Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

Bintu ɗiyar bayi ce (book 2) Chapter 1
Admin 001 Mukhtar Adam Nation
Tareda Naja'atu Lawal Rijau
@Whatsapp 08083232323 09060202323

WAIWAYE
Daga cikin Masallaci aka fara abinda ya had’a jama’a a
wannan masarauta, wato d’aurin aure, in da aka umarci
waliyin Ango da Amarya su matso kusa. Waziri ne ya fito daga
6angaran Sa’ayrasa, Fabarusa kuma Sarki Abdulrahaman ne
ya nuna kan sa a matsayin waliyi.
Daga waje Khalil ne ke ta yiwa Yarima Barde hira, amma shi
ina hankalinsa na ga Gimbiya K'amariyya, Allah Allah ya ke a
shafa fatiha ya tafi garera don jin soyayyar ta ya ke har ransa,
bare kuma yau gabar da ke tsakanin Masarautasu za ta kau, za
su yi soyayyarsu a zahirance ba tare da wani shakku ba. Jin an
shafa fatiha Yarima Barde ya tashi ya na mai fad’in.
‘’Alhamdulillah tunda an amra sai ku tashi mu tafi ko?’’
Har Khalil da Jafar sun tashi, tuni su ka tsaya cak jin marok’a
na fad’in
‘’An d’aura auren *Yarima Abubakar BARDE* tare da *Gimbiya
Fatima* akan sadaki (50000 CFA)"
Yarima Barde da sam bai lura da abinda su ka ji ba tsabagen
hankalinsa ba ya wajan, a hasale ya kai kallonsa ga
abokannasa ya na mai fad’in
‘’Me ku ke jira ne? Mu tafi, Allah Allah na ke na gana da
Gimbiyata.’’
Su kuwa marok’a ba su fasa shela ba. Khalil ne yayi k’arfin hali
ya ce
‘’Da ma kai ne Barde?’’
Cikin rashin fahimta Barde ya ce
‘’Ni ne wa?’’
‘’Angon da aka amrawa amren.’’
Jafar ya bashi amsa a tak’aice. Kai Yarima Barde ya girgiza
cike da murmushin irin ban son rainin hankali fa. Khalil ya ce
‘’Saurara ka ji Barde’’
Nan kuwa muryar wani marok’i da ya zo giftawa ta dafda su ya
doki kunnan Barde, fad’i ya ke
‘’An amra auren Yarima Abubakar Barde da Gimbiya Fatima....’’
Nan ya ya tsaya cak tamkar wanda aka zarewa rai, su kansu
abokannasa sun girgiza kwaran gaske.
Daga cikin masallaci, ana gama d'aurin auren, inda kowa ya ke
mamakin sauyin al’amura da aka samu, musammam jama’ar
Sa'ayrasa, shi kuwa Aisar tunanin hanyar fita daga cikin jama’a
yake, domin zuwa neman Bintu ba tare da Junaidu ya ankare
ba. Bayin Sa'ayrasa ne d’auke da farantin goro da alawa, su ke
bin kusirwa kusirwa in da suke mik’a farin tin jama’a na d'iba
san ran su.
Bawan da ya zo kusurwar da su Aisar su ke, Aisar ya fara
mik’awa, in da ya girgiza masa kai alamar ba ya buk'ata, har
bawan zai wuce, nan idanun Aisar su ka sauka bisa yatsun
bawan, me zai gani? Zobensa da ya bawa Bintu ne cikin
yatsun na shi, bai ankara ba sai ji yayi Aisar ya damk’o
hannunshi, a tsorace bawa ya saki farantin hannun sa dan ko
shakka babu ya san tawagar shugaban k’asa ne
gabansa.Hakan ya dawo da hankalinsu Junaidu da sauran ‘yan
tawagar garesu. Aisar na mai duban idanun bawan ya furta
‘’Ina ka sami wagga zo6en? Menene dangantakarka da mai
zo6en? Ina Bintu d’iyar bayi?’’
Babban gida kuwa 6angaran Jakadiya, Bintu na zaune tare da
su Jakadiya sai ga Gimbiya K’amariyya ta shigo, ta yi kyau
kwarai cikin jajayen kaya, ta d’aura alkyabba ruwan zuma bisa
kayan, ga bayi nan biye da ita. Ta zo kar6ar mabudin wajan aje
baki na musammam domin kar6ar Yarima Barde.
