Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

kwallar data zubo mata.

Haka aka ja motar suka tafi suna fatan sauka lfy.

****

Da yake tsakanin Kano da jigawa ba wani nisa,Koda Tara tayi sun shiga garin,a irin hakan ne,malama Garba ya kalli malam Shu'aibu yace,"Amma fa munyi sauri,duk da ba wani nisa tsakanin Kano da jigawa,amma gashi har mun iso".

Yana shirin bashi amsa,Maryam ta saito bakinta tace,"wace jigawa Kuma? Badai wadda nakeji a state and capital ba? Kenan a filing jirgin jigawa zamu tashi?"duk ta jero wannan tambayar tana jiran amsa.......


_to readers Ku fada Mata gaskiya mana🀣_


*Gaskiya Naga ruwan comments jiya,na Kuma gode muku masoya Allah yakara kauna,Ku tayani addu'a Banda lfy wlh*



*Alkalamin khady* ✍
πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€

*_YAR CASKALE_*
( _Sanadin bakin uwa_)

*Ψ¨Ψ³Ω… Ψ§Ω„Ω„Ω‡ Ψ§Ω„Ψ±Ψ­Ω…Ω† Ψ§Ω„Ψ±Ψ­ΩŠΩ….*
____________________________________


*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🀝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________


1⃣1⃣-1⃣5⃣


Sai yanzu suka San sun tabka katobara na ambatar sunan garin da sukayi,Dan Haka dukansu suka kalli juna da ido kafin malam Garba yace,"wato malam Shu'aibu,Inka fahimci wani abu, shi zuwa madina a biyo ta jigawa sai Mai babban rabo,yanzu dai kaga sunan fa garinmu na asali shine bakada suna,amma yaran zamani suke kiranshi da Kano,bayan Kuma in zaka shekara cewa a kaika Kano bamai ganewa,inhar ka fita daga garin,sai dai kace a kaika kanoma,Kuma fa Inka sake mutum Bai gane ba kace ya kaika Kano to lamari ya b'aci,Dan gidan wannan mashahurin d'an yankan Kai za'a kaika wato d'an kano,dan Haka gara kawai kayi zamanka inda Allah ya ajiyeka".

Murmushi malam Shu'aibu yayi,danya fahimci inda zancen ya dosa,Yana shirin yin magana suka k'araso karamin kauyen,kofar gidan malam Jafaru mahaifin malam Garba.

Jama'ar garin sunyi murnar ganin malam Garba,Dan haka duk alamajiran malam suka shiga murnar ganin d'an malam d'in,dan ko ba komai Yana kawo musu tsarabar lemo da biredi,kun San dai k'auye,duk k'in ka da biredi ko baka ci,to idan kaje k'auye ka kwana biyu,wallahi saika yi marmarin biredi😜

Tunda motar ta tsaya malam Shu'aibu ya zagaya ya kwance Maryam a buhu,wadda ya zuwa yanzu ta jik'e da zufa,aikuwa Yana bud'ewa ta Fara rarraba ido,Nan idonta ya sauka akan tarin yaran da suka kewaye su.Zaro ido tayi kafin tace,"baba yana ganni cikin ba'kak'en fata,ba dai ta filin jirgin k'auye zamu tafi ba?"

Dariyar data bayyana hak'oransa ya yi ,sannan yace,"ai gurin bita muka kawoki,Kinga Yara can dayawa" yayi Mata nuni da tarin yaran dake zaune duk rike da alluna,sannan yaci gaba,"muna hanya aka fad'a Mana sai mun Fara kaiki gurin bita tukun,Dan haka muka kawoki anan in kin Gama haddace komai saiku wuce kawai,lokacin ma yarinyar ta k'ara girma ko?" Ya karasa maganar Yana shafa kanta,kafin ya kamo hannunta suka fito,yayin da suka doshi rumfar da malam Jafaru yake.

