Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

sai mu sami zarafin tanka maka.

Ran malam ya ɓaci dan duk abin matan nasa,bai taɓa fuskantar irin haka dasu ba,ko rikicin su sukeyi in yayi musu tsawa suna shiga taitayin su,amma ya fuskanci yanzu raini ya shiga tsakaninsu,dan haka cikin kakkausar murya ya shiga yi musu faɗa.Babu wadda ta tamka masa a cikin su,dan sunga ɓacin ran da basu taɓa gani ba.jin yana faɗan amma a cunkushe ,yasa Zuwaira ɗagowa da nufin bashi haƙuri,aikuwa tayi katari da fuskar malam.

😳zaro ido tayi,sannan ta kalleshi cikin sauri tace" Ala gafatta me ya sameka a fuska haka?"

Salame da maganar Zuwaira tasa ta kallon malam ɗin itama,aikuwa saita sheƙe da dariya ta shiga tafa hannuwa tare da rangaɗa ƙaramar guɗa "lallai wani kaya sai amale,wannan shi ake kira tafashi kaɗa miyar farin shigar girki,Ni da mandali,lallai yau malam kasan kayo aure, ashe mu duk sauƙi muka biɗar ma yau kayi babban kamu,ah lallai na yadda namiji baya tsufa da son duniya da yin ƙara'i,amma inba haka ba ina sauro ina Giwa,Ni wallahi na ɗauka ma yadda wajen yake haka cikin ma,ashe hangen dala bashi ne shiga birni,su ƙuda an tafi kwaɗayi gashi nan ana shirin gamuwa da ajali" ta ƙarasa zancen tana dariyar shakiyanci.

Cikin rashin fahimta Zuwaira ta kalli salame tace"wai ni yaya me kike nufi da Waɗan nan maganganun naki ne?"

Dariya salame ta kuma sawa kafin tace"haba zuwai sai kace ƙaramar yarinya,ki kalli Ala gafatta da kyau zakiga hannun mata ya shiga aka sashi a kwana,ki dubi can,tayi mata nuni da kan igiyar da Laraba ta shanya kayan ta,ai da gani kin san kwanan zancen,dan haka malam Barka da arziki dan an samu abinda ake nema,sannan kuma Barka da tsira da rayuwa...." Bata ƙarasa ba malam yakai mata wani harbi da ƙafa ta kauce da gudu ta faɗa ɗakinta,itama Zuwaira hakan tayi,yayin da malam ya shiga masifa yana ball da komai na gabansa.Nan ma salame ta leƙo tana faɗin "ina ni ina tsayawa sabon ango mai ji da ƙarfi ya bugeni,ah ah bada ni ba,kai dai ka tsaya ayi maka inda bazaka iya ramawa ba,amma mu bazamu bari can a ɗime ka ba ,mu kuma kazo ka rama a kanmu" nan tajawo windon ta rufe ruff ganin malam ya nufota.

Shikuwa malam yarasa meke damunsa kwanakin nan,"anya kuwa ba yarinyar nan ce Maryam ke da aljanna ba tabar kanta ta dawo kaina ba".tabbas da sake,dan haka dole yaje yayiwa kanshi ruƙiya yanzu.

A hanyarsa ta shiga ɗakinsa na zauren ya haɗu da Maryam zata shigo"cikin daka tsawa yace"ke Dan ubanki daga ina kike?"

Gyara tsaiwarta tayi sannan tace"Anty Laraba ce ta aikeni wai inyo cefane a dafa maka kaza?"

"Au to to Haka ne, i maza kikai mata dan nasan tana can tana jiranki hanzarta" harta juya da ledar dake hannun ta sai.kuma tace"to baba malam ta yaya zaka ci naman? Naga kaji ciwo a bakin?"

"Ke ban son shegantakar banza,idan an dafa kya ga yadda zanyi inci tunda ai ba bakin aka ciremun ba"

"To idan tayi yaji fa?" Ta jefo masa tambaya."Ko uban yaji tayi ba abinda zai hanamin cin naman nan".

