Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

murmushi, lallai kam idan kun gani saiku koya koh??, dariya ameera tayi ta ce, "to Abi!!.
Duk da larabci suke maganar, ina fassara mukune yanda zaku gane😜lol.
D'akin kusada papa ya shiga inda ya maida kayansa kafin yatafi, yay wanka, yaci abinci, kwanciya yayi domin yaďan huta.
Sai wayarsa ta hau wringing, mas'ud ne yake kiransa, ya ce, "ďan uwa ya akayine??, ya ce, "tambayata ma kakeyi?? To kafito muje wajen kamu.
Nawaf ya yatsine fuska, miye kuma kamu??, dariya mas'ud yayi ya ce, "idan munje zaka gani, kai malam nidai hajja haka ta ce, "mini sai gobe.
Dariya mas'ud yayi ya ce, "nima wasa nake maka, bari nabarka kayi barci ka huta, sai mun haďu anjima.
Okey bye🖐🏻Nawaf yafaďa yana ďaga masa hannu kamar yana ganinsa.
____________________________
A 6angaren yasmeen kuwa suna gidan su ameena anan ake zaman 'kunshi, gidan cike yake da 'kawayensu da dangin Nawaf larabawa da 'yan katsina, muta nen saudia dai basa jin hausa saidai turanci, dan haka gurin yazama dandalin turanci, tunda duk sunaji.
Wata mai 'kunshi aka ďakko tanama amare yasmeen da Ameena ta iya sosai, saikuma wasu su biyu sunayima 'kawayen amre suma kam gwanayene, yasmeen bata cikin walwala, amma bataso dangin Nawaf su gane dan haka ta saki jiki anata hira, Ameena ce kawai take gane damuwarta.
suma sai jida ita sukeyi, wata budurwace dai yasmeen takula batada walwala, tunda sukazoma tanemi guri ďaya ta zauna ita kaďai, (ummu habeeba ce) tana mutuwar son Nawaf, ita ce Nawaf ya ce, "ta cika 'kyau, kuma gsky ya faďa dan tafi sauran 'yammatan 'kyau gsky.
Sai dare aka maidasu gidansu Nawaf,, Nawaf yana zaune a harabar gidan tareda sauran samarin 'yan uwansa na katsina dana saudia, anata hira da raha.
Moto ci suka fara sauke 'yammatan, wajansu suka nufo suna mai farin cikin ganin Nawaf, gaisuwa aka shiga yi irinta al'adar larabawa, ummu habeeba kam saita tokare agefe ta'ki zuwa, Nawaf yana ganinta ya shareta, saida ga baya kuma ya mi'ke ya nufeta.
Tana sanye cikin ba'kar jallabiya ta naďe kanta da ďankwalin kamar yanda larabawa keyi.
Ya tsaya yana kallonta, ta harareshi nagode abi tafaďa tana turo baki gaba.
Yay ďan murmushi minayi miki kike yimini godiya??, tai far da idanu, ta ce, "kaima kasani.
Yay murmushi har fararen ha'koransa suka bayyana, yasan inda ta dosa amma saiya basar, ya ce, "kinga koma mikike ganin nayi miki to ki share ki tayani murnar aurena kamar yanda kikayi niyya tun farko, wananne zuwanki 9ja na farko ko??.
Bataso aka daina waccan maganarba amma yazatayi tunda ya nuna bayaso, ta ce, "eh shine na farko, ahaka dai sukaita hirarsu, cikin harshen larabci.
_______________________KAMU.
Yau takama kamu, kamu kuwa za'ayi irin na saudia ne, a harabar gidansu ameena za'ayi saboda yafi girma, an 'kawata gurin da kwalliya mai tsari, an baza 'katuwar darduma inda amarya da ango zasu zauna, agefe kuma an jere fararen kujeru inda sauran mutane zasu zauna.
Hajja ce tazo da kanta ta ro'ki su umma akan abarasu suma suyi al'adarsu ta larabawa a wajen kamu, su umma sukace babu damuwa suma sunada iko akan komai aii.
