Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

zai je don kai tallafi. Idan yaje din kuma sai ya zaga ciki ya gansu, ya gaisa dasu, ya shafa kawunnansu, yana mai godewa Allah cikin zuciyarsa dashi yayi masa ni’imar iyaye, masu kykkyawan asali daga tsatso mai albarka, iyayen ma jajirtattu irin ‘Nenne’ da ‘Dade’ da ba duk duniya ake da irin su ba.
Shi ba attajiri bane a lokacin dalibi ne, amma yanada attajirar zuciya, ‘philanthrophy’ musamman ga marayu a cikin jininsu ne na iyaye da kakanni.
Kusan zamu iya cewa ya gaji wannan (positive attitude) din na son marayu da son inganta rayuwarsu ne daga Kakansa. Sarki Akanni mai ran karfe. A zuciyarsa yana tausayin maraya a duk inda ya ganshi, yana kuma jin maraicin da suke ji a ransa, ba don shi din maraya bane.
Yana yawan kwatantawa a ransa inda ace shine su, yake rayuwar da suke yi a kange, babu Nenne da Dade a gefensa, a samansa da kasansa, ko yaya rayuwa zata kasance masa?
Yana kan hanyarsa ta isa gidan marayun Ambursa ne daga Birni Kebbi, inda yaje halartar daurin auren abokin karatunsa Bello Dasuki. Bello D. abokinsa ne tuntuni da sukayi karatun sakandire tare a Japan a lokacin Baban Bello Jakada ne acan, dan asalin Birnin Kebbi. Don haka ne bai ji kiwar yin tattaki tun daga Lagos ya halarci daurin aurensa ba.
Hira ce tayi hira tsakanin shi da Bello Dasuki bayan kammala reception na daurin aure, Dasukin na tsokanarsa da UBAN MARAYU! Inda sabo ya saba da wannan sunan daga bakin Dasukin, tun daga lokacin da ya nemi rakiyarsa zuwa wani gidan marayu a Bauchi. Dasuki yace dashi cikin hira ai kwanannan suma an bude musu sabon gidan marayu a garin iyayensa wato Ambursa.
Zancen ya wuce, kamar bai ji ba ma, suka shiga wata hirar ta abubuwan da suka shafesu na POLO.
Har sukayi sallama da Bello Dasuki zai wuce Airport, inda daga nan zai tashi zuwa gida Lagos, bai gaya masa zai ziyarci gidan marayun nan da ya bashi labari ba. Kawai tunaninsa na alkhairi ya gaya masa akwai bukatar yaje sabon gidan marayunnan ya gani, domin akwai wasu kudade tare dashi masu dan dama da yayi niyyar kaiwa gidan marayu na jihar Gombe, kuma ya tuna bazai samu zuwa Gombe ganin Kakarsa Oummana kafin ya wuce Japan ba lokaci zaya kure masa, tunda kuma daga Birnin Kebbin zuwa Ambursa babu nisa bari kawai ya karasa can, ya basu tallafin sannan su wuce Airport din Sokoto.
Umarni yayiwa direban Bello Dasuki wanda ya dauko shi a motar Dasukin, da ya karkata kan motar ya juya dashi zuwa Ambursa. Ya ce dashi ko basu san wajen ba suyi ta tambaya.
Don haka suka tasarma kauyen Ambursa, kuma koda suka shiga garin basu sha wahalar tambaya ba kasancewarsa kwararren direba kuma dan gari, suka samu sabon gidan marayun, wanda ba’a dade da kafashi a jihar Kebbi ba, sakamakon yawaitar tsintar ‘ya’ya da walagigin marayu a jihar. A saman gidan manyan rubutu ne da shudiyar kala an rubuta AMBURSA ORPHANAGE.
Shugabar gidan marayun Mrs. Taibat ta karbeshi sosai, domin da gani babu tambaya; irin bakin da suke maraba-lale dasu ne, wato ‘ya’yan manyan kasa masu zuciyar taimako. Wato masu kawo tallafin kudi, ko na karatu ko na suttura ko abinci ga yaran, duk da bata san waye shi ba, amma ko daga yanayin tafiyarsa da kasaitarsa da maganarsa tasan dan manya ne, mai alaqa da sarauta.
