Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

cikin tsatsarrni da ido sannan ta maida dubanta gun Abba " Alaji ka fahimtar dani don girman Allah bansan inda zancenka ya dosa ba wallahi me ya faru don Allah?", Ya ce "karki raina min hankali ana haWa baki da ke ana munafuntata shi ne zaki wayance?",
Ta ce "wallahi Alaji bansan ya akayi ba bansan me yake faruwa ba ka yarda dani", ya ce "to gaki ga ta nan ta faWa miki", Yaya Auwal ya ce "Mama ashe abinda yarinyar nan take aikatawa kenan wannan wanda ta kawo ashe har gidansa take zuwa har Wakinsa take binshi gantali sannan kuma in ta fita islamiyya ba can take zuwa ba gidan Ball take zuwa har Abacha youth center ta shiga cikin gungun mazan nan ana Ball da ita iskanci kala kala kinganta nan shegiya ´ar ba™a munafuka",
Mama ta rasa bakin cewa don an Waureta da jijiyoyin jikinta nikam in banda kuka babu abinda nake jin an haWamin ™arya da gaskiya banji ba ban gani ba", Mama eta ce "shikenan in kinga rayuwar da kika Waukar wa kanki daidai kenan kici gaba duniya ce gaki ga tanan", Abba ya ce "ai ita da gidan nan ta gama tunda iskanci ta zaSa wallahi ba'a gidana ba taje can gaba tayi Iya da Babanta Abdulhadi sunce akwai wani da sukani za'a haWasu Aure kuma na ce wallahi bazan karSi ko sisi ba sadaka zan bayarda shegiya wallahi Wallahi kinji na rantse ko kaffara bazanyi ba *AUREN SADAKA* zanyi miki Wallahi babu gudu babu ja da baya duk da ance ci da gidansa ma wahala yake masa amma haka zaki tafi na cireki daga cikin ´a´ana kije can ki ™arata an riga an tsaida rana jibi in Sha Allah dabara ta rage me shiga rijiya.. ya kaWa Babbar rigarshi ya fice ya barmu.
Mama ta kalla su yaya Auwal cikin ta'ajjubi da damuwa ta ma rasa me zata ce kanta ya kulle gaba Waya yaya Auwal ya taso ya dafa gwiwanta cikin kwantar da murya da lallashi ya ce "Mama kiyi ha™uri don Allah kar ki Waga hankalinki akanta batasan kinayi ba in wani abu ya sameki muke da asara ba ita ba saboda batasan kinayi ba don Allah Mama ki kwantar da hanaklinki kinji ki ta addu'a Mama", ya share mata hawayen da suka gangaro mata", cikin sheshe™a nima na ce "Allah Mama sharri akayimin bana bin maza wallahi Mamana...", Ban ™arasa ba yaya sani ya taso a zuciye don dama a zuciye yake tunda aka shigo falon beyi magana ba ya zare belt Win jikinsa ya fara laftata duka tamkar an aikoshi kamar ya samu jaka haka yai ta duka na ina ihu da ro™onshi yayi ha™uri, amma ina yayi nisa bayajin kira kuma babu wanda yai yu™urin dakatar da shi har da Mama, Saida yamin shegen duka ya farfasa min jiki sannan ya ™yaleni nai Waki a guje ina gunjin kuka.
Bayan sun fita Mama ta kira ´an uwanta take faWa musu abinda ke faruwa suka jajanta mata kan cewa gobe zasuzo a ji yanda za'a yi bayan sun gama wayar Alwala tai tayi sallah raka'a biyu tana ro™on Allah ya kawo mata mafita ta Alkairi,

