Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ne,nan dai suka gama tattaunawa suka ajiye maganar tasu akan su saurari yankin ja'i.




Bayan an watse a fadar Sarki Chubaɗo Arɗo da Baffa ne suke tafiya a hankali su na magana kasa-kasa,Arɗo ya ce
"Magaji, fatan kana sa a ido sosai a kan su AZIMA DA AZIZA?"

"E Arɗo ina iyakar bakin kokarina wajan saka musu ido, ita Azima baka iya gane gabanta,gwanda Aziza, gasu dai a tare aka haifesu amma halayyarsu ta sha bamban, a kwana biyun nan basu kula juna, Jumala sai korafi take yi a kan nayi musu magana ko me ya haɗa su, amma ban dauki hakan da mahimmanci ba sabida ba shi ya kamata na kula ba, kare rayukan yankin nan shine abu mafi mahimmanci" Arɗo ya gya ɗa kai ya ce
"Tabbas hakane, ba mamaki sun ɗan yi faɗa ne tinda ana samun irin haka" Baffa yace
"Eh nima haka nake tunani Azima bata da dadi ko kadan, Arɗo barin wuce gida"
"To a gaida Jumala da Azima da Aziza"
"Zasu ji" Baffa ya fada tare da yiwa Arɗo sallama.



🍃🍃🍃🍃



Tun safe Aziza ke rafin jimulo tana wanke kayan Hajja da na Baffa, Azima kuwa dan Aziza na rafin jimulo yasa ita bata je ba tana gida, abinci Hajja ta ɗora amma Azima ta hana abincin dahuwa, har la'asar tana zaune a kan tabarma kaba tana saƙe wani igiyoyi, Hajja ta kalleta ta ce
"Wai ni kam Azima wannan saƙe-saƙen da kikeyi na miye ne? Tun safe kike zaune a wajan ba sallar azahar bare la'asar ki tashi kiyi sallah" ba tare da ta dago ta kalli Hajja ba ta ce
"BANA SALLAH!" 😏
Baki sake Hajja ta kalli Azima ta ce
"Kina fashin sallah ne?" kafin Azima ta bada amsa Aziza ta yi sallama da kaya a hannunta ta shige bukkan Hajja ta ajjiyesu sannan ta fito ta duƙa ta ce
"Sannu da gida Hajja"
"Yawwa sannu Azizatuna, kin dawo?"
"E Hajja na dawo"
"Ayya Aziza maimakon idan kin wanke kayan ki dawo gida idan ya bushe anjima a kwaso shine kika zauna har yamma a rafi ba tare da kin dawo gida ba? Ga shi haka kika fita ba ki ci komai ba" murmushi Aziza ta yi a ranta ta ce
"Idan na so zan iya wanke kayan nan na busar da shi a lokaci guda sabida karfin dafin da nake da shi,amma bana son hakan nafi son na samu ladar iyayena" a fili kuma ta ce
"Wlh ba komai Hajja bana jin yunwa ai"
"Allah ya miki albarka Aziza ke da yar uwarki, kinyi sallah ne?"
"Amin, E Hajja nayi sallolina a rafin jimulo ban bari lokaci ya shige ba" Hajja ta kalli Azima ta ce
"Azima kince baki sallah kina fashi ne?" da blus eyes dinta ta dago ta kalli Hajja ta ce
"Ni sallah ne kwata-kwata bana yinsa a rayuwata!" dam!dam!dam! Ƙirjin Hajja ya bada ta b'ata shuru tana bin Azima da kallo, da kyar ta buɗe baki zata yi magana amma Azima bata jira hakan ta faru ba dan kamar ƙiftawar ido ta tashi tare da tattare dogon igiyar da ta saƙa ta shige bukka, Aziza ganin yadda hankalin Hajja ya tashi da maganar da Azima ta faɗa ya sakata faɗin
"Karya take yi Hajja, kin san halinta bata damuwa da maganar da zata faɗi zai yi maka dadi ko akasin haka faɗi kawai take yi" sai a lokafin Hajja ta sauke ajiyar zuciya, Aziza ta ƙwaƙulo murmushi dan sallah kam Azima baya yi, ta ce
"Hajja ba a gama abinci ba?"
"Wollah Aziza ban san wani irin abinci yau nake dafawa ba, tin rana na ɗora kafin ayi azahar amma har yanzu ta ƙi nuna" shuru Aziza ta yi tana kallon tukunyar kasan na wani sakanni kafin ta ce
"To Hajja je ki ciki ki huta yanzu zan karasa"
"A'a Aziza yanzu fa kika dawo daga...."
"Ohh dan Allah Hajja ki je ki huta" murmushi Hajja tayi tana shigewa bukka, Aziza ta buɗe abinci ta ga rashin dahuwarsa yana da nasaba da sa hannu da Azima ta yi, rintse ido ta yi ta buɗe nan idonta ya koma fari sosai ta zaro harshenta ta hura wani hayaki a cikin tukunyan, nan kalar abincin ya canza alaman ya dahu, sannan ta rufe tana miƙewa tsaye ya yi dai-dai da shigowar Baffa da kuma fitowar Hajja daga bukka, sannu da dawowa suka masa, Baffa ya amsa yana zama a inda Azima ta tashi, kallon baƙin igiyar da Azima ta yi saƙa da shi ya gani guntun, dauka ya yi a fili ya ce
"Zaran saƙar dana? me yake yi a gidan nan? Wa ya kawo?"