Don haka ita da kanta tayi masa jagora har wajen jarirai da ake kulawa dasu da madara, daga nan suka isa gun toddlers, ya gansu, ya shafa kansu harda yi musu wasa sosai kasancewarsa mai son yara.
Sannan ta kaishi bangaren yara mata masu tashen balaga (teens) ‘yan makaranta. Anan idanunsa ya kyallo masa ita, bahaushiya ce, babu ko tantama mai kyau ce sosai, daga duba na farko zaka ga kyawun nata a zahiri, duk ‘yammatan sun lura da shigowar Madam tareda bakon, amma ita yarinyar bata lura ba, suka soma gaishe su duk hankalinta bai kai kansu ba, sai da Madam Taibat tace “Haseenah baki ga baki bane?”
Da sauri yarinyar ta dago jin an ambaci sunanta, yayi mata murmushi ya karaso har gabanta yace “sannu da karatu Haseenah!” ta amsa, ta kuma gaishe shi sai ya karbi littafin hannunta yana dubawa. “Basic Science and Technology” ya ga an rubuta a jiki. (For junior secondary schools). Yarinyar zatayi sa’ar Hakeem dan abokiyar tagwaitakarsa Murjanatu. Don haka kawai babu shawara da Nenne yace bari ya dauketa daga nan ya kaiwa Murja in yaso ta hadata da Hakeem su cigaba da makaranta. Kyawunta ya fisgeshi sosai a matsayinsa na namiji, sannan jan ajinta. Dama ance irin wadannan ‘ya’yan kyau ne dasu.
“Ajinki nawa Haseenah?”
“Bana na gama JSS” (tana magana kai a sama, cikin ko’in kula) da gani ba wadatar tarbiyyah.
“Kinada burin cigaba?”
“Sosai ma kuwa, Enginiya nake so na zama”. Sosai yaji yarinyar ta bashi tausayi ko don yadda take magana kanta tsaye da boldness kamar ba marainiya a gidan marayu ba, don mostly yaran zaka same su basu da karsashi, basu da ko guts na karfin gwiwar kallon mutane ma cikin ido, sabida (inferiority complex) dake dabaibaye dasu, amma ita kar take kallonsa cikin ido, idanunta a tsaitsaye, ko kuma don kasancewar fanninsa kenan wanda ta zaba din a matsayin burinta yasa yaji ta burge shi?
Don haka koda suka koma ofis shida Mrs Taibat yayi abinda bai taba yi ba tunda yake zuwa gidan marayu daban daban, watau yabi duk process din da ake bi na daukar yaro a gidan, na daga cike-ciken takardu ha a karshe yayi (adopting) dinta.
Amma a ransa ya san ba dai ya kaiwa Nenne ba, yayi abunsa kai tsaye without a second thought, saidai ya kaiwa Murjanatu, it ace mai biyewa komai yake so mai kyau ko mara kyau, in yaso ya dinga daukar nauyin karatunta a makarantar kwana, shi dai yaji ransa na son kyakkyawar yarinyar, in yaso in akayi hutu ta zauna gidan Murjanatu har ta isa shiga jami’a ya nema mata admission a fannin Engineering din duk da take so. Ko iya haka aka tsaya ya gina rayuwarta, tunda in ta gama zata iya samun aikin da zai isheta kula da kanta har watarana ta tallafi gidan marayunsu da marayu ‘yan uwanta.
***** ***** ****
Ya damka amanar yarinyar a hannun wato Aunty Murjanatu, ya kuma fara biyan komai na karatunta tareda Hakeem yaron Murja. Lokacin ba’a haifi Kiki ba. Murja ta kaisu makarantar kwana ta British int’l school a garin Lagos. Kasancewar duk abinda dan uwanta ke so bata opposing tana taya shi ne su cimma abinnan.
Ta dade da sanin philanthrophic heart dinshi, na cikin dabi’un shi masu kyau, da suka banbanta shi da sauran matasan zuri’arsu kaf!