****

Duk abinda yakamata ayi Kuma su Sani dangane da zaman Maryam anyi,Kuma Alhamdillah duk malam Shu'aibu ya gamsu,bayan sun gama ganawa akace a dauki jakar Maryam a shiga da ita ciki.Duk k'iriniya da rawar Kai da Kuma son ke ta hazo na Maryam Saida ta zubda kwalla da babanta zai tafi,bayan yayi Mata nasihan ta daina rashin ji da sauran k'iriniya,ta tsaya tayi haddarta Dan ta kasance a 'yan tashin farko.Haka suka rabu bayan ya bawa malam kud'i yace a dinga bata intana bukatar wani abun.Kuma itama ya zaro nera goma sabuwa fil ya Bata,hakan ya d'an sanyaya ranta.

****

Bayan an shiga da kayan Maryam itama ta shiga gidan malam.Babban gida ne irin na k'auye Daya kunshi bangarori da dama,matan malam biyu,yayin da duk yaransa maza ne baida 'ya mace ko d'aya.D'akin da aka Kai kayan Maryam,d'akine da akayiwa kanta irin wadda akeyiwa almajirai maza,sai dai su abin birgewa harda katifunsu.kuma dakin duk da na kasa ne amma a lailaye yake da sumunti,Kuma an shimfida musu katon buhu,inda kusan duk Mai gata a cikinsu ita keda katifa,wasu Kuma bargo,wasu Kuma tabarmi,daki biyu ne irin hakan,yaran matasa ne 'yammata,sai Kuma irin su Maryam d'in,dan gaskiya kusan sune ma kanana.


*****

Matan malam akwai iya salame itace uwar gida kasancewar mahaifiyar su malam Garba itace matarsa ta farko ta ladan noma Allah yayi Mata rasuwa da dadewa,a yanzu dai salame uwar gida itace yaranta duk manya maza,Dan malam Garba shi kadai ne mahaifiyar sa ta haifa.Sai matarsa ta biyu Zuwaira,ita ma yaranta duk mazan ne,amma kuma sune kanana,duk da ta daina haihuwa,autanta bazai wuce shekara 8 ba.


Zaman gidan malam Garba shima zamane na kishi,irin kishin kauyen nan.sam matan Nan basuda mutunci yaran da aka kawo irin su Maryam,su keyi musu shara da wanke-wanke harda girki.Idan kaga suna haba-haba da yarinya,to sunsan 'yar masu dashi ce,iyayenta in sunzo suna musu abin hasafi,Kuma in an kawowa yarinya kayan dad'i suna sammasu.

Tun daga kawo kayan Maryam da suka bude sukaga kayane na dangin irin namu ya ku bayi,Nan suka hau gatsine-gatsine,basuyi Mata wata tarbar mutunci ba.

*****"************"******

A d'an wannan lokacin zamu iya cewa marayam ta sake,dan ba ruwanta da bakunta,sa kanta da tayi a zata keta hazo,yasa bata fara Nuna Hali ba,Kuma Bata Fara halartar karatun ba,tunda litinin aka kawota,malam yace ta huta zuwa asabar saita Fara daukar karatun.

A iya wannan kwankin Maryam ta Fara fahimtar halin matan gidan,tazama mage Mai kwanciyar daukar Rai,saika rantse Bata San wani abu Wai shi rashin mutumci ba.


Yau aka tashi a dakin su Maryam anyi sata,aikuwa Nan fa gida ya kacame aka shiga tone tonen kaya,dayake yarinyar da akawa sata,wata 'yar kaduna ce,Kuma 'yar masu dashi,sosai su Zuwaira suke karuwa da ita,hakan yasa sukafi kowa zakewa akan abin,nan ko suka shiga bincike kayan kowa,ganin Basu samu ba yasa salame tsayawa ta rike k'ugu tace" Ni fa gaskiya abin Nan akwai abin mamaki,tunda muke cikin almajiran malam babu Wanda yataba Mana sata,nidai inaga wannan yarinyar" ta nuna Maryam" inaga sata ta addabi jama'a da ita shiyasa suka dungumo ta suka kawota gun malam,Wanda shi kowacce tantariya a cewarsa zai iya da ita,to ai Sai ya zo yayi Mata kafi,tun kafin ta Gama damu".

Dafe kirji Maryam tayi tare da zaro ido tace,"Ni d'in ce barauniyar ko wata?"