🍃🍃🍃🍃


COMMENTS AND SHARE

BY MOMYN AHLAN
[3/21, 12:30 AM] Fatima: 🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃

💥✨ *AZIMA DA AZIZA*💥✨
(🐍 _Macizai ne_🐍)


MALLAKAR.

*ZAHRA ABDUL(MOMYN AHLAN)*

SAHIBAR KAINUWA.


Littafin kuɗi, naira ɗari kacal dan masoyana, turo da kudinki ta wannan acct din
0096035983 balaraba hassan accees bank, ko kuma hoton kati ta wannan lambar 08165550116, pls ban da vtu.


Sanarwa.
Ga yan niger masu bukatar book din nan su tuntubeni dan sanar dasu yadda zasu biya kar ayi babu ku.


*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*

*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan*👇🏻

https://bakandamiya.com/group/71/kainuwa-writers-association

*____________________________________*

*MARUBUCIYAR.*
1- _HALITTA DAGA ALLAH NE._
2- _GUDU A JEJI._
3- _SHUHADA._
4- _NIDA ƘANNEN MIJINA._
5- _WA'YA KASHE ZAHRA'U?(#200)._
6- _COLONEL UBAIDULLAH._
7- _ITA CE ZUCIYATA(#200)._
8- _SAMIMA (MACIJIYA CE._
9- _GAWURTACCEN SOJA(#300)._
10- _DA NA SANI NA._
  11- _BADAWIYYAH_
12- _DEPUTY SUPERINTENDENT OF POLICE (DSP ALIYU HAIDAR)_
Now
13- _AZIMA DA AZIZA (MACIZAI NE🐍)_

_Follow me on wattpad,@Fateemah'0_


🍃🍃🍃🍃🍃


*NA GAISHEKI SIS NA🥰 SURRY BABY, ALLAH YA BAR MIN KE.*


*AZIMA DA AZIZA GRP NA GAISHEKU😂 MASU MAFARKAI DA TSORATA NA JINJINA MUKU, A CI GABA DA CHAPTAWA.*🤙🏻



*FREE..*
🅿️==1️⃣3️⃣↪️1️⃣4️⃣



"Zaran saƙar dana kuma?" Hajja ta faɗa tana kallon hannun Baffa da ya riƙe zaren yana kalla, Aziza ce ta matso kusa da Baffa ta duƙa ta ce
"Baffa me zaran ya ƙunsa?" shuru Baffa ya yi na wasu lukota kafin ya ce
"Ba ƙaramin hatsari wannan zaren yake da shi ba, ana amfani da shi wajan yaƙi! Ko kuma a ɗaure takwabi da shi, duk wanda aka sara ko aka yanka da takwabin da aka d'aure da shi to sunansa gawa! Walau mutum ko aljan! " a firgice Aziza ta ce
"Kenan mutum mutuwa zai yi?"
"E Aziza, wa ya kawo zaran nan gidan nan? Sannan ta ya aka samo shi? Dan nasan ba a samunsa nan kusa sai an je can cikin jejin lore, wanda wannan jeji tun kafuwarsa shekaru aru-aru babu wani ɗan adam din da ya taba zuwa idan ba ni ba" Hajja ta ce
"Ai kuwa dai Azima ce na ganta da shi dan tun safe take zaune a inda ka tashin nan take saƙa shi,bayan ta gama ta shige ciki, bata jima da shiga ba ka shigo" da sauri Baffa ya miƙe tsaye ya ce
"Azima! Azima! Azima!?" ya kwala kiran sunanta da karfi, Aziza ta ce
"Bari na kirata Baffa" cikin faɗa Baffa ya ce
"Nan da bukka ta ce bata jin kiran da na mata?" Hajja ta ce
"Ayye Baffan yan biyu ka bi a hankali mana, watakila bacci ne ya kwasheta Aziza kirawota" Baffa ya ce
"Ke da kika ce ina shigowa bata jima da shiga ciki ba shine har bacci zai kwasheta?"
"Ai Azima bata da wuyan bacci" cewar Hajja, shi dai Baffa shuru ya yi tare da gyara tsayuwarsa ya maida hannunsa baya yana jiran fitowar Azima.