&&& &&& &&&

Washe gari ´an uwan Mama kusan su huWu sukazo daga zaria ™annenta biyu sai yayarta Waya da ™anwar mamanta Waya su huWu, sukazo suka tarar da Mama jikin nata ma babu daWi ta labarta musu duk abinda ya faru sukai ta bata ha™uri da kwantar mata da hankali sukace ta bari aga yanda Allah zaiyi ko?
Saiga Baba Kalla ya aiko ana kiran taro na gaggawa ya tashi na Family za'a yi a Wakin Iya muna idar da Sallar La'asar muka tafi dukanmu ´an gidan daga mazan har mata kowa ya Hallara ana zaune ana jiran me gayya mai Aiki Hajiya iya ta zo, itama sai gata ta fito aka zauna Baba Isuhu ya buWe mana taro da Addu'a bayan an shafa Baba Kalla ya fara magana,
"Ah kamar yadda labari ya jewa kowa na wannan yarinya Sa'adatu kowa yaji abinda ta aikata ba abu ne me kyau ba tayi abinda ya saSawa tarbiyyar Shari'ar Muslunci da kuma kunya da Al'ada tamu ta Fulani don haka da har mahaifinta ya yanke mata hukunci ya koreta sai muka tausheshi kan cewa in hankali ya gushe nemoshi akeyi yin hakan bazai haifar da Wa mai ido ba yayi mata Aure kawai ta tafi gaba Waya ya ce SADAKA zai bayar da ita.. to Ala kulli halin dai duk aure sunansa Aure akwai wani bawan Allah shi za'a haWa su Aure tunda dama shi irin wannan Auren Malamai ake bawa ko ™olawa ko dai wani mara ™arfi don a taimakeshi don haka an yanke shawara za'a haWa shi Aure da ita Ranar juma'a gobe kenan in Allah ya kaimu don haka ki shirya ana Waurawa za'a kaiki,
Baba hadi ma ya Wora saura ki Wora da wani rashin tarbiyyar taki tunda dama bakida ita kin gada amma ba a wajenmu ba candai kika kwaso wallahi kikai masa wani rashin kirkin na bashi dama da lasisi ya naWamiki shegen duka kuma in kinyi yaji saidai ki shiga duniya amma ba nan gidan ba mai ba™in hali,
Ya ci faWansa babu wanda ya katseshi ya ™aremin zagi samfur samfur kowa na wajen sai da yayi min daga iyayen nawa har ´an uwana Yaya Deen ne kawai ban gani ba a wajen kuma ina zarginsa shi ya haWamin wannan makircin tuggun Iya ma ta ™aremin kafin taro ya watse kowa na faWar Albarkacin bakinsa,
Muka dawo sasanmu su Aunty Hafsa yayar Mama ta tasani da zaunar da ni suna tambayata me na aikatawa Iyayena har sukayi wannan mummunan fishin dani, rantse rantse na shiga musu ina kuka wallahi ban aikata komai ba sharri akayi min suka ce ya ainihin sharri ga abu ™iri™iri kin aikata na ™i magana sai kuka ba komai ke Wagan hankali ba sai tunowa Gobe zan bar gudanmu zan bar Abbana zan bar Mama da ´an uwana zan bar masoyi na Ademola zanbar school da Football da komai nawa zanje nai rayuwar ™as™anci za'a Wauramin mijin da ban sanshi ba talaka ™azami mummuna wayyo Allah na ni Ade an rabani da mahaifina duk ™aunar da yake min an rabani da shi zaiyimin *AUREN SADAKA*..
'þ




*AFUWA DA JINA SHURU KWANA 2*





*PAID BOOK 300 ONLY*
*SEND VIA THIS ACCOUNT=ØGÜ*

*SAFIYYA GARBA MUKHTAR*
*JAIZ BANK*
*0007688753*
*EVIDENCE OF PAYMENT HHERE=ØIÜ 09042684315 siyan na gari maida kudi gida*


*AUREN SADAKA BY SAFIYYA MUKHTAR GARBA*

#Share 'þ
#comment'þ
#EditingL'