Wajen 'karfe 4:00pm na yamma aka gama shirya amarya cikin ba'kar doguwar riga ba'ka mai ďan karen 'kyau, gashinta yasha gyara an ďaureshi abaya wanda bai saniba saiya ďauka itama balarabiyar ce, dan NAFISAR KADUNA ce ta tsara mata kwalliya wadda amaren zamani suke yayi.
Kowa ya hallara sai amarya datake falo tana jiran isowar ango, dan tare akeso su fito.
Bayan kamar minti10 ango ya iso da tawagar abokansa, kowa ya zauna inda ya dace, aka raka ango inda zai ďakko amaryarsa.
Kai kawai ya tura cikin falon batarda yayi sallamaba, tana zaune akujera hankalinta yana kan waya tana game.
Ai gogan naku yana tsaye ya daskare dan ganin tsarin hallita irinta ubangiji, gsky koba komai yayi dacen mata 'kya'ky'kyawa rashin kunyartane kawai matsalarsa.
Jitai kamar alamar mutum yana kallonta, ta ďago da sauri, Nawaf tagani tsaye kamar gunki yayi masifar 'kyau cikin kayan larabawa wando da riga farare, anyi musu kwalliya da golden ďin zare, sumarsa tasha gyara daka gansa kaga cikakken balarabe.
Saida ta murguďa masa baki😏ta ce, "malam lafiya??, katasani gaba kana kallo, mi naci naka??.
Hararar ta yayi ya ce, "ki ajiye makaman rashin kunyarki har zuwa nanda kwana uku, domin yanzu ina kan bin umarnin iyayenane, bazanyi abinda zai 6ata musu rai ba agaban ďumbin jama'ar dasuka tara.
Yay wani murmushin mugunta, yaďora da faďin amma nanda kwana uku, ko ance ki kalleni kimin rashin kunya wlhy baza kiyiba, dan zanyi maganinki 'karamar mara kunya kawai.
Ta buďe baki domin mayar masa da amsa sai aka turo 'kofar.....wata 'kanwar momcy ce Fateema, ta ce, "Abbuna ku ajiye wannan soyayyar taku sai nan da kwana uku dan yanzu mutane suna jiranku.
Nawaf yaďan sosa gefen wuyansa ya ce, "sorry Abla(aunty kenan) muna zuwa.
Ya juyo ya harari yasmeen sanan ya 'karasa wajenta, hannunta yakama, jikin yasmeen yay wani yarrrrrrr, shimadai gogan naku saida sassan jikinsa suka amsa, Abla fateema ta gyarawa yasmeen ďankwalinta tabaya, sannan ta rufe mata fuska da wani jan gyale.
Nawaf ya ce, "Abla ai bata gani, idan ta faďi fa??.
Abla tayi dariya kai ka bari tafaďi bayan kaine ďan jagora.
Ya ce, "hakane idanma kin amince na ďauketa gaba ďaya naje na dire awajan.
Abla fateema ta tuntsure da dariya ta ce, "babu ruwana.
Yasmeen ta ce, "azuciyarta mugu saika nemi wadda zaka ďauka amma baniba.
Catake a zuciya take magana bata san afili takeyiba dan Nawaf yana jinta, amma Abla bataji tunda da hausa take maganar kuma ahankali.
Bayan sun fito gurin ya ďauki tafi, wajen kujerar da'aka tanadar musu mai ďan faďi sukaje suka zauna, saidai sun matsu juna sosai, yasmeen sai takurewa takeyi.
Agaban kujera aka shimmfiďa dardumar daza ayi kamu.
Ba6ata lokaci akayi addu'a ga ma'aurata, har yanzu fuskar yasmeen a rufe take.
Nawaf tya ce, "malama nifa kin matseni.
Dariya bin yabama yasmeen dan haka tayi murmushi, ta ce, "kanka akeji wai mahaukaci ya faďa ruwa.
Nawaf yay murmushi mai sauti, kema za'aji kankine yarinya, dan ďazu ina jinki.
Idan kagansu saika ďauka hirar arzi'ki sukeyi.
Bayan angama addua aka fara shirin kamu, ango da amarya suka sakko 'kasa kan dardumar, suna fuskantar juna fuskar yasmeen arufe.