Tana kwance a gadon kara, rabin jikinta macijiya sai juyi take yi kanta a hargitse, Aziza ta shigo da sallama ko amsawa Azima bata yi ba, Aziza ta ce
"Ba ki jin Baffa na kiranki ne?"

"Mtswwwww! Na ji mana, tunda dai ni ba kurma ba ce! Je ki ce ba zan zo ba!" a fusace Aziza ta sa hannnu ta janyo wuyar Azima ta ce
"Wallahi! Wallahi! Wallahi! Kinji na rantse miki ko? To sai kinje, kuma dole ki ba wa Baffa amsar tambayoyin da zai miki, za ki tashi ne ko sai na b'ace dake a dakin nan na wujijjigaki!?" Aziza ta karasa maganar idonta da fatar jikinta suna canza kala, ganin haka yasa Azima miƙewa fuuuu ta fice, rufe ido Aziza ta yi ta dawo dai-dai sannan ta bi bayan Azima, a tsaye ta sameta Baffa na tuhumarta inda ta samo zaren sakar dana, cike da rashin tsoro da rashin kunya ta ce
"A inda ake samu na samo!"

"AZIMA!!!" Aziza ta faɗa a tsawance ta yi kanta dan ta kai mata mari, da sauri Hajja ta ja hannun Aziza sannan ta fashe da kuka, murguɗa baki Azima ta yi ta fice a gidan ma gabadaya, Baffa kuwa suman tsaye ya yi, Aziza kuma tana lallashin Hajja dake kuka.



Cikin kuka Hajja ta ce
"Wai ni meke shirin faruwa dani ne kam? Me yasa Azima ta zama haka? Kwata-kwata yanzu bata shakkar gaya mana magana! Aziza dame ku ke so naji? Idan ba ki taimakawa yar uwarki ki gyara mata halinta wa zai iya yin hakan?" Hajja ta ci gaba da kuka, Baffa kuma bukka ya shige ya zube a bakin gadon kara jikinsa na rawa, hakika jejin lore ɗan adam baya shiganta ya fito lafiya, duk ɗan adam din da ya shiga jejin lore to sunansa gawa! Shi ma sanadiyyar shigarsa jejin lore ya yanko zaren saƙar dana sadda zasu gwabza da Banju ne, rass! rass! rass! gaban Baffa ya bada nan zufa ta shiga tsatstsafo masa ta ko wace kusurwar gashi dake gangar jikinsa, a fili ya ce
"AZIMA BA MUTUM BA CE! TAYA ZAN GWADATA NA GANE HAKAN DAN NA WARKARWA ZUCIYATA TANTAMA DA ZARGI!? INNALILLAHI WA INNA ILAIHIRRAJIUN! YA ALLAH KASA KAR ABUN DA NAKE KWANA NAKE TASHI DA SHI YA ZAMA GASKIYA!" Baffa ya karasa maganarsa hannunsa a sama hawaye na gangarowa.