Zuwaira ce tayi caraf tace,"uwar wace bakuwar zuwa da bamusan halinta ba inba ke ba".

Hawaye Maryam tafara yi sannan tace" Ni d'in Nan 'yar Karamar yarinya Dani Ina Zan iya wani sata,Kuma ma idan nayi satar abinda kukace Ni da Banda aljihu Ina Zan boye,wallahi tunda kukaimin sharri da banyi ba ma nayi d'in".

"Dan ubanki mu kike murgudawa Baki,sharri zami Miki ko me?"

Maryam dai batace komai ba illah kuka data Fara yi, a zuciyarta tana jin ita Tama fasa zuwa makkan tunda akayi haka,gara azo a koma da ita gida tama yiwa ummita dukan datace zatayi Mata.

Haka dai aka karaci tujarar aka gama,shi malam ma baisan abinda ke faruwa ba.

*****

Ranar asabar kuwa kamar yadda Maryam taga kowa nayi itama Haka tayi,duk da ta tashi da kewar yayanta Isma'il da Kuma mamanta,tace ba yanzu zata tuna babanta ba,su din dai ta damu dasu da son gani,Dan tasan yanzu da umma ta lakada Mata duka yafi a kirga.Ina sonki ummana ta furta a hankali.Dayake duk kusan 'yammata ne shiyasa bamai bi takanta bare har ya tabota.


Yau su Maryam an hallara a makarantar,rumfar malam ta cika,Yara da manya,dayake ya hada da yaran gari suna zuwa daukan karatun.


Kamar a boko Haka malam ya dinga wa Maryam interview,bai samu komai ba,illah fatiha,Dan itama da kyar takaita,yayi mamaki kwarai,inda yasata ajin Yara aka Bata allo da aka rubuta basin mi'a ra,aka ce ta Fara da nan.

Aji-aji abin nasu yake cikin tsari,Dan Haka ajin Yara aka kaita,duk da itama yarinyar ce,amma tafi son akaita cikin manya,aikuwa nan Saida ta bayyana a fuskarta Bata so ba.

Tana zaune amma ba karatun take ba,wata yarinya dake bayanta,ta bude murya tace "malam ga wata Bata karatu".

Aikuwa malam ya zaburo Yana fadin "wacece?"

Nuna Maryam tayi,aikuwa ya tsulawa Maryam bulala,har Saida yayi Mata bulala biyar,Yana jaddada Mata Nan ba gurin Wasa bane.Kema dagas Maryam babu ko hawaye, aikuwa ta rasa me zatayi wa yarinyar ta huce,Nan ko ta dage ta gallara Mata mintsini,yarinya ko ta callara ihu,ko kafin malam ya juyo wata ta bude Baki da niyar Kai Kara ita data kusa da ita,aikuwa ta Maryam ta ankara,ta Kama kawunansu ta gwara,Suma ko kukan suka saka,Nan da Nan tahau rankwashin yaran da Kuma gwarawa wasu kawuna,kukansu ya karade ko'ina Wanda ya jawo hanakalin malam d'in,dama sauran wadanda ke karatu.

Ganin malam yayo gurin da Dan ganin duk yaran sun rude yasa ta kwasa da gudu tayi cikin gida,Wanda tana shiga dai-dai salame ta gama miyar dumamen tuwo,Dan jiya miyar karewa tayi,shine malam yanzu ya Aiko yace a bashi dumame Dan hantsi yayi yunwa yakeji,shine salame gimbiya tace yadan dakata Babu Miya za'ai sabuwa,yace to a kada Masa miyar kubewa,aikuwa tana saukewa Maryam na shekowa,akuyar dake tsaye bakin danga ta zabura tayi ciki da miyar Maryam na bayanta,aikuwa har wani salo miyar ta bayar gurin zubewa ji kake lemmmmmmmm........




_nagode da addu'arku Alhamdillah,Ina sonku sosai fans,Naga comment dinku ya girgiza zuciyata,da yasa nayi Mana addu'ar Allah yakara kauna.