"To idan.......,ke jakar ubanki nace,zaki wuce kikai kayan miyan ko kuwa saina zo,wallahi kadai wannan wannan yarinyar da magana a gurin nan,kima je ki haɗa kayan ki,dan nasa faɗawa ubanki yazo ya ɗaukeki,dan haka ki zama cikin shiri".

Batare data ƙarasa saurarar abinda yake ƙarasa faɗi ba tayi cikin gidan da gudu.inda bata zame ko ina ba sai ɗakin Laraba,ta tarar tana shara nan ta samu guri ta zauna ta miƙawa laraba ledar dake hannunta tace inji malam yace a kawo mata.Cike da farin ciki Laraba ta kaɓar,ko da ta buɗe sai taga rogo,aikuwa tayi murna dan ta kwana biyu bata ci ba,nan ta baje tace Maryam tazo suci tace ta ƙoshi,itako ta cinye abin ta dan dama yunwa takeji.Sai da ta gama nan Maryam ta kalleta tace"Ina na baba malam ɗin?"

"Me kenan?"cewar Laraba.

"Rogon mana,ce Miki fa nayi ki raba biyu ki ajiye masa nasa".

Cikin marairaice murya Laraba tace"wallahi banji ba,amma kije gida kicewa babarmu ta dafowa malam rogo"

"Kam bala'i, cewar Maryam,ai wallahi ba ruwana dan kafin ma inje gidan ai yazo ya tambaye ki,kije kice masa nice ban faɗa Miki ba,ya dakeni Ni kuma inda ya sakeki,kawai ki tashi ki kamo wannan kazar taki budurwa a dafa masa,dan dama dazan shigo naji yana cewa wani abokin sa shi kaza yake son ci,mai romo da ɗan yaji-yaji.Yauwa wai ni Anty meye yasameshi a baki naga ya daddauje ya kuma kumbura?"

"Wallahi faɗuwa yayi ina faɗa Miki, kwanukan Nan Kuma na jere suka faɗo masa,danma na shafe mishi da minsileta na gasa masa da ruwan ɗumi"

Dariya Maryam ta shiga yi tuni muguntar Tata ta motsa,jin wai babanta zaizo ya tafi da ita,ai yaseen saita yi na karshe.Dan haka ta kalli Laraba tace"Ai Anty ba minsileta zaki shafa masa ba, Wannan baya warkar da ciwo da wuri,loko zaki kawo a siyo masa,sai ki shafa masa yanzu kafin kazar ta dahu Kinga ya ɗan ji dama saiya cinye kayar sa,amma yace irin ta rannan yake so wadda tayi masifar yajin nan"

"Ke Maryam yaushe yace Miki haka,bayan kince abokin shi yake faɗawa".

"To ai nima bance Ni ya faɗawa ba,ji nayi nima,dan haka tashi mu kamo kazar in tafi da ita bakin kasuwa a gyarota, sai in taho Miki da lokon daga can harda ma kayan miya.".

Haka ko akayi suka kwamuso kaza,sannan ta bawa Maryam kuɗin gyaran dana loko dana kayan miya🤣




*Alƙalamin khady* ✍
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀

*'YAR CASKALE*
( _Sanadin bakin uwa_ )



*NA*

*KHADIJA USMAN*
( _Real Tame gari_ )



*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*

*🌈🇰AINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*



5⃣3⃣-5⃣4⃣


_________________________________

*ALHAMDILLAH! Wannan shafin dukansa sadaukarwa ne ga Admin of admin wato yaya Hayat,ina farin cikin tayaka murnar ƙara shekara, Allah yaƙaro shekaru masu albarka,arziƙi da dukkan nasaran rayuwa,kasancewa cikin amincin Allah da tabbatar dukkan alkhairinsa* _HAPPY BIRTHDAY TO YOU YAYA HAYAT,ADMIN OF ADMINS_ 🎂


_____***************_____


A taƙaice dai,saida Maryam ta taya Laraba duk abinda Yakamata,idan tayi wani abun sai Maryam tace baiyi ba ta gyara,haka dai ta biye mata har suka gama dafawa malam kaza mai yaji da romo.
Wanka kuti Laraba ta ɗauka,Maryam ta callara mata ɗaurin ɗan kwali,tace irinshi mamanta takeyi in tayi kwalliya,ta taɓa tambayar mamanta ya sunan ɗaurin,tace mata ɗaurin fati Muhammad.Haka dai tasa Laraba a kwana.