Da kyar Aziza ta ɗaga Hajja ta shigar da ita bukkarta tana lallashinta amma ina Hajja ta kasa tsaida hawayenta, kasa juran kukan nata Aziza ta yi ta miƙe a hankali ta fita zuwa randar kasar dake tsakar gidansu ta ɗibo ruwa a kwarya ta bude bakinta ta zuba abu a ciki sannan ta koma ta ba wa Hajja, ƙin karba Hajja ta yi ta ci gaba da kuka, Aziza ta ce
"Dan Allah Hajja kiyi shuru ki daina kuka, kin ga gidan nan bamu da sauran ganyen magunguna balle na haɗa miki ki sha idan kanki ya fara ciwo, zan yiwa Azima magana ga ruwan nan ki sha zuciyarki ta yi sanyi" da kyar Hajja tasa hannu ta karbi ruwan ta sha, tana shan ruwa ko minti uku bata yi ba, ta zube a jikin Aziza, hawaye ne masu zafi sosai suka zubowa Aziza a fuskarta a fili ta ce
"Kiyi hakuri Hajja ki yafe min ba zan iya ci gaba da kallon kukanki ba, baccinki shine mafi alkhairi, tun a yau da ba ki san su waye mu ba kina irin wannan kukan ran da kika sani za ki hadiyi zuciya ne Hajja? Ina ba zan bari hakan ta faru ba! Ba zan iya rasaki ke da Baffana ba! Zan ci gaba da boyewa tare da dakatar da yar uwata, ko da kuwa zamu kashe juna" Aziza ta karasa maganarta tana sake rungume Hajja, ta sha kuka sosai kafin ta gyarawa Hajja kwanciya ta fita.


sallama ta yi a bukkan Baffa, da sauri Baffa ya share hawayensa ya ce
"Shigo Aziza" cikin natsuwa ta shigo,zama ta yi kusa da kafarsa ta ce
"Baffa kuka kake yi?" girgiza kai Baffa ya yi ya ce
"A'a ba kuka nake yi ba Aziza" shuru Aziza ta ɗan yi kafin ta sauke ajiyar zuciya ta ce "Baffa
ina so na san meke ƙunshe da wannan zaren da Azima ta saƙa"


"Me kuma kike so ki sani bayan wanda na gaya miki Aziza? Hatsarin da ke cikin wannan zaren ba zai faɗu a baki ba tsananin yawanta, da ace za a dauki kwaya ɗaya tak! A jefata a cikin rafin jimulo, ina mai tabbatar miki duk wanda ya sha ruwan wannan rafi zai mutu!" dam! dam! dam! gaban Aziza ya bada nan ta shiga saƙe-saƙe a ranta tare da tunane-tunane, shin wa Azima take son kashewa da wannan zaren? *"BAFFA"* wata zuciyar ta bata amsa da sauri ta miƙe tsaye a firgice tana zare ido tare girgiza kai gami da fadin
"A'a karya ne! Ba zai yu ba! Ba zan bari hakan ta faru ba!" ganin yadda ta ruɗe lokaci ɗaya ne yasa Baffa tashi da sassarfa ya kama hannunta ya zaunar da ita ya ce
"Aziza natsu mana! Tsaya...kina ji? Menene? Gaya mini? Miye ba za ki bari ya faru ba?" kuka Aziza ta fashe da shi mai tsanani tana kwanciya a jikin Baffa, sosai hankalin Baffa ya tashi yana tambayar Aziza meke faruwa!.



Cikin kuka Aziza ke faɗin
"Me yasa! Me yasa! Me yasa!" da kyar Baffa ya shawo kan Aziza ta yi shuru ta daina kuka, Baffa ya ce
"Aziza meke faruwa ki gaya min gaskiya karki boye min komai, ni mahaifinki ne" saita natsuwarta Aziza ta yi ta ce
"Baffa, haihuwarmu ta yi muku rana?"
"Subhanallahi! Wannan wace irin magana ce kike faɗi Aziza?"
"Baffa kukan da Hajja ta yi a kan Azima dazu bazan sake bari hakan ta faru ba, ba zan sake bari ba!" ajiyar zuciya Baffa ya sauke,ita kuwa Aziza ta yi hakane dan kawar da shakku a zuciyar Baffa, shuru na ɗan wani lokaci ne ya ratsa wajan kafin Aziza ta ce
"Amm Baffa? Taya za a lalata zaren saƙar danar da yake hannu Azima?"


"Wannan ba shi bane abunda nake tunani Aziza, yadda aka yi Azima ta samu zaren nake tunani"

"Amm amma Baffa ta ce inda ake samu ta samu! Ya matsayin hatsarin jejin lore yake?"