Ta na zaune ta na jiran Jakadiya ta shiga ciki dan d’auko mata
mabud'in, su ka ji an shigo 6angaren Jakadiya an gud’a. Tuni
hanjin cikin Bintu ya kad’a don kuwa ta san ta faru ta k’are an
yiwa mai dami d’aya sata, aure dai an aura. Tuni ta fashe da
kukan da dama ya tsaya k’asan mak’ogaran ta.
Jakadiya ta fito d’auke da mabud’i, yayinda Ladiyo ta shigo jiki
na rawa, sai tafa hannu ta ke cikin salati da sallallami.
Jakadiya ce ta tambaya ko lafiya, yayin da hankalin kowa ya
koma gareta.
Cike da ladabi Ladiyo ta durk’usa gaban Jakadiya ta na mai
fad’in
‘’Yau na ga lafiyar Allah Maigari gauro talaka da mata hud’u.’’
Cikin k’aguwa Gimbiya K’amariyya ta ce
‘’Me ya faru ne Ladiyo?’’
‘’Wato Allah shi taimaki Gimbiya, ji da gani dai ba ya k’arewa
sai randa kurman bebe ya makance, Sarki Abdulraman na
Fabarusa cike ya ke da abin mamaki, wani lamari sai shi.....’’
‘’Yo to wani abin mamaki? Ya ce ya fasa ne?’’
Jakadiya ta tambaya cikin rashin fahimta. Kana Ladiyo ta ce
‘’Eh to ya fa fasa be kuma fasa ba, da ya tashi yin bazata, sai
ya amrawa d'ansa Barde Bintu.....’’
Hakan yayi daidai da ihun da Gimbiya K’amariyya ta kurma ta
na mai zubewa k’asa sumammiya. Nan da nan aka yi kanta.
Bintu kuwa yanda maganar ya doki kunnenta ta tabbatar ta
zama kurma, don kuwa ba ta jin hayaniyar da ake gabanta
‘’Ya amra ma d’an sa Barde Bintu....’’
Maganar da ke ihu jikin kunnenta kenan.
1⃣
Tuni waje ya kaure da salati da salallamin bayi, Jakadiya ce ta
sa aka yi maza aka shigar da K’amariyya daga cikin d’aki
gudun gulman da ta san tabbas sai ta yad’u daga bakin bayin
da ke wajan. Bintu kuwa ta ma kasa gane komai, kukan ta
kawai ta ke, aure dai an d’aura mata, ko ta na so ko ba ta so
tafiya ne dole a tafi da ita. Gashi a rasa wanda za a d’aura
mata sai saurayin Gimbiya K’amariyya, Yerima Barde na
Fabarusa! Hannu biyu Bintu ta d’aura bisa kan ta ta na mai
fad’in
‘’Wayyo ni Bintu alk’iyama ta ta zo’’
Daga cik’in uwar d’aka, bayan an kori duka bayin da ke
b’angaran Jakadiya, Hajja Kilishi da Inna Salti wanda Jakadiya
ta aika Ladiyo da Kyallu su sheda ma su abun da ke faruwa ne
su ka shigo d’aya na bin bayan d’aya, biye da su Gimbiya Binta
ce, wacce ita ma labari tuni ya je mata.
Jakadiya ta umarci bayin da su ka taka mata baya su yi jiran
ta waje. Bayan an watsa ma Gimbiya K’amariyya ruwa, da
rokan Allah ta farfad’o ta na mai bin su da kallo kamar lokacin
ta fara ganin fuskokinsu. Kanta bisa kan cinyar Inna Salti,
Jakadiya zaune gaban ta sai kuma Gimbiya Binta wacce ta
dad’e da gigicewa da jin lamarin da ya faru, in ban da kuka
babu abinda ta ke don gani ta ke duk laifin Bintu ne ko shakka
babu ita da uwarta ne su ka sa musu hannu wannan balk'in ya
fad’a kan ‘yar uwarta.
Ko da idanun Gimbiya K’amariyya ya sauka kan Gimbiya Binta,
ita ma d’in ta fashe da kuka don sai a sannan ne ta dawo cikin
hayyacinta sosai. Cike da damuwa Hajja Kilishi ke tambayar
‘’Menene ne? Gide menene ke faruwa? Tun dazu fa nake
tambayar ki Binta amma amsa ta gagara daga gareki, yanzu
kuma mun samu ta farfad’o maimakon a sami sauki ina, kun
maishe da gida kamar wajan makoki! Shin ba kwa gudun
abinda zai je ya dawo? Kun fa san gidan ga cike yake da baki
da kyar na sami hitowa daga cikin jama’a, ko rufa mana asiri
ku sheda mana abun da ke faruwa.’’
Cikin kuka muryarta dak’yar ya ke fita, Gimbiya K’amariyya ta
amsawa Hajja Kilishi, ta na mai fad’in
‘’Na shiga uku Hajja, Inna Salti na shiga uku, na d’au wuk’a na
dab’a ma kaina, Allah Ya nuna min ikonSa, Barde…..Yarima
Barde na Fabarusa……’’
Kuka ya ci k’arfinta, ta kasa k’arasawa sai shasshek’a ta ke.
Cikin rashin fahimta Inna Salti ta ce
‘’Barde? Me ya faru da Barde na Fabarusa?’’
‘’Ni kam ta dad’a sa kai na cikin duhu, jakadiya wagga yarinya
ba gamo ta yi ba kuwa?’’
Cewar Hajja Kilishi cike da damuwa.
‘’Yarima Barde da Didi masoya ne, shi ne dalilin ta na k’in
amincewa ta auri sarkin Fabarusa wanda yake mahaifi a
gareshi.’’
Gimbiya Binta ce ta amsa ma su.
‘’Kayya! Kai wagga lamari da me yayi kama! Kun ga irin ta ko?
Gashi dai an cuci d’iyar mutane kin kuma cuci kanki
K’amariyya, anyi gudun gara an tadda zago! Jakadiya dai ga
irinta nan dai kin gani don kuwa wagga kulli ke da wagga d’iya
ku ka kulla.’’
Fad’in Inna Salti ta na mai nuna matuk’ar b’acin rai.
Jakadiya da tunda aka fara maganar ta sha jinin jikin ta, jikinta
ya yi sanyi kamar wacca aka tsunduma cikin ruwan sanyi
cewa ta yi
‘’Uhum Allah shi ja da ran ki, yo to ni me zance? Ni ina naga ta
ce wa? ‘’
Cikin kuka don kuwa idanunta sun rufe K’amariyya ta furta
‘’Don Allah ku taimaka a warware wanga lamari, don Mai
Sama, kwarankwatsa zan iya rasa rayuwata, dan Allah ayi
maza a shedawa takawa kafin na rasa raina, Ammu ki taimaka
min…..’’
Kai Hajja Kilishi ta jinjina kafin ta ce
‘’Gide Takawa zai saurari wanga azzance kuwa Jakadiya?
Yanzun ga ya na can wajan liyafar d’aurin amren nan......’’
Kafin Jakadiya ta amsa Gimbiya Binta ta yi saurin taran
numfashin ta ta hanyar fad’in
‘’Ku taimaka tun kafin a makara, dan kuwa ba Sidi ba ko ni ma
ina tara muddin ba a warware wanga
amre ba, ya d’iyar bayi za ta amri mutum kamar Barde, dan
Allah Jakadiya ki sama mana mafita tun kan na had’iyi zuciya
na mutu dan kuwa ciwon da na ke ji ya ma fi na Didi’’
‘’Makara kam an riga an makara, saidai fa a jira bayan komai
ya lafa a yiwa Takawa magana watakil shi bai zai rasa dabara
ba.’’
Cewar Hajja Kilishi yayin da tashi tsaye jiki sanyaye, tak’ara da
fadin.
‘’Kunsan mu na da baki, duk abinda za ku yi kada ku manta da
martabar Takawa, ku kula ku kame kanku kada ku jawo mana
abun da zai halaka yankin ga gaba d'aya’’
Ta na gama Magana ta juya abun ta ta fice, ta bar Inna Salti
tare da Jakadiya cikin al’ajabi. Gimbiya Kamariyya gani ta ke
sam Hajja Kilishi ba ta damu ba saboda ita dama ba ta ta6a
haihuwa ba shi ya sa sam ba ta damu da lamarinsu ba. Ita
kuwa Gimbiya Binta abinda ya tsaya mata a rai bai wuce na ta
na murnar raba Bintu da masoyin a Aisar, sai gashi ta zama
matar wanda har ta gama rayuwar ta a doran k’asa ba za ta
sami kamar shi ba, abun takaici ta yiwa yar uwarta asarar
masoyi, duk akan wanda sam be ma san ta nayi ba.

Bintu ɗiyar bayi ce (book 2) Chapter 2&3
Admin 001 Sayyadi Sadiq
@Whatsapp 08146934644
2⃣
Daga cikin masallacin Sa’ayrasa, ko da bawa ya tsinci kansa
gaban Aisar, hannunsa damke cikin na sa yayinda yake jero
masa tambayar da shi kansa bai ta6a jin ko da makamancin
sunan ba a matsayinsa na bawan barga da kwananan ya dawo
cikin sawun bayin da ke kula da lambu. Zufa ne ya shiga keto
masa, cikin kame-kame da in’ina ya ce
‘’Eye? Na’am lillahi warasulihi wanga zoben tsintarsa na ka yi,
idan kuwa na yi karya aratta kashe ni….’’
Maimaikon Aisar ya saki bawa sai dad’a damke hannu bawa
yayi. Cikin neman d’auki bawa ya kai dubansa ga sauran yan
tawagar na shugaban k’asa ya na mai neman d’oki. Hakan
yasa Junaidu tausaya ma bawan duk da ko shakka babu ya
san zoben hannun bawa mallakin d’an uwansa ne. Kana ya na
mai shiga tsakanin bawa da Aisar ta hanyar ciro hannun Aisar
daga cikin na bawa yayinda yayiwa bawa nuni da ya ciro
zoben, nan da nan bawa ya ciro zoben, ya mik'awa Junaidu kai
durkushe ya na mai fad’in
‘’Tuba na ke, aradun Allah tsinta na kai, ku min rai……’’
Nan bawa ya fashe da kuka, wanda hakan ba k’aramin dad’a
kular da Aisar ya yi ba, ji yake kamar ya shek’eshi har sai ya
matso gaskiya daga bakin bawan.
‘’Ka ga ba kuka za ka yi ba, babu abun da zai ma muddin ka
fad’a masa gaskiya, shin in aka sami wanga zoben?’’
Cewar Junaidu ya na mai kok’arin saka idanunsa cikin na
Bawa don gano inda bawa ya dosa. Shi kuwa bawa ya gama
rikicewa sai rantse rantse kawai yake, fad’i yake
‘’Tsinta na ka yi, kwankwasi tsinta na ka yi a lambu, aradu
tsinta na ka yi.’’
Jin an furta
‘’Ko shakka babu gaskiya ya ka fad’i, don na shedi wanga
bawa mai gaskiya ne.’’
Gaba d’aya hankalinsu ya koma ga mai maganar. Sanye ya
yake cikin bakar jamfa wanda aka masa ado da bakin zare,
idan ka d’auke rawaninsa da yake fari komai na jikinsa bak'i ya
sanya, kai kace wani taron bakin ciki ya halarta, ko da shike a
nasa 6angaran hakan ta ke. Kallo d’aya Aisar ya masa ya
d’auke kai ya na fad’in
'’A matsayinka na wa za mu k’ar6i shedanka?’’
‘’A matsayinsa na Yarima Nuhun Sa’ayrsa ranka shi dad’e.’’
Fad’in bawan da ke tafe da Yarima Nuhu kenan, ganin idan ba
a yi dagaske ba yanda ran Yarima Nuhu ya ke a dak’ule komai
mai afkuwa ne. Jin haka Junaidu ya bawa Yarima Nuhu hannu
suka gaisa haka sauran yan tawagar amma ban da Aisar
wanda idan ransa yayi dubu ya 6aci, don haka a kusa ya ke.
Sanin hakan ne ya sa Junaidu yin saurin yiwa Yarima Nuhu
bayani, ya na mai nuna ma sa zoben. Ganin zoben da kuma jin
wanda Aisar ya ke tambaya Yerima Nuhu ya san ko shakka
babu Bintunsa ta arziki a ke nema, zoben nan shine zoben da
ya kar6a daga hannunta ya wulgar. Wato wannan shi ne Aisar
d’in da yake soyayya da Bintunsa….
Bawan nan dai da ke tafe da Yarima Nuhu ne cike da ladabi ya
furta
‘’A hakik’anin gaskiya wanga bawa ada bawan barga ne, be
dad’e da dawowa sahun bayinmu masu kula da lambu ba,
saboda haka ina mai tabbatar maka ba zai san wagga d’iyar
bayi da ku ke magana akai ba, dan yanda alama ya nuna ko
shakka babu ta na daga cikin bayin cikin babban gida tun da
har aka iya tsintar zoben hannunta cikin lambu, haka nima da
na ke bawan kofar gabas, ba mai yiyuwa ba ne na santa,
domin kuwa ba mu da wata alak’a da zai had’amu da bayin
cikin babban gida’’
‘’Shin ina za mu sami wagga d’iya?’’
Aisar ya tambaya ya na mai fatan samin mafita daga bakin
bawa. Nan take bawa ya masa alk’awarin tayashi cigiyar Bintu
nan ba da dad’ewa ba, sannan su ka sallami wannan bawa da
zoben Bintu ke gareshi. Yarima Nuhu ya shaida mu su abinda
ya kawo shi gare su, wato sheda ma su ana buk’atar su d’akin
taro. Ya na gama shaida mu su yayi gaba dan kuwa yanzun da
ya gane Aisar shi an samrayin da ya kwace zuciyar Bintu ya fi
ma sa d’aci akan auren da aka d’aurawa Bintu a yau, dan
wannan ya san ba mai d’orewa ba ne musammam idan aka yi
la'akari da wanda aka d’aura mata.
Dakyar Junaidu ya lalla6i Aisar, sai da ya masa tuni da ba fa
su kad’ai ba ne, akwai manya cikinsu, sun zo d’aurin aure ne
bisa wakilcin shugaban k’asa ba wai hakan nan bak’akatan su
ka zo ba, sannan ya samu ya d’an shawo kansa, ta hanyar
masa alk’awarin bayan komai ya lafa Junaidu da kansa zai
tsaya har sai sun samo Bintu kafin su juya gida, ko da kuwa
hakan ya na nufin raba tafiya da tawagar ta su. Da wannan su
ka yi tattaki zuwa d’akin taro ba tare da sun bari manya daga
cikinsu sun fahimci abinda ke faruwa ba.
Yarima Barde kuwa da dabara Yarima Jafar da Khalil su ka ja
shi mota, gaba d’aya ya zame mu su tamkar mutum mutumi,
ya d’auke mu su wuta. Cikin mota sai da su ka d’au kusan
rabin awa babu wanda ya iya furta komai.
Dogarin Masarautar Fabarusa ya zo ya buga musu kofa, nan
ya zube ya na mai sheda mu su umarnin Sarki Abdulrahman
na a ma su iso gareshi.
‘’Su na cikin masallacin ne?’’
Yarima Jafar ya tambaya, in da Dogari ya ba shi amsa da
‘’A'a, sun wuce ga d’akin taron masarauta tunda jimawa,
Yarima kad’ai ake tsimayi ranka shi dad’e.’’
‘’Mu na nan tafe.’’
Cewar Khalil, yayinda Dogari ya tashi da sauri ya na fad’in
‘’A iso lafiya.’’
Yarima Jafar na duban Yarima Barde ya ce
‘’Ka bawa zuciyarka hakuri mu amsa kiran Mai Martaba’’
Ko kallonsa be yi ba bare ma ya nuna alamar ya san da shi
ake, kamar an aje dutse. Ganin haka Khali ya ce da Yarima
Jafar.
‘’Ka san halin Barde a sama ya ke, ina zaifi mu lalla6a mu je a
dai ga fuskarshi, in ya so sai mu nemi izinin tafiya ta hanyar
ba da uzirinmu ga Mai Martaba.’’
Da wannan shawara su ka fito daga motar, amma Yarima
Barde fitowa ta ma sa wuya, sai da Yarima Jafar ya ma sa tuni
akan wanda ya sa a yi kiransa sannan ya fito cike da k’asaita,
dama shi idan ransa ya 6aci nan fa sarautar ta sa ke bunk’asa.
Ko da dogarawan da ke tsimayinsu su ka ga fitowarsa tuni su
ka rufa musu baya, zuwa d’akin taro, kai kace Sarki
Abdulrahman na Fabarusa ne da kansa ke tafe.
3⃣
Dakin taron ya cika fal da jama’a, tawagar Aisar da shigowar
su ke nan, na su 6angaran na shugaban k’asa su ka zauna.
Haka ma hakiman Sa’ayra da Fabarusa, Agadez, Diffa da
sauran Hakiman yanki da sassa na jamhuriyar Nijar wajan su
na musammam su ka zauna. Haka kuma yankin Sarakuna
wanda Sarkin Sa’ayrasa mai gayya mai taro ya hakimce, kusa
da shi kuma Sarkin Fabarusa ne zaune cikin aminci. Hakan ba
k’aramin farantawa jama’a rai yayi ba, wai ashe dai akwai
ranar k’arshen gaba tsakanin Sa’ayrasa da Fabarusa? Shin
dama akwai rana irin ta yau da za a ga Sarakunan wanga yanki
zaune cikin aminci?
Busa na alkgaita ke tashi daga waje, jama’ar Sa’ayrasa kwan
su da kwarkwatar su sun yi dandazo cikin d’akin taro, murna
gun su ba a cewa komai domin kuwa a yau yunwa zai kau a
k’asar su. Ganin shigowar su Yarima Barde tuni dogarai su ka
hau yiwa ango kirari. Shi kuwa Yarima Barde sam ba cikin
hayyacin sa ya ke ba, amma in aka d’auke Yarima Jafar da
Khalil wanda dama sun san halin da abokin na su ya ke ciki
babu wanda zai kalle shi ya ce ya na cikin wani hali, sai dai ma
ayi tsammanin tsabar sarauta da miskilanci ne yake d’ibar sa.
Sai kuma Mai martaba Sarki Abdulmalik na Fabarusa, wanda
kallo d’aya ya yiwa d’an na sa Yarima Barde bayan ya kai
gaisuwar sa ga Mai martaba Sarki Sule na Sa’ayrasa, ya gane
halin da ya ke ciki, kasancewar wajan mahaifin na shi ya yo
gadan kafiya, cijewa da kuma yin burus kamar be san abun da
ke faruwa da shi ba, amma in aka tona cikin zuciyar su, Allah
kad’ai ya san tafasar da ta ke. Murmushi Mahaifin na sa yayi,
cikin ran sa kuwa yacewa ya yi
"d’an mu Abubakar, alkhairi ne mu ka kulla ma ka ba sharri
ba, nan gaba za ka gode ma na kwaran gwaske’’
Ganin Yarima Barde durk'ushe gaban Sarki Sule, haka ma
abokan na sa biyu, hannun su na dama dunkule suna mai
jinjina ga Sarki Sule, fadawan Sa'ayrasa su ka amsa ma su da
"Jinjine dama lafiya alher, gaishe ka Yarima Badde, an gaishe
ku samari"
Sarkin Sa’ayrasa kuwa cikin nuna ya amsa gaisuwar ta su shi
ma ya dan daga na shi hannun daman a dunk'ule. Yarima
Barde ya shiga ran sa saboda kamala da kwarji na sa, ji ya ke
ina ma ina ma, ina sirikin na sa ne na gaske, da ya san haka
Sarkin Fabarusa zai aikata, da ya bayar da d’iyar sa ko da
kuwa ba a san ran ta ba ne.
Ko da Yarima Barde ya had’a ido da Mahaifin na sa, sai ya yi
saurin saukar da na sa idanun. Duk wannan abun da ke faruwa
a kan idanun yayan Barde, wato Yarima Sadauki na Fabarusa
wanda tun da ya ji abun da mahaifin na su ya aikata bisa ga
auran da ya d'aura ya k'ara jin tsanar Barde ya dad'u a kirjin
sa. Domin kuwa shi ya kamata Sarki ya d'aurawa aure shi da
ya ke babban d'an sa ba k'anin sa, hakan da yayi shi ya nuna
k'arara Sarki Abdulraman ya fi kaunar Barde, ya kuma fi fifita
shi akan Sadauki. Hakan ne kuma Yarima Sadauki ba zai
lamun ta, dan ya san ba k'aramin girma aka zubar ma sa ba a
idanun jama'a, dole kuma ya d'au Mataki. Idanun sa kan
Barde, cike da tsana ya ke duban sa yayin da aka yiwa su
Barde nuni ga na su wajan zaman, wato kusa da Yarima
Sadauki da abokan sa su ka zauna.
Tun shigowar su Yarima Barde idanun Yarima Nuhu ke kan sa,
ji yake kamar ya je ya sheda ma sa wacece Bintu in ya so
kowa ma ya rasa. Haka ma Aisar wanda ya san burin Bintu na
ganin Yarima Barde ko da sau d’aya ne a rayuwar ta, wai ta
rasa wanda za ta kira mai kyawun duniya sai wanga buzu!
Cewar Aisar cikin ran sa yayinda wani bakin kishi ya ta so ya
mamaye ran sa, shi dai fatan sa Allah ya sa ya sami damar
ganin Bintu tin ka a tafi da ita cikin bayin da za su raka gimbiya
Binta Fabarusa, ko dan Yarima Barde dole ya d’auke ta, sam
jinin su be had’u ba, dan haka Bintun shi ba za ta yiwa matar
Barde bauta ba, ko da kuwa duka dukiyar sa za a buk’ata
domin mallaka ma sa Bintu, a shirye ya ke ya rasa komai.
Bayan an sami nutsuwa ne aka bud’e taro da addua’a, sannan
aka shiga abun da ya tara su a wajan. Su Yarima Jafar sun so
su nemi izinin tafiya, amma hakan be samu ba, sai hakura su
ka yi su ka zauna kamar gumaka, ba um ba um um, ga abokan
Yarima Sadauki da shi kan shi Yarima Sadauki sai harbin iska
su ke. Barde kam duk be san ana yi ba.
Sarkin fabarusa ne ya fara jawabi, ya mai nuna farin cikin sa na
kulla aminta da auratayya wacce ta kawo k’arshen gaba
tsakanin Masarautar ta su biyu. Bayan haka ya gabatar da
takardar shedar sun bayar da bashin da masarautar Sa’ayrasa
su ka buk’ata, ya kuma ce tun da an zama d’aya, sa iya biya a
tsanake sannu a hankali ba tare da tashin hankali ba.
Nan waje ya kaure da ihu da sowa na jama’a, kowa na nuna
jin dad’in sa da kuma alfahari da halin girma irin na sarkin
Fabarusa. Dogarawan Fabarusa su ka shiga jera kirari ga
Sarkin Su, fad'i su ke
"Lafiya Sarkin yakin Sarkin musulmi
Lafiya maida garin wani kango
Lafiya Barden mahadi
Lafiya Sukukun bakaka
Lafiya Darzaza amalen sarakuna
Lafiya ba hau da wani ba sauke wani
Lafiya hana kangara
Lafiya Sakaka babban bako
Lafiya Bango madafar bayi
Lafiya hadarin kasa maganin mai kabido
Lafiya kwankwason jimina mai wuyar shafawa. Lafiya adali,
lafiya salamun, salamun salamun"
Jikin sarkin Sa’ayrasa ba k’aramin sanyi yayi ba. Sai da waje
ya lafa sannan Sarki Abdulraman ya k’are jawabin na sa da
adduar zaman lafiya tsakanin Masarautar da kuma fatan Allah
ya bawa shugaban k’asa lafiya.
Sai da sarkin Sa’ayrasa ya sa hannu a takardar ta hanyar
amfani da hatimin masarautar ta sa, yayi na sa jawabin na
nuna farin ciki da godiya ga masarautar Fabarusa, sannan
kuma ya yaba da halin dattako na Sarki Abdulrahman dan har
ga Allah ya bashi mamaki matuk’a. ya k’are jawabin na sa tare
da fatan alkhairi tsakanin Masarautar biyu. Cikin ran sa

Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5

Please Login or Register in order to submit comment