Ta yarda ta amince babu mutum mai zuciyar halin girma da daukar girma tun bai girma ba cikin jikokin gidansu kamar Prince, duk wani hali irin na Kakansu Emir Abdulrasheed ya kwashe shi ya bar kowa da sudin kwano. A kafatanin zurri’ar gidansu ba mai kyakkyawar zuciya ta taimakon mara galihu irin ta dan uwanta Prince. Tun daga kan kannen mahaifin su, har zuwa tulin ‘ya’yan da suka haifa, ba wanda baya shan rabar taimakonsa (in one way or the other).
Shi Da daya ne tamkar da goma ga iyayensu. Gidansu ba’a tara ‘ya’ya maza ba, shikadai ne namiji a cikinmata amma ya tarewa iyayensu gurbin misalin yara maza goma!
**** **** ****
Shekaru uku suka zo suka wuce da tarin cigaba ga yarinya Haseenah, bai yi kasa a guiwa ba yana biyan kudin karatunta tare dana Hakeem duk shekara, wadda da aka tashi bata permanent name a makaranta sai ya bata surname da sunan marigayin abokinsa Bello Ambursa, wanda ya rasu gaba kadan da daurin aurensa.
Hakika Prince ya ji mutuwar Bello ba dan kadan ba, kullum ya ga Hasinah sai ya tuno shi har kaunarshi da Bello Ambursa ta shafi Haseenah Ambursa, ko bakomai sanadinsa yaje har inda take ya daukota. Daga kan Bello bai kara yin aboki ba sai Tokumbo wanda dama Cousin dinsa ne da suka taso tare.
Duk sanda ya zo kasar Najeriya zai je wajenta a makaranta suyi ta tadi, in kuma suna hutu ne tana gidan Murjanatu acan yake ganinta har sabo mai tsanani ya gitta a tsakaninsu.
A haka har Haseenah ta gama sakandire, a shekarar data kammala ya samar mata gurbi ya kuma yi sponsoring karatunta a wata jami’a a kasar da yake nasa karatun a lokacin, wato Tokyo.
Wannan ne ya kawo kusanci na kamshin soyayya tsakanin sa da marainiyar da yake riko Haseenah, wanda (in no time) ya rikide musu zuwa soyayya. Har shi da Murjanatu suka yanke shawarar ya aureta kawai, don a zamanta a Japan duk da a hostel take rayuwa, tofa kullum tana like dashi a gidansa fiyeda sanda take hannun Murjanatu da gaisuwa da hirar makaranta kadai ke shiga tsakaninsu, acan kuwa bata san kowa ba sai shi, shiyasa koyaushe take like dashi a gidansa a lokutan da bata da karatu, musamman da idanunta suka fara budewa da maza ta san menene soyayya.
Sun yanke shawarar shawo kan Nenne don ta yarda ya auri Haseenah shida Murjanatu gudun sharrin shaidan ya gifta tsakaninsu, to kullum suna tare a inda ba idon kowa nasu a kansu, yace da Murjanatu yana tsoron watarana ayi abinda ba shikenan ba duk da yana fin karfin zuciyarsa, amma Nenne ta kafe ta ki. Soyayyarsu shi da Hasinah tayi tsananin karfi a lokacin har suka soma sakin layi. Sun buga sun buga da Nenne ta bari ayi auren har lokacin ta ki, don zaman da take yi dasu ma Nenne bata so, tafi so kowanne irin taimako zata yi maka tayi maka shi daga nesa, ba tareda ta dauko ka ta saka cikin zuri’arta ba gudun kada a bata mata tarbiyyarsu. Wannan ne dalilin da yasa suka kawo har lokacin da Hasinah ta shiga mataki na uku a jami’a suna soyayya ba tareda sunyi aure ba.
A irin hakane har ta saba da cousin dinsa mai zuwa gidansa lokaci-lokaci yana sauka a wurinsa wato Adetokumbo Akanni.
Tokumbo a Japan yake harkokin kasuwancinsa, Automobile Business Mogul ne. A daya gefen shi da Murjanatu suna cigaba da fama da Nenne akan dai ta yarda ayi auren haka, amma Nenne tayi tsalle ta dire tace sai a bayan ranta danta zai auri adopted orphan.