*Alkalamin khady* ✍
πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€ πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€

*_'YAR CASKALE_*
( _Sanadin bakin uwa_)

*NΓ€*

*KHADIJA USMAN*
( _Real Tame Gari_ )



*Ψ¨Ψ³Ω… Ψ§Ω„Ω„Ω‡ Ψ§Ω„Ψ±Ψ­Ω…Ω† Ψ§Ω„Ψ±Ψ­ΩŠΩ…*
____________________________________


*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🀝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________


1⃣6⃣-2⃣0⃣


"Kam balastin!" salame ta furta a fusace,hakan ko ya jawo hankalin Zuwaira dake d'aki tana magana da yaranta.Dukansu tsaye sukayi suna kallon maryam,wadda ta tsaya wuk'iiii tana kallon kowa.Ganin hakan yasa salame yo kanta tana fad'in"yau Banga shegen Daya Isa ya hanani cin uban yarinyar Nan ba,Ni dama tunda aka kawota Bata kwanta min ba Dan Haka yau sai kinsan kin taba salame".

Shan gabanta Zuwaira tayi tana fadi'in"ah ah salame,gara ki Kira malam ki fad'a Masa,dan kin San Bai bamu izinin dukan dalibansa ba,Dan Haka Ni ba ruwana".

"Dayalla gafara can tsohuwar munafuka,wato Dan ba miyarki aka zubar ba shine Zaki ce kada in daketa,ke uwar tausayi,harda wani yen yen yen! Mayam jeyi fata" tayi maganar tana kwaikwayon Wai maganar zuwaira.Dan haka saina daketa wallahi".

Tsalle Zuwaira tayi taci d'amara tana fad'in" Ni Kuma zanga uban dazai tab'ata,miyace an zubar,Kuma ma ai akuyar lado ce ta zubar kibi akuyar Mana ki daka in gaskiya kike bi".

Aikuwa Nan hayaniya ta kaure,yaransu ma suka shiga cikin rigimar,itako Maryam tana tsaye gefe tana kallonsu,ganin sai cacar Baki sukeyi sunki suba hammata iska yasata fad'in"mu in zakuyi kuyi dan Allah kubar sa Mana rai,nagaji da kallon tsohon yayi".

D'aya daga cikin yaran malam me suna Idris ya kalli Maryam yace"A daina sa muku rai da me?"

"Da fad'an Mana,in zasuyi suyi kawai musha kallo".Suna Shirin yin magana sukaji sallamar malam da gyaran murya,Nan da nan kuwa kowacce ta nutsu,dan duk bala'insu,to yanayi musu kwarjini kuma basayi a gabansa,Dan haka suka nutsu kowacce taja baya.

Tsayawa yayi Yana Kare musu kallo kafin yace "Ku kuma lfy naganku tsaye kamar tab'are?"

Zuwaira ce ta gyara tsaiwarta sannan ta ce,"wallahi malam gara da Allah ya kawoka,wai fa wannan 'yar kwiciciyar yarinyar ce,sabuwar dalibarka,ta shek'o da gudu inaga ko Kashi takeji,shine tsautsayi yasa tabi takan miyar da Yaya salame tayi,to shine fa tace yau saita Mata mugun bugu,shine na hanata nace tabari idan kazo ta fad'a maka,shine ta taso zata dakeni".

"Ke uwar 'yan sharri!cewar salame,ni d'in ce nace Zan dakeki,to in dakeki ince na daki wa?"

"Kin daki uwarki,shegiya Ni Zaki tambaya ma in kin dakeni kice kin daki wa? 'yarki ce ni ko k'anwar ki,in kina ganin damata ko zamu gwada ne.Jin hakan yasa salame fusata suka kacame da dambe.Su malam da ke gefe sai sukaja da baya,Dan wata mulmula da akayi da Zuwaira ji kake makkkkk an maka ta da k'asa.Ganin hakan yasa Maryam rugawa da gudu, ta dauko wata k'arama da wani sillen Kara tazo ta tsugguna saitin inda aka tΓ ushe Zuwaira,ta shiga kid'a tana fad'in"jaruma! Jaruma! Baba Zuwaira jaruma! Wannan kid'an ya fargar da Zuwaira taji wani sabon k'arfi,aikuwa saita juye da salame ta shiga kintsimar ta,ganin haka yasa yaran sukayo caaa! malam ya dakatar dasu,Babu wanda ya raba su,malam ya Hana,saida suka gaji sannan suka Bari,bayan an daddaki bakin juna.Kuma har wannan lokacin maryam bata daina kid'an ba.Sai da kowacce ta koma gefe tana mayar da numfashi, itako Maryam ta janye fanteka gefe ta zuba musu ido bayan ta tallafe fuskarta da duka hannuwanta biyu.