Wani haďaďďen kwando aka ajiye agefensu wanda yake cike da turarurruka kala2 masu tsada da 'kamshi, abla ta su'ko tanama Nawaf magana acikin kunne da larabci, wanan yasa yasmeen bataji abinda suke faďaba, yay murmushi tareda jan kwandon gabansu.
Saida akasaka wa'ka wadda akayima ngo da amarya amna da larabci, sannan aka bama ango umarni yashiga cikin gyalen da'aka rufe fuskar yasmeen dashi.
Ya yaye ahankali ya rufa akansa, yazama su biyune aciki.
Kan yasmeen na 'kasa Nawaf ya ce, "ina fata dai al'adarmu ta 'kayatar dake, taďan ďago ta kalleshi ganin ya kafeta da idanu yasa ta maida kanta 'kasa da sauri.
Turare ďaya aka mi'ko masa yashiga fesama yasmeen, harda mugunta saida ya 'karar da turaren duka ajikinta, saboda 'karamar kwalba ce, fitinannen 'kamshin ya gauraye wajen.
Ya yaye mayafin daga fuskokinsu, gaba ďaya gurin aka saka tafi, daganan kowa yataso saiya ďauka a kwandon yazo yaďan fesa musu, saida kowa ya fesa sanan aka rufe taro da addu'a kowa ya kama gabansa.
____________________________
Yau aka ďaura auren mas'ud da Ameena, ALLAH yasanya alakairi mas'ud.
Da yamma aka tafi bababan filin kwallo na kano anan za'a buga wasan biki, wanda (KANO PILLAS SUKA SHIRYA DOMIN KARRAMA ANGO) an tsara wasanne 6angaren ango da amarya, abokansa 'yan kwallo dasukazo daga 'kasashe daban2 da 'yan kano filas, 'kuria aka yi idan ka ďauki 6angaren ango kona amarya to suzaka bugawa.
Wasankuwa ya 'kayatar dan har a labari aka nuna, antashi 8 da 5, ango 5 &amarya 8.
------------------------------------------
Da daddare aka shirya kai amare ďakinsu anan naga kuka, yasmeen kuka take kamar ranta zai fita, sai nasiha da lallashinta akeyi, hakama ameena.
Da 'kyar aka 6an6are yasmeen daga jikin umma, tanata kuka dafaďin bazatajeba itafa tafasa aueren, amma ina, tuni aka dannata amota, sai gidan ango.
An mi'ka Amin gidansu mas'ud yasmeen kuma gidan su Nawaf, a ďakin momcy.
Bayan kamar minti30 aka shiryasu zuwa wajen gagarumar dina da abokan Nawaf suka shirya, amma sun haďe harda mas'ud, ammafa wajen ya 'kayatu sosai.
Amare sunsha shiri cikin rigunan aure, yasmeen sai masifa takeyi, wai rigar arna, Nawaf yana jinta yay mata banza.
Komai ya 'kayar agurin, amma wajen bada cake Nawaf saida ya ciji hannun yasmeen, tai wata 'yar 'kara, wadda tasa muta nen gurin ihun dariya a zatonsu duk cikin soyayyane😜lol.
Sai shabiyu aka tashi, idanun yasmeen cike da barci, suka fiffito tana tangaďi, ga wani dogon takalmi data saka, tako goce zata faďi da sauri Nawaf ya tarbota ta faďo jikinsa, sai kawai ta lumshe idanu dan barci takeji.
Girgizata yayi da 'karfi, ke dallah malam tashi karki karya mini hannu, inko ba hakaba zan sakeki ki faďi 'kasa ALLAH.
yasmeen batasan yana yibama, Kausar ta ce abi! ka ďauketa kawai wlhy barci takeyi tagaji dayawa ne.
Bayaso danginsa su gane komai gameda auren, dan haka ya sa6eta kawai sai ďakin momcy, ALLAH ya taimakesa ma 'yammatan ne a 6an garen momcy, kuma babu wadda yake jin kunya acikinsu.
Ruwa ya ďauka a saman madubi da wata tasha tarage, yazuba ahannusa ya shafa afuskar yasmeen, tako kawo numfashi.
Ahankali ta buďe idanu tana kallonsa, ya ce, "ke kitashi kicire wanan rigar, sanan ki kwanta yana gama faďa yafice, da'kyar ya iya tashi tacire, ta koma ta kwanta................✍🏻

Na ce, "asuba tagari yasmeen.