*AUREN SADAKA 19&20*



*AS.Episod one.pg19&20*. *E*O*W

*09042684315*=ØÞÜ

=Ø…Ü*FC'- 'D5/B)*



*ALHAMDULILLAH=Ø
Þ SATI NA BIYU KENAN DA FARA AUREN SADAKA LAST WEEK MUNYI 5pgs naji Godiya and comments some many people said wai wannan salon daban ne ba kamar SA˜AR ZARE ba any way haka salon yazo don haka NVM kudai sha karatu kawai*,


*SECOND TO THE LAST FREE PAGE KU HANZARTA KU SAI NAKU KAR AYI BABUKU*



Yau ya kasance juma'a Babbar Rana, ranar Waurin Aurena da miskini kuma ranar ba™in ciki guna ranar kuka a gareni hawaye suna kwaranyowa Abbana ya daina sona haka Mamana haka ´an uwana kodayake su dama tun can basu sona wa'inda suke son nawa sun ma daina ballantana su,
Ana sakkowa daga masallacin juma'a aka Waura mutane da yawa sun halarta, ina kwance a Wakina na ™udundune na ji sallama dama ina jiyo hayaniya sama sama a falo na buWe idona da yamin nauyi tsaban kukan da naci yayi luhu luhu yayi ja har yaji yaji yakemin, muryan Aunty Hafsa naji a kaina tanamin magana wai na tashi nai wanka na kimtsa Baba Hadi yana jirana za'ayi min faWa kamin a rakani gidan mijina,
Banida zaSin da ya wuce nabi umarni haka na mi™e ina tangaWi kaman zan faWi ta ri™eni ta rakani har toilet nayi wanka da yin brush don inajin bakina babu daWi sam, na Waura Alwala na fito nasa doguwar rigata ta lace me shegen tsada Winkin Bubu wanda a ™alla kuWin lace Win ya tasamma Wari na sa na Waura Wankwali da sa hijabi na tayarda Sallah na idar ina zaune a wajen ban motsa ba ina tufka da warwarar yanda zan samu mafita ina ta SA˜AR ZARE ina kwancewa amma na kasa samun mafita,
Na ™ulla a raina guduwa kawai zanyi guduwa zanyi zan bi Ademola mu shirya plan mu Gudu don wallahi bazan taSa iya zaman Aure da wa ni can miskini wanda ban sani ba haka kawai na je ma ko Aljanine ko mahaukaci za'a la™aba min masifa to ba da Ade ba badani ba, naita sa™awa da kwancewa a raina Aunty Hafsa ta sake shigowa ta kawomin Abinci tace nai maza na ci na kalli abincin ko sha'awar cinsa banyi ba saboda zuciya ta ba daWi jimawa kaWan ta sake shigowa ganin ban taSa abincin ba yasa ta fara min faWa ta ya zan azabtar kaina da yunwa haka kawai? Ta tasani gaba dole sai da naci abincin kaWan na tsakura don banji taste ko Waya a bakina ba,
Ina gamawa ta ri™a hannuna mukayi Falo na tarar sauran ´an uwan duk suna nan harda Mami itama ta zo Mama ma shigowarta kenan ta ce "Yaya hafsa har yanzu baku gama ba? zasu fara faWan nasu wai suna jiranta, ta ce "wallahi kinganta tun Wazun nake mata magana sai yanzu ta gama bata ce komai ba ta wuce Wakinta nikuma Aunty Hafsa da Aunty Fiddausi ™anwar Mama suka kama hannuna muka fita mukayi sasan Iya suna zazzaune harda Abbana muna shigowa ya tashi ya fita muka zauna Baba Isuhu da Baba Kalla sukayimin faWa sosai da nasiha akan na kula ibada zanje ba shashanci ba zaman Aure zani don haka na kula kar naje nayiwa mijina halin da nakeyi anan gidan kishiyoyi zaa kaina na zauna da abokan zamana lafiya,