A girman nasaba irin tasu, wannan babban abin gori ne a gareta ko a wurin faccaloli, ace duk matan duniya da wadanda ke cikin family din mahaifinsa da nata ace wai Prince ya rasa matar aure sai akan Haseenah da take tsintacciya zai kare kamar wanda uwa tacewa jeka ka gani?
Cikin wannan rikicin suke shi da Nenne har kawo yau, Murjanatu na taya shi fighting gun Nenne don shi Dade dinsu duniya ta shaida mijin tace din Nenne ne, shima da bakinsa yana fada “I obey her decisions because she leave no stone unturned”. Duk hukuncin da Nenne tayi bashi da ja, saboda tsabar yarda da sahihiyar soyayyarsa gareta.
A ganinsu shi da Murjanatu babu wadda zai aura da zata girmama shi, ta kaunace shi saboda Allah irin Haseenah, ga Prince da son girma musamman daga matar da yakeso, kai duk bayeraben basarake akwai tsananin son respect daga mace, a ganinsu ita kadai zata aure shi ba don arzikin su ko don tarin “FAME” dinsa ba (shahararsa a idon duniya).
Duk wata mace da zata aure shi a halin yanzu abubuwan da zata duba kenan (sarauta, kyau, arziki, da shahararsa), sun yi amanna banda ‘yar da ya raina ya ginawa rayuwa da kansa, har a yau take jera kafada da ‘yammata masu gata da ilmi ‘ya’yan manyan Najeriya a jami’ar da take wato Haseenah Bello Ambursa.
Hasinah ta tsinci kanta rana daya a soyayyar ubangidanta kamar koma fiye dashi, bata kuma san daga wane lokaci shakuwarsu ta rikide zuwa soyayyah ba. Duk da banbancin yare dake tsakaninsu, ita Hasinah bata tuna cewa ma ita bahaushiya ce saboda cakuduwa dasu Aunty Murja dashi kansa Prince da ba hausar yake yi bama kwatakwata, ko ya iya ko bai iya ba Allah masani. Duk da ita Haseenah na ganin bata kai matsayin da Prince zai aure ta ba, amma kaninsa Tokumbo dake tare da shi kuma suke shiri itada shi irin sosai kullum yana yawan karfafata da cewa.
“If she’s lucky…. Probably zata iya samun auren PRINCE!”
A bakin Tokumbo Haseenah taji cewa Mamanshi ma bahaushiya aka auro musu ita, tazo ta haifesu shi da su Murja. Shiyasa taga shi da Prince duk da suke ‘yan maza zarr basa kama da juna.
Yace su din surki ne na yare guda biyu; Fulani/Yoruba wato sun hada duka jinin yammaci da arewacin Najeriya, ba kamar sauran ‘ya’yan family dinsu ba da gabansu da bayansu Yarbawa ne.
**** **** ****
Taiwo tayi ajiyar zuciya data tuna asalin haduwar shi da Hasinah da kuma irin sakayyar da Hasinah tayi musu yau. Ita ba suruka ta dauki Haseenah bama face ’yarta ko kanwarta. Don haka taji ciwon lalacewarta duk da tayi iya kokarinta a kanta.
Tafi ganin laifin Haseenah akan na Tokumbo. Ko maiyasa? Don itace mace, kuma ita ta bada kafa har ya sayi mutunci da martabarta daga ido da zuciyar Prince.
Ta tabbatar Hasinah tayi rashi, rashin da duk duniya ya kamata ta taru ta jajanta mata, domin tabbas tayi rashin mai kaunarta da gaskiya sabida son duniya, kwadayi da biyewa zuciya da rashin sanin girman zina da illarta aikatata ga mai yinta a addinin musulunci. But who knows? Ko itama ta hanyar da aka sameta kenan? Sannan bata yi islamiyya ba.
Dr. Taiwo, ‘yar uwa mai rike sirrin dan uwanta, ko bai roketa ba, ya san wannan magana zata cigaba da zama sirri ne a tsakaninsu su kadai, sai ko Allah da ya halicce su, da kuma Hasinan da Adetokumbon. Ko iyayensu tayi alkawarin bazasu ji wannan mummunar maganar daga bakinsu ba.
Domin wani abu ne da zai kawo hargitsi mai girma ga zuri’ar Akanni gabadaya, watakila har ya jawo rarrabuwar kai, wanda basa fata. Jiharsu bakidaya ta shaida hadin kan zuri’ar Akanni da duniya bakidaya, na kasancewarsu tsintsiya madaurinki guda, don in wani ya yarda Adetokumbo zai aikata hakan a gareshi, duba da irin amintakar dake tsakaninsu, da irin taimakon da Abdulrasheed din keyi ga business din Tokumbo, wani bazai taba yarda ba, za’a ce sharri ne, ba don komai ba sai don kasancewar zuri’ar Sarki Akanni tsaftatacciyar zuri’ar kabilar Yoruba da basu yarda da ko bakar al’adar nan tasu ta a fara yin ciki a waje kafin aure ba, sannan bai da amini kaf zuri’arsu irin Adetokumbo Abdulfatahi Akanni.
Adetokumbo shine (favourite cousin) dinsa a cikin tarin kannensa maza da suke ‘yan maza zar kaf a family din Emir Abdulrasheed Akanni, wanda ya kasance Da yake ga Dan Iyan of Ilorin, daya daga cikin kannen mahaifinsa.

**** **** ****







ASALINSU
(ILORIN EMIRATE)
Bari mu dauko tarihin tun daga tushe, wato asalin kafuwar masarautar Ilorin. Kamar yadda kowa ya riga ya sani Masarautar Ilorin da aka fi sani da ‘Ilorin Emirate’ tana nan a jihar Kwara a yammacin Najeriya, tana daya daga cikin manyan masarautun Najeriya masu dimbin arziki, Ilorin Emirate, wata babbar attajirar masarautar Musulman Yarbawa ce a kasarmu mai dimbin albarka, wadda kafuwar tarihinta ya faro ne daga rayuwar Shaihu Salih Janta, da aka fi sani da (Shehu Alimi).
Kenan su din duk da kasancewarsu Sarakai, kuma manyan sarakunan kabilar Yoruba, to manyan Malamai ne, ma’abota sani na na addinin Musulunci da kyakkyawan riko dashi. Su din, har ila yau, sun kasance Shehunnan Yarbawa ne masu dauke da sani na Alqur’ani da Hadisi, wadanda sukayi gadon sahihiyar sarauta ta malunta da arziki mai dimbin yawa daga Kakan-Kakan su Shehu Alimi, sarautarsu sarauta ce mai asali da da kyakkyawar nasaba tun kafuwar kasar Ilorin.
Ilorin Emirate, ta kasance (multiethnic Muslim Kingdom) wato cakude take da kabilu da yarurruka daban – daban na kasar Najeriya guda hudu, wadanda suka hadu suka samar da Ilorin Emirate din, sun hada da; Balogun Gambari (Hausa), Balogun Ajikobi (Yoruba), Balogun Fulani (Fulani), Balogun Alanamu (Yoruba).
Kowanne bangare wato kowanne Balogun, nada (district head) wato sarkin dake wakiltar wannan bangaren/yankin, karkashin babban Sarki Emir of Ilorin, dattijo mai ran karfe Sarkin wannan zamanin da muke ciki a lokacin yanzu, wato Emir AbdulRasheed Dan Abdullateef Akanni.
Engnr. Edrees Abdulrasheed Akanni, ya kasance Da na farko ga Sarkin Ilorin; Maimartaba Sarki AbdulRasheedu Akanni, (the 11th Yoruba-Speaking Fulani Emir) wato Sarkin Ilori na goma sha daya.
Engnr. Idris shikadai ne Da a wurin mahaifiyarsa marigayiya Olori Murjanatu (Olori na nufin Queen bisa ga al’adar masarautar), tun Edrees yana yaro ta rasu sanadin cutar sankarar mahaifa.
Sai bayan rasuwarta ne aka bawa Emir Abdulrasheed Sarautar mahaifinsa, aka kuma kawo masa mata har hudu daga garuruwan yammacin Najeriya daban-daban ya sake aure, sune suka haifa masa sauran ‘ya’yan sa maza guda tara, har Edrees da matarsa ta farko Morjanatu ta haifa in an hada su goma kenan gabadaya maza ‘ya’yan Sarkin na Ilorin.
Emir Abdulrasheed da ya tashi yiwa dansa na fari aure wato Edrees Akanni, sai ya tsallaka ya auro masa Gimbiyar Gombe mai suna (Sappa) diyar abokinsa maimartaba Sarkin Gombe, Ahmadu Umar Jalloh (CFR) daga can cikin yankin jihar Gombe dake arewacin Najeriya.
Engr. Idris Akanni tun lokacin da mahaifinsa ya aura masa Sappa Allah ya zuba masa matsananciyar soyayyarta, aure ne na gata irin na ‘ya’yan sarakuna don bai wuce shekaru 27 ba lokacin da aka aura masa Sappa, ita kuma bata fice 17 ba, tun daga lokacin yake kula da ita, don yana matukar son ta kamar ya hadiyeta.
Sappa a hannun mijinta Engnr. Idris ta karasa girma ta kuma san rayuwa, ya shiga da ita duniya ta budi ido, wata irin soyayya Idris Akanni yake mata irin dai soyayyar Yarbawa ga kyawawan matan Fulani, (mazan Yarbawan Ilorin na matukar son matan Fulani) har dai in aka yi katari kyawawa ne masu farar fata da gashi yalalaa kamar dai ita Nenne Sappa din.
Auren nan nasu ya kafa tarihi a cikin duka zuri’arsu daga bangarensa da nata, domin aure ne irin wanda ba'a taba yi a masarautar Ilorin da masarautar Gombe ba, wato aure tsakanin masarautar Ilorin data Fulanin Gombe, albarkacin amincin dake tsakanin Babansa Emir da mahaifinta Sarki Ahmadu Umar Jalloh (Uban Kasar Gombe).

Sarki Ahmadu Jalloh Umar wato (Uban Kasar Gombe) da Sarki AbdulRasheed Abdullateef Akanni (Emir of Ilorin) sun hadu ne tun kafin su zama sarakuna magadan iyayensu, wato tun suna samari ‘yan bana bakwai a jami’a, sun hadu ne a yayin karatun digiri na farko da sukayi tare a can kasar Venezuela (South America) da iyayensu suka turasu inda dukkanninsu suka karanta siyasar duniya (International Politics).
Kenan mahaifinsu Idris Akanni wato Emir of Ilorin (AbdulRasheed Abdullateef Akanni aboki ne na jiki tun na kuruciya ga Baban Nenne Sappa, sarkin Gombe Ahmadu Umar Jalloh.
Kowa da ya sansu ya shaida Idrisu Akanni na ma Sappa wani irin mashahurin so, kamar babu wata mace a fadin duniya bayan ita. Banbancin harshe da yare bai zamo musu barrier ga soyayya ba.
Da fari Nenne ta samu kanta cikin bakunta, kasancewar ta shigo cikin wata kabila da ba tata ba, al’adu da dabi’u sun banbanta, amma gradually tayi hobbasa ta koyi yarensa duk da wahalarsa cikin dan lokaci, shima kuma dama ya iya fulatanci, wannan ne ya taimaka mata sosai wajen zama a cikinsu.
Sai ya zamanto Idris tun daga kanta bai kara marmarin auren kowacce mace ba har zuwa inda yau ke motsi da suka cimma shekarun girma shi da Nenne Sappa, da zaratan tagwayen ‘ya’yansu saiti biyu.
Bayan aurenshi da Sappa da kadan ya samu aiki da wata masana’antar safarar jiragen ruwa a kasar Japan (Japanese shipping authority), sai ya dauketa da karamin ciki ya tafi da ita Japan, ya saka ta a makaranta tayi ilmin zamani mai zurfi a fannin aikin jinya (Nursing) ba don tayi aiki ba sai don ta samu ilmin kula masa da lafiyar yaransu a gida.
Sappa ta fara da haihuwar ‘yan biyu mace da namiji a haihuwarta ta fari. Yaran da al’adar Yoruba ta riga ta basu suna “Taiwo” da “Kehinde” watau Hassana da Hussaini. Taiwo sunan Kakarsu ta wajen uba mai rasuwa taci wato “Olori Murjanatu”, Kehinde kuma kai tsaye ya samu sunan Kakansa Emir (Abdulrasheed) ake kiransa “Prince”, kenan Sarki aka yiwa takwara.
Taiwo da Kehinde sun taso cikin koshin lafiya da samun kulawar iyaye wanda ya haifar musu da saurin girma, saidai kowannensu da irin halinsa da irin dabi’unsa.
Kowa ya shaida Taiwo nada fitina, korafi, da mita tun tana karama, duk wani hali na matan yarbawa Taiwo nada shi musamma daukan tsegumi daga kannenta. Nenne Sappa bata shiri da Taiwo saboda kiriniyarta da wadannan halayen nata, gata da tsokanar yara ‘yan uwanta, Abdulrasheed kuwa gashi dai bas hi da aboki na jiki kamar Taiwo to kwatakwata halinsu ba daya bane, mahaifinsa na kiransa “Prince” Emir kuma yace masa “Kehinde”, a zahiri shi irin yaran nan ne kamammu, salihai, introvert, wadanda magana ma wuya take musu a zahiri saidai suyi action a gani, wato Abdulrasheed lumbu-lumbu ne da ake cema wutar kaikayi saidai yanada temper, babu mai sanin abinda ke zuciyarsa don fuskarsa bata bada expression na abinda yake ransa, wato kwarai ya iya waskewa da shanye expression, Nenne Sappa kadai ke iya karantarsa tana ganewa in abu yayi masa a fuskarsa ko bai masa ba. Babansu da suke kira “DADE” sanda suka fara budar baki shi da Taiwo, yaga yadda Prince yake saka Taiwo kuka ta ruwan sanyi, ba tareda iyayensu sun san me yayi mata ba, ya kance “Prince GREEN SNAKE ne”.
Sun rayu tsayin shekaru kusan goma sha biyar shi da Sappa da ‘ya’yansu na fari a kasar Japan, domin saukar su a Japan da watanni kadan suka haifi ‘Prince Kehinde’ da ‘Princess Taiwo’.

Abdulrasheed ya shiga ran Kakansa matuka, kasancewarsa namiji kuma jika na farko a gareshi, ya zama (favourite jika) ga Kakansa Emir of Ilorin, kuma babban aboki na jiki ga Kakansa Sarki Abdulrasheed.
AbdulRashid (Kehinde) da Murjanatu (Taiwo) sunyi primary da secondary duk a Tokyo/Japan, ba tareda an yi masu kanwa ko kani ba, Taiwo na gama sakandire akayi mata aure da Toufeeq Adam Adebayo, wanda aure ne na (family friends) tsakanin iyayen su, Toufeeq Bayarabe ne dan abokin Engnr. Idrees ne, sun zauna a Ilorin da farko inda ta shiga Unilorin ta fara karatu, Taiwo ta jima tana karatu kafin ta fara haihuwa.
Sau da yawa mahaifin Idris Akanni wato (Emir) yana yin tattaki har Japan in yana son ganawa da babban dan nasa Engnr. Idris Akanni, ko kuma in yana son ganin jikansa mafi soyuwa a ransa wato ‘Prince AdulRasheed’, sai da ya soma tsufa sosai ne ya daina yawon bin Idrisu kasar Japan inda yake zaune, don sauran ‘ya’yansa maza sun kawo karfi, sun taru sun hanashi fita daga Najeriya kwata-kwata, ko don kula da lafiyar sa data fara samun tasgaro da maida hankali ga hakkin talakawansa dake rataye a wuyansa.
Daga baya Idrisu din yayi ritaya daga kamfanin safarar jiragen ruwan da yakewa aiki ya dawo gida Najeriya gabadaya da iyalinsa, amma still yaki

Please Login or Register in order to submit comment