Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Prince da zai barta (lokacin rabuwa da gatanta Prince Abdulrasheed yazo) ko taki ko ta so, duka wannan ihu ne take yi bayan hari Abdulrasheed bazai taba mantawa ba balle ya yafe mata, wanda shine komai nata kuma masoyin da suka kulla alkawurran soyayyar da bazasu lissafu ba, soyayya mai tsabta wadda ikon Allah ce kadai ta wanzar da ita don ta san bata kai nan ba, bata is aba, bata kai matsayin ba. Haba! Wannan tunanin yasa sai ihunta ya ninka na baya.
Ta kuma kasa ambaton sunan Allah don tasan shima Ubangiji bata da uzuri a wurinsa don bata yi godiya da ni’imar da yayi mata ba ta bata sahihiyar soyayyar Abdulrasheed ba don isarta ba.
Bata taba tunanin akwai abinda zai iya yin sanadin da Prince zai ce mata “You! The bastard WHORE! Don’t dare show me your ugly face again!!!”.
Wadannan sune kalaman Prince na karshe a gareta, mafiya daga hankalinta, domin a sanda ya fadesu ta tabbata ya fadesu ne baka da zuci babu wata rana da zaiyi nadamar furtasu.
Tunda abinda yayi Kehinde shi yayi Taiwo. And they often share the same feelings, kowa nasu ya san hakan. To idan har Aunty Taiwo ta ji laifinnata ma, anya zata kara kallonta da idanun rahma? Ko dubanta da aminci da kaunar da take mata wanda duk sanadin Prince dinne???
Kowa bai ishi Murjanatu kallo ba, in dai baida sarauta, mulki ko dukiya, itama din albarkacin Prince ta ci hawa-hawa a wurinta tunda har ta riketa na shekaru a hannunta, sai kuma jininsu yazo ya hadu daga bisani saboda dukkansu halayensu yazo daya masu son rayuwa ne sosai.
Wannan tunani ya kara dugunzuma zuciyar Hasinah, ta kara kururuta kukan da take yima Dr. Taiwo a waya kamar zata fasa dodon kunnenta, fatan ta dai Murjanatu taji tausayinta. Ta kuma tuna ita marainiya ce, da bata da kowa sai su.
Murja ta kasa gane komai akan kukan Hasinah da maganganunta, wadanda bata san ina suka dosa ba, ta bata su ne a lullube, a kudundune, amma hakika ta daga mata hankali fiyeda yadda Hasinan tayi zato, kasancewar Taiwo a very cool and reserved person, wadda ko kusa bata son iface-iface da hayaniya yasa ta sa hannu ta toshe kan wayar da hannunta, ita dai ta san daga ita Hasinah har ubandakinta AbdulRasheed son juna suke kamar su hadiye juna don soyayyah, AbdulRasheed na takun-saka da mahaifiyarsu Nenne akan taki yarda ya auri zabinsa Haseenah, wani cikinsu bai taba kawo karar dan uwansa gareta ba sai yau da Haseenah ta kawo karar Prince, don haka Taiwo ta kasance a uku, ta rasa bayan wa zata bi a cikinsu. Da kyar ta nisa tace da Hasinah cikin lallashi, da gajiyawa da jin kukan da ihun nata na marassa tawakkali, cikin nuna matukar concern ga damuwarta tace.
“Hold on Hasinah, kina ji na ko? Ki bar kukannan haka take it easy Hasinahty, ki tsaya har in yi magana da shi yanzu, idan na samu ya daga kirana, I will get back to you ASAP.
Nima yau kwana uku kenan ban ji shi ba, bai kira ni ba, nima kuma ban samu na kira shi ba, abin yana raina matuka amma yawan karatun dake gabana kuma bai barni na bi ba’asin long unusual silence dinnasa ba”.
Irin kukan da Hasinah ke yi har zuwa lokacin yayi matukar daga hankalin Murja, duk kuwa da cewa Hasinah ta rage karfinsa sai sheshsheka da jan majina, maraicinta da rashin gatanta in babu su a tare da ita, ya fito karara ta cikinsa.