Na sake fiddo idona waje jin an ambatomin kishiyoyi na shiga 100 ni Ade harda wasu kishiyoyo to wallahi bazan iya ba na dinga haukana ni kaWai a raina muryar Baba Hadi ta katseni "saura kije ki nuna musu mugun halinki dama in kikayi abinda ya gaji da halinki ya koro ki to ki nemi wasu ahalin amma ba mu ba wallahi kinji me na ce miki?", Ya faWa a tsawace na gyaWa kaina da sauri don in na buWe bakina kuka zai iya kufcemin aka gama iya ma tayimin yawanci duk ba™aken maganganu ne kamin akace mu tashi muje mu zama cikin shiri ana idar da sallar La'asar zamu Wauki hanya don ba nan bane zaria ne sannan bazaa Wauki yuyan mutane ba muka koma Waki nai jugum a zaune su kuma sunata hada hada da shirin tafiya duk da ransu a Sace yake don basuji daWin abinda ya faru ba.
Mama ta fito Hajiya ™anwar mamanta ta ce "wai ni banga kayan da za'a tafi da su ba na amarya ban kuma ji anyi batun jeren kayan Waki ba ko an yi?", Mama ta girgiza kai "a'a bai yimata komai ba kuma ya ce bazaiyi ba halinta ya jamata ya ce ko tsinke bazaya siya ba kuma nima in na siya bai yafe ba haka za'a kaita abinda mijin ya siya ya bata ta haWa ta jalauta",
Mamaki ya kashe Hajiya"to a ina aka taSayin haka zakukai ´a gidan miji haka tsiya tsiya? Ga kishiyoyi? Ai ba a haka in kukayi haka bakuyi mata adalci ba", Mama ta ce "to wallhi dai kinji abinda yace Hajiya kuma banida ja akan haka", sukayi ta tattauna batun kamin su lallaSa Mama da ™yar ta bada kuWi ko babu yawa a saimin ko katifa ce da tabarma kamin aga abinda Allah zaiyi ta ce to ta Bayar kuwa suma suka haWa gudunmawarsu aka bari sai anje can an siya akayi kiran sallah mukai sallah muka Wau harami a lokacin banida sarki sai Allah naga dgsk dai tafiya zasuyi dani hankalina ya tashi na kalla Mama suna tsatsatsaye na faWa jikinta ina kuka mai tsuma rai da zuciya duk ™o™arinta na SanSareni a jikinta amma ta kasa saboda tsatsauran ri™on da nayimata,
Su Hajiya suka cireni a jikinta suna lalláshina suka Wauko min mayafina da takalmina da wata doguwar rigata da na fito da ita na aje kan gado don Ance kar a Waukarmin kayana in banda na jikina, muka fito harabar gidan su yaya Auwal suka shigo suka Wanmin faWa da nasiha sukamin fatan Alkairi muka shiga mota da Aunty Hafsa da Aunty Maimuna da Aunty fiddausi ™annen mama sai Hajiya sai kuma Baba Hadi zai jamu a motarsa zaaje kuma shi kaWai yasan gidan muka Wau hanya ™arfe huWu daidai sai Birnin Zazzau.
˜arfe shida ana gab da kiran maghriba muka isa awanmu biyu a hanya har ™ofar gidan Baba ya ce su hanzarta suyi maghriba da isha'i zaizo wanda zai koma kano su juya wanda zai zauna a Zaria Tom saboda su Aunty Maimuna dama Mamana asali ´ar asalin zaria ce don haka su gida sukazo amma munada nisa sosai su a tsakiyar birni cikin gari suke nikuma ™auye ne amma ba sosai ba inda aka kaini, muka sauka muka shiga shikuma ya juya da mota ya shiga cikin gari,
˜ofar gida ne Langa langar kwano mukayi sallama muka shiga tsakar gidane dogo sannan yanada faWi kaWan da Wakuna bazance ga adadinsu ba saboda duhun magriba sannan da mutane a tsakar gidan sunata kai komo da ´ar hayaniya kamar masu biki,
Su Hajiya suna ta kwaWa sallama da™yar aka samu aka jisu aka amsa musu suka zauna kan tabarma suna gaida mutanen gidan da™yar aka amsa musu suna wani shahararre su kamar sunga wata halitta daban anata faman kallonsu suka tambaya ina ne Wakin da za'a saka amarya? Nan ma banza sukayi musu sai wata a cikin yaran ce ta nuna musu yana daga can baya don shi ne na farko a barandar muka mi™e muka shiga duhu sosai Aunty Maimuna ta kunnan wayarta aka haska Wakin duk ™ura kaman Wakin shirgi ga shi ba flasta a bango bulo ne gashinan mutane sama kam babu silin sai kwano da katakon rufi ba laifi Wakin yanada Šan girma kaWan,