"Aziza faɗin hatsarin jejin lore ba zai yu ba, dan yafi karfin ki fasalta shi da komai, taya har Azima zata shiga wannan ƙasurgumin jejin ta fito tana yar adam? Wannan shine tambayar da nake yiwa zuciyata amma na kasa samun amsa, ban san meke shirin faruwa da mahaifana ba"


"Baffa ka rabu da maganar Azima, kasan wani lokaci ba hankali gareta ba, yawwa kuma Baffa na mance ne ban gaya maka ba, Azima kamar tana da aljanu! Dan cikin dare sai na dinga ji kamar tana ta buge-buge da sambatu ita dayanta, Baffa na tabbata su ne suke saka ta rashin kunya,kuma ba mamaki karya take yi ba ita taje jejin lore ba, sai dai idan aljanun ne suka je suka kawo mata, ka yarda dani Baffa gaskiya nake gaya maka" Aziza ta karasa maganarta tana riƙo hannun Baffa, jinjina kai Baffa ya yi ya ce
"Kenan wani irin aljanu Azima ke da shi? Wanda har zasu iya kawo mata zaren saƙar dana? Me zata yi da shi? Kuma har tasan yadda ake saƙata?" zare ido Aziza ta yi ta hau rawar murya tare da in'ina
"Amm....eh.....umm....ohh...Baff....Baffa ....kar...ka...da..mu...da...Azima...ni nan zanji da ita, zan mata hayaƙin aljanu zata warke da yardan Allah na san ka yarda dani ko Baffa?" murmushi Baffa ya yi yana jin kaunar Aziza a cikin ransa, hakika ba zai ce baya son Azima ba tunda ita ma ƴarsa ce, amma aka ce mai kyautata maka shi ne wanda yake rayuwa a cikin zuciyarka,
"Na Yarda da ke Aziza, Allah ya miki albarka" murmushi Aziza ta yi ta miƙe tsaya tare da fadin "Amin Baffana" fita ta zo yi a bukkan har ta duƙa sai kuma ta ɗago tare da juyowa ta ce
"Amm Baffa? Baka faɗa mini abunda zai iya lalata zaren saƙar dana ba?"
"Aziza sanin wannan ba sauki garesa ba, har sai an koma jejin lore, jejin da mutane ba su shiga"


"To amma Baffa kai a garin yaya ka shiga ka fito?"

"Tsoron tarihi ne Aziza, kun dai sannin a matsayin mahaifinku! Amma har kwanan gobe baku da tarihin mahaifinku, na sha miki alƙawari zan baki tahirin jarumtar mahaifinki! Abunda yasa bana son faɗi yanzu sabida jarumtar bata jawo min komai ba sai babban kuskure"

Da sauri Aziza ta dawo ta zauna ta ce
"Baffa kamar ya? Dan Allah ka gaya min"

"A'a Aziza dama kin tashi kin tafi ne da ya fi miki alkairi, dan ba zaki ji komai ba a yanzu" ganin yadda Baffa ya yi maganar yasa Aziza miƙewa a hankali ta fice, tana fita ta koma bukkansu tana tsaye tana ta saƙa da warwara, a fili ta ce
"Kenan domin dakatar da Azima nima sai naje jejin lore? Idan kuwa hakane! *yau din nan zanje domin dakatar dake, amma kafin nan sai kin gaya min wanda kike hari da zaren sakar Azima!" Aziza ta faɗa tana harɗe hannuwanta.




🍃🍃🍃🍃🍃


Zaune suke a fadar sarki Chubaɗo, da sauri Maga Isar da saƙon kwana ya zo ya zube a gaban sarki ya ce
"Ranka ya daɗe! Sako ce daga yankin ja'i" da sauri wa inda suke zaune a wajan suka mai do da kallonsu kan Maga Isar da Sako, wazirin kwana ya ce
"Maga Isar da sako, buɗe ka karanto mana abunda yankin ja'i suka rubuta" jiki na rawa Maga Isar da saƙo ya zo zai buɗe sakon sarki Chubaɗo ya dakatar da shi da cewa
"Dakata! Maga Isar da Saƙo, wannan saƙo ba na iyakar mu na nan kawai za a karanta ma wa ba, a'a yanzu maza kuyi aike a tara mutane,kuje ku sanar da Mai unguwa Ori, ku kira Arɗo tare da Baffa Mandi, da Magaji Bawa duk a hallara yanzu" Maga Isar da sako ya amsa da to, sannan ya mike da sauri dan isar da saƙon sarki chubaɗo.