Kamar ance karshenta yazo ne, idan Prince AbdulRasheed ya juya mata baya. Kamar zautatta sabon kamu haka sai ta hau sakin zance a kunnen Taiwo.
Ni Hasinah da ba Uwa ba Uba ba dangi, ba asali ba nasaba ba tushe, sai Abdulrasheed da Taiwo dinsa, da suka karbeni a hakana, duk da rashin asalin nawa.
I was ungrateful, selfish and greedy.
Shine komai nawa, my life support and also a guardian, idan ya bar ni a dalilin kuskurena ina zan koma yanzu a karbeni banda GIDAN MARAYUN AMBURSA?
Zancen zucinta kenan da har bata san yaushe ya fito ya subuce daga bakinta yake shiga kunnen Taiwo ba.
Taiwo ta tabbatar al’amarin da ya saka Hasinah mai soyayyen idanu kuka da nadama irin haka akan AbdulRasheed, harta zauce haka, wanda kusan a baya sai abinda tace masa yake yi, saurayin kan-tace ne Abdul. Abdulrasheed din da ransa ne kawai bai fitar ya baima Hasinah ba don SO na gaskiya, ko meye wannan laifin zai kasance ba karamin laifi bane tayi masa da bazai iya yafewa ba.
A takaice zamu ce Taiwo tafi kowa sanin irin son da Abdulrasheed ke yiwa Hasinah sabida itace confidant dinsa.
Don haka ta katse wayarta da Hasinah ta dauko komatsanta ta fito daga motar zuwa ciki, tana shiga gida bata nemi su Kiki ba, da mai rainonta Bunmi, ta tadda babban danta Hakeem yayi dai-dai yana barci a falo, da alama ya kwaso gajiyar makaranta ne, a gigice take sosai da lamarin nasu, don haka sai ta wuce dakin barcinta kai tsaye ta rufo kofa jikake bamm! Kafin daga bisani ta zauna a bakin gado, tana warware mayafin laffayar jikinta, sannan ta ciro wayarta da gaggawa ta kira dan uwan nata.
Wayar ta jima tana ringing har saida ta katse kanta, akalla Murjanatu ta kira ta kara kira ya kai sau uku kafin tayi sa’ar samun Prince ya daga, shima kuma ba tare da yace da ita komai ba.
In da sabo ta saba da sarautarsa da ginshirarsa. Amma yau bayan jan aji na sarauta da ginshirar ma tabbas akwai wani abun. Tunda akalla duk jan ajinsa shi zai fara gaisheta.
An dauki lokaci tana maimaita masa sallama cikin kwantar da murya da nema masa sassauci, tareda nema masa amincin Ubangiji ta hanyar cikakkiyar sallama, har saida ta kai ga jawo masa Hadisin daya yi umarni da wajabcin amsa sallama ga musulmi da mafi kyawunta ko mayar da martini da makamanciyarta.
Kafin ta samu Engnr. AbdulRasheed (Kehinde) Idris Akanni, ya amsa mata da kyar. Kuma ciki-ciki. Ta hanyar cewa;
“Wa’alaykumussalam-warahmatullah”.
Bayan haka sai bai kara cewa ko uffan ba.
Wannan wani abu ne weird daga Abdulrasheed zuwa gareta a wurin Murjanatu-Taiwo. Ko Prince zai ma kowa kyaliya irin wadda ya saba yiwa wanda ya bashi haushi banda ita Taiwo dinsa, amma me? He has his reason. Wato tuni ya riga ya san zancen da Taiwo tazo zata yi masa, bana komai bane na ‘yar dakinta Hasinah ne, ya riga ya san yadda soyayyarsa da Hasinah ta assasa aminci mai girma tsakaninta da ‘yar uwar tagwaitakarsa, Taiwo, sanadin zamanta tare da ita na wasu shekaru tana karatu a hannunta.
Ya riga ya kwana da sanin cewa ta kanta Hasinah zata fara bi, da sunan a sulhuntasu, a bashi hakuri ko a lallashe shi. Yau ba Taiwo ba ko lallashin Nenne ne bazai ji ba, in dai akan matsiyaciya Hasinah ne.