Mamaki sosai suka shiga yi wanda abin ya tsoratasu ba kaWan ba Hajiya ta ce "ammanan lamarin babu adalci a ciki ya zakuyi ku kawo yarinya nan?, Cikin wannan gidan wannan Wakin kamar kurkuku", Aunty fiddausi ta ce "kinga Hajiya mai faruwa fa ta faru muyi muyi abinda ya kawomu kinga fa ko tsinke babu a Wakin nan muyi mu siyo abinda ya sauwa™a kafin ya dawo kinsan hali", ta ce "hakane muyi sallah sai mu fita muga me zamu siyo, nidai ina jinsu banda ta cewa don ba sosai nake ganema lamarinsu ba kaina ™iris ya rage yai bombing,
Suka fita suna tambayar toilet nan ma aka musu banza sai wata yarinya ce ta nuna musu suka jawo ruwa a rijiya zasu shiga wani uban zarni da wari ya doko su suka fito da sauri kowa ta ce bazata iya shiga ba sai haka sukayi Alwalar suka dawo Waki suka kaekaWe Wan kwalinsu suka shimfida suka tayar da sallah nima banida zaSin da ya wuce naje nai Alwalar suna idarwa suka nufi kasuwa ya rage daga ni sai Aunty Hafsa,
Sai bayan isha'i suka dawo a haka ma sunyi sauri suna tsoro karsu dawo su tarar baba ya dawo suka kunna sabuwar fitila da aka siyomin suka zage suka fara shara suka Webo ruwa aka zazzaga klin aka fara wanke tsakar Wakin da yake suminti ne sai inda ya kuje ba a rasa ba suka goge yasa iska aka shimfida tabarma ™atuwa aka maida katifa ´ar sala mai cin mutum Waya irin ta ´an bodin sai filo da zanin katifar da net aka kafa ™usoshi aka sa Waya tabarmar aka shimfida daga gefe sai sauran tarkace su tsintsiya buta bokitin roba babba na zuba ruwa Fo wai na huta da fita fitsrin dare nayi abuna da safe na zubar baho da bucket kayan cin abinci su flate tukunya Wan turmin karfe abun haWa gawayi kurfoti harda gawayi Wauri Wauri a leda kusan na dubu Waya tarkace dai komai na bu™ata daidai ™arfin talaka don kuWin bai ma isa ba saboda sun mata basu siyo ledar tsakar Waki ba an siyomin dogayen riguna roba masu arha saboda ban taho da kaya ba sai abinci da suka siya dafaffe zamu ci da Wanye da aka saimin kaWan shima don baifi kwano huWu ba shinkafa da wake sai taliya da mai da maggi,
Suka gama aiki tsaf suka ci abinci sai lokacin Baba hadi ya ™araso ya ce su fito suka ce to suka shirya aka fito dani gun matan gidan aka mi™ani wajensu ana min nasiha wai mu zauna lpy su kuma su ri™e ni amana kowa ta she™e da dariya da cewa kowa halinta ya ™waceta ba ruwansu baa karbar amanar kishiya jiki a salube su Hajiya suka dawo dani Wakina suka daWamin nasiha mai ratsa jiki sannan suka tafi, Na zauna a tsakar Wakin nai kuka kaman raina zai fita saboda tsananin ba™in ciki har ajiyar zuciya nake sauke wa kamin bacci ya kwasheni a wajen.
Cikin dare kaman a mafarki naji ana kiran sunana a hankali da wata murya da ban santa ba, a hankali na farka naga mutum zaune a gabana na mi™e a firgice ina ja baya ina zare idanuwa kaman nayima sarki ™arya, ya ce "barkanki da wannan lokaci sannunki da zuwa ya hanya? Nine me gidan naki", na sake zabura ina ja baya jin abunda yake cewa mutum yana zaune a gabana shi ba kuturu ba shi ba makaho ba yana kira wai shine mijina...
'þ