Shi kam malam baice dasu komai ba,illa zuwa da yayi ya kama hannun maryam yaja ta itako batare da Nuna tsoro ba ta bishi,Dan tasan dai bazai wuce ya daketa ba.

D'akinsa ya nufa da ita,batare da yace da ita komai ba ya zaunar da ita Kan wani buzu dake gefe.Wata jaka ya jawo ya dauko wani daurin magani ya jawo wani kwano ya dauko d'aurin rubutu ya tsiyaya a Kofi ya hada da wannan maganin.Yakai wajen minti biyar Yana Kara tofa addu'a a ciki,sannan ya mikowa maryam yace ta karba tasha.

Zaro ido waje tayi sannan tace"miyau d'in zansha malam?"

"Wane irin miyau Kuma maryama,bakya ganin addu'a nayi miki,Dan haka yi hakuri karbi Kisha kinji mairoro" ya fad'a Yana Mata alamar rarrashi.

Karba tayi takai bakinta da niyyar sha sai Kuma ta dawo dashi tace"tsakaninka da Allah malam ka wanke bakinka kafin kayimin addu'ar Nan?"

Yak'e malam yayi yace "nawanke Mana baki gani ba tun safe nake asuwaki".

"Tab da da asuwakin safe zaka tofeni wallahi bazan Sha ba" ta fad'a tana dungurar da kofin.Duk yadda malam yakai ga lallaba ta kin Sha tayi,hakan ko ya fusata shi,Saida ya dauko wata narkekikiyar bulala wadda yake maganin irin su Maryam da ita ya zuba mata,.Duk yadda ta Saba da duka Amma taji wannan bulalar ta dabance,aikuwa ta shiga canyara kuka,shi kuwa Saida ya tabbatar tayi laushi sannan ya kyaleta Kuma bayan ya tabbatar ta shanye rubutun,ya fada Mata da niyyar da zata Sha a zuciyarta amma sai cewa tayi a zuciyar tata"ka da Allah ya shiryeni".

**************


Wannan dukan da malam yayiwa maryam Saida ya sata zazzabi,dayake kusan d'aliban suna da had'in Kai a wannan fannin Kuma ganinta k'arama yasa suka kula da ita.Babanta yayo Mata aike amma baizo ba hakan yasa ta samu k'arin wasu kayayyakin,wanda suke masu dadi,duk da take yarinya Amma ta lura da halin matan malam,Dan Haka saita Zama zakara me neman suna bada kwaya kaci tsakuwa,hakan yasa suka d'an Fara janta a jiki,duk da su a tsakaninsu babu wata jituwar kirki.


Tun dukan da malam yayiwa maryam yasa ta nutsu,Nan shida kanshi malam ya Kira babanta Yana Masa albishir da ci gaban da aka samu,nan kuwa ya Nuna farin cikinsa har yake fadawa huwaila,wadda tace in an kwana biyu zasu zo suga Maryam din.

************************

Yau ta tashi da niyyar aiwatar da kudurin dake ranta,Maryam yarinya ce Mai ra'ayin rik'au,batada hak'uri Sam,duk da batada yawan shekaru,amma tanada akidar rama abinda aka Mata,sannan ga bak'ar mugunta a gun Yara sa'anninta,Sam batada tsoro ta Saba da duka da zagi,hakan yasa duk wani duka ko hargagin mutum baya tsoratata.

****
Duk da irin kyautar datayiwa su salame,hakan baisa sun barta haka ba,Saida suka bi suka k'ara da wasu abubuwan a gabanta,Dan Haka tace Suma sunci bashi.