A cikin yan mintuna ƙalilan kowa ya hallara a fadar sarki Chubaɗo , kowa yana fargaban kar yankin ja'i ace sun rubuta ba zasu taimake su ba.


Bayan kowa ya bada hankalinsa sarki Chubaɗo ya ce
"Maga Isar da sako karanto mana abunda yankin ja'i suka rubuto" Maga Isar da sako ya amsa da to, sannan ya buɗe wasikar yankin ja'i ya fara karantowa kowa naji.


" _Wa'alaikumussalam, da fatan yankin kwana su na lafiya? Ya kuma fargaban iftila'in da ku ke ciki? Kashh! Ayya! Allah Sarki! Wasikarku ta iso garemu na neman taimako! Tunda har yankinku ya duƙawa tamu yankin,mun yarda zamu taimaka muku da Innu Maciji! Zai zo gobe, amma abun mamaki ace kuna da mutum a yankinku kamar Magaji Bawa har sai kunzo yankinmu neman taimako? Koma miye daukakarmu ce, tunda yankuna yanzu zasu shaida kun watsar da makamanku wa yankinmu, saƙo daga yankin ja'i, mun karb'i ƙudirinku!_"


Maga Isar da sako yana gama karantawa Baffa ya miƙe cikin fushi ya ce
"Sadda muka tura wasika yankin jimo dan su taimaka mana da jarman macizai magana mai dadi suka mana sannan suka jajanta mana suka amince da bukatarmu, amma yanzu wannan wasika na yankin ja'i har da izgilanci a ciki" Arɗo ya mike shi ma ransa a b'ace ya ce
"Duk abunda aka gaya mana laifin waye Magaji? Na ce laifin waye!?" tsohon Sarkin fulanin kwana Baffa Mandi ya ce
"Yanzu ba lokacin nuna fushi bane sabida halin da muke ciki, tunda sun amince zasu taimaka mana shikena!" Garkuwan fulanin kwana ya ce
"Amma abunda Arɗo ya faɗa gaskiya ne, Magaji da ace ka yi wani abu a kai da yanzu wannan bala'in an gama shi, me yasa ba zaka dawo yadda kake da ba? Idan ka manta da takenka sai a tuna maka....!"
"Ya isa haka Garkuwa!" Baffa ya dakatar da shi idonsa jajur, Ori ya ce
"Garkuwa yana da gaskiya Magaji, da ace kayi wani abu a kai da yanzu yankin ja'i basu gaya mana magana ba" Wazirin kwana ya ce
"Tabbas hakane Magaji, da ace kayi wani abu a kai da har yaushe zamu duƙawa yankin ja'i balle su mana izgili kamar mu muka ɗorawa kanmu masifar!" haka kowa yasa Baffa a gaba ana cewa duk abunda yankin ja'i suka faɗi har da laifinsa, jikin Baffa ne ya hau rawa ya daka tsawa da faɗin
"NA CE YA ISAAAAA!!" ya juyo yana kallon mutanen da suke wajan ya ce
"Wai ku baku duba gagarumin bala'in da nake hangowa ne? Na koma na haƙo kayayyakina da na binne tamkar haƙo maƙabarta ne wa yankin nan! Dan karku manta da aljanun da mayun da na rufe! Duk abuna ban cika kisa ba sai inta kama dolen- dole! Tunda na kashe Banju nayi sallama da kwanciyar hankali, wanda a yau duk faɗin yankin kwana babu yaran da ake zargi kamar yarana AZIMA DA AZIZA! duk da ba zan hanaku zarginsu ba, amma ko da sau daya ne zaku min uzuri! na rayu ne wa yankina inda nayi aikin tuƙuru da jinina da lafiyata! naje na haƙo abunda na binne duk aljanu da mayun da na ɗaure tass zasu kunce, me ku ke tunani zai faru da iyalin da nake da shi a halin yanzu?" Baffa ya faɗi yana fashewa da kuka yana dukawa, jikinsu ne ya yi sanyi sosai, yayinda Arɗo ya dago Baffa yana rarrashinsa inda sarki Chubaɗo da mai unguwa Ori suka hau ba shi hakuri tare da nadaman ganin laifinsa, Arɗo ya ce
"Kayi hakuri Magaji, yanzu abunda za ayi a rufe wannan maganar, Allah ya kaimu gobe Innu Maciji ya zo ya warware mana wannan sarƙaƙiyar" Sarki Chubaɗo ya ce
"Kowa zai iya kama gabansa"


Da kaɗan-kaɗan aka fara watse wa, Arɗo da Baffa Mandi da Baffa ne suka fara tafiya, Baffa Mandi ya ce
"Amma na rasa me yasa Magaji kake yawan maganar Banju" Baffa ya ce
"Sabida ni kaɗai nake ganin abunda nake gani a gidana" yana gama faɗin haka bai jira amsarsu ba ya yi gaba, Arɗo ya sauke ajiyar zuciya ya ce
"Mandi, akwai abunda yake damun Magaji" Baffa Mandi ya ce
"Nima haka nake gani, amma anya baya da nasaba da yaransa da ake yawo dasu ake zarginsu kuwa? A gaskiya Magaji ya yiwa yankin kwana hidima bai kamata a dinga masa haka ba"
"Gaskiya kam hakane" tafiya sukeyi a hankali suna tattaunawa, Baffa kuma hanyar gida ya ɗauka.



🍃🍃🍃🍃

Zaune ta sameta a rafin jimulo, ita ma zama ta yi kusa da ita ta ce
"Azima tambayarki na zo yi"
"Wai ni Aziza me yasa kika rainani ne? Ba nice gaba da ke ba?" murmushi Aziza ta yi ta ce
"Au haba dai da gaske? Rainin babu dadi ne? To haka iyayenmu suke ji a ransu idan kika musu, balle ni da ba ki bani ko da kwana daya bane, kawai iskar duniya kika rigani shaƙa" Azima ta kyalkyale da dariya ta ce
"Macijiya Aziza me ya kawo ki wajena?"

Kallonta Aziza ta yi ta ce
" ZAREN SAƘAR DANA! WA ZA KI KASHE DA SHI!?" sake kyalkyalewa da dariya Azima ta yi ta ce
"Idan naki faɗi fa me zakiyi?"



"Sai na gwada ta wata hanyar!" Aziza ta faɗa tana mikewa tsaye, da sauri Azima ta mike ta ce
"Muje zuwa" tana gama faɗi ta hau ajijiya, Aziza na tsaye tana kallonta.



🍃🍃🍃🍃


COMMENT AND SHARE

BY
MOMYN AHLAN
[3/21, 12:31 AM] Fatima: 🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃

💥✨ *AZIMA DA AZIZA*💥✨
(🐍 _Macizai ne_🐍)


MALLAKAR.

*ZAHRA ABDUL(MOMYN AHLAN)*

SAHIBAR KAINUWA.


Littafin kuɗi, naira ɗari kacal dan masoyana, turo da kudinki ta wannan acct din
0096035983 balaraba hassan accees bank, ko kuma hoton kati ta wannan lambar 08165550116, pls ban da vtu.


Sanarwa.
Ga yan niger masu bukatar book din nan su tuntubeni dan sanar dasu yadda zasu biya kar ayi babu ku.


*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*

*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan*👇🏻

https://bakandamiya.com/group/71/kainuwa-writers-association

*____________________________________*

*MARUBUCIYAR.*
1- _HALITTA DAGA ALLAH NE._
2- _GUDU A JEJI._
3- _SHUHADA._
4- _NIDA ƘANNEN MIJINA._
5- _WA'YA KASHE ZAHRA'U?(#200)._
6- _COLONEL UBAIDULLAH._
7- _ITA CE ZUCIYATA(#200)._
8- _SAMIMA (MACIJIYA CE._
9- _GAWURTACCEN SOJA(#300)._
10- _DA NA SANI NA._
  11- _BADAWIYYAH_
12- _DEPUTY SUPERINTENDENT OF POLICE (DSP ALIYU HAIDAR)_
Now
13- _AZIMA DA AZIZA (MACIZAI NE🐍)_

_Follow me on wattpad,@Fateemah'0_


🍃🍃🍃🍃🍃

🤦🏻‍♀️🤦🏻‍♀️🤦🏻‍♀️
*KASSH! WLH ALLAH TAMBAYAR NAN TA ISHENI! TUN BAN SO NAYI MAGANA BA AMMA INAJI DOLE NAYI YAU
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On AZIMA DA AZIZA MACIZAI NE
avatar
ubaidah

4 months ago

Reply

The novel is very interesting and entertaining

Please Login or Register in order to submit comment