Babu yadda Maryam batayi ba akan Laraba ta bata naman nan takai wa malam,amma Laraba tace ah ah,ita zata kai masa da kanta.Hakan yasa Maryam nuna jin haushinta amma sai taga wannan karon Laraba ko'a jikinta,hakan yasa ta tashi ta koma gefe tana ta tunanin yadda zata ɓullowa Laraba taci naman nan,dan Laraba wannan karon kai tabawa Maryam ita kuma taci ƙafafun ta ajiyewa malam kaza sukutum.Da farko Maryam bata damu ba da Laraba ta bata kai,dan tasan ita zata cinye kusan rabin kazar ko duka ma,sai kuma gashi Laraba ta gwanya mata.
Haka taita saƙa wa lokacin Laraba ta shige ɗaki,dan haka ta ta tsaya jiran ta fito.Koda Laraba ta fito da hijabinta tana niyyar sawa nan Maryam ta tareta tana faɗin"ai karma ki wahalar da kanki Anty,yanzu malam ya aiko yace a faɗa miki gashi nan shigowa.Jin hakan yasa Laraba saurin ɗaukar langar ta ƙara gogewa ta faɗa ɗaki,tare da ɗauko turaren ta samfur ɗin wanda na faɗa muku a baya ta ƙara fesawa.Itako Maryam tashi tayi ta nufi ɗakin zauren na malam.sallama taitayi amma shuru ba'a amsa ba,kawai saita yanke shawarar leƙewa taga ko baya ciki ne.Tana yaye labulen ta hango malam lulluɓe da bargo yana hayaƙi,sallamar ta kumayi, nan ya yaye duk ya haɗa zufa da kyar ya amsa mata,"Baba malam meya same ka? Ko bakin naka kake gasawa ne da hayaƙi?"

A kaikaice yake kallonta a zuciyarsa yana faɗin"kaji min shegiyar yarinya,ko ma meye ai ke nake yiwa,dan idanma aljanar kanki ce ta dawo kaina to na mayar miki abarki, kuje can ku ƙarata da iyayenki,dan gobe goben nan kina gidanku i War haka,ko ubanki bai zo ba Ni zan kaiki"amma saiya saki murmushi yace,"Eh bakina nake gasawa ko na ɗan ji dama".

"To da zafi ne naga ka kwaɓe fuska zakayi kuka?"ta jefo masa tambaya.

"Yaushe zanyi kuka kuma Maryam?" Ya faɗa yana ƙara faɗaɗa murmushin sa".

"Gashi nan yanzu ma ka ƙara alamar kuka zakayi da yawa".Sai yanzu ya lura da abinda take nufi,wato murmushin dayakeyi shine kukan,nan da nan ya mayar da fuskar ya haɗe sannan yace" ke tashi ki bani guri dan gidanku,ba nace ma ki haɗa kayan ki ba,me kika tsaya yi kuma har yanzu.

Gyara tsagunnon tayi tace"dama Anty Laraba ce ta aikeni nayo mata cefane,nakuma kai kaza aka yanko tayi maka farfesu,shine yanzu ma tace inzo in kiraka,ince maka komai ya kammala"

Murmushin yakuma niyyar yi,tunawa da abinda Maryam zata kuma faɗi saiya haɗe kayansa yace"ina nan zuwa kinji jeki faɗa mata".

Aikuwa da sauri Maryam ta koma ta faɗawa Laraba cewar ga malam ɗin nan shigowa fa,bayan ta sanar da ita wai ta ɗora ruwan ɗumi taƙara gasa masa bakin.
Haka Laraba ta tashi da ɓarin jikin ta ɗora ruwan ɗumi,shikuwa malam bai samu shigowa ba dan yaga magariba tayi saida ya tsaya yayi sallar magariba da ishsha.

