hanaki saka hijabi da xaki shiga wanka kamar yadda kikeyi da?" sakeena tace "Yi saquri iya banxaci ganinsa yanxu ba shiyasa na fita haka" tayi tsaki tace "to daga yau inxaki shiga wanka ki dunga rufe jikinki domin ko babu mijinki a gidan akwai surukanki da kuma qannansa saboda haka karki kuma fita wanka haka gantsar gantsar ke dama ga jiki masha Allah" sakeena cikin kunya ta amsa to Iya.



Kamar yadda Deni ya umarta haka akai Baba ya saka Iya ta raka sakeena makaranta ta fada musu tayi aure shekaranjiya lahadi abunne yaxo baxata shiyasa basu jiba sai yanxu. Malaman suka dunga taya sakeena murna iya na amsawa da amin sunaiwa sakeena tsiya ashe tana da mr right dinta shiyasa bata shiga sabgar kowa.




Data dawo hardasu Hajjo ayi mata sannu da xuwa ta amsa a darare dan tsoron Hajjo take a matsayin surukarta. Iya ma dai wannan sabuwar fuskar da Hajjo ta saka ta yiwa sakeena kirki bata gamsheta ba don tafi kowa sanin halin Hajjo unguluce bata jelar banxa dole tasan akwai wata qulalliya a qasa.




A daki ta yini sur dan sai taji ta kasa sakewa duk kuwa da babu wanda ya caja mata fuska.



xuwa magrib Iya ta gama girkin dare yayin da kowa yana daki yana shirin sallah ita kuma tana bakin famfo tana wanke muciyar datai amfani da ita. Taji andafata, ta dan juya a raxane dan bataji taku ba, tayi arba da Deni a tsaye xatai magana yayi mata alamar tayi shiru, ya miqa mata

Please Login or Register in order to submit comment