©2016



💞bilyn Abdul💞
💞Mrs Abdus'salam💞
💞luv u oll my fan's💞
[1/12, 8:59 PM] mrs bilkisu: ☆☆☆☆☆☆☆
🎾 NAWAFF 🎾
☆☆☆☆☆☆☆






NA BILKISA IBRAHIM💞



Page👉🏻27 & 28

......Washe gari akayi walima, dakuma wa'azi wanda manyan malamai suka gabatar.
Masha ALLAH wanda akayi dansu sun 'karu sosai, daga 'karshe aka rufe taro da addu'a.
Kowaya kama gabansa, musamman ma abokan Nawaf dasukazo daga 'kasashe daban2, karfe 2:30pm na rana jirginsu ya ďaga, cikin 'yan katsinama wasu sun tafi mazansu da matansu, sai 'yan kaďan aka bari.
'Yan saudia ne dai sai gobe wasu zasu tafi.

8:30pm
Da daddare aka shirya yasmeen tsaf, dan za'a maida ita 6angaren Nawaf, wata 'kanwar papa tashigo tana faďin amarya tashi akaiki ďakin ki ko??.
Yasmeen ta marairaice fuska kamar zatayi kuka, ta ce, "inna dan ALLAH abarni anan, yafi daďi ga abokan hira.
Murmushi tayi, ta ce, " 'yanan idan anbarki anan ďakinki kumafa, da angoki, mukuma dakike gani nanda jibi bazakiga kowaba fa?, dan haka tashi muje kinji 'yar albarka.
Badan yasmeen tasoba ta tashi suka rakata, wooow!! Lallai an gyara 6angaren Nawaf sosai an sake masa fenti, sannan komai na 6angaren an sake, tundaga kujeru labulaye tv kayan gado, komai ansake, dama papa cayayi karsu abba suyi komai, amma duk dahaka saida umma tasayi kayan kichin masu yawa, aka kawo, gakuma wanda momcy tasaya, kichin ďin kam aii ya 'kayatu da 'kyau.
Tana kuka suka tafi suka barta bayan an kaita bedroom ďin Nawaf, wanda shi kaďaine a6angaren nasu.
Falo ne babba sai bedroom, kichin da sito, dakuma wani 'karamin ďaki agefe wanda Nawaf yacika da kayan motsa jiki, sai kuma wani ďan fili awaje wanda aka 'kawata da kujeru masu 'kyau domin hutawa, komai yayi awajen kuma komai naciki 6angare lemon green ne.
Yasmeen tana zaune a tsakkiyar gado inda su inna suka barta, kuka taketa yi, na ce, "dama aike gwanace wajen iya kuka.
Har 'karfe goma Nawaf bai shigoba ta mi'ke ta cire kayanta ta canja da marasa nauyi, gadon ta haye batareda wani tunaniba ta kwanta abinta, dan danan barci yay awon gaba da ita.
Nawaf kam yana ďakin daya koma harma ya kwanta, momcy tazo kawoma papa lifton sai taga wuta a kunne, ta ce, "oh ni modebbo akunne yabar wutar ďakinnan, tura 'kofar tayi tashiga da nufin kashe wutar, turus tayi dan ganin Nawaf bisa gado yayi ďai2 yana barci.
Kai ta girgiza ta 'karasa gaban gado tafara kiran modebbo! Modebbo!!.
Nawaf ya buďe idanu ahankali yana kallon momcy.
Ta ce, "mikakeyi anan???.
Ya ce, "momcy kamar ya??.
Hararar sa tayi, ta ce, "shine kabaro matarka ita kaďai kazo nan ka kwanta, maza katashi kafin raina ya 6aci kawuce ďakin matarka.
Baki ya buďe zaiyi magana........da sauri momcy ta ďaga masa hannu🖐🏻kaga bana son jin komai, katashi kawai ka tafi.
Bayanda zaiyi dole ya mi'ke wayoyinsa kawai ya ďauka, dan tunda rana momcy tasa Anwar yamaida masa kayansa 6angarensa, yafice yana turo baki gaba.