Itako Maryam koda tabar ɗakin laraba ɓangaren matan malam ta tafi,babu wadda ta kula ta,dan sun san 'yar ɗakin Laraba ce yanzu.Ganin nan ɗin babu wani farin jini,yasa ta koma ɗakinsu gurin 'yan uwanta,nan suka shiga hira har magariba suma kowa ya tashi yayi sallah.

Ko da malam ya shigo ya tarar da wannan Gara,ga ƙamshi nata tashi,saida ya lumshe ido,tare da haɗiyar miyagu,duk da bakinsa da ciwo,amma zaisa yanzu a ɗan ƙara gasa masa dan yaji daɗin cin abinda aka dafa masa,sai ma ya gama cin daɗinshi zaije yayiwa su salame rashin mutunci,danya lura yanzu sun raina shi wallahi.Cike da ladabi Laraba tayi masa sannu da zuwa,bayan ta idar da sallar ta,aikuwa ya amsa cike da jin daɗin siririyar Muryarta.Nan yasamu guri ya zauna a kan tabarmar da aka shimfida,babu ko jiran a gabatar masa da abinda ke kwanon yace" Ɗan taimakamin ki sake gasamin bakin nan kafin inci abin nan ko naji dama-dama".

Cike da ladabi ta amsa da "Toh yallaɓai"(cikin salon da mamanta ta koya mata,da sunan da yayarta tace ta dinga faɗa masa dan jan hankali🤣)miƙewa tayi ta fice,yayinda malam ya bita da kallo yana kallon yanda kayan masarufi ke motsi😜.

Haka dai harta dawo da ruwan ta ajiye ta ɗauko tsumma ta zauna gefensa,yayinda ta shiga ga sa masa a hankali tana masa sannu.Sai da ta gama ga sa masa sannan ta fito da lokon dake kan cinyar ta ta buɗe.Kallonta yayi yace"Amarya ba'a barin man nan kuwa sai nazo kwanciya a shafa,dan kinga abinci ai baya ciyuwa da maiƙo a baki ko".

Mayarwa tayi ta rufe tana murmushi,yayinda ta buɗe masa murfin kwanon da ƙamshin daddawa ya bugi hancinsa,nan ko ya jawo kwano tare da jawo dankwaleliyar tsoka yasa a baki.Tsananin azabar da yaji yasa shi haɗiye naman tun bai gama tunawa ba.nan ma naman ya tsaya masa a wuya yasashi wata kwarewar data sa Laraba miƙewa da sauri ta bashi ruwa.Har naman ya wuce bai daina jin raɗaɗin a bakinsa ba,dan haka ya fuzge kofin ruwan ya kafa kai yana sha.Duk hankalin Laraba ya tashi,dan tsawon lokaci yana zaune ya jingina da bango Ya saki baki miyau nata dalala,nuni ya shiga yiwa Laraba da hannu akan ta kawar da kwanon kazar,aikuwa taja ta rufe.nan tayi tagumi dan bata da meke damun malam ɗin ba.

Sun jima a haka, kafin malam yasamu raɗaɗin ya lafa,nan ya juya ya kalli Laraba cikin haɗe rai yace"Ke wannan wace irin dahuwa kikayimin,dake ƙoƙarin kasheni da raina kinji ɗan karen yajin dake ciki kuwa?".

"Dama Maryam ce....." Zuruf suka ganta ta faɗo ɗakin tace"salamu alaikum gani Anty,an ragemun ne?"

Baki buɗe Laraba ta kasa magana,shima malam haka,har Maryam ta fita da kwanon basu sani ba,saida malam yace"ke kika kira wannan tauraruwa me wutsiyar?"

"Ni ban kirata ba wallahi ,inaga dama tana kusa ne,jin na ambaci sunan ta shine ta ɗauka ko kiranta nayi".