*PAID BOOK 300 ONLY*
*SEND VIA THIS ACCOUNT=ØGÜ*

*SAFIYYA GARBA MUKHTAR*
*JAIZ BANK*
*0007688753*
*EVIDENCE OF PAYMENT HHERE=ØIÜ 09042684315 siyan na gari maida kudi gida*


*AUREN SADAKA BY SAFIYYA MUKHTAR GARBA*

#Share 'þ
#comment'þ
#EditingL'













*AUREN SADAKA 21&22*



*AS.Episod one.pg21&22*. *E*O*W

*09042684315*=ØÞÜ

=Ø…Ü*FC'- 'D5/B)*



*ALHAMDULILLAH=Ø
Þ SATI NA UKU KENAN DA FARA AUREN SADAKA LAST WEEK MUNYI 5pgs naji Godiya and comments some many people said wai wannan salon daban ne ba kamar SA˜AR ZARE ba any way haka salon yazo don haka NVM kudai sha karatu kawai*,


*LAST FREE PAGE/EPISODE WANNAN SHINE PAGE NA ˜ARSHE DON ALLAH NA RO˜EKU KAR WADDA TA KARANTA BATA SIYA BA YIN HAKAN SAAWA DOKA NE, BA'AYIWA WANDA SUKA SIYA ADALCI BA IN KINSAN BAKI SIYA BA KARKI KARANTA SABODA BAKYASO DA KINA SO DA KIN SIYA KARKI KARANTA BAKI SIYABA=ØAÞ>Ø2Ý*




*LAST FREE PAGE/EPISODE*

Ganin kamar na tsorata da shi yasa ya ce "yi ha™uri dama Abinci na kawo miki ko zaki Wan taSa babu yawa ya ajiyemin ba™ar leda ya mi™e ya fita ni sai naganshi ma kamar gurgu don ™afarsa kaman cangala ta yake hannunsa ma kamar ya shanye dukda ban gama tabbatarwa tabbatarwa ba amma ai da hasken tocila,
Tashin hankali wanda ba'a samasa rana ta tabbata dai gurgu na Aura miskini kuma fa™iri na Wora hannu aka ina cigaba da kukana, tunda nake a rayuwata ban taSa irin wannan kukan irin wannan ba tundaga ™asan zuciyata yake tahowa ban taSa zaton zanyi kwatankwacin wannan rayuwar ba ko a mafarki sai gashi yana faruwa bi da bi daga wannan sai wannan na yi kukana ma'ishi sannan na mi™e na tuSe lace Win jikina don ya dameni sosai har under wears Win na cire nasa doguwar rigata mara nauyi da na taho da ita, jin fitsari ya cikamin mara ya sa nayi a FO na wanke fuskata nazo na kwanta a katifar ina cigaba da zubar da hawaye da tunane tunane Wanda su ka cikamin ™wa™walwata a ranar dai sai bacci Sarawo ne ya saceni,
Tun farar asuba naji ana ™wan™wasa min ™ofa nai juyi da yin salati ina sake komawa, na ko sake jin wani bugun nai tsaki ina tashi zaune na ce "waye", shi ne na jiya da daddare cikin muryarsa mai sanyi sosai ya ce "ki tashi lokacin Sallar Asubah yayi kiyi Sallah", ni sai lokacin mana tuna ba'a gida nake ba na yi shuru ban magana ba inaji ya fita na maida kai na kwanta,
Sai ™arfe takwas da kusan rabi na farka lokacin gari ya tangare rana har ta fito na mitstsike idona inabin ko ina na Wakin da kallo tundaga sama har ™asa bangon yasha faci ga kwanon rufi muraran ina kallo duk bule ana gano hasken rana sumintin ™asan ma duk yasha faci sai ´an tarkaceni ´an tsugul a gefe kamar ´ar cirani... Tunawa da banyi sallah ba yasa na mi™e da sauri na Wauki butata a bayan ™yaure na buWe ™ofar Wakin, ´ar danga akayi ta langa langar aka kewayemin iya ™ofar Wakin sannan akayi makwarara sai ´ar ™ofar itama ta langa langar, jiya kam ban lura ba sam banga wannan dangar ba ko don ina cikin ruWu ba a hayyacina nake ba?", Shiyasa ban lura ba,
Na tsuguna a ™ofar Wakin na Waura Alwala na koma Waki na tayar da sallah na idar na zauna ina addu'a da istigfari Allah ya yafemin jinkirin sallar danai, sannan ya fitar dani daga wannan ™angin wahala da na faWa ya fitar dani a wannan kurkukun,
Ina nan zaune naji an taSa ™yauren an shigo ya Waga labulen da yin sallama kamin ya shigo na ™are masa kallo, Ba™ine kamar ni sannan gurgu hannunsa da ™afarsa ta hagu shanyayyace cangalasu yakeyi daga ganinshi kaga mugun talaka fa™iri wani haka haka da shi kamar mahaukaci kamar taSabbe kayan jikinsa sun yayyage sun zama kamar tsummokara saboda tsabar tsufa da jin duniya kansa duk gashi buzu buzu sam bashida kyau ga ™azanta yanda na tsani ™azanta a rayuwata kamar tsoho ma ni na ganshi ko tsaban talaucin ne ya maida shi haka? Ya katsemin tunanina da gaisheni cikin sanyinsa,
Tun kallon da na masa naji wata irin ™iyayyarsa mai zafi ta Warsu a zuciyata naji na tsani na buWe ido na kalleshi ma zuciyata da zafi kamar na haushi da duka.. ganin kamar banji me ya ce ba ya sake gaisheni "Ina kwana ya ba™unta? Abin kari ne dama na kawo miki", ya turomin kwanon silba a rufe gabana na watsa masa wani mugun kallo idona kaman zai faWo saboda wutar bala'i tun kafin nayi magana ko ya sha jinin jikinsa, na daka matsa tsawa "kai wawa! tashi min a gaba da wannan ruSaSSen kwanon naka kafin na kifa maka shi a wannan mummunar fuskar taka! ", Na faWa ina nuna ™ofa da Wan yatsa na fuskata cike da wutar Sacin rai, bai min musu ba yayi tsam ya mi™e ya Wau kwanon da hannunsa na dama me Lafiya ya cangala ya fice, inajin ya fita na kifa kaina kan dadduma kukan ba™in ciki da Sacin rai ya tahomin na hau rera abuna babu mai dakatar dani balle ya lallasheni,
Na ™arfin awa biyu a haka ina kuka na fili da na zuciya daga bisani naji kaina yana barazanar fashewa saboda tsananin azabar ciwo na saurara shima ba don ba hawayena sun daina zuba ma haka har baccin wahala ya saceni inayinsa cikin rashin daWi a takure a ™asan dadduma ban tashi ba sai azahar shima Hayaniyar ´an gidance ta tasheni kamar ana ™aramin ya™i ko taron biki inbanda ihun yara da hayaniyar magana kaya kaya ni sai naji ma kamar faWa akeyi, sannan ga uwar yunwa
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6

Please Login or Register in order to submit comment