Momcy ta bishi da kallo tana girgiza kai.
Nawaf yashigo ya rufe ko'ina mai makon yatafi ďaki saiya kwanta saman kujera doguwa.
Can dare Nawaf yakasa barci dan bai saba kwanciya ahakaba, sai tsaki yakeyi yana juyi, ga kujerar ledace.
Ya sakko 'kasa saman kafet ya kwanta aii saiyaji tamkar ana tsira masa allurai, yatashi zaune ya rabga uban tagumi kamar wanda uwarsa ta mutu, ga barci yana cin idanunsa.
Tashi yay yanufi ďakin, ahankali ya tura 'kofar, amamakinsa saiya jita abuďe, baiyi zaton hakaba.
Yasmeen tana kwance ďai2 dan barci ya saceta, ga gajiyar biki, yanda ta kwanta saida ya ta6a zuciyar Nawaf.
Ya kauda kai daga kallonta tareda fitar da huci mai zafi daga bakinsa, asanyaye ya zauna saman kujerar dake ďaki, yakai minti biyar ahaka, sannan ya tashi yanufi bayi, shawa🚿 yasakarma kansa, na ce, "ai dama ka saba.
Yadaďe ruwa yana ji'kashi, wanda 'karar ruwan tasa yasmeen farkawa atsorace, tana nan zaune yafito jikinsa ďaure da farin tawul, hannunsa ri'ke da 'karami yana tsane sumar kansa.
Kallo ďaya tai masa ta kauda kai, shima haka, durowar gefen gadon ya buďe yaďakko wasu magunguna ya watsa abaki ya kora ruwa, gefen gadon ya zauna yana faďin ya salam!!.
Ahankali yasmeen ta sauka daga gadon ta koma saman kujera ta kwanta.
Yakai minti5 azaune kafin yatashi yahau shirin barci.
Yabi yasmeen dake kwance saman kujera da kallo, ahankali yafurta kin taimaki kanki yarinya, gadonsa ya haye yay kwanciyarsa harda jan bargo.
Yasmeen tana kallonsa taďan ta6e baki, itama ta maida kanta ta kwanta, babu daďewa barci yay gaba da ita.

WASHE GARI
da safe yasmeen ta tashi ta gyara ďakin tsaf ta wake bayi sannan tayi wanka, dan Nawaf tundaga sallar asuba bai dawo ďakin ba, yana ďakin motsa jiki.
Gayu ta ďauka cikin atamfa siket da riga tayi 'kyau sosai, bawata kwalliya tayiba fauda kawai tashafa.
Ta le'ko falo azatonta Nawaf yana nan, saitaga babu kowa ta fito ta lalle'ka ko ina, komai ya burge ta, tagama zagayawa tazo tashare falon duk da bawani datti yayiba, amma taďan 'kara gyarawa.
Har waje ta fito ta gyara tsaf, alokacin Nawaf yafito daga ďakin motsa jiki yashiga bedroom, wanka kawai yashiga yadaďe sosai kafin yafito, bayan fitowarsa ya shirya.
Yasmeen tana zaune afalo tayi shiru tana tunani.
'Karar takunsa yasata juyyo da sauri, Nawaf tagani cikin shadda orange color, ďinkin zamani yayi masa 'kau sosai, amma fuskarsa babu walwala.
Ta ďauke kanta daga kallonsa, dan ganin gurinta ya nufo.
Cikin takun 'kasaita ya 'karaso gareta dan iña ganin yau sarautarce ta motsa, ya ce, "k ki tashi muje mu gaida mutane.
Banza tayi masa.
Hannu yasa ya fincikota "k 'karamar mara kunya har kin isa ina miki magana kimin banza.
Ta ce, "anyi maka ka ďauki mataki mana, ta murguďa masa baki😏.
Shi dariyama tabashi, amma saiya gimtse, ya ce, "zanyi maganinki ki bani lokaci.
Tayi wata dariyar rainin hankali, aii ba saina baka lokaciba yanxu yadace kaďauki mataki.
Ya zaro wayarsa dake wringing momcy ce, cikin girmamawa ya ce, "momcy ina kwana??.
Daga can ta ce, "lafiya lao abbuna kun tashi lafiya.
Ya ce, "lafiya lao my momcy, ta ce, "ina ďiyar tawa bata mugaisa.
Ya ce, "momcy ai yanzu zamuzo gaisheku ma.
A'a modebbo karka wahalarmin da ďiya kabarta ta huta.
Haba dai momcy yazamu zauna bamu gaida su hajjaba, bawani wahalar da ita daza ayi.
To shikenan bata mu gaisa.
To, juyowa yayi domin yabata wayar, saiyaga bata nan, bin bayanta yayi zuwa bedroom, batareda yayi mata maganaba ya manna mata wayar kawai a kunne.
Tabuďe baki zatayi magana saitaji maganar momcy tana faďin ďiyata kin tashi lafiya??.
Cikin girmamawa ta zamo daga kujera ta ce, "momy ina kwana??, lafiya lao ďiyata ya ba'kunta.
Ta ce, "lafiya lao.
Masha ALLAH momcy ta faďa, ta ďora dafa ďin babu wata matsala dai ko??.
Eh babu komai momy.
To shikenan gasu talatu nan zasuzo suďan gyara miki inda aka 6ata kinji.
Lah momy ai bama sai sunzoba nariga na gyara.
Kai ďiyata damme??, daga yau karki 'kara wahalar da kanki akan aiki, akwai masu yi kinji.
Ta ce, "to momy ngd ALLAH ya'kara girma.
Momcy ta ce, "amin ALLAH yay muku albarka.
Ta ce, "amin.
Nawaf yaji daďin yanda yasmeen ta girmama mahaifiyarsa, amma sai ya kanne dan yasan matar tasa 'yar haya'kice.
jallabiya ya ďakko ya cilla mata, gashi nan kisaka mu tafi.
Kai taďago daniyar yimasa rashin kunya, amma saitaga ya tsare gida kamar bai ta6a dariyaba, bata ta6a jin shakkar yimasa rashin kunyaba irin yau, ďauka tayi tana zum6ura baki tanufi bayi ta canja, tayi mata matu'kar 'kyau dan rigar ta haďu, shi kansa saida ya yaba amma bai nuna mataba, ya ce, "muje, yafaďa yana nuna hanya👉🏻.
Batayi musuba suka tafi, 6angaren papa suka fara zuwa yayi farincikin ganinsu, yasmeen ta zube tana kwasar gaisuwa wajen surikin nata, shima Nawaf yakai tashi gaisuwar, papa yay musu nasiha mai shiga jiki.
Daga nan wajen momcy sukaje suka gaisheta, itamadai nasihar tayi musu.
Sai 6angaren dasu hajja suke, cikin farinciki hajja ta rungume yasmeen itako sai kunya takeji.
Nawaf kuwa tsakkiyar kakanninsa yaje ya zauna yana gaishesu cikin harshen larabci, suka shiga tambayarsa ya amarya.
Ya ce, "gata nan lafiya lau.
Taďan yi 'ko'kari wajen gaishesu da larabci, saboda islamiyya datake zuwa, daga nan sai Nawaf yakoma yimusu tafinta, idan sunyi magana da larabci ya fassara mata, idan tayi da hausa ya fassara musu, Nawaf sai dariya yake mata wai bata iyalarabci ba.
Momcy ta ce, "rabu dashi yasmeen kema zaki iya indai larabcine.
Yasmeen ta ce, "momy sainama fishi iyawa insha ALLAHU.
Nawaf ya harareta wazakifi iyawar??,
Ta ce, "kaimana.
Haka dai sukaita hirarasu, saida hajja ta ce, "su tashi suje 6angarensu.
Tun ahanya aka fara faďa, na ce, "kai ALLAH ya shirya waďannan gays ďin.
Talatu da ladidi suka shigo da kayan break suka jere a dinning, sanan suka tafi.
Nawaf yatashi yanufi dinning batareda yabi takan yasmeen ba, abincinsa yaci ya 'koshi kunsandai 'yan kwallo sun iya ci😜.
Yasmeen tana zaune a falo ko kallo bai ishetaba, saida yagama yafita sanan taje taci nata, ta gyara wajen.
Falo tadawo ta ďauki wayarta tahau chatting dan tarage kaďaici, dama kallo bai cika damun yasmeen ba.

``````````````````````````````````
Sai bayan sallar la'asar Nawaf yashigo gidan lokacin tasake wanka cikin sket da riga na shadda tayi 'kyau, tana bedroom bayan ta idar da sallar la'asar, zaune ta ke kawai tunani fal zuciyarta.
'Karar buďe 'kofa yasata juyowa da sauri tana kallonsa, kallo ďaya yay mata ya ďauke kai, itama kanta ta maida gefe, tana ganin yafara cire kaya tatashi ta fice, yarakata da harara.
Tana nan zaune afalo saiga 'yammatan danginsa na saudia, suka zauna ana hira harda ummu habeba, yau tasaki jiki anayin hirar da'ita.
Suna nan zaune Nawaf yafito sanye da 'kananun kaya sai zabga 'kamshi yakeki, kan hannun kujerar da yasmeen take zaune ya zauna, suka shiga gaidashi, daga nan aka ďora da hira, ummu habeba sai kallonsa takeyi, ita dai tana 'kaunar Nawaf, amma gashi ya zagaye yayi aurensa ya barta, kwata2 ta kula ma shi nunawa yake baisan tana sonshiba.
Sai gab da magriba suka tafi 6angaren momcy.
Shikuma Nawaf yatafi sallahr magriba masallaci.

____________________________
Yau jirgin muta nen sudia ya ďaga, hajja kawai aka bari zatayi ďan kwana biyu sanan ta tafi, da'kyar tayarda ta zauna.
Yau gidan shiru babu kowa saisu kaďai.
Nawaf yadawo daga motsa jiki ya zube afalo saman doguwar kujera yana faďin wash ALLAH na nagaji yawa yau.
Yasmeen tafito hannunta ďauke da kofin kunun gyaďa dan tana sonsa sosai, tundaga lokacin da Nawaf ya ce, "bayasan 'yan aiki awajensu idan bazatayiba tabarshi.
Momcy ta ce, "bata yardaba yasmeen ďin nawa take daza a sakar mata aiki, dayaga momcy ta dage saiya ce, "to saidai ita ta rin'ka musu girki, dan bazaici girkin 'yan aikiba.
Momcy ta ce, "wanan mai sau'kine, yasmeen kiringa yimuku girki tunda ku biyune kafin yatafi, dan tuni mijinki baya cin abincin 'yan aiki.
Yasmeen ta ce, "to momy hakanma yayi, nima nafiso nayi da kaina.
Yabita da kallo danganin shigar dake jikinta, wandone iya guywa da 'karamar riga mara nauyi, rigar ta fallasa asirin jikinta sosai, kanta yasha gyara sai wal'kiya yakeyi.
Tasan babu wanda zai shigo musu shiyyasa tayi wannan shigar, dan Tun agida yasmeen tanaso shigar 'kananun kaya damma wataran umma tana hanata ne.
Ta wuce kamar bata ganshiba.
Ya ce, "k zonan!, banza taiyi masa tunda ba "k aka raďa mataba agidansu, bedroom tashige abinta.
Nawaf ya haďiye wani mugun yawu jikake 'kuttttt, gaba ďaya ta rikita masa lissafi ya rintse ido ya furzar da huci mai zafi, ya ce, "wai sai yaushe za'a kai 'karshene??, wata zuciyar sa ta ce, "randa ka shirya kwatar ha'k'kinka dan kasan indai dan itace ayita zama ahaka.
Yay wani murmushin mugunta, afili ya ce, "aii ko ankusa zuwa 'karshen, ya mi'ke yanufi bedroom domin yin wanka.
Koda ya shiga ďakin baibi takantaba yashige wanka abinsa, ita kuma tadawo falo tana faďin ďan rainin wayo ai wlhy yanzu na daina zama kana raina mini hankali, idan zaka shekara kiran "k! Bazan amsaba tunda bashi iyayena suka raďa mini ba.
Tana nan zaune yafito shima cikin 'kananun kaya, kusada ita ya zauna, bata ko kalli inda yakeba taci gaba da shan kununta.
Gashin kanta yaja aiko ta kwala 'kara,

Please Login or Register in order to submit comment