“Let her GO please! I will take her back to where I adopted her!”.
Cikin murya ta lallashi da nuna kauna, irin tasu ta ‘yan biyun Nenne Sappa da kowa ya sani, wadanda ko a cikin tagwayen duniya bakidaya su twins ne na musamman ta fannin fahimtar juna da kaunarsu da juna, haka kulawarsu ga damuwar kowannensu mai girma ce, don ta zarta ta common Yaya da kaninta, saidai ace ta wadanda suka fito duniya daga mahaifa daya, sannan a lokaci guda.
Ubangiji Subhana da kansa yaga damar ya dunkulesu ya haliccesu tare a mahaifa guda, don haka zukatansu sau tari suna aiki da bugawa tare ne.
Taiwo ke yiwa (twin brother) din nata Prince Abdulrasheed magana cikin lallashi na hikima da taushin murya.
“Kehinde, me ke faruwa tsakaninka da Hasinah haka? How can I let her back to orphanage a shekarun girmanta don kawai ta bata maka rai?
A kowanne relationship, na soyayya ko mu’amala, dama ai akan samu sabani which is normal, amma a wannan lokacin hankali bata yake yi bat, sai ayi kokari asa hankali ya nemo shi.
Dama ka daukota da niyyar watarana in ta bata maka rai zaka maidata ne? Ko kuwa ka daukota ne don ka aureta ba don tun asali ka taimaketa ba?”
(Daga ita sai Kakansu Emir da Babansu Dade suke kiransa Kehinde, kowa PRINCE yake cewa) kannensu kuma suce masa HAMMA.
Maimakon ya bata amsar tambayarta kamar yadda ta bukata sai taji muryarsa (in despair) cikin wani yanayi yana fadin.
“Taiwo Please! Let that PIG go I said! (Ki bar wannan Aladen ta tafi nace), in kuma kin ki toh, ya rage naki. For now, ki hada ni da Kiki!”.
A yadda Murjanatu taji muryarsa kadai ta fahimci yana cikin matsananciyar damuwa da kunar zuciya, kuma da gaske yake muryar Kiki kadai yake son ji da shirmen zantukanta ya fiye masa zacennan da take masa na wadda ya kira “karya” kuma “alade” Hasinah.
Kiki kadai yake bukatar saurare a wannan lokacin, baya son wani zance bayan nata, koda ABCD dinta zata yi masa ya fiye masa wannan wa’azin na Taiwo mai kama da a kafa mata drum ta hau kai tayi ta yiwa wasu amma bas hi ba.
Jiki sanyaye Murjanatu tabi umarninsa, ta fito da wayar a hannunta zuwa dakin da Kiki-Ruqayyat take wasa da mai rainonta.
“Uncle AK wants to speak with you Kiki!”
Taiwo ta fadama Kiki, tana mika mata kan wayar. Da zumudi mai yawa yarinyar ta dirgo daga dan gadonta ta amsa, tana dokin jin muryar Kawun nata, wanda koda take yarinya karama ta san girman kaunarsa gareta ko Daddynta Toufeeq albarka.
Sabida yadda yake janta a jiki har ta saba dashi a waya. Balle kuma in ya zo gidansu, tayi ta sukuwa a jikinsa kenan. Taiwo ta koma gefen gado ta zauna cikin damuwa ta zuba tagumi tana kallon shirmen da Kiki ke masa a waya na sunayen dabbobi da suka fara da harafin “A” fuskarta fal annashuwa, shi kuma Uncle din ya dage yana biye mata cooly. Dama tone na muryarsa kullum is cool amma na yau is more than cool is despair.
A tunaninsa a wannan yanayin da yake ciki muryar Kiki-Ruqayyat kadai da shirmenta ne zai mantar dashi ya debe masa kewa, ya rage masa zogin zuciya da radadinta kan abinda ya gani, wato ya mantar dashi abinda Hasinah tayi masa. Kiki his beloved little niece, amma ina! Ko Kiki ta gaza yau, domin ta kasa mantar da shi bacin ran Haseenah dake kasan ransa, still yana nan yana sakadar ruhinsa har zuwa lokacin. Kiki ‘yar lukuta yarinyar data shiga ran Engnr. Abdulrasheed matuka, itace diyar Taiwo ta biyu bayan Hakeem.
Ganin sun ki gama shirmensu shi da Kiki, ita kuma an barta cikin ci da zuci, yaki ma ya saurareta balle ya gaya mata hakikanin abinda ya faru, sai Murjanatu ta karbi wayar daga hannun Kiki ta bar dakin, don ita tafi kowa sanin yanayin da Abdulrasheed zai iya kasancewa a wannan lokacin in har da gaske ya yanke shawarar rabuwa da Hasinah kwatakwata.
Ta san Abdulrasheed bai iya sabo ba, sabo yana wahalar dashi, wholeheartedlhy yake sabawa da mutumin da ya kwanta masa, balle sabonsa da Haseenah na kusan shekaru biyar, kasancewar ta san ba karamin so yakewa Hasinan ba, kafin ya iya yakiceta daga ransa zai sha matukar wuya.
Hausawa suka ce wai sabo akewa kuka ba mutuwa ba! sabon da yayi da Haseenah shi zai fi wahalar dashi fiyeda soyayyarta, wadda dama tausayi ne jigonta da wasu hujjoji nasu. Don haka ta bar dakinsu Kiki ta soma takawa zuwa dakin ta don kaucema kunnen Bunmi.
Sai da ta zauna a gefen gado ta tattaro nutsuwarta sannan ta sake koro masa tambaya, (wannan karon sounding absolutely serious with seniority domin kuwa da sunansa na yanka ta kira shi, wanda da wuya kaji Taiwo tayi hakan. Itada Kakansu Emir (Kehinde) kawai suke kiransa wato sunan shi na al’ada wato (Hassan).
“I said what’s happening ABDULRASHEED? Tell me! Nace me ya faru? Ko me ke faruwa tsakaninka da baiwar Allah Hasinah haka?”
A shaqare (kamar wanda aka shaqe maganar a makogaronsa AbdulRasheed yace da ita.
“Babu komai! Ki yarda babu komai! Amma ki sani KARYA ce kuma ALADE ce!!!”
“Naji na kuma yarda, amma yanzunnan ta kira ni tana kuka, kuka fa as in screaming any how, tace ka daina daga wayarta yau kwana biyu kenan, kuma kayi mata iyaka da zuwa inda kake…. Kace kada ta kara nuna maka mummunar fuskarta.
Me tayi maka haka da zafi? Bansan yaushe ka koyi wannan halin na saurin yanke hukunci da daukarsa a hannunka ba.
Anya Kehinde, ba zaka dinga hakuri kana sassauta fushinka akan kananan abubuwa ba ga na kasa da kai alhalin kaida ita kuna shirin zama abu daya???
Mu fa mata duk inda muke sunanmu mata, daga lankwasashshen kashin hakarkarin kirjinku aka halicce mu, dole ayita hakuri damu, balle Hasinah da har gobe yarinya ce da bata kai ashirin da biyar ba, kuma marainiya… sannan…. sannan…kasan batada ko….”.
Cikin karaji da nashi screaming din da ya firgita Murja. Wanda ya dame na Haseenah AbdulRasheed ya katse Taiwo, da iyakacin muryarsa yace.
“Maraici nasa mace zama Alade ko dabba mai iya saduwa da shaqiqin mijin da zata aura, saduwar ma irin ta dabbobi? Irin…irin…”. Ya kasa karasawa sakamakon wani makoko da yazo ya tokare a makoshinsa, image din nasu ya kara gilma masa.
“Hasbunallawu wani’imal wakeel”. Inji Taiwo “ko dai ka sha kwaya ne Kehinde?”
Ya rintse ido da karfi. “Don Allah don Annabi daga yau sai yau…. Maman Kiki, na rokeki da darajar iyayenmu, ki manta da mun taba saninta, kada ki kara yi min maganar wata Hasinah daga yau na rufe babinta a rayuwata.
Nenne ta fimu gaskiya, tsintacciyar mage bata mage, matsiyaci matsiyaci ne ko a tandun mai ka saka shi kandas dinsa zai fito ya nuna asalinsa na zina da halinsa na kwadayi, kada ki kara tuna min ita!
I AM PURE AND I LOVE PURITY. Ni dan Sunnah ne cikin Uwa da Ubana, daga tsafta na fito ba najasa a jikina. Ki manta kin taba sanina da wata halitta wai ita Hasinah saboda Dabba ce…. karya ce!
In dai a sanadina kika santa, kike kuma alaqar uwardaki da abota da ita, to daga yau na raba ku nasa almakashi na datse duk wata alaqa tsakanin ku, from thousand milestones.
I hate them, I repeat I hate them!
Har abada bani ba su!!!”.
Murjanatu Taiwo, taji hankalin ta yafi nada matukar tashi, maganganun da yake yi are very dirty. Daga inda ya dauko Hasinah kadai, ya kawo ta kusa dashi, cikin rayuwarsa, zaka shaida girman son sa gareta.
Tabbas ruwa baya tsami a banza inji Murjanatu, kalamansa kadai sun gama bayyana komai duk da cewa indirect ya fadesu.
Taiwo sai nan da nan ta soma kuka don tana tsoron kada yayiwa kansa lahani. Gashi babu kowa a tare da shi a inda yake.
“Abdulrasheed, my Kehinde, I am your only twin sister TAIWO! Gaya min me ya faru daku, ka ji Kehinde dina?
As always, ka sani, zan rufe sirrinka, kuma ni zan fahimceka in karbi uzurinka, koda duk duniya bata fahimceka ba ni zan fahimta, zan kuma kasance a bayanka kamar kodayaushe, koda duk duniya bata bayan ka, be rest assured that your Taiwo will stand by you!”.
Da irin wannan lallashi da ban bakin Taiwo take shawo kan Abdulrasheed, to yau ma da irin sa ta dage don ya gaya mata abinda ya faru tsakaninsa da Hasinah Ambursa exactly, ita da wa yake cewa ya tsane su haka babu ko sakayawa?
Kalamansa dai, da wasu daga na Hasinah sun gama tona komai na kazantar da Hasinah din ta aikata, amma so take ya gaya mata abinda ya faru da bakinsa don tana shakka tana kuma tabaab Hasinan zata iya aikata hakan. Tunda dai a sanin ta da Abdulrasheed baida abokin fada balle masoyiyarsa, matar da yake burin zai aura yana kammala project na masters dinsa wanda Polo ya dauke masa hankali da tun shekaru biyun baya ya kammalashi?
Inda wanda bazai taba boyewa damuwarsa a duniya ba komai girmanta ko muninta to Taiwo ce, abokiyar tagwaitakarsa, his very own twin, his confidant Murjanatu-Taiwo, duk abinda yake ciki a rayuwa ita yake fara fadamawa kafin kowa, komai zafinsa.
Taiwo da Abdulrasheed sunada wani irin (twin bond) ga junansu da ko mahaifiyarsu Nenne Sappa, wani sa’in bata sanin girman sirrin amanar dake tsakaninsu.
Itama kuma Taiwo hakan yake a gareta, Abdulrasheed shine confidant dinta, har sirrinta na mata wanda a matsayinsa na namiji bai kamata ya sani ba, amma Adulrasheed ya san komai na mata akan ‘yar uwarsa Taiwo, kamar lokacin da Taiwo ta samu girma wato lokacin data fara jinin al’ada lokacin suna ‘yan shekaru sha biyu shi ta fara sanarwa cikin tashin hankali da tsoron ko wani mummunar abu ta aikata, Abdulrasheed shi yaje chemist aka hado shi da always pad ba tare da Nenne ta sani ba, sai daga baya ne Nenne ta sani, bayan tuni Murjanatu ta iya kula da kanta da taimakon kaninta, akan Taiwo zai iya batawa da kowa itama haka, in yace kowa yana nufin KOWA!
Itama din kuma haka yake a gareta, idan Taofeeq ya bata mata rai Abdulrasheed kadai take iya kira ta gayawa, domin a wurinsa ne kadai zata samu duk wani lallashi da shawarwari da kwarin guiwa da kuma goyon bayan da duk take nema cikin kowanne yanayi duk da kasancewarsa namiji.
Abdulrasheed ne ya fara sani lokacin da ta samu cikin Hakeem, ko Toufeeq din bai sani ba yana can yawon duniyarsa, saida cikin ya girma. Abdulrasheed shi yayi ta kula da ita har ta haihu don gidanta ya koma da zama yana kaita asibiti da makaranta, don cikinta nata na Hakeem irin mai masifar laulayi ne kamar bazata kai ba, ga miji baya kusa. Taiwo da Kehinde kaunar ‘yan uwantaka sukewa juna irin wadda ba duk ‘yan biyu ba.
A hankali Murjanatu taji numfarfashin Abdulrasheed a kunnenta, wani abu da bazata iya tuna (when last) ta ji shi ba, watakila tun farkon balagar su, lokacin da suna sakandire a kasar Japan idan Dade dinsu (mahaifinsu) ya hana shi hawa Doki ya janye shi daga bargar Dawakan Polo ya rankwasheshi yace ya tafi makaranta.
Haka zai yi ta furzar da numfarfashin bacin rai kamar mai nakuda, don baya iya kuka a rayuwarsa. Wannan numfarfashin (is a replica) na kuka a wurin Prince AbdulRasheed, “her very own Kehinde”.
Don haka lamarin ya daga hankalin Murjanatu fiyeda tsammaninsa.
Kiris ya rage Taiwo ma ta fashe da nata kukan na zallar kaico, da taya dan uwanta bakin ciki da kishi da Allah wadai, he is totally heartbroken a baka da zuci, lokacin da yake yi mata bayanin abinda ya faru dasu kwana biyu da suka wuce tsakanin sa da fiancée dinnasa Hasinah, da dan uwansu cousin dinsu kuma amininsa guda daya a family da ya janyo jikinsa yake amfana dashi wato (Adetokumbo).
Cewa yayi ya gansu suna irin sex din dabbobi akan gadonsa.
“What a betrayal!” Taiwo kanta a karshe (could not control her own tears), ta barsu suka zubo a kundukukinta. Sabida feeling din Prince nata ne. And she feels the pain din har fiye da shi, don ita da hannunta ta rike masa Hasinah ba da sanin maahifiyarsu ba da farko, don sun san bazata amince ba, har sai bayan ta fara nisa sosai da karatun sakandire ma a hannun Murjanatu sannan Nenne ta san da zamanta wurinta.
Zuciyar Murjanatu ta hau tafarfasa. Data tuna wacece Hasinah, da irin gatanta rayuwarta da Abdulrasheed yayi, kirjinta ya hau tururi kamar wuta ake hurawa.
Ta tuna wanene kaninta Prince Abdulrasheed, gatan da yake dashi da girman nasaba da matakin rayuwar da yake kai, amma duk bai duba su ba, sabida halin tawali’unsa irin na Nenne, ya zabi Hasinah a matsayin life-partner din da yake burin mallaka, against the wishes na mahaifiyarsu, ita kuma a matsayinta na mai son duk abinda Kehinde dinta yake so sai ta mara masa baya, ta taya shi son Hasinah a haka da zuciyarta daya.
Yau shekaru biyu kenan da suke ta takun saka da mahaifiyarsu a kan neman yardarta da amincewarta da aurensa da Haseenah, don Nenne ta kafa ta tsare bata boye ba, duk kirki irin nata da yawan taimakonta ga kowa kiri-kiri tace bata yarda Abdulrasheed ya aure ta ba, ba don komai ba sai don NASABA wani abu ce mai girma da muhimmanci a Aure. Amma a wannan lokacin, a wannan gabar, Taiwo ta san Prince support dinta kadai yake nema ba ingiza mai kantu da rura wuta ba.
Idan bata karfafeshi ba yau, waye zai zama karfinsa???
Nenne me zata ce in taji? Banda Allah ya kara? Ta dade tana cewa dasu bata kin Hasinah, amma tsintacciyar mage bata mage. Shi garin banza duk kyawunsa a farau-farau din banza ne.
Abin nufi wato mara tsarkin asali da kyawun nasaba ba duka keda tsarki ba. Shiyasa har gobe ba’a yi auren ba, ake ta jan lokaci. Don neman yarda da albarkar Nenne.
Ashe da rabon zancen Nenne zai tabbata gaskiya tun tana raye kuma tun gabanin cikar alkawarin dake tsakaninshi da Haseenah?
Taiwo ta kara fada a fili cikin girgiza kai “lallai tsintacciyar mage bata mage”. Kuma “Garin banza a farau-farau din banza yake karewa!”.
A tunanin ta Hasinah zata dubi maraicinta da daga darajarta da Abdulrasheed yayi a tsakanin mata tsararrakinta, musamman fiddota da yayi daga gidan marayu na garin Ambursa ya dauketa cikin mutunci ya kaiwa ‘yar uwarsa, ta yi sakandire ta ‘ya’yan gata, kafin daga nan ya kawota kasar Japan, yasa a makaranta, cikin ire-iren marayun da yake ponsoring scholarship dinsu a kasashen waje ba wanda ya kawo jikinsa wato inda yake zaune sai Haseenah, a tunaninta ko wannan ya isa yasa Haseenah ta tsayar da soyayyarta da sha’awarta da hankalinta akan sa shikadai, ta zame masa matar rufin asiri, ba kamar sauran ‘yammatan da ke haukar son shi don wasu kyale-kyale nasa ba, kamar kasancewarsa “basarake” kuma “celebrity”. Sannan gashi “Handsome Yoruba Demon” da shaidanun matan Africa dake kasashen ketare ke rububi don son sheke aya dashi kawai ba.
Ta dauka Hasinah zata barranta kanta daga masu neman soyayya ta watsewa bayan shigarta Jami’a, ta dauka Haseenah zata zama mai kamewa data iyawa maraicinta, ta dauka zata tsaya ga matsayin da Allah ya bata na fiancée din da Abdulrasheed ya yarda zai aura da zuciya daya cikin dimbin matan dake son shi da suka fita gata da kyawun nasaba, ko don kasancewarta musulma kuma bahaushiya, ashe kame kai ba daga yare ko kabila yake ba, saboda kyawun surar dan uwanta ma kadai ya ishi duk wata mace mai lafiya da dogon buri akan samun miji na nunawa sa’a tinkahon duk da zata yi a kan kowanne da namiji.
Taiwo ta zabi su bar maganar nan a tsakaninsu. Suka binneta a ranar, ya zama wani sirri ne da ko iyayensu bazasu iya fadawa ba.
Taji ta tsani Hasinah daga yau, da shima Toks din, wato dan uwansu (Tokumbo) fiye ma da yadda Abdulrasheed ke ikirarin ya tsanesu. Bata taba tsammanin akwai dan akuya cikin zuri’rsu ba sai yau.
Shi ya san cewa (he has someone on his corner), all the time he need (a kowanne lokaci ya bukata), wata wadda zai iya kira (his own person) wato tashi, a duk sanda ya bida, wadda ba kowa bace sai ‘yar uwar tagwaitakarsa “Dr. Murjanatu-Taiwo Akanni”. Kafadar da zai jingina akai yayi kuka ko dariya a lokuta na bacin rai irin wadannan.
***** **** ****
WAIWAYE ADON TAFIYA (2)
(AMBURSA ORPHANAGE)
Ambursa karamin gari ne a jihar Birnin Kebbi. Prince ya saba da irin wadannan tafiye-tafiyen cikin garuruwa da kauyukan Arewa a duk lokacin da yazo kasarshi ta haihuwa, kasancewar rayuwarshi tafi yawa a yankin Tokyo ta (Japan).
Dabi’arsa ce kaunar marayu, don haka duk inda ya samu labarin akwai gidan marayu ya kan ziyarta, komai nisan garin daga inda yake, baya kasa a gwiwa

Please Login or Register in order to submit comment