Laraba me d'an bagalaje,irin narka-narkan matan Nan ne,saboda ma girmanta yasa tak'i auruwa,Dan gaskiya ita d'ince komai nata na musamman ne,hakan yasa dataga tak'i auruwa,saita Fara sana'o'i kala-kala,da sana'ar cikin gida takeyi,to kun San matan aure da cin bashi,yazamana idan mace taci bashinta,har gidanki har dakinki zataje ta jawo ki,in kin Bata kudinta kin tsira,in Kince Babu kuwa,Nan zata kamaki kamar 'yarta taita jibga,har sai anzo an kwaceki,hakan da takeyi ne yasa duk aka daina siyen kayan ta.Saita yanke shawarar komawa sana'ar yara,Kuma da biyar goma tana samu abinta.Tunda Maryam tasan da ita duk wani tattalin arzikinta ya Fara k'arewa a can.

Yauma can ta nufa,tana zuwa kuwa laraba tahau washe Baki,Dan jininsu ya had'u Dana maryam,aikuwa ta tsugguna tana me kokarin bude murfin da aka rufe farantin d'an malele,Saida ta k'ara zambada yaji a iya Wanda zata iya siya,dayake yau batajin cin d'an ba galajen ,d'an malelen take sha'awa,kuma gashi yau yajin laraba yasha kafi zabo yayi chauuu dashi.
Jin cikinta kamar ta shafa mota ga wani mugun kwadayi datakeji,ji take idan aka Bata farantin d'an malelen tana iya cinye shi.dan haka ta gyara zamanta saman wani d'ab karamin dutse tace,"Anti laraba kin San me?"

Dai-dai tana make wata yarinyar data siyi d'an malele ta tsaya lasar faranti tace" sai kin fad'a mairo?"


Gyara zaman ta kumayi sannan tace "Wai malam naji yace Yana sonki".Tsabar farin cikin Jin wannan kalmar me tsada yasa laraba ta saki Baki da hanci ta kasa motsi,illa jawo hannun yarinyar data make yanzu da tayi ta dan gwarar da ita,da kyar ta iya bud'e baki tace "cinye duka"Aikuwa yarinya ta gyara Zama tana washe baki,ganin haka yasa itama Maryam matsowa tana saka hannu suka hau cin d'an malelen,yayinda laraba take fad'in" taho farar yarinya me farin labari ki k'ara fad'a mun inji a wane kalar yanayi ya furta Miki Yana so na"

"Um um Anty laraba, Bari in gama tukun"sam laraba tak'i barin Maryam ta sake da cin d'an waken,fad'i take ta taso inta Gama Bata labarin zata yi Mata Wanda yafi wannan dad'i,amma Sam Maryam tak'i bari.Ganin haka yasa laraba tasowa cak tayiwa Maryam daukar jarirai ta zauna ta d'ora ta bisa cinyarta tana fadin,bani labarin malam ja'afar d'ina ta fad'a tana karkada ido".

"Nidai gaskiya Anty laraba ki daina marmar da idon Nan kina tsorata ni kamar fa zabi yar aljana haka Kika koma".

Duk da taji haushi amma Dan Jin ance ana sonta ta maze tace to na daina fad'amin kinji,Dan in munyi aure da malam bazaki k'ara kwana d'akin Nan ba,sai d'akina kece 'yar tayin kwana na".

😳"amma ba gado d'aya zamu rink'a kwana ba dai ko?"

"A gado d'aya mana,ai Ni yanzu banida wadda ta fiki".

"Har babarku da babanku?"

"Eh Mana,yanzu dai tashi muje nayiwa malam girki me dadi,ki tafar mishi da shi".

Aikuwa suka rankaya gidansu laraba,ranar ma danba galajen harshi kyautar shi ta bayar.

Danwaken fulawa tayiwa malam,aka daka Masa had'ad'd'en yaji Wanda yaji onga,itama Maryam an sammata nata nana ta k'ara ci ta sud'e kwano sai kace me cikin zani.


Cikin kwanukan da aka d'ebi shekaru ana tarawa Dan jiran ranar aure.Ciki aka dakko falleliyar langa aka zubawa malam a ciki ,har Maryam ta d'auka zata tafi saita ajiye.Da sauri laraba ta kalleta tace "tawajena ya akayi ne?"

"Ba komai,kawai jinai bazan iya Kai Masa bane,abin yayimin nauyi"

Da sauri laraba ta matso tana fad'in"haba 'yar d'akina ,taimaka kikai Masa,kice Masa Nima Ina sonsa ungo wannan ma,ta ciro naira ashirin ta Bata, aikuwa Nan da Nan Maryam ta d'auka ta fice.Laraba dake tsaye mamanta na tayata murna kawai saita buga tsalle,Amma abin mamakin ko rabuwa da k'asa batayi ba,illa mazaunan ta da sukayi sama da k'asa da Kuma teb'arta datayi rawa.

***********************

Tana shiga gidan cikin sa'a ta Sami duk ahlin gidan a hallare,aikuwa gaban Zuwaira taje ta mik'a Mata d'anwake,Koda Zuwaira ta bude ta gani nasha-nasha da Mai,babu tambayar daga Ina,kawai tahau juyawa tahau kasaf ta shi,bayan ta jefa biyu a bakinta tana fad'in "um um um,gaskiya kowace tayi d'anwaken Nan ta kwararriya ce",Nan ta mikawa kowa ya d'auka.

Saida kowa ya cinye ana sid'e hannu sannan salame ta juyo ta kalli Maryam,wadda Dan tsabar dadin da d'anwake yayi,an Manta da ita data kawo a rabo ko Bata ba ai ba,tana gefe tadau wani siririn Kara tana Wasa dashi a k'asa taji salame nacewa"'yar albarka Ina Kika samu uwar d'aki harta Baki wannan danwaken,Dan nasan wannan na musamman ne".

Batare data d'ago daga abinda takeyi ba tace"budurwar malam ce"

Wata irin kwarewa Zuwaira tayi,wadda tasata Fara kelaya Aman danwaken dataci,itako salame cewa tayi "wane malam din Kuma?"

Saida Maryam ta d'ago wannan karon,harda cewa zuwaira,"sannu baba" sannan tace "malam Mana,Daya dakeni rannan a dakinsa,malam dai na Nan gidan,baban su Idiris".

Cikin hargowa da bala'i dukansu suka shiga fad'in,malam yaci amanarsu wace shegiyar ce wannan,harda Masa girki,wato shiyassa yau yak'i cin abinci yace a koshe yake,ashe dama abincinta yake jira,aikuwa yau zaizo ya samesu,Nan suka kalli maryam sukace ta fada musu wacece ta aikota.

Cikin ko in kula tace" laraba tirela"

A tare suka dafa kirji suka maimaita "Laraba tirela fa kikace!"

Hakan yayi dai-dai da shigowar malam Wanda Bai San wainar da ake toyawa ba yace "me laraban tayi naji ana Kiran sunan ta..........."




_kuyi hakuri wallahi Banda lafiya ne,Amma nasami sauki Amma ban warke ba,insha Allah idan na warware zaku jini sosai_



*Alkalamin khady* ✍
πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€ πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€

*_'YAR CASKALE_*
( _Sanadin bakin uwa_)

*NΓ€*

*KHADIJA USMAN*
( _Real Tame Gari_ )



*Ψ¨Ψ³Ω… Ψ§Ω„Ω„Ω‡ Ψ§Ω„Ψ±Ψ­Ω…Ω† Ψ§Ω„Ψ±Ψ­ΩŠΩ…*
____________________________________


*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🀝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________

2⃣1⃣-2⃣5⃣



_Hakika masoya basa taba k'arewa a rayuwa,Allah yak'ara k'auna da zumunci amin_


_Gasikya ba abinda zance muku sai godiya_

*TAME GARI FANS NOVEL,1,2,3*
*KAINUWA FANS*
*HAUSA NOVELS GROUP 1,2*
*HAZAK'A GROUP*
*KOMAI DA RUWANKA GROUP*
*MUTUNTA JUNA GROUP*
*MASOYA NOVELS GROUP*
*MUK'ARU DA JUNA GROUP*
*KOWA NAMU NE GROUP*
*Kai alk'ur,an Kuna da yawa bazanma iya lissafa ku ba,dukka wadannan groups din,sune Kan gaba wajen yimin comment,nagani Kuma nayaba na Kuma gode,Allah yabarmu tare yabamu aron rai da lafiya*

_________________________________

Dukansu shiru sukayi suna huci.Shikuma cikin rashin lura da yanayin su yak'ara cewa"nace me laraban tayi ake Kiran sunanta?fatan dai ba wani yaron bane ya tsokano ta,Dan ni bana son rigimar yarinyar nan wallahi".
Tsaki salame taja sannan tace"dama Ina zaka so Yara su tsokano amaryar ka,tunda kasan abinda ka k'ulla,ashe shiyasa kwana biyu in an kawo maka abinci sai kace ka k'oshi,dama kasan inda kake zuwa kake cika cikinka,to asirinka ya tonu yau d'in nan,Kai inba ma rashin Sanin kala ba,me zakayi da laraba tirela, yarinyar da naji Yara na fad'in da daddare tifa take Zama,shi ne Kai zaka je ka kwaso Mana ita ko,duk tabi dare ta markad'e mu ace munyi hatsari da safe,to nidai wallahi zan furta haram,kawai ka sakeni nace astagafirullah daga baya" ta k'arasa zancen tana girgiza.Itama zuwaira ta amshe da fad'in" kema kenan Yaya da kukayi aure tun zamanin k'uruciya har aka girma tare,bare ni sabuwar zuwa wadda ko yau ya shek'e zan iya aure in haihu,da dai a auromin laraba tirela a matsayin kishiya,wallahi na gwammace a kaini gidan mahaukata in dinga musu burushi".

"Wai ni duk ku tsaya"ku wane munafikin ne yace muku zan k'ara aure,auren ma Kuma Wai yarinyar Nan laraba, yarinyar da aka Haifa a gabana".
"Oho dai,ko ma dai Kai ka karbi haihuwar mudai bazamu yadda ba"cewar zuwaira,"Dan tun yanzu anayo maka wannan zazzak'an girkin Ina zaka iya hakura"

"Wane girki Kuma? au shi munafikin har ce muku yayi tanayo min girki kenan?

Samiran da aka kawo d'anwake salame ta dauko ta dungurar a gabansa tace"ga shaida Nan ai Kuma ga Maryam Nan ka tambayeta Dan ita ta aiko"
"Hummm! Kawai malam yasami zarafin cewa,Dan ya lura yau sharri matan nasa sukeji,Dan Haka ya juya ya kalli Maryam dake zaune saman wani d'an dutse tana gwagwiyar taura yace"ke maryama waya Baki abinci ki kawo,Kuma wa akace ki kaiwa kikayi batan Kai Kika kawo Nan?"
Saida ta tsotse kwallon ta yar sannan tace"Anty amarya ce tabayar a kawo maka,Kuma tace Wai kazo da wuri yau tunda ba makaranta,sannan Wai in fad'a maka,malum- malum dinka dakaje da ita rannan ita zakasa Wai kafi kyau,saika koma kamar halifa d'anka,sannan Wai ka tafi Mata da lemon Nan na jarka irin na jiya Wai taji dadinsa,Kuma Wai maganar kazar baba Zuwaira dakace......" Uban babanki!πŸ™Š Malam ya furta a fusace bayan yayo kan maryam,wallahi kedai wannan ba k'aramar jaraba bace,ashe shiyasa aka had'oki aka kawomin ke,dayake uwarki 'yar k'aramar hukumar Gama ce,shine Kika zo ki gama ni da iyalina tun kin 'yar kankanuwar ki Ina ga kin girma Kuma,gashi marabina da ashariya tun banfi shekara shida zuwa bakwai ba,harna manta harrufan da ake hadawa ayi zagi,amma yau gashi kin sa na tunosu a guje,Dan haka yau sai jikinki ya fad'a miki,sai kin furta da bakinki cewar karya kike".

Dukansu suka Sha gabansa suna fadin yafara bugunsu kafin ya daki Maryam,danta Fadi abinda yake boyewa shine zai musu borin kunya.Hakan ya Kara fusata
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment