Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya

Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us

Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT

This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels

*KARAMCI WRITERS ASSOCIATION*
_[karamci tushen mu'amula tagari]_

https://www.facebook.com/110308337320465?referrer=whatsapp

https://www.youtube.com/channel/UC1cigRjL8UfjxSLNtt-x4MQ

💖💘💘

*SO KO HAUKA?......*

💘💘💖


(Daga Marubuciyar ISHARA.)

Ayshatour Abdul-falalu.

Mommy n Yusif.

(Labarin Meenat ƴar gata.da Shatun (ƙauye labari mai cike da RIKITA-RIKITAR ZAMANI ZALLAR SOYAYYA TAUSAYI AL-AJABI DA KUMA MAƘIRCI.




book one.

page-1-5.







📲______________CIKIn gurɓatacciyar hausarsa da bata fita yake duban meenat 'yar gata,

a yayin da wani mugun sonta ke fisgarsa.

''Meenat idan na rasa ki bansan yadda zanyi ba da rayuwata ina sonki Meenat.

''Meenat 'yar gata ta ɗago cikin murmushi tana duban josphen,

Josphen cikin fara'a yace, ''Ya kamata kizo muje kiga Mommyna kullum i yi mata zancen ki.


''Wai josphen Ina Daddy ɗinka? sam ba ka yi min maganarsa, kullum sai maganar Mommyn ka.


Annurin fuskar josphen gaba ɗaya ya gushe
ya gaza furta uffan.
Domin kuwa idan akwai abinda Dadyn nasa ya tsana bai wuce musulmi ba domin kuwa ba zai manta da lokacin da yayansa moses ya so musuluunta ba, a gabansa ya
saka bindiga ya harbeshi har lahira.

Domin kuwa shi ɗin ya kasance pasto babban malamin chochi.

Meenat ƴar gata tace, ''Yaya naga ranka ya ɓaci daga yi maka tambaya?
Koko dai maganata ta ɓata maka rai?


ƙago murmushi yai a ƙagauce yace,

''Meenat Golden girl kenan '' Kina yawan yimin questions akan Daddy na ya kasance ɗan kasuwa ne, Business ba ya barinsa yana da Company ninnika a ƙasashen waje, kuma yana yawan xiyartarsu.
shiyasa da wuya ki ganshi Nigeria.

Meenat ta gyaɗa kai cikin gamsuwa domin kuwa sam batayi wa Josphen musu komi ya fad'a mata ba zatayi gardama ba ta ba shi Amana sosai a rayuwa.

A tare suka miƙe cikin motarsa parado suka jera suna tafiya duk wanda ya kallesu yasan suna cikin shauƙin so.

Shi ke tuƙa motar yayinda Meenat ƴar gata ke gefen hagunsa.

Hannu yasa ya shafota yayinda hannu ɗaya ke riƙe da sitiyari.

Wani irin ƴarrr!!! taji a jikinta sai'ilin da ya taɓata a yayinda shed'an ke kitsa mata ina ma ta kasance da shi a haka?

daƙyar tayi ƙoƙarin sai sai ta nutsuwarta idonta yai narai-narai uwa mai shirin yin kuka ta kamo hannunsa laushin da taji a jikin hannun nasa ya sa ta lumshe ido saboda wani shooking da taji na wucin gadi
tabbas tana matuƙar ƙaunar Josphen.

Josphen My love ta kirasa cikin wata murya
mai daɗi tamkar busar sarewa,

''Addinina na musulunci me tsarki yayi hani da aikata hakan a yayinda kukuma naku addinin hakan ba wani abu bane,

''Kada ka kuma taɓa jikina My love Josphen har sai munyi aure domin kuwa niɗin ba muharramarka ba ce,

Josphen ya ɗaure fuska kana yace, ''Golden girl kenan addinin nan naku ya cika tsauri da kuma dokoki iri-iri,

Murmushi tayi kafin tace, tana lumshe ido, ''Josphen kenan addinin musulunci kenan addini mai daɗi, me tsafta,

''Josphen ina maka sha'awar shiga addinina na musulunci.