Bai ce mata komai ba,sai zamewa da yayi ya kwanta,itama Laraba Batace komai ba,sai da suka ɗauki lokaci a haka kafin tace" yallaɓai katashi ka koma kan gado" laushin hannunta yasa shi lumshe ido dan haka ya miƙe da kyar.

Ita ta kama shi dan a halin dayake ciki ko abinci baya sha'awar ci,dan haka suka ƙarasa ɗakin nan fa labari yafara canza salo,domin duk yadda yaso kawar da kai abu yaci tura,haka dai fa malam ya runtse ido ya kawar da batun ramuwa ya fara lulawa duniyar masoya da Laraba.

🔅🔅🔅🔅🔅🔅🔅🔅🔅


Gari ya waye duhu ya yaye,malam kam ya dangwali arziƙin Laraba,ya manta duk wata damuwa,jinsa yake yi kamar ba wanda yakaishi kasancewa cikin farin ciki,dan jinsa yake kamar bai taɓa kusantar irin wannan ba,dan haka tuni yayi watsi da batun ɗaukar fansa.......


_Kuyi manage,wallahi yanzu ma daurewa nayi nayi muku zama ɗaya_


*Alƙalamin khady*✍
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀

*YAR CASKALE*
( _Sanadin bakin uwa_ )

*NA*

*KHADIJA USMAN*
( _Real Tame gari_ )

*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*

*🌈🇰AINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*


5⃣5⃣-5⃣6⃣



" Kiyi maza ki shirya mana Huwaila,dan malam Garba yacemin yakamata muje da wuri,dan inaga malam ɗin baida lafiya ne,yake son aje a ɗauko ta tazo ta kwana biyu saita koma,saboda haka dan Allah kiyi sauri,shi Isma'il ɗin ya shirya ko?"

"Gani nan malam hijabi kawai zansa, Isma'il yana ɗakin sa ai inaga ya shirya,dan tun ɗazu yayi wanka".

"Yauwa to yi sauri dan Allah kin san jira ba daɗi".

A hannu ta fito da hijabin tana faɗin"malam Allah dai yasa bawani abun matsayaciyar yarinyar tayi ba aka mana kiran gaggawa,amma ai kai kanka kasani babu yadda za'ai kwatsam ace azo a ɗauki yarinya sama ta ka,bayan kai da kanka ka faɗa cewa,malam ɗin yace sai anga nutsuwar yarinya tukun,sannan ake bada damar tazo gida ta kwana biyu,amma ban sani ba ko ciwon ajali ne yakama tsohon tunda kace ya tsufa".

Ransa a ɓace yace"wai ke Huwaila yaushe zakiyi hankali ne?haka jiya ma inajinki kina cewa Isma'il maƙetaci la'ananne,shin ke wai har abada alkhairi baya fita a bakinki akan yaranki sai sharri,in sun lalace waye zai kaiki baƙin cikin hakan,shashasha, wadda bata san ciwon kanta ba" yaƙarasa maganar yana me ficewa a ɗakin.

Taɓa baki tayi ta faɗa a hankali" kaji malam da wata magana,da kuma bana tsawatarwa ace na cika sakaci,to yaran yanzu kana tsawatar wa ma ya aka ƙare,bare ka zuba musu ido,to wallahi bada ni ba,inna kyalesu sakaka kuma a zagen" Tana kaiwa nan tasa kai ta fice a ɗakin,tana saka makulli a ƙofar ta shiga kwalawa Isma'il kira,jin yayi shuru ya tabbatar mata da ya fita wajen baban shi, kenan ita ake jira,dan haka ta ƙara sa kulle ko ina ta fice ta damesu a waje suna jiranta.Dayake tasan ran mai gidan a ɓace yake,saita buɗe baya ta shige abinta ita da Isma'il suka ɗauki hanya.....


🔅🔅🔅🔅🔅🔅🔅🔅🔅🔅

Tunda asuba malam inka lura dashi zaka tabbatar yana cikin farin ciki,haka yabi duk ya tashi jama'ar gidan nashi dan suyi sallah.Ko yau a masallaci malam ne yayi limanci, yayinda tsabar farin cikin dayake ciki yasa yau har karatu da wa'azi ya gabatarwa da mazan ƙauyen akan riƙon aure.