Waro jajayen idonsa yai da sukai mankas da giya ya ɗaga hannu da nufin sharara mata mari, amma da ya tuna cewar masoyiyarsa ce abar ƙaunarsa sai ya ajiye hannunsa ƙasa ya juyo yana dubanta kafin yace,

''IMposibble'' Golden giril kada na kuma jin magana makamciyar wannan a bakinki kinji ko?

"Wato kina san Daddy ya kashe ni?
Kamar yadda ya kashe yaya na moses?

Shiru tayi na ɗan taƙin lokaci daga bisani tace, ''Kace Daddynka tsaurin ra'ayi ne da shi kamar Daddyna?

''Shi yasa a kullum nake fargabar tunkararsa
da maganar aurenmu domin kuwa ni kaɗai nasan waye Daddyna.
''Bansan ta yaya zan iya sanar mishi cewar ''kaine wanda xan aura ba.


Josphen ya juyo kana ya ce, kenan ke har kina fargaba akan soyayyar mu?

Ki sani na rantse da (yesu)akan ki Daddyna
da ya kasance tsohon soja bana ja akan yaji
Alaqar mu xan iya rabuwa da kowa akan ki meenat, Domin kuwa a kan ki na gwammace na mutu wallahi''



A dai dai nan suka tunkari katafaren gidan da( ni kaina Ayshatour nai ta rarraba ido ina tambayar kaina anya ba garin neman gulma
da tsuguddi na kawo kaina gidan fillai kaiba?(dariya))

Katafaren gida mai kimanin get shidda wanda kowanne Soja riqe da zabgegiyar bindiga yana jiran ko ta kwana.

Tun ina ƙirga motocin da ke harabar wani special parking space,Kai har na gaji nayi shiru na dai tabbatar dukiya na kuka a gidan su josphen.

Duk inda Josphen ya gifta sojoji ne fululu ke sara mishi.


A cikin ƙayataccin kujerun da suka yi ma falon ƙawanya, ƴar gajeriyar bayerabiyar, baƙa, amma ba wuluƙ ba, tana da hanci dai-dai misali, zaune take a cikin ƙyataccen falon hannunta riƙe da remot control, a hankali tana kurɓar lemu cikin wani kofin tangaran mai tsananin ƙyawo.

Kanta yasha kitson Attarchemen gana wiving manya.

kanta a buɗe yake wanda kallo ɗaya zakayi mata kasan ba wani gashin kirki ne da ita ba.

Hey! Mommyn!.

Da gudu ta saki remote ɗin ta ruga tare da rungumshe.

'My son! Josphen ta fad'a tare da ware hannayenta ya fad'a

Meenat 'yar gata dake tsaye ta zuba musu ido tana dubansu sunyi matuƙar bata sha'awa matuƙa.

Sai a sannan ta lura da meenat ta ɗago ta zuba wa menat ido.

Josphen yai mata signa da ido alamar cewa
Mum sirikar ki fa ce.

Sai kuwa ta washe baki tare da Jawo meenat ta haɗa da josohen ɗin ta rungumesu.

"Oh Sorry my daughter What is your name?

Aminatu Kabir (k'araye) d'an takarar deputy Governor.

"Wow "Nice Name.


mai aikin su janet, ta ƙwallawa kira ta kawo abinci, tundaga nau'in na hausawa har na yare daban -daban babu wanda meenat bata gani ba.

Da baki josphen ya din ga bata ita kuwa duk sai nonnekewa take tana jin kunyar mommyn.

ita tana ganin a gaban Momynsa ne fa amma ga mamakinta sai taga Mommyn sam ba tasu take ba bata damu dasu ba ma .

A haka ya dinga bata abincin tun tana noƙewa har dai ta gaji ta safko ta saki jikinta.

Kammala cin a bincin keda wuya

Madan Gloria ta kira Josphen a keɓantattcen wuri,

''Josphen kana ganin soyayyarka da ƴar
musulmai abu ne mai sauƙi?
Ka fasan irin mummunar tsanar da Daddynka yai wa musulmi a gabanka ya kashe min babban yarona mousse.

Just think about it.

"Shin kana San hakan ya kasance da Kai?

Nima fa basan musulmai nake ba.
Naga ka rud'e a kan babyn bana san ka zautu shi yasanya "Wai mema babyn nan ta ke da shi da 'Yar yayata grass bata da shi ne?

Idan sha'awar ta kake me zai hana ka zo ka biya buk'atar ka da ita in yaso ko mi ya biyo baya muna da kud'i.

Zaro ido yayi,
" Momy 'yar deputy Governor ce fa!

Alh.kabir ƙaraye.

Mom tace ka na ganin Dadyn ka ba zai iya ja da su ba kar ka manta babban pesto ne bayan haka shugaban sojoji ne.


Josphen ya sauke ta gumen da ya rafsa da hannuwa bibbu kana yace,

''Look Momy ba za ki ga ne ba ne ina wa Meenat son da ba kowacce mace na ke wa
irninsa ba domin kuwa ita ɗin jinin jikina ce.


''Bazan iya aikata zina da Meenat ba Momy duk da cewa mu addininmu ba wani a bin kunya bane saɓanin nasu addinin da yai hani da aikata hakan.


Ta shafa kansa ta na cewa, ''Josphen duk cikin ƴaƴa na fi sonka ba nasan rabuwa da kai My son.


Meenat suka tarar tana shan Coffe,
kamo hannunta Mommy ta kamo hannun josphen tareda Meenat ta dunƙule waje ɗaya,

''Ina so ku riƙe amanar juna domin kuwa gagarummin yaƙi ke shirin tunkaro mu,

We have got an opportunity with a lot of difficulty .


Josphen yace, ''Wallahi Mom komai Daddy zai min bazan iya rabuwa da meenat ba domin kuwa ita ce abar ƙaunata.

Mommy tace, ''Da yardar (yesu )
babu abinda zai faru ma,

Josphen ya sargayo hannunsa izuwa ga wuyan Meenat ya na faɗa mata ƙyawawan
kalamai.



............................


"Rijiff!!! "Dummm!!!!
Suka ji faɗowarsa abinka da ba musulmi ba. ba sallama ba komai, Idanuwa jawur kamar gauta, fuska ɗaɗaɗaure kamar kashin shanu baƙine wuluk mummuna na ƙarshe ɗamɓarere, me katon kai mai mazaunai uwa wata mace,

Da gudu Mommy taje a domin taryarsa,

Tsawa ya daka mata da ƙarfi idonsa ƙur akan Meenat 'yar gata,

"Me ya kawo min ɗiyan musulmi a cikin gida?

Ya fad'a yana zare jajayen idonsa.


Meenat ta karewa zabgegiyar bindiyarsa kallo ga wasu takalma da zasu Kai tsawo. Yaro d'an shekara 2.



Ni kai na da gudu na sheqa k'auyen kereriya domin saduwa da shatun k'auye.











Ku CI gada da kasance wa tare da "Ayshat Mommyn Yusif a domin jin jumurd'ad'd'en Al_amarin da zai nishad'antar da ku a cikin wanna zazzafan labari me cike da sark'ak'iya game da al_ajabi da Kuma tausayi.



So ko hauka fans'n gp.



Dokokin group .

Idan kinsan ba Zaki karanta ba karki shigo min group.
Bana San tallah.
Bana San Link kowanne iri.

Idan kinsan ba soyayyar book Dina zata shigo dake ba karki shigo!!!!!;;;;

Ya zama Dole yin comments da sharhi akan
Duk book din da za'a turo.

Din girman Allah kar namijin da ya shigo min.

Da zarar kin shiga kiyi vioce don na tantance mace ce ko namiji.

Idan kinsan book d'ina bai miki ba to ki sha zaman ki kar ki shigo.
Zaku samu littafan marubuta da dama.

Ya zama dole yin coment da sharhi rashin yin hakan na nufin zaju ji ki a waje

Ga link nan a k'@sa
👇👇👇

Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/IksQIIqESXZHKQ6RADR5To



*KARAMCI WRITERS ASSOCIATION*
_[karamci tushen mu'amula tagari]_

https://www.facebook.com/110308337320465?referrer=whatsapp

https://www.youtube.com/channel/UC1cigRjL8UfjxSLNtt-x4MQ

💖💘💘

*SO KO HAUKA?......*

💘💘💖


(Daga Marubuciyar ISHARA.)

Ayshatour Abdul-falalu.

Mommy n Yusif.

(Labarin Meenat ƴar gata.da Shatun (ƙauye labari mai cike da RIKITA-RIKITAR ZAMANI ZALLAR SOYAYYA TAUSAYI AL-AJABI DA KUMA MAƘIRCI.













Page 6-10.




Dukkaninsu sai da suka firgita musamman ma meenat da ƙyar take jira ta zura zawo.
Madan Gloria taje da nufin taryarsa tsawa ya daka mata da ƙarfi, ya na nuna meenat da gundumemen yatsan sa manuni .

''Me ya kawo min 'yar MUSULMAI a gida?.

Meenat ta ida rikirkicewa,maganar Joseph ta faɗo aranta inda yake cewa, Dad ɗina baya ƙaunar musulmi saboda tsanar da yaiwa musulmi saboda tsanar da yai wa musulmi yaya na Moses da ya zo musulunta yasa bakin bindiga ya harbeshi.

Yau ita ta shiga ukunta gata gashi a gida ɗaya mema ya kawo ta gidansa.?
Soyayyar ɗansa Josphen xuciyarta ta tunasar da ita.


To nima Mom Yusif yaU tsugudidi ya kawo ni gidan Soja Wayyo ni Allah,
da gudu na arce wani tsurkukin ƙauye dake cikin ƙaramar hukumar charanchi donjin wainar da ake toyawa.





ƘAUYEN ƘERERIYA.


Shatu tsaye cikin rana tana ta faman surfa geron da zata daka fura, tatafi tallah,
ƙaɗan-kaɗan kuwa sai ta tsaya ta dinga kartar dunƙulallen gashin kanta wanda ƙwar-kwata ta cinye rabi.

Idan tana ƙarta gashin har miyau ke dalala saboda daɗin da takeji.
Wani lokaci kuwa har jini ke zubowa amma bata damu ba.

bulala taji antsula mata, da sauri tayi firgigit ta dawo hayyacinta tana zabure -zabure.
Cikin masifa Inna Hansai ke faɗar,

''Ke dai anyi asararriya tsintacciyar mage wacce bata mage, Duk ta yadda akayi keɗinnan shegiya ce wacce uwarta ta guji abin kunya ta jefar.

Shatu bata ce uffan ba ta ci gaba da daka tana sharar ƙwallah,

Mal. Bello yai sallama ya shigo.
riƙe ya ke da ɗan ƙullin rakensa tsara bar kasuwa,


Da gudu Shatu ta miƙe tare da taryo shi ta kai hannu da nufin ƙarɓar ƙullin Inna Hansai ta ƙwaɓe ,

''To tsohuwar kilaki, ko da yake barewa bazatayi gudu ba ɗanta yai rarrafe duk yadda akayu i ''Uwarki tsohuwar karuwa ce shiya sanya ke ma kin tsotsi mugun nono. . . . . .
Hannu yasa ya dakatar da ita ''Ya isa Hansai
''Ke yanxu kina matsayin matata ace na dawo ba sannu da zuwa wacce ta kulani kin hantare ta, ga naki ƴaƴan a zaune ba wanda ya iya furta min sannu kin ƙyauta kuwa,

Inna hansai ta murguɗa baki tace, ''Kai fa Malan muddin za'a taɓa wannan tsintaccitar wacce babu ma wanda yasan ko da asalinta, to an taɓoka ''To wai mema zai hana ka aure ta?

Salati Malan Bello ya saki ba tare da da ya kuma furta uffan ba ita kam shatu kuka ta saki da ƙarfi.

Sam abin bai dame Inna Hansai ba illah ƙullin raken da ta jawo ta sami ƙafcece ta dinga kafta ma bakinta.
Tana sha tana sababi ''kai ma Mal. Ace kaje kasuwa ko ɗan tsire ka siyo mana A'a ka sami wasu ƙafta-kafta rake ka siyo. . . . . . . . . . .
Mal. Bello bai ce Uffan ba illah adduar shiriya da yai mata.


Misalin ƙarfe uku ta kammala dakan furar.
Gaban Inna Hansai ta isa ta durƙusa tana cewa, Inna na kammala daka furar, ''Don Allah ki barni naje na watsa ruwa ko da kuwa ba sabuli na ɗan ji sanyi.

''Ba zaki yi shi va munafuka sai dai ki mutu da ƙazanta wallahi.


Shatu tayi jim kafin tace, "Innah Wallahi a yanxu an dai na siyen furata saboda bana wanka.

Marin da Innah Hansai ta kifa mata yasa ta yin shiru batare da ta shirya ba inna,

" Don Ubank baki san a yanxu juye a keyi ba a shagon samari? Duk wanda ya kira ki ki dinga tafiya kina rangwad'a kina kada gabank sai ki ga mutum d'aya ma ya siya ya baki kud'inki.

Innalillahi wa inna ilaihirraji'una.
"Hansai kiji tsoron Allah ke yanxu idan yarki ce zaki so a yi mata haka? Ki sani tun a duniya sai kinga ISHARA.

Ya juyo ga shatu wacce ke durkushe,

Shatu ki rik'e mutumcin ki duk runtsi kadda ki zubar da mutumci ki na 'ya mace kinji Shatuna?

" To Baba insha Allah zan kiyaye hakan.
Shatu ta mik'e tare da d'auko xungureriyar hijab d'in ta wacce ta dafe, tare da sharb'a-sharb'an takalman ta da duk sun sha k'ullin leda ta nufi kasuwa , duk wanda yai ma shatu kallo ɗaya baya fatan kuma sake kallonta abokan tafiyar ta gaba ɗaya sun siyar da furarsu saura ita kaɗai ta rage.

Zulai ta dubeta kana tace, ''Wai ke shatu don Allah me yasa bakya tsafta?
Da (kwaran-kwatsa,) idan zaki juri zowa haka to ko kare ba zai sinsina furarki ba
baki san yanxu lokaci ya chanxa ba tsaftar mai tallah tsaftar abin siyarwa muddin kina so ki samu ciniki ki dinga tsafta.

Shatu ta matso ƙwallar fuskar ta kana tace,

''Wallahi Zulai babu yadda banyi ba da Innah
ta barni ko da banyi wanka ba na sake sabon suttura ta hanani , Taci gaba da shisshekar kuka.

Raliya tace, ''Ni na rasa wannan kalar zalunci irin na Innah Hansai Hanya ita ta haifeki kuwa?

tayi tayi ɗan jim kafin tace, ''Tambayar da na daɗe ina yiwa kaina kenan duk da cewa da bakinta take cemin TSINTACCIYAR MAGE.

Tausayinta ya cika zukatansu Raliya ta Amshi furarta suka juyo a kwanonunsu da nufin siyar mata saime?

mintina 5 ba'ayi ba sai ga ruwa shaaaaaaaaa!



ku ci gaba da Kasancewa da ni domin jin cigaban labarin,

idan kin karanta kiyi Comments.





















*KARAMCI WRITERS ASSOCIATION*
_[karamci tushen mu'amula tagari]_

https://www.facebook.com/110308337320465?referrer=whatsapp

https://www.youtube.com/channel/UC1cigRjL8UfjxSLNtt-x4MQ

💖💘💘

*SO KO HAUKA?......*

💘💘💖


(Daga Marubuciyar ISHARA.)

Ayshatour Abdul-falalu.

Mommy n Yusif.

(Labarin Meenat ƴar gata.da Shatun (ƙauye labari mai cike da RIKITA-RIKITAR ZAMANI ZALLAR SOYAYYA TAUSAYI AL-AJABI DA KUMA MAƘIRCI.





page 11-15


Wajen Magriba aka ɗauke ruwan Shatu ko sisi bata yi ba.
Hankalin Shatu yai mummunan tashi jin yadda Raliya tace, ''Kiyi haƙuri Shatu munyi niyyar siyar miki da furarki Amma kinga yadda Allah yai nasa ikon.
́

''Ba komai Raliya ''Nagode da taimako na da kukayi niyyar yi''

su Raliya sukayi mata karo-karo ta samu kuɗin mashin ɗin dawowa gida.

A ƙofar gida ta iske Abu ɗaya daga cikin ƴaƴan Inna Hansai rungume a jikin saurayinta.

Cikin ran Shatu tace, Tun ba'aje ko ina ba gashi abinda Inna Hansai ke jifana dashi kan ƴaƴanta,

Abu tayi Wuff! tana faɗar, ''Wacce shigeya ce?

Au! Tsintacciyar mage karuwar gida sai yanxu a ka dawo yawon ta zubar d'in?
cikin dare sai da aka gama iskancin.

Abu tai ta maganganu barkatai har sai da saurayin nata ya saka baki sannan ta bar shatu ta tafi.

Inna Hansai tsaye, tsakar gida koda isowar shatu ta miƙo mata hannu tana cewa, damƙar kuɗin tallah.

Shatu tace, ''Wallahi Inna ba ai ciniki ba. . . . . . . . . . Bata rufe baki ba inna Hansai ta dinga tsula mata bulalar bedi wacce ke riƙe a hannunta Asabe da Jummala suka ƙyal'ƙyale da dariya,

Inna Hansai ta dage iya ƙarfinta tana ta labtar Shatu hakan yaba makota damar fitowa abinka da ƙauye.

Bakin Innah Hansai na kumfa take cewa ''Wallahi bazan ɗau asara ba sai kin biyani kuɗina
ko yawan iskancin da kika saba zski kije nidai kuɗina na sani.

Da Zulai da Raliya suka faɗo ɗakin sukace dakata Inna Wallahi da kwaran-kwatsa ba laihin shatu bane ke ce ke hanata wanka shiyasa ba'a siyen furarta.

Inna Hansai ta juyo ga Zulai a ƙufule, ''To zabaya faɗi bala tambayeki ba. Shedar zur ko?
ɓace man da gani.

Zulai ta ƙwalla da gudu daga nesa tace HANsai aji tsoron Allah a daina cutar da Shatu.
Da gudu tabi Zulai tana sababi.

Mal. Bello yace dakata Hansai furar ta nawa ce?

ɗari uku da hamsin ta faɗa bakinta na ƙyarma.

Ya zaro ɗari biyar idonta idon kuɗin sai cewa tayi ta ɗari biyar ce.

gyaɗa kai yai ya wuce ya barta tsaye.
Raliya ta leko ta katanga tace , Babansu Shatu 'wallahi furar ɗari biyu da hamsince

da gudu ta biyo su suka ruga suna ƙyal-ƙyatar dariya.


****************


da yake yanayin na zafi ne yau. Mal. Bello kullum shike koyawa yara karatu. To Inna Hansai sai ta dinga tura yaranta zance a ganinta hakan shi yafi saboda ana zowa da kifi ko awara.

Shatu kaɗai ke zaune saman buhun.
Shatu mai nacin karatu amma ayau sai Mal. Bello yaga ta karkace tanata kuka .

Haƙiƙa Aishatu nasan kina cikin matsala ki sani ita rayuwa duƙƙaninta kalubale ne ke cikinta , dukkanin wanda kika ga yayi nasara a rayuwa to sai da yai haƙuri.

Sanar min meke damunki?
Ince dai matsalar Hansai ba bakon abu bane wajenki. Domin kuwa Wuya bata kisa!


tasa gefen zaninta ta share ƙwallah kana tace baba kalaman Inna a gareni sun munana matuƙa ada bansan me ƙalmar 'yar
tsintuwa ke nufi ba sai yanxu.
Anya ita ta haifeni mesa abinda take min batayi wa sauran 'yan uwana?
Meyasa take dukana bata dukan sauran yan uwana?__________________



KATSINAN DIKKO.

maganar josphen ta faɗowa Meena arai inda yake cewa Daddyna baya san musulmi saboda tsanar da yai wa musulmi da yayana Moses yazo musulunta yasa bindiga ya harbeshi.

General Eberi ya juyo ya dubi Meenat waccece wannan?
Me ya kawo 'yar musulmai a gidana?


Gaban Mommy ya fad'i
Ta ɗaure tace oh my husban friend ɗin Josphe ce.

What?
Meye hadinsa da 'yar musulmai har suka zama friend?

''Oh my God! Husband ka cika qaution
"Wai fa addinimu ta ji ya bata sha'awa shine take so ta shiga.


Da sauri ya juyo yana duban Meenat , wacce gabanta ya sake bada daram.
Sai kuma kuma taji ya ƙyal-ƙyale da wata mummunar dariya da ita kanta abin ya bata mamaki kallo ɗaya zakayi masa kasan bai saba da dariya domin madadin tayi mishi ƙyau sai ta daɗa masa munin fuskarsa.

Bata anƙara ba taji yazo daf da ita ya rungumeta yana wani kalar yare da ta kasa tantance na meye yarrr taji ita ba abun ta ƙwace ta yi ficewarta ba.

Shigewa yai bayan ya saki Meenat ba tare da yace wa kowa uffan ba.

Mum tayi wa Josphen signa da ido alamar su fece.

Wani katafaren Super market suka isa, inda ake siyar da chaculate kala-daban daban.

Fitowar su kenan hannunsa sargaye dana Meenat yana bata kiss ta ko ina, A kuma dai-dai wannan lokacin Meenat ta ɗaga ido sukayi ido huɗu da kyakkyawan saurayin dogo kyakkyawa mai cikar kamala,

zabura tayi na ganinsa a wann an lokacin amma don ta daɗa ƙular dashi sai ta daɗa ƙamƙame Josphen a jikinta aikam, ta ƙular dashi ɗin kuwa matuƙa kishi ƙarara kamar wani zaki haka ya fusata.

Amma sai ya danne kishin yazo gaf da ita ya tsaya tare da cewa ''Meenat!
Cikin murya kalar tausayi

Harara ta ballaƙa masa tare da sake ƙanƙame Josphen sukayi gaba

Oh my God Hafeez ya faɗa tare da daƙar sitiyarin da ƙarfi, Allah sarki soyayya.


***********
tsuke. take cikin cikin jar rigar t. Shet wandon ya matseta matuƙar gaske tayi kyau sosai abinta.
Ƙafar ta wacce tasha zanen jan lallai duk da cewa batayi make up ba amma tayi matuƙar yin kyau sosai.

A tsarin ƙwalliyar tata bata buƙatar mayafi a haka ta fito falo.
Mommy tace "Wow my daughter wanna gayu haka kamar ba yar nigeria ba. Ina zuwa haka, ?

Mommy zanje Shan ice cream ne.
Amma da security Zaki fita ko?
Kinga zab'e na dad,a kusantowa

No mom gaskiya bazan fita da security ba Ni kadai zani fita bazan jima ba fa.
Ta fad'a tare da shagwaggwabe murya.

To kadda ki jima kinji daughter.

"Thanks Mom.

A chance inda sukayi mahad'@ da Josphe ta k'arasa..

Tsaye Meenat tayi tana dubansa tana murmushi na ganin irin kyawon da yayi matuka.

Rungumota yayi yana Bata kiss kamar yadda suka Saba a
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4

Please Login or Register in order to submit comment