Wajen ƙarfe takwas malam ya shigo gidansa,bayan yasa an sayo masa Lipton da Suger ,tare da ɗuma-ɗuman biredi ya shiga dasu gidan.Batare da damuwar komai ba ya ware iya na matansa kowacce,dan tunda akayi auren nan ya lura basa bawa Laraba abinci insun dafa(kunji fa malam sai yau yasan da hakan) Allah sarki 'yar marainiya bata ko damu ba,yanzu idan ya koma zaisa ta lissafa masa abinda ta kashe tsawon wannan kwanakin🤣

Duk wadda yabawa a cikinsu babu wadda tako kalleshi,shima bai damu ba,dan yasamu biskit ɗin zuciyarsa,dan haka ya shige ɗakin Laraba hankali kwance,baiwar Allah kun san dai yadda budurwa take duk girman ta in har Bata siyar da mutuncinta a waje ba,dayake zazzaɓi take ɗan ji,amma haka ta daure ta yi masa sannu da zuwa,ya miƙa mata Lipton da Suger ɗin,tare da lalubo sachet ɗin madara da bombita(oh su malam an iya almundahana ashe🤣)gashi maza tashi ki dafa mana shayi,sannan ki haɗa da waccan yarinyar mairamu,dan itama tare damu zata karya da ita,dan yarinyar na yaba da hankalin ta ba tun yanzu ba,bari ma in kirata mu ɗan taɓa hira kafin shayin ya dahu tunda naga a madafin zamani kike girki" ya ƙarasa zancen yana me fitowa ƙofar ɗakin,daga nan ya shiga kwalawa Maryam kira"Maryama! Kina ina mairamu?" Ya shiga tambaya yana daga bakin ƙofar Laraba.

Daga cikin ɗakinsu ta amsa masa,ta fito sanye cikin kayanta masu kyau da hijabin ta.Sai da ta ƙara so gabansa ta ɗan tsugunna tace"Gani Baba malam"

Washe baki yayi kafin yace"yauwa 'yar albarka taso dama neman ki nake yi shigo ciki kinji" ya faɗa yana me juyawa ya shige ita kuma Maryam ta miƙe tabi bayanshi.

Zuwaira da salame dake can gefen ɗakunan su da yau ɗin nan suka tashi da sabon haɗin kai, kowacce saita ja dogon tsaki suka saki dariya a tare suka tafa.

************

Gefen tabarmar malam ya nuna mata ta zauna,aikuwa tasami guri ta zauna,tare da aro ladabin kunama tayi shiru.A haka har larabar malam ta kammala haɗa shayin aka kawowa kowa nasa,nan ko Maryam ta zage tasha abinta,dan saiya zame mata abin marmari,dan tunda tazo bata sha ba,danma ita ɗin hamburin hayam ce,ba ruwanta da zaɓar abinci, komai in zaiyi Mata maganin yunwa to tana maraba dashi.

Bayan sunsha sun ƙoshi nan fa malam hira ta ɓarke,ya shiga bawa su Laraba labarin samartaka da irin gararin da yayi lokacin dayaje almajiranta,ita kam Laraba wani farin ciki take ji ,wai yau itace da miji suke hira.Yayin da ita kuma Maryam sam hankalinta na ga gida,danta matsu a zo a tafi da ita taje taci uwar ummita😡.Tana shirin tambayar malam shin yaushe su babanta zasu zo? Kawai sai taji ihun yara suna faɗin, ga yaya Garba! Ga yaya Garba na kano.Aikuwa a zabure ta miƙe tayi waje,yayin da sukayi ido huɗu da babanta suna gaisawa da wasu mutanen ƙofar gidan.A dai-dai nan ta ga Isma'il na ƙoƙarin fitowa daga motar.Da gudunta cike da murnar ta ta nufeshi,shima da sauri ya fito,a nan kuma taga ummanta itama ta fito aikuwa da gudu ta canza akala ta nufeta, tare da fashewa da matsanancin kuka,itama umman saida zuciyar ta tayi rauni,hawaye suka fara zubo mata na ganin 'yar Tata da tayi.Haka suka rungume juna,kafin malam Garba yayi musu jagora zuwa cikin gidan.

Koda malam ya gansu ya nuna farin cikinsa,dan yanzu duk abinda ya shafi Maryam to yana daraja shi,dan shi Sam Yama manta shiyace Suzo su ɗauki 'yar su.


'Ɓangaren su salame ya musu jagora,yayin da suka shiga ɗakin salame,amma sam babu wadda tayi musu koda kallon arziƙi,hakan yasa jikin umma yin sanyi,ganin hakan da malam yayi ne yasa yakama yin yaƙe tare da cewa"Maryama idan sun gama gaisawar maza ki raka su ɗakin amarya kinji" yafaɗa yana me juyawa ya fice,dan su gana da mahaifin Maryam ɗin.

Batare da ɓata lokaci ba kuwa Maryam tace"Umma tashi in kaiki ɗakin Anty Amarya dan ita tanada kirki,amma yanzu tsofaffin matan Baba malam sun koyo rashin mutunci".

Jin furucin na Maryam yasa umma jin kunya,ta kalli salame dake duƙe tana leƙa ƙarƙashin gado,kome zata ɗauki oho,bata bi takansu ba har Maryam taja hannun Isma'il suka Umma ta bisu a baya,har zuwa ɗakin Laraba.

A kwance take kan tabarma, dan zazzaɓi takeji,hakan yasa koda suka shiga da kyar ta iya ɗagowa ta amsa musu,dan ciwon da kanta keyi.Jinjina kai Umma tayi datayi arba da Laraba ,a zuciyarta tana jinjina girma da ƙudura irin ta Ubangiji,"Allah me halitta kenan" ta furta a zuciyarta,a fili ta shiga amsa gaisuwar da laraban keyi mata,bayan tayi musu nuni da gurin zama, Isma'il ma ya shiga gaisheta ta amsa mishi cikin sakin fuska kafin ta yunƙura da niyyar miƙewa."Wash Allah "ta furta a hankali,Da sauri Maryam tace," Menene Anty?"

Cije baki tayi kafin ta furta" Bakomai" ta ƙarasa miƙewa da kyar ta je ta ɗebo musu ruwa.Nan ma da kyar ta zauna,duk umma na lura da motsin ta, amma saita kyale Ita kuwa Maryam sai hira take yiwa Isma'il tana tambayar shi ina 'yan layinsu,sannan ina su Rakiya? Nan take faɗa mishi ai ita tama fasa zuwa madinan nan,dan ta tambayi su Hafsa (waɗan da suke ɗaki daya)suka ce mata ai ba'a zuwa Madina ta ƙauye,nan suke faɗa mata duk wanda taga an kawo shi nan,to kangararre ne,dan haka wayo aka mata dan a kawota nan ɗin.Tunda taji haka tace itama saita nuna musu tanada wayo,badai ita za'a kai ba,to saita ce tafasa zuwa Madina a maida ta gida,kuma wallahi koya za'ai da ita bazata zauna ba.
************************
Tunda umma ta kalli Laraba ta fahimci inda matsalar take,dan koda take da ƙiba gamai hankali inya lura zaiga yadda tafiyar ta ta sauya.Ganin da umma tayi maryam taja hannun Isma'il sun fice wai zasuyi sirri,nan tasamu damar kallon Laraba tace"Ni kam amarya in tambayeki Mana?"

"To Innar Maryam" cewar Laraba dake rawar sanyin zazzaɓi kaɗan-ƙadan.

"Mene ne ya jawo miki zazzaɓi haka? Ko bakya kwana cikin gidan sauro ne?"

"Ah ah,ai bama Musa sauro,kawai dai inaga dan....."sai kuma tayi shuru.

Sosai Umma ta shiga nazarin ta,zuwa wani lokaci,sannan tace"kin gasa jikinki da ruwan zafi ne?"dan ta fahimci kamar abinda ya faru wannan ne na farko.

Girgiza kai tayi a hankali tace"ah ah,dan ban san ma ana gasawa ba ai".

Cike da tausayin ta,da kuma yaba tarbiyya irin ta yaran ƙauye tayi,domin dai duk da ana kiransu da kidahumai to Gara hakan,dan yanzu wata wayewar da buɗewar idon basuyi ba.

Kallon ta tayi sama da ƙasa,taga yadda mazaunan nan suke,ta jinjina kai,to yanzu ya za'ayi a gasa wannan,dan ko bataga robar da zata ɗauke Laraba ba,amma dai bari tasa a samo ta wankan jego ko zata yi,dan haka tace " a ina za'a samu baho irin babban nan na wankan jego?"

Kanta a ƙasa Laraba tace"ai inada shi,dan Innar mu ta siyomin tace wai mu fara tanadi ,robar tafi ɗa wuya".

"Tohhhh ! Umma ta faɗa tana riƙe haɓa ,tare da mamakin abun,amma saita cewa Laraba ta ɗauko robar.Haka ta miƙe ta ɗauko robar ta kawota gaban umma,umma ta shiga gyaɗa kai a zuciyarta tana faɗin"lallai wannan uwa tasan 'yarta dan robar ma kamar ƙirar kamfani,dan kamar an auna larabar ne akayota fankaceciya.Miƙewa tayi tace" to ina madafin ku yake ?"a ɗora ruwan zafi".

"Ai ni bana girki da ice Maryam ta hanani,sai da riho"

Kallonta umma tayi tace au kema sunan mamanki Maryam kenan,lallai mama bata son 'yar nan tata tayi ƙaurin hayaƙi ko?"

Murmushi Laraba ta sannan tace"Ah ah maryam fa 'yarki itace ta hanani girki da ice"

"Wai kina nufin Maryam dai dana sani?"

Gyada kai alamun ita.

Dariyar takaici umman tayi,tabbas mai hali baya fasawa amma inba haka ba,yanzu Maryam yazatayi da wannan rushe shiyar idan ta tsokano ta,to a yadda take gani ko ita da Baban su Maryam ɗin ai sai sunci ƙaniyar su gurin ta,dayake ma da sauƙi dan taga akwai jituwa a tsakanin su,sai dai ta lura Laraba girman ne kawai ba wayo.Haka dai tasa Laraba ta kunna risho aka ɗora ruwan zafin.

A banɗakin Laraba umma ta haɗa ruwan bayan takai robar,sannan ta ce Laraba ta tashi taje ta faɗa mata yadda zatayi cikin hikima.

Umma na zaune kusan minti goma taga laraban ta shigo ɗakin kanta a duƙe.Umman ce ta kalleta tace "har kin gama gasa jikin naki?amma dai ba baki shiga ruwan nan da kyau ba,inba haka ba du-du-du mintinki nawa,dan haka maza ki ɗauko bokitin a ƙara zuba wani,in kin tsaya son jiki kece da wahala,dan kar kiga mijinki tsoho,su maza kullum jinsu suke kamar sabbin ƙyanƙyasa,dan haka maza miƙo a ƙara wani ruwan".

"Dama ba ƙin shiga nayi ba ina zama ne sai robar ta fashe"

"Ta fashe fa kikace?"umma ta faɗa tana zaro ido waje😳



*Alƙalamin khady* ✍
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀


*YAR CASKALE*
( _sanadin bakin uwa_ )


*NA*
*KHADIJA USMAN*

_Real Tame gari_



*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*

*🌈🇰AINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*


5⃣7⃣-5⃣8⃣



"Oh ni Huwaila,tunda roba ta fashe ya zamuyi? Gashi dai ba abin a samo daro ba ya ɗau zafi duk kibi ki ƙone,garin neman gira kuma a zo a rasa ido,ya muka iya,kawai ɗauko butar ki babba a zuba ruwan
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment